Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Saudat kid'a tasaka a b'angarenta saboda farin ciki sai cashewa takeyi tana rawa, tana juyawa Yau duniya tamata dad'i, gaba d'aya ta manta da mijinta dake kwance akan gadon asibity."

Har sauban yadawo gida batasaniba,
Hakan ya nufi part d'insa ya shiga toilet yayi wanka yafito, yasaka k'ananun kayansa marasa nauyi farin wando riga bak'a,
Yunwa yakeji amma babu abinci a b'angaren nasa,
Hakan ya janyo 'ya'yan itatuwa ya soma ci,
Ciyakeyi yana lumshe ido
Babu abinda yake masa yawo a kai sai magagganun da hajjah tayi akan Safna, sune suke masa yawo sunaso su birgita masa,
kwakwalwa,
Wad'anda take cewa _dole ne a binciko asalinta atabbatar da suna da kyakkyawan asali basa da wani abi fad'i, domin duk wacce taza shigo gidan sarauta dolene sai in tana da cikakken asali mai kyau_

To yanzun idan sarki ya shiga bin ciken asalinta yasami cewar tsintar ta akayi a gefen hanya,
ana nufin bata da asali shegiyace Shikenan."

Rasa zaiyi bazai taimaki rayuwarta ba?"
Runtse idonsa yayi yanajin zuciyarsa tana k'una,
Jiyakeyi duk abinda zai faru sai dai yafaru amma bazai tab'a barin rayuwar safna ta sallawanta ba, akan wani dalili can nasu na masarauta."

sautin kid'a yakeji yana tashi a part d'inta Wanda duk ya damesa ya hanashi sukuni bare yayi tunanin mafitar abinda yake damunsa, kwakwalwarsa da kansa duk sun har gitse,
Cikin zafin rai yafita yanufi part dinta,
Har ya tura k'ofa yashiga batasaniba abinda baitab'ayiba shiga d'akinta."

Manyan mata yagani su hud'u kwance a kan gadonta KO wacce ba kayan kirki a jikinta,
Tana tsaye a tsakiyar d'aki sai rawa takeyi tana juyawa, irin rawar da turawa sukeyi idan suna cikin farin ciki."

Wani bak'in ciki ya kamasa ya kashe soket d'in,
Jin shurun da tayi ba sauti t
Yasa ta juya a fusace domin ganin Wanda ya kashe mata sauti."

Ido biyu tayi dashi tsaye a bayanta,
Anan take gabanta ya fad'i,
Ta juya da sauri ta kalli matan da ta ajiye a kan gadonta."
ajiyar zuciya ta sauke ganin ba abinda suke aikatawa a kwance kawai suke,

Kallonta yakeyi cike da tsana da takaici da ace shi ma'abucin dukan macce ne da yau babu abinda zai gana ya daki saudat yayi mata duka irin na mutuwa."

*REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 29*






******* A lokacin da aka nufi asibity da Safna ba rai bare numfashi a tare da ita,
Kai tsaye Emergency aka nufa da ita cikin gaggawa likitoci suka k'arb'eta suka duk'ufa a kanta domin ceto rayuwarta da tsayar da jinin dake fita a hanci da bakinta."

Sosai hajiya LAILA ta girgiza da ganin yanayin da yarinyar tashiga, danko fuskarta bata tsaya ganiba hankalinta a tashe yake matuk'a."

Hajiya laila mace ce mai mai tausayi mai son 'ya'ya,
haihuwarta d'aya a duniya 'yarta d'aya macce mai suna *SUHAILAT* wacce ta b'ata tin lokacin da ta haifeta bikin sunanta kawai akayi washe gari aka wayi gari babu ta ba alamarta tab'ata."

B'acewar da har yanzun ba labarinta bare a san dalilin b'atan nata,
wacce a kullum hajiya laila take kukan rashin 'yarta kwaya d'aya tilo wacce take tunanin itace kwanta a duniya, tun daga gareta KO b'atan wata bata kumayi ba, amma sai dai tanaji a jikinta Suhailat d'inta bata mutuba, tana raye domin tana yawan mafarkin 'yarta ta girma tana cikin mawuyacin hali."
A kullum Addu'a takeyi Allah ya bayyanar mata da tilon yarta cikin k'oshin lafiya"
Cire glass din idonta tayi ta share hawayen dake zuba a idonta,
snn ta mayar da glass din a fuskarta,
takoma cikin mota ta zauna tare da jinginawa akan kujera,
Wayarta ta d'auka kira mijinta Alhaji *HABIB SANI NAIRA*,

*RINGING* d'aya zuwa biyu Alhaji Habib ya d'auka, a lokacin yana office suna mitting tare da yaransa akan cigaban da aka samu a kanfaninsa,
Yana ganin kiran nata Saida yasaki murmushi ya kalli wayar,
Snn ya tsayar da maganar da yakeyi,
Snn Ya d'auki wayar , Cikin so da k'aunar matarsa, kuma Amaryarsa yake fad'in "Amarya bakya laifi koda kin kashe d'an masu gida, da fatan kin isa lafiya."

Murmushi tasaki tana fad'in "Alhajina akwaika da tsokana shekara goma shatakwas kake kirana da Amarya,
Da ace Suhailat tana raye aida munfara shiga sahun iyaye dan kuwa kasan kamar yanzun mun sami suriki."
Murmushi yasaki domin shi kansa ta tayar masa da dafin b'atan 'yarsa wacce tafi soyuwa a ransa,
Itama yanzon yasan tashiga cikin damuwar domin yasan da zarar akayi zancen suhailat sai ta zubar da hawayenta,
Gyaran murya yayi yace "Amarya kamar yanda yake kiranta meyafaru dake ne?" domin najiya a jikina kina tare da matsala."

Share hawayen dake zuba a idonta tayi, cikin da sanshinyar murya tace "Alhajina muna kan hanyar tafiya,
munzo gaf da fita cikin gari muka samu matsala,
Yahuza direba ya bige wata yarinya 'yar fulani tana sanye da kayan fulanin a jikinta , a lokacin tana k'ok'arin k'e tara titin, yanzun hakan muna Asibity."

"Subahanallahi Alhaji Habib Naira yace,
Tare da mik'ewa tsaye a firgice,
yayiwa yaransa Alama da hannu akan sutafi sai ya k'ara nemansu,
Cikin Sauri yanufi hanyar fita , Da waya a kunnensa yana fad'in wacce asibityn kuke a halin yanzun?"
Hajiya laila ta fad'a masa sunan asibityn."

OK gani nan zuwa yace "yanufi wurin motarsa escort dinsa suka bud'e masa yashiga,
Suma suka shinshiga cikin nasu motocin suka nufi Asibityn."

***************

Kwance yake akan gadon Asibityn Sauk'i yasamu garesa Dan kuwa ba abinda yakeji yana masa ciwo a jikinsa,
Likita kawai yake jira yashigo ya sallame shi,

Gabansa yakeji yana fad'uwa akai akai,
Da zarar yaji hakan ba wacce take fad'o masa a rai sai Safna,
Tabbas yasan tana cikin mawuyacin hali,
Musamman rashin ganinsa da batayi ba, bataga yatura wurin maigariba domin a tsayar da ranar aurensu, dolene tashiga cikin damuwa."

Runtse idonsa yayi yanajin wani abin yana bugar masa zuciya wanda yarasa ko meye shi,
Babu abinda yake gani sai Fuskar safna yake kallo a idonsa,
a lokacin da take ce masa , "Yarima inasonka zanyi biyayya a gareka, zan zama tamkar baiwa a gareka,
Kada kajuyamun baya idan katina DA ni shigeyace bana da iyaye."

Hawaye suka shiga zuba a gefen idonsa,jikinsa yasoma rawa,
ji yakeyi kamar ya tashi ya tafi k'auyen a d'aura masu aure da ita ya d'aukota ya taho da ita domin yabata gata tabbatar da cewa *MARAYU MA 'YA'YA* ne kamar kowa.,

Hajjah tana ganin zubar hawayensa wanda har tagaji da ganin suna fita a idonsa,
tin Tana Tausayinsa tana tambayarsa damuwarsa har ya Kai ta zuba masa ido tana kallonsa,
Dan tasan halin sauban sarai akwaishi da zurfin ciki, idan zai shekara dubu da abu a ransa yana damunsa baxai tab'a furtawa ba, hakan zai barshi a ransa yayita damunsa, yana ramewa sai dai idan kai ka fahimta da kanka snn ka magance masa matsalar cikin salama."
Hakan yayi a lokacin Auren Saudat bai furta baya sonta ba,
Sai da akayi bikin yashiga cikin damuwa yana ramewa,
Tambayar duniya ba wacce ba'ayi masaba akan ramar da yakeyi kodai auren da akayi masa ne baya so,
Hakan zai girgiza kai alamar yanaso shi ba abinda yake damunsa,
Sai daga baya da hajjah ta saka masa ido anan ta fahimci baya son Saudat shine dalilin ramar tasa,
Hakan tayita kwantar masa da hankali akan ya rik'e matarsa hannu biyu tinda anriga da and'aura auren har ankawota gidansa,
Dole ne Ya koyawa zuciyarsa soyayyarta illaso daga baya idan yasami wacce yakeso sai ya aure ta."

sai gashi shigowar Saudat gidan lokaci d'aya tashiga ran hajjah saboda tsananin son da takeyiwa sauban wanda bata iya b'oyeshi a duk inda take ko a gaban waye,
Snn shigowar saudat cikin gidan lokacin sauban yasami kwanciyar hankali da zama a lafiya a cikin masarautar dan kuwa gimbiya jamila tsoron mahaifiyar saudat takeyi."

Maimartaba ya turo k'ofa yashigo da sallama,
Ganin hawaye suna zuba a idon yarima ya dakatar da fadawa akan kada sushigo su dakata waje ya mayar da k'ofa ya rufe."

Cikin takon mulki yake takowa ya isa gaban gadon sauban ya sanya hannu ya dangwalo hawayen dake fita a gefen idonsa,
ya dubesu da kyau cike da mamaki ya tabbatar da tabbas hawaye ne ke zuba a idon magajin sarki,
Cikin gid'ima sarki yake kallonsa bakinsa yana rawa yace "magajin Sarki hawaye a idonka?" Ina raye a duniya?"
Meyafaru?"
Ina yake maka ciwo?"
Sam ba girma bane hawaye su dinga fita a idon gwarzon namiji kuma magajin Sarki, tashi zaune muyi magana."

Jiki a sanyaye sauban ya tashi zaune yana kallon mahaifin nasa,
Hannu Sarki yasaka ya shafe masa hawayen fuskar tasa,
Yana kallonsa yace "bani labarin abinda yake damunka Wanda inada raina da lafiyata magajina yake zubar da hawayena akansa."

Kallon mahaifinsa sauban yayi ya sunkuyar da kai yace "Abba damuwata safna ce."

Sarki yasaki wani murmushin irin nasu na manya,
Hajjah taja dogon tsaki ta juyar da kai gefe, domin ita wlh ta d'auka wani abin can daban yake damunsa ko yake masa ciwo wanda yake sakashi yana zubar da hawaye.
Ita tarasa ko yaushe sauban ya susuce yazama raggo hakan DA. har yake zubar da hawayensa Mai tsada a kan macce."

Sarki ya juya ya kalli hajjah yasaki murmushi snn ya nemi wuri ya zauna a gefen gado a kusa da sauban ya kallesa yana murmushi yace "fad'amun meyasami safna d'in?"

Kallonsa sauban yayi ya sunkuyar da Kai k'asa yace "inaji a jikina akwai wani mummunan abu da yasameta,
Abba Safna abar tausayice bata da iyaye bata da kowa sai Allah saini dana d'auki Alk'awari Zan taimaketa,
Abba bawai son safna nakeyiba kawai ina tausayin halin da take cikine,
DA kuma Wanda zata shiga idan tarasani,"
Abba Ina neman Alfarma a Karo na farko a wurinka itace katura fadawa yanzun nan sutafi k'auyen domin a tsayar da ranar aure na da Safna,
domin gudun kada asami Matsala a cikin Al'adarsu."

Murmushi Sarki yasaki Wanda har sai da hakoransa suka fito,
Yana kallon sauban cike da wauta wai ba sonta yakeyi ba, bayan ga soyayyarta nan ya gani k'arara a cikin idonsa,
Murmushi Sarki ya kuma saki yana kallon sauban Yace "hakan kakeso a aiwatar yanzun magajin sarki?"

D'aga kai sauban yayi alamar eh."

Sarki yace to "idan maigari yace a lokacin yake so d'aura
auren naku a tsaya a amso maka aurenta ko kuwa abarshi rana kawai kakeso asaka maka?"

Shuru sauban yayi ba amsa.
Sarki yasaki dariya wacce yasaka sauban shima ya d'an murmusa cike dajin kunya,
Sarki yace kabani amsa kai nake saurare domin da kaina zantafi ba aikeba "

Cikin jin kunya sauban ya sunkuyar da kai yace "duk yanda kace ranka ya dade a aiwatar da hakan."

Sarki ya kuma sakin dariya yace "wnn amsar kai zaka bani ita,
Saboda a lokacin da kake zubar da hawayen k'auna baka nemi shawara daniba."

Cike da jin kunya sauban ya kuma sunkuyar da kai sarki yana ganin hkn ya had'e fuska cike da zulaya yace "to shikenan Zan fasa tafiyar zan tura fadawa Zan ce masu da zarar suntafi akace za'a d'aura aure a lokacin zance kabada umurnin "kada a d'aura kai baka ra'ayin hakan, rana kawai kakeso asaka maka,
Idan sukace ba hakan sukeyiba,
Zance kace kabarwa duk Wanda yake sonta a d'aura dashi."

Da sauri sauban ya d'aga Kai ya kalli Sarki yaga da gaske yake ba wani alamar wasa a tare dashi yace "ranka ya dad'e ba hakan nake nufiba, a d'aura auren dani, sutaho tare da ita."

Dariya ta sub'ucewa sarki wacce tasaka sauban jin kunya,
Yayi saurin kwanciya tare da juya baya yana murmushi cike da jin kunya."

Hajjah tana jin duk abinda sukeyi bata tanka masuba domin ta dade da sanin Sarkin Abdullah shi yake sakanta sauban yake yin duk abinda yaga dama."

Sarki ya mik'e tsaye yana murmushi ya kalli hajjah yace "umma zamutafi karb'owa jikanki Aure a k'auyen gidan gonarsa, saiki shirya tarbon kishiya ta biyu."

Mere baki hajjah tayi tace kafin a d'aura ayi binciken asalinta da abinda ya kashe iyayenta domin naji yana fad'in bata da iyaye,
Snn a tabbatar da asalinsu mai kyau ne tafito a cikin gidan asali, da daraja basa da wani abin fad'a,
kodan samun zuri'a mai tsafta,
Snn kada ka manta a cikin gidan sarauta zata shigo shi kuma gidan sarauta duk Wanda kagansa yashigo cikinsa a matsin matar Sarki KO d'an Sarki KO jikan Sarki dolene ya zamana yana da asuli Mai kyau.
Idan babu wnn to tabbas bata cancanta da zama matar saba dole ne ya barta duk son da yake mata."

Gaban sauban ya fad'i dajin furuncin hajjah."

Sarki yace "tabbas hakan ne umma,
Sai dai inaji a jikina kamar farin cikin da mahaifiyarsa take fad'ar masa zai samu a cikin gidan gonar sa,
Ina hasashen shine ya fara bayyana a garesa." Domin samun macce ta gari babban farin cikin d'a namiji, yasami rabin duniyarsa domin kullum cikin farin ciki zaiyi ta zama har k'arshen rayuwarsa

Yanufi k'ofar fita yace "muntafi,
Hajjah tace "adawo lafiya."

Snn Sarki yafita ya bawa fadawa umurnin sushiga mota,
ya fad'a masu inda za'a tafi,
Suka d'auki hanyar k'auyen Lassa."

Suna fita daga asibityn Anawa Sarki jiniya,
Alhaji Habib Naira shima yashigo da tawagarsa sarki yabada umurni a tsaya,
hakan shima Alhaji Habib yaba da umurni a tsaya, anan suka fito daga motar suna dariya suka shiga gaisawa da juma cike da farin ciki da kewar juna,
Tare da tambayar yaushe rabo,
Domin Alhaji Habib business dinsa baya barinsa zama yau yana wannan k'asa gobe yana wancan k'asa jibi yana wancan k'asa."

Anan Alhaji Habib yake tambayar Yaya Sauban?" Ai yanzun
Yasan yaron ya girma sosai."
.dariya sarki yasaki yana fad'in sosai kuwa har yayi aure,
Yanzun hakan k'arb'o masa auren mata ta biyu zamu tafi muyi."

Kuma tab'awa sukayi suna dariya Alhaji Habib yace "yaro yayi gadon ajiye mata da yawa,
kaine baya ko ni."

Sarki yasaki dariya yana fad'in lafiyar kenan, ai duk Wanda ya ganmu yasan ba rangwanci a tare damu."

Suna dariya tare da zolayar juna sukayi sallama ko wanne yashiga motarsa Alhaji Habib yana fad'in abokina kafin natafi zan shigo fada domin asakamun Albarka,

Sarki yana dariya yace "badamuwa sai ka shigo,
Sukaja mota suka tafi cike da farin cikin ganin juna domin abokanaine sosai kasuwanci ne yarabasu da junansu."

Sarki yana fita daga asibityn likita yashigo ya k'ara duba jikin sauban yaga yasami lafiya,
Anan take ya sallamesu direba tare da fadawa suka d'aukesu a mota suka nufi gida su."

****************

Dawowar dakaru da labarin da sukaje dashi na tarwatsa k'auyen su safna ba k'aramun farin ciki yasaka Saudat da mahaifiyar taba,
Musamman dasukaji cewar Safna ta mutu domin,
Sunce dajin da tabi da gudu anan ne maciji ya kashe biyu daga cikin mutanensu, suma dakyar suka sha,
Suna da yak'inin ko gaggar jikin safna baza'a gani bare gawarta shikenan ta mutu sai dai wata ba itaba"

Wayyo dad'i a ranar Saudat kid'a tasaka a b'angarenta saboda farin ciki sai cashewa takeyi tana rawa, tana juyawa Yau duniya tamata dad'i, gaba d'aya ta manta da mijinta dake kwance akan gadon asibity."

Har sauban yadawo gida batasaniba,
Hakan ya nufi part d'insa ya shiga toilet yayi wanka yafito, yasaka k'ananun kayansa marasa nauyi farin wando riga bak'a,
Yunwa yakeji amma babu abinci a b'angaren nasa,
Hakan ya janyo 'ya'yan itatuwa ya soma ci,
Ciyakeyi yana lumshe ido
Babu abinda yake masa yawo a kai sai magagganun da hajjah tayi akan Safna, sune suke masa yawo sunaso su birgita masa,
kwakwalwa,
Wad'anda take cewa _dole ne a binciko asalinta atabbatar da suna da kyakkyawan asali basa da wani abi fad'i, domin duk wacce taza shigo gidan sarauta dolene sai in tana da cikakken asali mai kyau_

To yanzun idan sarki ya shiga bin ciken asalinta yasami cewar tsintar ta akayi a gefen hanya,
ana nufin bata da asali shegiyace Shikenan."

Rasa zaiyi bazai taimaki rayuwarta ba?"
Runtse idonsa yayi yanajin zuciyarsa tana k'una,
Jiyakeyi duk abinda zai faru sai dai yafaru amma bazai tab'a barin rayuwar safna ta sallawanta ba, akan wani dalili can nasu na masarauta."

sautin kid'a yakeji yana tashi a part d'inta Wanda duk ya damesa ya hanashi sukuni bare yayi tunanin mafitar abinda yake damunsa, kwakwalwarsa da kansa duk sun har gitse,
Cikin zafin rai yafita yanufi part dinta,
Har ya tura k'ofa yashiga batasaniba abinda baitab'ayiba shiga d'akinta."

Manyan mata yagani su hud'u kwance a kan gadonta KO wacce ba kayan kirki a jikinta,
Tana tsaye a tsakiyar d'aki sai rawa takeyi tana juyawa, irin rawar da turawa sukeyi idan suna cikin farin ciki."

Wani bak'in ciki ya kamasa ya kashe soket d'in,
Jin shurun da tayi ba sauti t
Yasa ta juya a fusace domin ganin Wanda ya kashe mata sauti."

Ido biyu tayi dashi tsaye a bayanta,
Anan take gabanta ya fad'i,
Ta juya da sauri ta kalli matan da ta ajiye a kan gadonta."
ajiyar zuciya ta sauke ganin ba abinda suke aikatawa a kwance kawai suke,

Kallonta yakeyi cike da tsana da takaici da ace shi ma'abucin dukan macce ne da yau babu abinda zai gana ya daki saudat yayi mata duka irin na mutuwa."




*REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 30*





*ALHAMDULILLAH ALLAH NAGODE MAKA DOMIN KAINE ABIN GODIYA,*
*INA KUKE MASOYA DA ABOKANAN ARZIKI INA GODIYA A GAREKU DOMIN KUN NUNAMUN KULAWA BABU ABINDA ZANCE SAI DAI NAYI MAKU FATAN ALHERI A DUK INDA KUKE, DA MASU KIRAN WAYANA DA MASU TUROMUN MASSAGE DUKA NAGODE ALLAHU YA BAR K'AUNA NAJI SAUKI SOSAI ALLAH YABANI IKON FARANTA MAKU NAGODE NAGODE NAGODE*🤝🏻🤝🏻







******* kallon tsana Sauban yaci gaba da wurgawa Saudat, cike da jin haushi da tak'aicinta,
yaja dogon tsaki ya juya ya bar wurin yanufi d'akinsa,
Kan gado ya kwanta rigingine ya rufe ido yana tunanin mugun hali irin na Saudat."

Saudat kuma tana ganin ya yafita,
A fusace ta juya ta kalli 'yan matan dake kwance a kan gadonta ta sakar masu harara cike da bak'in cikin ganin da mijinta yamasu a hakan, wani irin kishin mijinta taji ya taso mata, taja da baya ta jingina a bango tana sauke numfashi da sauri da sauri kamar wacce tayi gudu, hawayen bak'in ciki suka shiga kwarara a idonta, bakad'an taji zafin ganin da sauban ya masu cikin tsinanun kayan dake sanye a jikinsu ba,
Bud'e idonta tayi wad'anda suka rine zuwa launin ja, ta d'orasu akansu, ta warga masu kallon tsana,
A fusace ta daka masu tsawa tace "kutashi kufita na tsaneku, bana son nasake ganin fuskokinku,
Kuma kusani sai kun d'and'ani azabata mai tsanani sakamakon ganin tsaraicin da mijina yayi maku
Tin yanzun kuzab'awa kanku horo mafi tsanani kafin na zab'a maku da kaina."

Gabanta suka kai durk'ushe tare da had'e hannayensu wuri d'aya alamar ban hak'uri,
Suna fad'in ranki ya dad'e tuba mukeyi,
Ki gafarcemu bazamu sake ba, bamusan yarima zai shigoba ayi hakuri ya uwargijiya mai Adalci,

"Kufita nace tare da nuna masu k'ofa waje,
Cikin sauri suka fita suka bar d'akin."

Juyawa tayi tafita tanufi d'akin yarima,
tura k'ofar d'akinsa tayi sannu a hankali da sallama a bakinta,

Jin shuru ba'a amsa bata ba yasa taja ta tsaya tana kale kale a ina zata ganshi
A can kan gado ta hangosa kwance yayi rigingine idonsa a rufe tamkar Wanda yakeyin bacci,
Ajiyar zuciya ta sauke tashiga takawa sannu a hankali ta nufi wurinsa,
A gefen gadon taja ta tsaya a dai dai saiti kansa ta d'an sunkuyar da kanta tana kallon kyakkyawan gashin kansa wanda yake kwance a kansa tamkar gashin kan jariri,
Hakan ya kuma sanya fuskarsa tayi kyau da adon,
sajensa Wanda yake zagaye da fuskarsa har zuwa bakinsa, tashiga kallo anan take tsikar jikinta ta tashi tafarajin wata irin matsananciyar sha'awarsa tana dirar Mata,
Tana' tsananin son gashin bakinsa, tana son tayita kallon kyakyawar fuskarsa mai cike da Annuri,
A hankali ta sanya hannu ta shiga shafa masa gashin bakinsa tana fad'in "Sadaukina kayi hakuri idan na b'ata maka rai."

Idonsa ya bud'e ya d'orasu a kanta ya wurga mata wani irin kallon tsana snn ya mayar da idonsa ya rufe."

Firgicewa tayi da kallon da ya Mata,
Ta kuma narkewa tana basa hakuri,
Shuru yayi bai tanka Mata ba,

sai da tayi magiya ta gaji, ganin baya da niyar tanka mata yasa ta tashi nufi kicin domin shirya masa abinci wata k'ila yunwa yakeji, ko ganin hakan zai sanya zuciyarsa tayi sanyi."

******************

Alhaji Habib Naira yana shiga cikin Asibityn gaba d'aya idon mutane sukayo kansa,
Anan take masu Neman taimako suka zagayeshi domin shi mutumin jama'a ne, mutum ne mai Alheri da tausayi
Dan hakan da zarar jama'a sukayi ido biyu dashi to kukansu ya kare domin Alhaji Habib Naira zaiyi masu kyautar girma da ban mmki."

Hakan aka zagayeshi sai kud'i yake bawa mabumuk'ata, da gajiyayyu,
Da gyar escort nashi suka da katar da sauran jama'a snn yasami hanyar wucewa ya isa wurin matarsa Hajiya laila wacce take zaune a cikin mota tana kallonsa."

Motar da take ciki escort nashi suka bud'e masa ya shiga,
Idansa akanta yana sakar mata murmushin so da k'auna a duniya bayan iyayensa babu abinda yakeso da ganin farin cikinsa kamar hajiya laila,
Janyota yayi zuwa jikinsa ya rungumeta yashiga share mata hawayen dake zuba a idonta, cikin sigar lallashi yake kwantar mata da hankali akan ta d'auki kaddara akan duk abinda ya faru ta daina sanyawa ranta damuwar b'atan suhailat."

Doguwar ajiyar zuciya Hajiya laila taja snn tasakarwa mijinta murmushi tare da rik'o hannunsa duka biyu ta saka a cikin nata hannun ta d'an matse kad'an cike da shauk'i
tashiga fad'in na daina mijina ina Addu'a a koda yaushe Allah ya k'aramun dauriya da dangana a kan rashin tilon yata danayi."

Dariya Alhaji yasaki yace "Ameen tare da kashe mata ido d'aya yana fad'in insha Allahu wnn dawowar danayi sainayi k'ok'ari nabaki wata Suhailat d'in kinga shikenan na kashe bakin magana."

Dariya tasaki tana fad'in "kai Alhaji bakada dama mezan iya tsofai tsofai dani."

Hararar wasa ya sakar mata yana fad'in "a Ina tsofan yake, a yanda nakejinki kinfi sabuwar budurwa dal a leda komai,
Dan kuwa duk Wanda ya kalleki yasan nayi dace nayi sa'a a cikin maza samun kyakkyawar macce mai tsafta da iya ado uwa uba ga k'amshi, ni kuwa me zanyi da wata macce a duniya idan kina tare dani."

Murmushin farin ciki take saki domin tana yawan jin wnn yabon a bakin gwarzon mijin nata,
."nagode mijina Allah yaci gaba da faranta maka kamar yanda kake farantamun."

Ameen yace tare da cire hannunsa cikin nata yana fad'in "mutafi naga marar lafiyar Allah yasa ta farfad'o."

Hakan suka bud'e k'ofa suka fita fuskokinsu cike da farin ciki escort suka take masu baya suka nufi d'akinda Safna take ciki a kwance cikin mawuyacin hali."

Wurin gadonta suka nufa inda Alhaji Habib naira yana yin ido biyu da fuskarta sai da gabansa ya fad'i, yayi saurin k'arasawa wurin gadonta yana kallonta,
Hajiya laila kuma ta juya tana bawa escort umurni akan su dakata a waje kafin sufito,
Snn ta juya ta cewa Alhaji mutafi, ganin baya kusa da ita, yasa
Cikin sauri d'aga kai ta hangosa a bakin gadon safna yana k'are mata kallo cike tausayi,
Wurin ta nufa taja ta tsaya a kusa dashi tana fad'in Alhaji kaga yarinyar ko gwanin ban tausayi,
Dam gabanta ya fad'i da tayi ido biyu da safna wacce a lokacin ta farfad'o daga allurar baccin da akayi mata."

Cikin sauri hajiya Laila tanufi wurin safna tana kallonta ido ciki ido Wanda itama safna kallonta takeyi hawaye suna mata zuba a gefen idonta,

Sannu yaya jikin naki Hajiya laila tace."
D'aga Kai safna tayi alamar da sauk'i,
Hawaye kawai kezuba a idonta ga wani irin fad'uwar gaba da takeji tarasa sanin kona meye."

Suna tsaitsaye akan gadon safna ba Wanda ya kuma yin magana dukansu su uku gabansu sai fad'uwa yakeyi bakinsu ya rufe ba Wanda ya kuma furta kalma d'aya,
Likita ya turo k'ofa yashigo tare da sallama."

Gaida Alhaji yyi snn yanufi wurin safna,
yacire mata ruwan da ya k'are ya kuma juna Mata masu,
Ido kawai safna take bin koya dashi tana kallo hawaye suna Mata zuba,
Gyaran murya likita yayi ya kalli hajiya yace "Alhmdulillah ba wata matsala a tare da ita,
Duk iya gwaje gwajen da mukayi mungano buguwa ce kawai tayi a kanta Wanda insha Allah nan da kwana biyu zata sami lafiya."

Alhaji yace Allah ya k'ara bata lafiya."

Suka amsa da "Ameen."

Muryar safna ta tsinke masu magana da take kallon Hajiya laila tace "umma zan sha ruwa, yunwa nakeji."

Dam gaban Hajiya laila

Please Login or Register in order to submit comment