Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta mutu? na uku wanda shine take jinsa sosai a ranta wato zuwan SGR, BABBAN YAYA,

tarasa me yasa ya tsaya mata a zuciyarta meyasa take jinsa, meyasa take fargabar ganinsa,
Zuciyarta tana azalzalarta akan son ganinsa, idanunta na kwaɗayin sa shi a idonta, Amma a ƙarshe tayi addu'ar Allah yasa ya zama alkhairi agare ta !!!

sai da asuba bayan ta shiga toilet ta canza pad ɗin cikinta, sanna fa bacci yayi awon gaba da ita,

A can ciki kuwa suna shiryawa zuwan Abban nasu, farin ciki a gun junaid ba'a magana, saboda ya gama tsara shagwa6ar da zaiyi masa in yazo, sannan akwai abunda yake burin ya sanar dashi ,

Har garin Allah ya waye sehrish batasan meke wakana ba, aunty azmi ta shigo ta same ta tana sharar bacci, ganin yadda jikinta ke kerma ya tabbatar mata da cewa sehrish ba lafia ba, har jikinta ta ta6a temperature ɗin jikinta yayi zafi,

Don haka bata attempting tayar da ita ba, kawai sai dai ta gyara mata blanket ɗin jikinta, sannan ta fice,

ganin cewa aiki zai yi mata yawa time zai iya ƙure mata, saboda baƙin da zasu zo yau, da buƙatar su kammala girke girken da zasuyi da wuri,

Kanal yusif ta nema ta sanar dashi halin da ake ciki na rashin lafiyar mai aikinsu tukur, taji daɗi da yasanar da ita cewa, akwai chefs da zasu zo kada ta samu damuwa,

tun 7 suka ƙaraso, kwararru ne a fannin sarrafa abinci kala-kala, su biyu ne, chef ummu da abokiyar aikinta momina, azmi taji daɗin zuwansu, nan fa kowa ya naɗe hannun riga aka soma gudanar da aiki,

Tuni ƙamshi ya soma gauraye ko'ina harta cikin hancina, irin ƙamshin da ke tada mutun daga bacci,

Wurin 9 na safe, jirginsu hajiya azeema yayi landing daga legos, ƙanwar Abbansu ce, hamshakiyar attajirar mai kuɗi ce, tatara har sunyi mata yawa, a tare da ita akwai Captain najeeb da Talal ƙannensu kanal yusif ne da take ruƙo a wurinta, saboda bata ta6a haihuwa ba, lalura ce ta same ta na rashin aihuwa, gashi Allah ya jarabce ta da sonsu kamar hauka,

Hakan yasa Abbansu ya mallaka mata su, a wurinta suka taso har suka girma,

Kanal yusif ne ya ɗauko su daga airport, izuwa gidan murna agunsa har ba'a magana, saboda ganin captain najeeb da Talal, an jima ba'a haɗuba duk da suna ƙoƙarin sada zumunci, aiki ne ya ke hanasu wani time ɗin, saboda aikin soja ba aiki bane na zama wuri ɗaya ba,

Bayansu sai general Ishaq wanda ya kasance shina first born a wurin abbansu wato yayansu gaba ɗaya, wanda ke zaune a kaduna state, tare da matarsa yazo shuwa'arab ce suna kiranta da Aunty Babba, saboda tana auren babban yayansu gaba ɗaya, sun zo ne tare da Hafsat yarsu ɗaya tilo, wadda take karantar military nurse, ynx haka ta kammala karbar training ɗinta aiki take yi, ta gaji abbanta kenan

daga su kuma sai mai bi ma ishaq wato na biyu a wurin abbansu, Abbas mai riƙe da muƙamin Colonel general, tare da matarsa yazo (AMANI) itama balarabiya ce ƙanwar Aunty babba ce yake aure, kuma dama ita ta haɗasu,
A nan cikin abuja suke da zama su ma, babu ƴa'ƴa a tsakaninsu soyayya suke sha,

daga shi kuma sai na ukunsu matashin saurayi bai ta6a aure ba,
Bakowa bane face brigadier general Abuhaisam, shi kaɗai yazo daga jos sai security ɗinsa,

Waɗannan sune suka samu damar halarta zuwa tarbar abban nasu sauran kuma suna kan hanya,
Ina fata dai kun riƙe sunan kowanne daga cikinsu saboda in labari ya tashi basai munsha Wahala ba, 😒

A babban main palour kowannansu ya hallara, domin dama nan yafi dacewa saboda girmansa da faɗinsa gashi set na royal sofas ɗin dake ciki guda biyu ne a jere,

Hajiya azeema ta hakimce a kujera mai mazaunin mutun biyu, jikinta na sanye da french less haɗaɗɗen gaske ash colour an mata riga bubu dashi, ta kashe ɗaurin ɗankwalin nan irin ture gaka tsiya, amma fa ita ba tsiya bace domin tana da gashi sosai shukune a kanta ta ɗaure da ribbom ya zubo har bayanta, hannayenta na sanye da diamond rings uku uku a kowane fingers na left & right hands ɗinta, price ɗin kowane ring ɗaya yayi 1.5million,
Haka ziririyar chain ɗin dake a wuyanta da earrings ɗinta, sun kai kimanin 200m, agogon diamond ɗin dake hannunta ƙirar graff diamonds ce, farashinta ko ba'a magana, billions ne ke magana 😯
Bata jin wuyar kashe wa kanta kuɗi, kai kace ruwan samansu ake tana kwasa, ko kuma daga saman bishiya take tsinkarsu 😂

takalman ƙafafuwanta kuwa kuɗinsu sun ishi wani talakan jari daga ciki hada ni,

aunty Babba kuwa tana cikin wata jigunanniyar riga haɗaɗiyar gaske,
Ta larabawa mai round neck yellow colour abunka ga fara sai ta fito ɗau kamar hurul aini, kafafunta na sanye da high heels tsadaddun gaske, launin rigarta, tayi rolling mayafi a wuyanta, ya sauka har kafaɗarta, amma hakan bai boye dogon gashinta ba,

tana zaune saman kujera mai mazaunin mutun uku (3 seater) mijinta ishaq shine a gefenta yayi shigarsa cikin manyan kaya namu na hausawa,

Hafsa na a zaune A saman 1 seater, kimono dress ne ajikinta, riga doguwa mara nauyi brown colour, ta ɗaure igiyar rigar a under chest ɗinta, babu head a kanta sai kitson manyan kalaba da akayi mata, ya zubo har gadon bayanta, fuskarta na sanye da light make up, tun da suka shigo kowa na tsoma baki ana fira dashi amma banda ita, cos she's very arrogant, ji dakai ne da ita, bata da mutunci ko kaɗan guyababbiya ce, fitinanniya, ga rashin kunya kamar 6eran gida,
hannunta na riƙe da waya kirar i phone 13pro, sai faman ƴan danne danne take yi,

Amani na zaune tare da mijinta a mazauni ɗaya,

Sai Abuhaisam na zaune jere tare dasu kanal yusif da Captain najeeb a saman 3 seater, sai talal a next chair din dake jikinta su , firar yaushe rabo suke yi, ana ta faman gaishe gaishe gida ya gama katsame wa,

wasu na dannar waya yayin da wasu ke tsoma baki ana fira dasu,

Su khaleed ne suka fito kowannansu na sanye cikin shiga ta alfarma wankan shadda gezna suka ɗauka launi ɗaya blue sky riga da wando, ba ƙaramin kyau tayi musu ba duba da launin fatarsu chocolate,

Nan fa aka shiga yan rungume rungume kowa cikin fara da nuna farin ciki, kowa ya fito amma banda mutun ɗaya wato junaid gashi kowa ya ƙosa ya ganshi,
Duk magana ɗaya biyu sai an ambaci sunan shi, ina junaid? Wai junaid baya nan ne,

azmi ce ta shigo tare da chef ummu hannunsu ɗauke da abunsha, jere acikin tray a cikin wasu fancy cups,

ɗaya bayan ɗaya suka bisu suna miƙa musu, kowa na ɗauka yana sha,
Hajiya azeema tace "ina fata dai an tanadarmana abunda zamu zubawa cikin mu domin ni ko breakfast ban tsaya ci ba na kamo hanya,' tayi maganar ne a lokacin da take ɗaukar cup daga saman tray ɗin da azmi ta miƙa mata,

da fara'a a fuska azmi tace "ae mun tanadarmaku abinci kala kala sai wanda kuka za6a,'

general Abbas ya kalli matarsa dake gefensa yace "me na faɗa miki? ai tun a gida nace ni bazanci komai ba, sai na zonan don na kwashi girkin azmi don ban mantawa da wannan farfesun nata mai zautar da mutun,'
dariya sukayi gaba ɗaya musamman azmi da ake yabon girkinta,

Aunty babba tace "ai ko munyi dabara domin ni kaina zumuɗin girkin azmi nake yi kamar kamar me,"

Cikin sanyin murya Amani tace "aunty azmi zanzo ki koyamin pls wannan dambun shinkafar sbd, baby na yana son shi ssae,'

Yadda tayi maganar cikin kwarkwasa ya basu dariya, aunty azeema tace"amma dai Amani ba ta ido, gashi nan kinsa mijin naki jin kunya, gaban ƙannensa kike ce masa baby da girmansa ,'

dukaddar da kai tayi tana murmushi, shima Abbas ɗin kansa na ƙasa Ya aza idonsa kan screen ɗinwayarsa, su kanal yusif sai murmushi suke yi,

Su azmi da chef ummu sun gama miƙawa koya abunsha don haka suka koma kitchen domin shirya abincin izuwa dining,

_wai dagaske ne su Babban yaya Zasu dawo gobe? Captain najeeb ne yayi tambayar_

_jin an ambaci sunansa yasa hafsat shaƙewa daga Kurbar lemun da take yi, tari ta shiga yi Ba don komai ba sai don jin sunansa domin ta ta6a shan Zazzafan marinsa_😂


Page *45 to 46*



_wlh am so eager so see Babban yaya too😢_


_Subhanah, Walhamdulillah,allahu Akhbar_




"Yeah but we are not sure, ba tabbacin cewa gobe zasu dawo, muna zuba ido dai,' kanal yusif ne ya bashi amsa,

Jinjina kai captain najeeb yayi tare da cewa "aiko bazan kwana ba, yau zan koma lagos, ba dani ba

dariya su kayi hajiya azeema tace "ashe muna da manyan baƙi, lion da tiger zasu dawo kenan, wannan karan bansan da wata rigima zai zo ba, Allah kaɗai yasan jinin da za'a zubar,'

Hankalisu twins ba ƙaramin tashi yayi ba dama suna zaune matse da juna, sunyi zuru zuru, zuciyoyi na bugawa,

Basu kaɗai ba hada fawan da su jabeer da irfan da sauran atakure suke jin kansu, a wurinsu zuwan Babban yayansu ba alheri bane, bawai don basu son shi ba, sai don tsoran abunda zai faru zuwansa,

"ae na jima ina bama ishaq shawara akan ya tunzura Abba, ya aurar dasu, wlh indai su kaji mace atare dasu zasu samu weakness ajikinsu su daina jin kansu tamkar dodonni,' sakin baki su kayi jin abunda aunty babba tace,

Azeema tace "da alama bakisan wanene RAFAYET ba, ai rafayet zuciyarsa tamkar dutse take ! ban ta6a ganin mutumin da mace sam bata gabansa ba irinsa, sam bai da shauqi akan mata, ke shi fa hasalima yadda yake kallon jinsin sa namiji haka yake kallon mace,' 😧

ta ƙarasa maganar tana kurbar lemun hannunta, general ishaq yace "kwara ki faɗa mata da kanki may be she will understand it now, i had been explaining to her about rafayet but taƙi fahimta,' ya ƙare maganar yana kallonta,

Murmshi azeema tayi tare da gyara zama tace "Anzo inda nafi auki, anzo dai dai wurin ba mai sauka, rafayet da kike gani ba mutun bane ........
dariya ce ta kubce mata su kansu dariyar suke ba don komai ba sai don maganarta takarshe da tace rafayet ba mutun bane,

dakyar ta saita dariyar ta ci gaba da cewa, " Ai dashi da mahaifiyarsa halinsu kusan ɗaya ne, kaifi ɗaya ne wasu irin bauɗaɗɗun mutanene, koda yake in mukayi la'akayi da cewa mahaifiyarsa baturiya ce, sannan kuma ba musulma ba, yanayin rayuwarmu da tasu ba ɗaya bace, amma gasky munsha Wahalar fatima fiye da tunanin mai tunani, ta azabtar damu saboda muna kwakwar ƴa'ƴanta, har yau fa ita bata yarda cewa Allah ɗaya bane, taƙi karbar musulunci, kuma bata yarda cewa ƴa'ƴanta sun musulunta ba, in har zasu taka suje wurinta to fa basu ba yin sallah ko karatun qur'ani sai dai in ba dasaninta ba, dakyar fa aka samu rafayet ya musulunta har yakai shekara 20 aduniya ba shi ba musulmi bane,

ta tsagaita da maganar tana sauke ajiyar zuciya, gaba ɗaya sauraronta sukeyi, musamman Aunty babba da Amani su da basu son komai ba game da su rafayrt ba,

Su twins kuwa da fawan jikinsu yayi sanyi domin ana magana ne akan mahaifiyarsu,

Aunty babba tace "nikam inaso nason wacece fatiman nan, ya akai abba ya aure ta ba tare data karbi addinin musulunci ba, Kuma har akayi gangancin barin ya'yanta suyi koyi da addininta ina nufin rafayet da ki kace yakai 20 yrs batare da yakarbi addinin musulunci ba, sannan ina fatiman take a yanzu, don ni ban ta6a ganin ta ba,'

Anzo dai dai wurin, ina fata kowa zai kasa kunnansa ya saurara muda akayi agaban mu, acewar aunty azeema

....... .............Bismillah......... .............

Asalin family ɗinmu Hausa fulani ne, mahaifin.mu bahaushe ne haifaffen garin zariya, mahaifiyarmu kuwa bafullata ce yar jihar damaturu, Haɗuwarsu tafarko a barikin sojoji na kaduna state Allah ya haɗa jininsu har takai su gayin aure ❤

Mu uku ne a wurin iyayenmu banban cikinmu Shine hussain wato (Abban sojoji) tagwaye ne su Allah yayiwa hassan ɗin rasuwa tun kafin su mallaki hankalinsu, Akwai tazarar shekaru a tsakanin mu sosai dashi, shi ne nafarko sai kuma ni azeema daga ni kuma sai ƙanin mu gaba ɗaya, wanda shine autanmu mun girme shi sosai, wato ABUSUFYAN wanda ynx yake zaune a Ƙasar turkey,'

tun yana 20years a duniya, wan mahaifiyarmu ya bashi auren ƴarsa maryam, yarinyace mai ilmin addini sosai ga hankali da natsuwa, maca ce mai saukin kai, bata ɗauki duniya da zafi ba,

Itace matarsa ta farko, sun sha sosai kamar laila da majnun, domin mu kanmu shaida ne akan hakan, duk in yana gari tashiga tarairayarsa kenan, idan aka turasa aiki kuwa nesa ba ƙaramain shiga damuwa take yi ba, duk tabi ta susu ce,

Abban mutunne mai son ƴa'ƴa koda yake bashi kaɗai ba, mu dukkan mu haka muke da son ƴa'ƴa zumuncin family ɗinmu yana da ƙarfi sosai, bama wasa da sada zumunci,

Cikin ikon Allah maryam ta samu ciki, kowa ya hau murna musamman ammin mu grandma ɗinmu, dayake maryam mutuniyarta ce tana sonta sosai kasancewarta yar yayanta modibbo,

Haihuwa tafarko maryam ta haifo kyakkyawan ɗanta, santalelen yaro yaci sunansa Ishaq (wato general ishaq) daga shi kuma sai Abbas wanda ynx yake rike da mukamin colonel general, daga Abbas sai brigadier general Abuhaisam gashi nan zaune kuna ganinsa, daga shi kuma sai major genaral Osman dukansu tazarar 2 years ne a tsakaninsu su duka, daga shine maryam ta ɗan huta,

Bayan nan ne tafiya ta kama su Abba izuwa ƙasar america, an tura su zuwa halartar wani special training na sojoji da za'a gudanar, da courses na dabarun aiki,

Hankalin maryam ba ƙaramin tashi yayi ba, jin za'a tura mijinta ƙasar turai, tsoranta kada wata tagansa ta liƙe masa Acan, saboda yana da farin jini sosai, 😇

Aiko hakance ta faru domin kuwa da zuwan su Abba u.s wata zankaɗeɗiyar budurwa kyakkyawar gaske ta ƙella ido tagansa taji cewa duk duniya bawan da take so sai shi,

baturiyar ƙasar amurika sunanta Alexandra ita ƴa'ce ga commender in chief na armed forces, 😯
Mace mai tsananin ji da kanta, ita a tsarin rayuwarta, Namiji baya gabanta, idan akayi mata maganar aure sai tace, ita jin kanta take yi tamkar namiji don haka ba abunda zaisa ta yin aure don tafi ƙarfin ta zauna a ƙarƙashin wani, idan akayi mata maganar ɗa kuwa, sai tace ita karenta tony ya ishe ta, wani jibgegen kare ne Wanda ta raine shi tun yana jinjiri har ya fara tsufa,

Abba shine namiji na Farko daya karya wannan kudurin nata, At first sight taji duk duniya ba wanda yai mata sai shi~

Kuma gadan gadan taji tana son aurenshi, Iyayenta sun so su dakatar da ita, amma dayake su in yaro ya wuce 18yrs yana da ƴanci ba wanda ya isa ya takamasa burki, har shari'a zai iya yi da iyayensa insun takura masa,

Hakan yasa suka ƙyale Alexandra ta auri Abba, ba tare da sanin family ɗinsa ba, shi kuma soyayya ta rufe masa ido baya ganin kowa in ba ita ba, dama fa su akwai iya tarairaya ga ɗaukar wanka da jan hankali,

A nan los angels california suke da zama a katafaren gidanta, nata na kanta dayake itama ta tara kuma ta fito daga babban gida, kuma ita ma soja ce tana riƙe da muƙamin major genaral,

Sunsha soyayya kamar romeo da juliet, acan kuwa 9ja sunyi mamakin jimawar abba, ganin sauran da aka tura Us tare dashi duk sun dawo sai shi kaɗai,

Ga maryam da ƙaramin ciki, kullum cikin zullumi take akan mijin nata,

time ɗin daya shirya dawowa 9ja yasha wahala kafin Alexandra ta amince cewa zata biyo shi na wucen gadi,

Aiko lokacin sun ga tashin hankali, ganin abba ya dawo da mata jinsin turawa, ran mahaifiyarmu baƙaramin 6aci yayi ba, saboda ta tsani jinsin turawa, sbd tasancewa basu da kunya fitsararru ne, an tada tarzoma a lokacin, gaba ɗaya danginmu sukayi masa caaa akan alexandra,

Amma abun mamaki mahaifinmu Salahudeen ya amince masa, kuma ya tsawatar da kowa akanta, ya hana kowa ya sa baki akan alexandra, haka yayan mahaifiyarmu modibbo ya tsawatar mata akan taja bakinta tayi shiru, haka kowa ya zubama sarautar Allah ido 👀

A katafaren gidansa dake abuja suke zaune ya ware mata part ɗinta daban, na maryam ma da ya'yanta daban, kowa baya shiga harkar kowa,

Sam maryam bata kishi da alexandra, tafison su samu zaman lafia a tsakaninsu,amma ita alexandra kishin maryam take ji, bakomai yaja hakan ba face sanin cewa su ba'ayi musu kishiya, basa zama da kishiya,

Cikin rashin sani sai ga ciki a jikin alexandra wanda ya tayar mata da hankali saboda tana shan maganin hana ɗaukar ciki don ita bata buƙatar ƴa'ƴa arayuwarta,

taita faman kiciniyar cire cikin hankalin abba ya tashi, faɗa sosai sukayi a lkcn, yasha wahalarta sbd sai da takai ga har zuƙunna mata yake akan guiwarsa yana roƙonta akan karta cire masa ciki yana so,

dakyar ta amince bisa sharaɗin inta haihu, ba ita zata shayar da yaron ba, kuma ba a nigeria zata haifesa ba, tafi so taje can ƙasarsu saboda tafi yarda da likitocinsu, kada a kashe ta tsoran mutuwa gare ta, 😂

haka ta maida Abba kamar ɗan aikinta da matsayinsa da komai haka zai zauna, yana mata aiki komai takeso shi zatayi, ita dai maryam bata cewa komai binsu kawai take da ido 👀

Hankalinta kwance saboda haryanzu Abba yana tsananin sonta bai wulaƙanta taba, bai kuma canza mata ba, sa6anin wasu mazan da zaka gani daga inda suka yi sabuwar amarya tofa ita waccen tazama expire product, 😥

wata rana yana zaune ɗakinsa saiga alexandra ta shigo da ƙaton cikinta, hannunta ɗauke da farar takarda da wani rubutu ajiki wanda aka rubuta da harshen spanish, ta miƙa masa takardar da biro tace yasa hannu,

_Gudun rigima yasa bai tambaye ta takardar mecece ba kawai ya raftaka signature ɗinsa, ajiki tare da miƙa mata , tayi murmushi ta kar6a, 😂_*💋ABBAN SOJOJi💋*

_mallakin_

_Hafsat Bature_ *Boss Lady*



_subhanallah_Walhamdulillah_Allahu akhbar_🙏


*page* *47* to *48*




_Dont worry your self guys, sergeon general is on the way soon insha Allah_😘

Ya Allah kaji ƙan waɗanda suka rasu, ka gafarta musu, muma in tamu tazo kasa mu cika da kyau da imani, 😔 Mutuwa ake kamar hauka, yakamata muji tsoran Allah muyiwa kanmu tanadin kyakkyawan ƙarshe tunkan tazo kanmu, mu kasance a cikin shiri domin akowane lokaci mutuwa zata iya zuwa😭 Ya Allah kasa mu cika da kyau da imani, Ya Allah ka haife mana zunubbanmu, Ya Allah ka kare mu daga aikata aikin dana sani😢 mu rage dogon buri a rayuwa, mu rage kwaɗayin abun duniya wanda daɗinsa ƙalilan ne, wannan rayuwar bata da tabbas wlh, amma wasu sun mai da ta wurin zama, suna aikata abunda suka ga dama, zalunci iri iri basa tunanin menene makomarsu 😭 Allah kasa mu dace 🙏 wlh sai mun gyara indai muna so muga dai-dai arayuwarmu 😔




Bismillah




a na nan lokacin haihuwarta yayi, abba dakansa yakai ta Airport kamar yadda yayi mata alƙawari,
kuma ya cika,

Cikin sa'a Alexandra ta haifi santalelan yaronta na farko, wanda ya gigita kowa, kyakkyawan gaske mai matuƙar ɗaukar ido, komai nasa na mahaifiyarsa ne ya ɗauko, hatta launin idonta blue eyes,

Ta jima a us kafin ta zo nigeria, domin ta gwada musu babynta, aikuwa nan fa dangi suka susuce akansa, amma ta hana kowa ya ta6a mata yaronta, iya kallo daga nesa, jinsa take tamkar gold koda yake darajarsa tafi darajar zinari,

Abba yayi mamakin ganinta tana shayar da yaron, bayan ita da kanta tace anemi mai raino don baxata shayar dashi nono ba inyazo duniya, da alama soyayyar yaronce ta kamata,

A lokacin itama maryam ta haifi nata yaron kyakkyawan gaske wanda duk cikin ya'yanta bamai kyansa, farinciki a wurin abba ba'a magana a lokacin yama rasa ina zai tsoma kansa, saboda ƙaunar yaran nasa da aka haifa masa,

Babban tashin hankalin shine, Alexandra ta tada 6alli akan cewa yaronta addininta zai biyo kuma tasanya masa suna Alex, nan fa hankalinmu ya tashi, kowa ya harzuƙa akan lamarin,

Ran abba ya 6aci sosai kamar yayi ihu, a ƙarshe daya takura mata akan cewa shifa yaronsa addininsa zai biyo, sai ta ɗauko masa wannan takardar daya sa hannu ajiki wadda akayi rubutu ajikinta da harshen spanish ta nuna masa,


Cikin rashin sanin ma'anar hakan yace "me wannan ke nufi"?
Dariya tayi masa tare da cewa " wannan takarda dace, ta yarjejeniya dake nuna cewa ka amince ƴa'ƴana su bi addini na! in har ka matsamin zamu shiga court ne ayi shari'a, kuma kada kayi tunanin zaka iya ɗauke takardarnan domin akwai copy ɗinta awurina ba ɗaya ba, signature ɗinka ne ajiki, 🙆

Hankalin abba fa ya tashi, bai ta6a dana sanin auren Alexandra ba sai alokacin domin takaisa ƙarshe, Ashe wayau tayi masa, tasan hakan zai faru shiyasa tayi rubutun da harshen spanish, shi kuma gudun rigima ya sa bai tambayi menene fassarar abunda aka rubuta ajiki ba kawai yasa hannu, 😥

yaso ya tada 6alli akan koma mai zai faru sai dai ya faru , amma maryam ta dakatar dashi takwantar mashi da hankali ta nuna masa cewa, inya bi komai asannu wata rana ita da kanta zata canza, canjin da har yau muke jira amma Alhamdllh an samu ci gaba,

Bakowa bane wannan yaron da ake tada jijiyoyin wuya akansa ba face Surgeon general Rafayet wato BABBAN YAYA,

tun yana jariri bai ta6a kuka da hawaye ba, kuma likitoci sun tabbatar da cewa lafiyarsa garas, amma momynsa har ƙasar waje ta fiddasa aka ƙara dubasa aka tabbatar mata da lafiyarsa, sannan ta yarda,

A lokacin da yana yaro yayi tashen ƙiwuya, ya tsani bakar fata indai launin fatarka ba fara bace irinta mahaifiyarsa tofa kun raba jaha,

Duk bala'inka baka ɗaukarsa, hatta mahaifinsa dake mutuwar son shi, bai yarda da shi duk da hasken fatar abban nasa, tsakaninsu sai dai kallo daga nesa , sai kuma in yana bacci uban ya lalla6a yaje ya zuba mishi ido yana kallonsa,

Shi kuma yaron da maryam ta haifa, ba kowa bane fa ce Marshal omer tazarar satittika ne a tsakaninsa da Rafayet,

Tun suna yara omar ke son wasa da rafayet, amma bai yarda dashi ba duk da kasancewar omar fari ne sosai kamar balarabe, yabiyo mahaifiyarsa Maryam bafullatana,

Gashi shima rafayet ɗin yana son Omar amma tsakaninsu sai dai daga nesa a rinka jefawa juna murmushi 😊

daya ƙara wayau hankali ya fara shigarsa, wata irin shaquwa ce ta shiga tsakaninsa da omar, duk da momyn shi bataso yana hulɗa dasu,
kai har takaiga idan dare yayi sai ya saci hanya daga bedroom ɗinsa izuwa nasu, ya haye saman gadonsu wurin omar ya kwanta kusa da shi,

Shima omar ɗin harya gane idan dare yayi, yazauna yaƙi bacci yayi ta zaman jiran rafayet, har sai yazo sannan su kwanta tare suyi bacci,

Maryam kaɗai ce ta lura da hakan, ita dai ba ruwanta, tana son rafayet tanajinsa kamar ɗan cikinta, haka zata je tayi musu addu'a tashafa musu kawunansu,

Ranar da alexandra ta gane hakan akan idonta, taga rafayet ya shiga ɗakinsu omar tsakar dare , aiko washe garin ranar tarinƙa zabga masifa har sai da kowa ya gaji,

Bayan wannan lokacin maryam taci gaba da haihuwa a inda ta sake haihuwar namiji again wanda yaci sunan shi najeeb, gaya nan kuna kallonsa, wato captain najeeb,
daga shi kuma sai Kanal yusif shima gashi nan zaune, daga yusif kuwa sai commender haroon, daga haroon sai Captain adams,

daga adams sai khaleed daga shi kuma sai jabeer da irfan, haka ta haifesu, daga nan ne ta dakata,

A bangaren Alexandra kuwa shiru sbd tace ta kammala nata, abba najin baƙin cikin musamman inyaga Ya'yansa zasu masallaci sun haɗu su duka amma babu rafayet acikinsu,

Ya so ya sake tada 6alli akan yaron, saboda yana da hanyar da zai kwaci kayansa daga faɗawa daga halaka, amma mahaifiyarsa tayi masa tatass akan cewa lokacin da ya aurota dawa yayi shawara, taja masa kunne akan cewa kada ya kuskura ya ƙara tankawa akan alexandra,

A dolensa yaja bakinsa yayi shiru bisa umarnin mahaifiyarsa,
A karshe ya koma yana nuna mata soyayya don yaja
DOWNLOAD
DOWNLOAD

6 Comments On ABBAN SOJOJI
avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
muhammad-4-3-8

6 months ago

Reply

I want it

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
husaini

2 months ago

Reply

I love this novel

Please Login or Register in order to submit comment