Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

nata tace "ina kuka ne ba don kai na ba sai don Husanna dr yace in ba mu fara biyan kudi an mata aiki ba , mutuwa zatayi kuma ynx haka kudin gado ya kare sallamar mu zasuyi ko kudin magani babu ," hankalin Sehrish ba karamin tashi yayi ba,
Hajajju dake tsaye tana kallonsu, jikinta yayi mugun sanyi saboda tsananin tausayi, ita kanta wadda sehrish takira da Jahad akwai wound a goshinta, anyi mata dressing da bandage duk jini a jikin sa , hannunta ma akwai kanula alamun anyi mata karin wani abu jini ko ruwa , a kagare hajajju take da taji labarin wadannan y'an ukun lallai bakaramar wahalar rayuwa suka sha ba.

Muryar Sehrish ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta shiga "Jahad ga hajajju ku gaisa kuma kiyi mata godiya sbd itace zata sama mun aikin da zan fara yi nasamu kudi nabiya ayi maku aiki," matsawa tayi gaban hajjaju tana share hawayenta cikin girmamawa tace" ina kwana hajiya ," murmushi hajajju tasaki tare da dafa kadarta tace "lafiya lou ya jikin naku "? Jahad tace "Alhamdllh ni da sauki husanna ce abun sai kara gaba yake yi don dr yace koda an mata aikin ba lallai ta dawo yadda ake so ba...."

Kuka ne yaci karfinta har takasa karasa maganar , rungumo ta hajjaju tayi a jikinta tana lallashinta " am sorry my daughter stop crying insha Allah everything will be ok , cikin kuka ta amsa da "zandaina mungde ssai ," karasawa Sehrish tayi wurin husanna dake kwance rai hannun Allah , gefen gadon ta zauna tana kallonta idonta cike tab da kwalla tace "Allah ya baki lafiya yar uwata ina jin duk wani irin radadi da kike ji a zuciyarki wanda yayi sanadiyar shigarmu cikin wannan halin bazai taba gamawa da duniya lafiya ba Allah ya isa tsakanin mu dashi mugu azzalumi macuci ..." a karshe ta fashe da kuka ta kwantar da kanta a saman jikinta , har cikin ranta take kukan.

Tsohuwar dake kula dasu ce ta shigo cikin sauri hannunta rike da magunguna da takarbo masu , a nan tasamu hajjaju tsaye ita da jahad tana lallashin ta , jin alamar shigowarta yasa suka jiyo suna kallon , cikin sakin fuska tace "Sannun da zuwa hajjaju ke ce da kanki ," murmushi hajjaju tasaki dama sun son juna da alama , " kwarai kuwa nice gwaggo dama ke ce ke rike da yarannan amma ni ban taba ganinsu ba gsky ," murmushi gwaggo tayi tace "bakya leko mune shiyasa amma sun jima wuri na ni nake kula dasu ," jinjina kai hajjaju tayi tace "hakane amma gwaggo jikokinki ne su"? Goggo ta girgiza kai tare da cewa "a'a Allah ne ya hadani dasu nima labari ne mai tsawo , amma ynx bani da kwanciyar hankalin da zan zauna na baki shi , ki bari saina samu natsu," tana gama fadan hakan ta mika ma Jahad magungunan "karbi nan naki ne dakyar nasamu kudi na siyo su," godiya tayi mata ta karba , a tare suka taka izuwa inda sehrish ke kwance jikin Husanna , cike da nuna tsantsar tausayi hajjaju tace "Allah ya bata lafiya Allah sarki mutum baya sanin halin da duniya take ciki wani sa'in sai ziyarci asibiti nan zai ga marasa lafiya iri iri gwanin bantausayi hakika na tausayawa wannan yarinyar tana cikin hali Allah ya kawo musu sauki da duk marasa lafiyan dake fama da ciwo ," amsawa sukayi da amin , har time din sehrish bata dago da kanta ba , ita kadai tasan yadda take ji aranta.

Hajjaju ta mayar da idonta kan Gwaggo tace "idan ba damuwa muje ki raka ni wurin likitan zanyi magana dashi ,"
fita sukayi a tare , wuri Jahad tasamu ta zauna a chair din dake facing din gadon mara lafiyar, kallonsu takeyi su biyun tana kara jin kaunar y'an uwan nata , taji dadin zuwan rishi har cikin ranta , jajircewarta akan ganin sun samu rayuwar mai kyau yana kara mata ninkin son yar uwarta ta, tazama tamkar uwa agare su , alhalin ita age dinsu daya duk da tare suka zo duniya amma sun tsere wa rishi da mintina a wurin haihuwa , tunani iri iri ke zo mata a ranta runtse idonta tayi hawaye na kwaranyo wa daga idonta

Gabad'ayansu sun shiga cikin yanayi , duk sunyi zurfin tunani , numfashinta suka soma ji da karfi da karfi wani irin sauti mai matukar razanarwa , a firgice sehrish ta dago da kanta cikin rudu ta furta "Subhanallah! jahad husanna ta cire oxygen da aka samata," a rude jahad ta matso kusa da su hannu tasa ta tana kokarin mayar mata roban oxygen din , buge mata hannu tayi tana wani irin gurnani ga zufa sai ke to mata take yi ga wani irin tari da take yi cikin kuka take ambaton "Seh..seh..sehrish ,"

Dakyar sound din ke fita , hakan ya tambatar masu da cewa so take tayi ma Sehrish magana amma takasa , matsawa sehrish tayi kusa da ita tare da sa hannu tana shafa mata gefen fuskarta cikin kuka tace "pls husanna kiyi hkr kinji Allah zai baki lafiya , nasan mai kike ji a zuciyarki, zanyi kokari koda zan rasa raina ne wurin ganin kin samu lfy , wlh sai inda karfina ya kare , ina sonki sosai my sister," gaba dayansu kuka sukeyi , mayar mata da roban oxygen din Husanna tayi , bin ta su kayi da kallo ganin tana kokari kakaro murmushi a fuskarta , wani sabon kukan suka sake fashe wa dashi.

"Yar'uwata kada ki tafi kibarni ni nafiso na mutu a gabanku dan Allah kada ki tafi ," lokacin da sehrish ta tuna da wannan kalami na Husanna sai jikinta ya kara mutuwa lukus , kamar ba kasusuwa a jikinta, zamewa tayi ta zauna kasan tiles din tare da jingina kanta gefen gadon , wasu abubuwa ta dinga tunawa arayuwarsu wanda in har taci gaba da tuna su to tabbas zuciyata zata buga ne! komai ya dawo masu sabo fal , komawa Jahad tayi ta zauna tana shesshekar kuka hada majina a hancinta ,
Hannun husanna taji cikin nata , dayake ta aza hannun nata a saman bed din, ta rike shi gam cikin nata , dagowa sehrish tayi da fuskanta wadda tayi jawur , ga idonta sun kada , fuskarta tayi kwaba kwaba cikin kasalalliyar murya tace "Husanna ki daina zubar da hwayenki nasani abun da ciwo , zafinsa yakai kunar wuta amma ki daure pls , ba irin whalar da bansha ba wurin ganin nasamu kudi an miki aikin nan ke da jahad especially ke , kai karshe ma an kokarin bada kaina nayi amma dana tuna abunda mama ta fada saina gaza , duk da haka ban hkr ba na soma kokarin samun wanda zai siye ni yabani kudi kawai na kawo muku ni natafi amma saina tuna cewa in na tafi wazai kula daku ? duk da nasan akwai Allah shine gatan kowane bawansa ...' muryarta ce tashaqe ta gaza idasa maganartata saboda kululun bakin ciki daya tokare mata makoshinta .

Jahad da ke sauraron maganar yar uwarta su sai taji wani sabon kukan ya balle mata, domin duk wannan gwagwarmayar da Sehrish tayi sam basu sani ba a boye tayi kayanta.

Sun sha kuka kamar ba gobe nima na tayasu kukan duk da bansan takaimaiman tarihin rayuwarsu ba da kuma dalilin kukan nasu.

A haka goggo da hajjaju suka same su gwanin ban tausayi , wayar hajjaju dake cikin yar purse dinta sai ringing take yi don haka tace ma serish ta taso su tafi , cikin kuka ta tashi a hankali take tafiya tana waiwayansu , goggo tace " kada ki damu rishi hajjaju ta biya mana kudin gadon kuma tace zata samu koda bashi ne a fara biyan kudin aikin inyaso daga baya kin fara aikin kin samu sai ki biya,"
Ba karamin dadi sehrish taji ba , haka jahad ma godiya suka shiga yi mata , a karshe tayi masu sallama suka tafi ,
Har a cikin motan kuka takeyi dakyar hajjaju ta lallashe ta tayi shiru....

Time din da suka dawo , larai na kitchen ita da y'an matan kauyen nan tana koya masu wasu abubuwan daya kamata su sani.

A falon suka zauna gaba daya jikinsu a sanyaye, sehrish na zaune kasan carpet jingine da 2 seater , tana sauraron abunda hajjaju zata ce ,
magana ta soma mata "Sehrish ni yanzu bansan ya zanyi dake ba, game da aikin nan m, gashi ni already ina da y'ar aiki kuma gsky ko da ace ban da ita, ba zan iya daukarki sbd kina bukatar kudi masu yawa ni kuma iya salary din da nake biyan larai 10k ne."
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️
───────────────────────
*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~

Page 5-6


Jin wannan bayanin daga bakin hajajju yasa jikin Sehrish yin sanyi , bata ce mata komai ba sai ma ta ci gaba da wasa da yatsun hannunta. Ci gaba da magana hajajju tayi "abunda za'ae tunda dai naga sisters din naki kuma munyi magana da gwaggo da take kula daku , ynx ki koma ki ci gaba da kula dasu saboda suna bukatarki kafin Allah yasa asamu aikin ,"
Kamar an dasa ta haka tazauna idonta suka ciko da kwalla, kiris take jira ta fashe da kuka , dama bata jima da gama wancan kukan ba
Wayar dake hannun hajajju ce ta soma ringing , picking tayi tare da karawa a kunnan ta tana fadin " Manyan manyan gari ! Abban sojoji ashe kana nan ba'a neman mu , koda yake dama ku hamshakan masu kudinnan ganin ku sai an cike file."

Natsuwa sehrish tayi tana sauraranta , ta lura da yadda hajjaju ke washe baki da alama koma wanene take wayan dashi Babban mutum ne ,
tuna damuwar da take ciki yasa ta daina sauraron wayar tasu ta shiga tunani kala kala a cikin zuciyarta , har hajjajun ta kammala wayar bata sani ba sai da taji tace "Ga samu ga rashi !!" dagowa tayi da idonta tayi tana kallon , hannu hajjaju tasa ta dafe kanta alamar takaici.

Sehrish tace "Hajiya meya faru?" Hajajju tace "Aiki ya samu mai tsoka , jin hka yasa sehrish ta soma murmushi "amma sai dai kash Namiji suke so mai aiki ba mace ce ba !" lokacin da hajajju ta idasa maganar tuni sehrish ta gumtse fuska hankalinta ya tashi.

Hajjaju ta ci gaba da cewa "ina tayaki bakin ciki gsky, sbd kinga mutumin nan daya kira ni ba karamin mai arziki bane , cos they can pay u 50k as your salary after that zasu dauki dukkan responsibilities din ! Ci da shan ki wurin kwana lafiyayye sannan har school zasu iya saka ki ga sutura ya kike gani "?
Takaici ya hana tace komai ga samu ga rashi , ji take kamar ta cire takalmanta ta watsa da gudu saman titi kota rage radadin da take ji a zuciyanta ,
"Sehrish kinyi shiru baki ce komai ba "? ta jima ba tare da ta ce wani abu ba sai da tayi zurfin tunani kafin tace "ZanJe ! Zan yi aikin a matsayin NAMIJIN akan y'an uwana babu abunda bazan iya yi ba don nayi basaja a matsayin namiji wannan abune mai sauki a wurina ,"
In serious matter take mgnan ba tare da jin wani dar a zciyarta ba dagaske take dai , murmushi hajjaju tasaki don ba karamin burgeta tayi ba saboda tana da confidence akan komai da take so , " hmmm sehrish kenan how can u change ur creator frm a girl to a boy i dont think u can act like a male zasu gane ki ne , "
Matsawa tayi kusa da hajiyar tare da rike kafarta tace "Don Allah hajiya ki taimake ni wlh zan iya , indai za'a samu makeup artist din da zai tsara ni ya mayar dani kamar namiji this is a simple thing , kawai amincewarki nake bukata,"
hannu hajjaju tasa ta cirewa Sehrish hannunta data rike mata leg dinta dashi sannan tace "Babbar magana ! tun da nake bantaba yin wannan kasadar ba , natura house maid mace a matsayin namiji , sannan wannan mutumin da kika ji ina magana akan sa wato Abban Sojoji , y'ay'ansa maza goma sha takwas kuma dukkansu sojoji ne masu rike da manyan mukamai , dalilin dayasa yace namiji suke so a matsayin d'an aiki saboda ba yadda za'ai mace ta iya , bai ma dace ba , balle ma yaransa da kwata kwata basa da sauki , zafin rai ga ji da isa , "
Kamar zata yi kuka ji take in har hajajju bata amince mata ba zata iya rasa ranta , cikin kasalalliyar murya tace "Hajiya ki amince mun kawai ae ni nace zan iya wlh idan baki amince ba shinkafar bera zanci kawai na mutu kowa ya huta don bazansu naga mutuwar y'an uwana ba , " zaro ido hajajju tayi jin ta anbaci zata je taci shinkafr bera , kuma dagaske take ba alamar wasa a mgnrta ,
ruko hannunta tayi saboda harta mike zumbur zata figi hanya , "Meya yi zafi haka dawo ki zauna kinji , ni bazanso nayi sanadiyar mutuwar wannan innocent face din ba ," komawa tayi ta zauna tana sauke ajiyar zuciya ,
Shiru suka yi na wani lokaci daga ita har hajajju , jin shirun yayi yawa yasa tace "Hajiya baki ce komai ba am so eargerly to hear frm u ," ta karasa maganan tana kallon ta ,
Wan nan shirun da hajajju tayi sake sake takeyi a cikin zuciyarta "taya zan kai yarinyar nan gidan soldiers a matsayin namiji ! duk ranar da asiri mun ya tonu daga ni har ita kashin mu ya bushe , maganar da sehrish tayi ce ta dawo da ita , " Sehrish i dont know what to do am just comfused ina tsoron hakan fa ,"
"Nima ina goyon bayan yarinyar nan" larai ce tayi maganar shigowarta kenan taji suna tattauna wa , bin ta su kayi da kallo , wuri ta samu ta zauna kafin taci gaba da magana "Wurin samun biyan bukata rai ba abakin komai ya ke ba , tun da har tace zata iya kawai ki amince mata ! saboda ni na taba kallon wani korean film irin haka actress din ciki ta yi shigar namiji ba tare da wani ya gane ta ba kuma tacimma nasara ," jinjina kai hajajju tayi tare da watsa hannayen ta tace "Shikenan Finally i agree tunda har larai ta Jefa miki kuri'a kun rinjaye ni ," dariya sukayi su duka ba karamin dadi sehrish taji ba , ynx hajajju ta yarje mata sauran shirin yarda abun zai kasance ,
Mayar da idon ta kan larai tayi tace "To ynx ta ina zamu fara "? Larai tace "ae magana ta kare kawai mu da muke da Professional makeup artist a hannu ko kin manta da Mariiiya ? murmushi hajajju tasaki tare da cewa " ae Mareeya karshe ce ! Indai wurin canzawa mutun kamanni ne insha Allah gobe zan yi inviting din ta kuma a gobe za'a kammala komai don ya ce mun Jibi suke son mai aikin ta je ,"
Har larai ta bude baki zatayi magana ta jiyo muryar yaran nan dake cikin Kitchen wadanda take koyama aiki , suna kokoyi muryar d'aya daga cikinsu taji tana cewa "Aunty larai gatanan xata wanke gas cooker da ruwa ," da sauri ta mike ta nufi hanyar kitchen din tana cewa "Allah ya wadaran naka ya lalace har waning nayi muku kada ku taba komai amma saboda kan kifi gare ku baku gane komai salon kujama mutane ko !?
Hajajju tace "ke ma da laifinki akan me zaki baro min su a kitchen salon suyi mun barna ," mayar da idon ta tayi kan Sehrish "ki je ki huta time din sallah ma yayi nima bari na tashi ,"
Ta shi tayi ta shiga ciki , wanka tayi ta dauro alwala , ta fito ta shimfida prayer mat tayi sallah , kamar yarda ta sama kullum sai ta daga hannayenta tayi sama da 30mins tana rokon Allah cikin harshen larabci take jero addu'oin ta da bukatanta da damuwarta tana neman Allah ya yaye mata su ,
Bayan tagama ta tube hijabin ta ajiye , sannan ta hau saman bed ta kwanta dama jiya bata samu isasshen bacci ba , don haka lokaci guda bacci ya kwashe ta , tana cikin bacci y'an matan nan suka shigo , sai faman fadin wash Allah suke , koda sukayi arba da ita kwance ta baje gashi ta cire hijabin kan ba head tie, nan fa suka fara santin gashin kanta , ita dae bata son meke wakana ba tadai ji sama sama ana ja mata gashin kai ,
Zama sukayi kamar sun sami television sukai ta kallonta , ba karamin lalata sukayi ma kanta ba duk sun cukuikuye mata gashi yar kalaban nan sun warware mata ita , sun mai da karamar mahaukaciya ,
Nauyin bacci ne ya hana ta farka amma tabbas taji ana shafa mata kai kasa kasa ,
Sai da ana kiran sallan isha sannan ta farka , mika tayi tare da yin hamma , time din sun fita daga cikin bedroom zuciya sauko da legs dinta tayi kasan tiles din tana sauke ajiyar zuciya , kafin ta mike ta shiga toilet , tana cikin yin alwala tayi shafuwan kai ta shafo gashin kan ta mamaki ne ya kamata jin ba kitson dake kanta da sauri ta idasa alwalar ta je gaban mirror ita kanta sai da ta firgita da ganin yadda suka susuce mata gashinta , amma ba wannan bace damuwarta , zullumin kada husanna ta mutu da kuma aikin da zata fara ,
Zama taci gaba da yi a bedroom din , tana tunene tunane , ga yunwa tana ji amma takasa fita ta nema ,
Turo kofan sukayi suka shigo hannunsu dauke da tray abincin aka zuba musu shinkafa da miya ne sun cinye sun rage mata d'an kadan, ajiye mata sukayi suna dariya suka fice , abunda basu sani ba ita kallon Shashashu take masu ,
Bin a bincin tayi da kallon ba don tana jin yunwa ba da bazata ci Ba don sun jagula shi, haka ta zauna ta dinga turawa a baki kamar zatayi kuka , har dare yayi tana zullum abu daya kuma dashi ta kwana,
.......................................ABBAN SOJOJI
.......................Story by MrsBature
..................Part 1

In the morning
Around 10:30am makeup artist dinan ta iso gidan a time din duk sun hallara a falon hajjaju , bayan sun gama gaisawa , ma'reea ta bukaci ganin Sehrish , kwala mata kira hajajju tayi fitow tayi da sauri ta iso inda suke , bin ta da kallo mareeya tayi frm head to toe , sannan tace "Wannan ae mai sauki ne , naga tana da tsayi jiki ne dai babu sosai , abunda za'ae kayan maza za'a samo riga da wando oversize saboda su kara mata girma , sannan wadannan abubuwan , tayi magana tana nuna kirjinta da hannunta " dole a matse su don naga suna da girma ssae tubarkalla , " cikin jin kunya rishi ta dukar da kanta kasa , murmushi larai da hajajju sukayi , su kuwa y'an matan nan dake baje a kasan carpet dama basu da burki washe baki suka shiga yi wato anzo dai dai inda suke so ,
Hajajju tace "ynx me za'a sa a yi tighting dinsu "? Ma'reeya tace "mai sauki ne akwai wani abu da muke amfani dashi na matse tumbi shima zai iya yi ," hankalin rishi ba karamin tashi yayi ba har bata son lokacin da tayi subul da baka ba tace "in suka bace fa ya zanyi ,"? gaba dayansu suka kwashe da dariya mareeya tace "wato kada su bace a rasa nayiwa miji gayu ko ," cikin jin kunya ta dukar da kai , larai tace " dagaskiyar ta fa nono ae yana daya dagacin abunda ke kayatarda maza in suka bace ae ba magana ," ta karasa magana tana dariya , duk kunya ta gama kamata,
Ma'reeya ta ci gaba da magana "Sannan naga kamar tana da tsayin gashi ko,"? hajajju tace "Sehrish cire hijabin mana tagani , hannu tasa ta cire hijabin ta rungume a kirjinta ,
Hada baki sukayi wurin cewa "Tubarkalla masha Allah ," ma'reeya tace " yarinyar kamar balarabiya wurin tsawan gashi, gsky ni kishi nake da wannan gashin naki don haka dama dole indai zakiyi acting a matsayin namiji sai an datse miki shi ya koma guntu kamar nawa dai", nan fa hankalin ta ya tashi saboda tana bala'en son gashin nan nata , kamar zatayi kuka tace "don Allah hajajju karki bari ayimun aski ni inason gashi na ," takarasa maganar tana kallon hajjaju ,
Murmushi hajajju tayi tace " Sehrish ba Aski zata miki ba rage miki shi za'ae , ke da zaki neman kudi wake ta wani gashi , "
Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta , larai tace "Gsky yarinyar nan da ace a matsayin mace zata je aikin nan tsaf zata auren mai gidan," hannu hajiya tasa abaki tace "ke ! tab y'ay'an sa kuwa da sun yi farfesu da namanta sojoji fa akace hmmm !! " dariya sukayi su duka , mareeya ta cigaba da bada bayani "Sannan dole a canza mata suna daga SEHRISH zuwa TUKUR ," a tare suka hada baki wirin cewa "Tukur kuma !"? murmushi ma'reeya tayi tare da jaddada masu maganarta ta " kawai kuwa ! sannan zan sa mata gashin baki irin na maza wanda ake fixing dinsa tare da eyebrows na kanti.

*_Hafsat Bature_*
~(Boss Lady)~


Page 7-8


Hajajju ta ce "Gashin baki dai. wannan dana nasani ? amma me amfanin hakan "? ma'reeya tace "Wannan wani salo ne kuma ina tabbatar miki da zaiyi aiki , duk da sehrish yarinya ce har a fuskarta amma indai nasa mata gashin baki dana jagira , zata kara suffanta da namiji zata koma kamar d'an daudu kuma dama in kin lura yanayin jikin y'an daudu basa da kiba sai tsayi ,"

Gaba daya sun amince da maganar ma'reeya , shiri na musamman akayi ma Sehrish a washe garin ranar cikin riga ta maza milk colour mai maballai a gaban rigar , sai wani burgujejan wando falazu da aka sama ta kamar kafar agwagwa haka yake pink colour , sun matse mata kirjinta , shafe ta koma kamar babu su , an datse dogon gashin kanta an barmata guntu irin nawa sai suka samu kallabi irin launin trouser din suka nannade mata shi akai kamar rawani , kallabin nada tsayi sai da yar jela ta zubo ta gefe , sai ta koma kamar d'an chali chali , ga gashin bakin da suka sanya mata , ya hau radau ya zauna , haka jagirar da suka samata , ta zauna cuf , duk wani abu na ado na jikin y'a mace babu shi a tattare da ita yanzu ,

Shin koya wannan wasan kwaikwayon zai kasance ? mezai faru ranar da suka gane cewa sehrish macace ba namiji ba ? Kowa yasan ya sojoji suke 👊.
Tunda a sussuba suka kama hanyar zuwa abuja , ita da hajjaju , zuciyarta sai dar dar take yi mata , a natse hajjaju ke driving dinsu , yayin da sehrish ke gefenta , idonta nakan glass din motar , tana kallon yadda suke wuce wurare daban daban , zahiri tana kallon bishiyoyin da suke giftawa na cikin dajijjikan da ke a side road kamar suna gudu da kafafuwansune , a hankali zuciyarta ta sauya mata akalar tunaninta izuwa rayuwarsu ta baya , nan take taji wasu zafafan hawaye na sintiri a idonta , zuciyarta ce ta soma yi mata magana "Sehrish kowane d'an adam yana da irin tasa kaddarar, Allah yana jarabtar bayinsa ne domin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

6 Comments On ABBAN SOJOJI
avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
muhammad-4-3-8

6 months ago

Reply

I want it

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
husaini

2 months ago

Reply

I love this novel

Please Login or Register in order to submit comment