Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

komai ma in akwai hada ƙanzo ma azubo mana muna ci pls , mu ko ciyawa ce in dai za'a sama ta miya muna so," 😹😹😹
Dariya kamar zata kashe saude, haka ta ɗauki tray ɗin ta wuce dashi kitchen, duk wannan budirin da akeyi goggon katsina bata sani ba, tana can haye saman gadonta,daga sauraron radio bacci ya kwashe ta,
Sai da jahad da hosana su kayi kulu wash rabu hani'an , sannan suka dawo hayyacinsu, sun ƙarar da abincin gidan duka, dole saude ta ɗaura wani girkin,
Bedroom ɗinta ta shigar dasu,bin ɗakin su kayi da kallo komae tsaf ba tarkacen hauka, sai ƙamshi ke tashi, daga bed sae wardrobe, ƴar bedside loka da sauransu,
Toilet ta nuna musu tare da cewa "nasan zaku buƙaci yin wanka, ga toilet nan, ku cire kayan jikin ku naga sun tsufa kuma sunyi datti, kusanya munsu acikin laudry basket ɗincan," tayi maganar tana nuna inda basket ɗin yake gefen wardrobe ɗinta,
Sannan tace " duk abinda baku gane ba kuyi mun magana, just feel free,"
"Mun gode sosae aunty," acewar jahad, murmushi saude tasaki tace "kada ku samu damuwa, ni zan shiga ciki," tayi maganar tare da fice wa daga ɗakin,
"Wai !! Allah hosana kin ga yadda Allah ke ikonsa ko? mun fita daga wancen kurkukun kaddarar (Next novel) ynx gashi zamu fara sabuwar rayuwa mai kyau,"
Murmushi kawai hosana ke saki, gaba ɗaya hankalinta nakan Marshal Omar duk in ta tuna yadda lamarin ɗazu ya wakana sai taga abun kamar a mafarki," 😊
Sun jima suna shiririta, kafin jahad tafara shiga wanka, komai na toilet ɗin a tsaftace, ya ji tiles har jikin bango, shower ce ta tsaye, sai kwandon wanka, mai ɗauke da sabulu mai ƙamshi da lallausan soso,
Bakomai ya burgeta ba acikin toilet ɗinba sai shampoo da tagani jere, saman mirror, saboda gashinsu yayi dauɗa, duku-duku sai uban wari, ga ƙura, murmushi tasaki cikin sauri ta tu6e rigar jikinta kamar tsumma, ta yi hanging ɗinta jikin towel holder,
Baƙaramin dauɗa jahad ta fidda ajikinta ba, sai da ta wanke ko'ina tayi shaving gashin under ɗinta dana armpit ɗinta da Shaving cream, dogon gashin kanta ma yasha wanki da shampoo,
Zanso ku ga yadda jahad ta fito daga toilet ɗinnan, Fesss fesss kamar wadda tayi wanka da ruwan zam zam, da daurin gaba ta fito, towel tasanya ajikinta, hannunta kuma na riƙe da rigarta, cikin laundry basket tasanya rigar kamar yadda saude ta basu umarnin,
Sakin baki jahad tayi ganin hosana nata faman sharar bacci a tsakiyar shimfidaɗen gadon saude, girgiza kai tayi tare da faɗin "basa ban ba, gida babu makwabta babu gidan miji ba tabbas" 😂
( this reminds me our class mates Allah sarki, wannan sararsu ce, wato daga anyi abu sai suce gida babu makwabta babu gidan miji ba tabbas)
Allah sarki hosana dole kiyi bacci baiwar Allah, munyi rayuwar ƙunci sosai, yanzu lokaci ne da Allah ya amshi addu'armu, zamuyi rayuwa ta jin daɗi da walwala," jahad ce tayi wannan maganar sannan ta ƙarasa, inda hosanar take, ta ɗan russina tare da sa hannu da bubbuga ta, " Get up hosana, bacci bazai yi maki daɗi ba, da datti ajikin ki, ki tashi pls," a hankali hosana ke buɗe dara daran idanuwanta, tana lullumshe su, cikin kasalalliyar murya tace " meyasa kika tashe ni dan Allah ! bakiji yadda nake ji ba, '
"Sorry hosana, nasan ba daɗi amma ki tashi kije ki cire dattin dake jikin ki, wlh zakiji wata irin ni'ima mai daɗin gaske na shigarki, ba ki ga yadda nayi fess ba"? tayi maganar tana jujjuya mata jikinta don tagani dakyau,'
Murmushi hosana tayi daga kwancen da take tana kallonta, miƙa mata hannunta tayi tare da cewa "pls taimakamin na tashi kasala nake Ji 🤗


*Hafsat Bature* 😎*🪄🪄🪄ABBAN SOJOJI🪄🪄🪄*


*Mallakin*


*💋Hafsat Bature Moh'd💋*


*❤‍🔥BossLady❤‍🔥*


*Junaid was the heart beats of my story not because i loved him so much, zaku shaida hakan*

~page 76-~

Murmushi hosana tayi daga kwancen da take tana kallonta, miƙa mata hannunta tayi tare da cewa "pls taimakamin na tashi kasala nake ji ajiki,"
Ruƙo hannunta jahad tayi daker ta miƙar da ita tsaye, tana faɗin "wash Allah ba dole ki ji kasala ba, kinci uban abinci kin kuma zo kin kwanta," acewar Jahada,
Wuce wa hosana tayi tare da shigewa toilet ɗin, tana jiyo muryar jahad tana cewa "Hosana akwai shampoo ciki pls ki wanke wannan mahaukacin gashin kan naki, mara tsari nasan ki da taurin kai, bakisan wanke sumar kan ki, ko nazo na taya ki wanke wa.."? ta tambaya tana jiran amsa,
"Banso,' ta cikin toilet ɗin tabata amsa, dafe kai jahad tayi tare da cewa "Oh God!!" saboda tasan hosana bazata ta6a yarda ta wanke sumar kanta ba, kuma bata so wani ya wanke mata, shiyasa kullum gashin kanta a cukurkuɗe yake, gashi duk tafisu yawan gashi da cukowa, duk da kowa da yawan nasa,
jahad na zaune saman stool gaban mirror tana shafa cream ajikinta, sai ga saude tashigo da sallama, da fara'a a face ɗinta tace "wow masha Allah, tubarkallah wannan dogon gashin fa kamar na larabawa," tayi maganar tana kallon sumar kan jahad wadda ta zubo mata har wurin waist ɗinta,
Cikin jin kunya jahad ta sunnar dakai, saude taci gaba da cewa "duk da nake bafullatana, nima ina da gashi amma bai kai ko rabin naki ba, ke wata ƙabila ce ? Jahad tace "BUXUWA,"
Saude tace "No wonder, shiyasan ya, hakan na nufin cewa ku ƴan niger ne ko?
"Mahaifiyar mu buzuwa ce ƴar niger, amma mahaifin mu bafullatani ne ɗan nan,"
saude tace "Wow wow!, haba ! ae dole kyau ya haɗu a wurin nan, dole kuyi kyau yara," murmushi kawai jahad ke saki, ganin yadda saude ke zuzuta su duk da itama ɗin kyakkyawa ce,
Wuce wa ciki saude tayi ta buɗe wardrobe ɗinta, riguna ta ɗauko musu dogaye sun sha guga ninkakku, ta ajiye musu asaman gadon sannan tace "Gashi nan kusanya rigunana ne, duk da nasan sunyi muku tsayi sosai,"
"Mungode sosai aunty, Allah yasaka da alkairi," saude tace "mention not pls," sannan tafice don tabasu damar wataya wa,
"Jahad kinji yadda iska ke shiga jikina, ga wani ƙamshi dake fitowa sako da lungu na hammata ta," hosana ce tayi maganar wadda fitowarta kenan daga toilet ɗin,
A lokacin jahad ta kammala sanya doguwar rigar da saude ta fiddo masu, na materials ne pink colour masu kyalkyali, ba karamin kyau su kayi mata ba, cikin 6acin rai take kallon hosana
"Meyasa wai baki da hankali ne, ke shashashar ina ce? Ba sai da nace miki ki wanke sumar kanki ba,"? ta tambaya a ƙule tana kallon hosanar,
Da buɗar bakinta sai cewa tayi "Gashina ne ko Gashin ki"? Shiru jahad tayi don tasan ynx zata tada rigima har ajisu,
"Gashin ki ne hosana, zo kisanya kaya gashi nan aunty ta fiddo mana mu sanya," wuto wa tayi daure itama da towel ajikinta, ta zura rigar materials ɗin, tayi kyau amma gashin kanta sai uban wari ya ke yi, babu yadda jahad ta iya da ita, bayan sun kammala shiryawa, atare suka haye saman gadon suna facing ceilling, "what are u thinking about jahad"? Hosana ce ta tambaye ta, cikin sanyin murya jahad tace "SEHRISH, ke fa me kike tunani? Murmushi hosana tayi kafin tace "Wannan kyakkyawan mutumin, mai ƙarfi wanda ya ceto rayuwarmu daga shiga haɗari, daga na rufe eyes ɗina shi nake gani, lokacin da na faɗa jikinsa, bakiji ƙamshi ba wlh ya haɗu" 😇
Jahad tace "shegiya ashe kina cikin hayyacin," 😂 dariya su kayi gaba ɗayansu

......................SEHRISH.....................

Ta gyara komai tsaf na bedroom ɗinsa, tsayawa tayi tana kallon hoton dake jingine saman side drawer ɗinsa bayan bedside lamp, hannu takai ta ɗauki hoton tana kallo, wata mata ce acikin hoton fara tas baturiya, mai kyan gaske kai kace itace tayi kanta don kyau, jikinta sanye da uniform ɗin na sojoji, kakin ba ƙaramin kyau su kayi mata ba, tsaye take tayi saluting a cikin hoton, bin sumar kanta sehrish tayi da kallo, launin gashin matar yayi yellow mai tsayin gaske, kwayar idonta kuma blue colour ce, wannan ba kowa bace face*Alexandra* Ummu Rafayet, ummun Ayan da jahan kuma ummun micheal(makel) da ROMEO 💞

Murmushi sehrish tasaki matar ta burgeta, duk da batasan kowacece ba amma kamannin fuskarta sak irin na Babban yayansu, akwai kyau, daga ganinta wayayyiya ce ajin farko,"
Hannu sehrish tasanya tare da shafa hoton a fili tace "kowacece wannan matar amma ta haɗu kuma ta burge ni, gashi tana kama da Babban yaya sosae," ta karasa maganar tare da mayar da hoton inda yake ta ajiyesa,
Sannan ta tura kopar toilet ɗinsa ta shige 😯 uhmmm hmmmmmm, tsayawa sehrish tayi tana tunanin anya ba kuskure tayi ba, wannan ae ba toilet bane, jimmmm tayi tana ƙarewa toilet ɗin kallo, lokaci guda ta dabarbace saboda haɗuwarsa, an raba shi biyu 6angaren toilet da kuma na bathroom wurin wanka kenan, ba ƙaramin girmane dashi ba, kamar a mafarki take bin komai da kallo, shiga ciki tayi ƙamshin wurin na dakar hancinta,
ba komai yaja hankalinta ba face wurin wankansa, wato irin standing jacuzzi ɗin nan ne (kwamin wanka), wande ke zagaye cikin glass, sakin baki sehrish tayi galala tana kallon ikon Allah, mayar da eyes ɗinta tayi kan bathroom cabinet ɗinsa, jerun wasu matsiyatan Shampoo ne, mayuka iri iri masu kyau da tsadar gaske, duk na gyaran jiki ko mace albarka wannan,
Jinjina kai kawai sehrish ke yi, haɗaɗɗen mirror ɗin dake cikin toilet ɗin mai girman gaske, ga wash basin agabansa, mai ɗauke da taps biyu na ruwa, daga gefe kuwa soap dispenser ce, gashi an ƙawata shi da vase a ajiye ƙasa, (Tukunyar flowers)

Zuƙunnawa sehrish tayi ƙasan hadaɗɗen tiles ɗim mai walkiya, ta zabga tagumi, aranta tana mamakin cewa wai nan toilet ne ? Idan har nan toilet ne to mukuma irin namu toilet ɗin ya sunan shi ? (Nace ba kewaye ko ki ce banɗaki) 😂

ta jima tana shirita, domin ba abun da ke buƙatar gyara a toilet ɗinsa, komai tsaf, kallo kawai ta tsaya yi daga bisani ta ɗanyi goge goge kawae ,
Fitowa sehrish tayi ta sauko down tana ko zata ganshi, basa nan ba kowa duk sun fita,
Wuce wa nata room ɗin tayi, tayo wanka, ta fito ta zura riga ta maza dai dai guiwa, ta zauna gefen gadon tana tunanin duniya, kallon sama tayi tana cewa "Oh ni yanzu wata rana nima zanyi saurayi, har nayi aure na haifi ƴa'ƴa,? When ? Ina so nima nayi shiga irin ta mata, na wataya nayi rayuwar ƴanci yaushen hakan zata faru ? 😥
Ajiyar xuciya tasaki tana tunane tunane,
Kwankwasa kopan akayi, cikin sauri tace" wanene? Azmee tace "wa kika sani yake zuwa ɗakin ki in ba ni ba,"?
Murmushi Sehrish ta saki tare da miƙewa ta buɗe mata kopan, sanye take da hijabi milk colour hannunta riƙe da Cazbaha, da murmushi a fuskarta tace "ƙanwata ina fata dae ba zaune kike hakanan ba kina tunane tunanen duniya? karfa ace bakiyin zikri? Ba istigfari da sauransu?
Sunnar da kai sehrish tayi, don kuwa batayi, ae tun ran da tasanya SGR a idonta, ta rage duk wani abu da take yi,
"Hmmm dama raina ya bani, gsky zamuyi faɗa dake muddin baxaki, daina zama hakannan ba kina sa damuwa aranki ba,
"Insha Allah aunty azmee zan rinƙa ƴi," jinjina kai azmee tayi kafin tace "Albishirin ki,"?
Cikin mamaki sehrish tace "Goro,"
Azmee tace " an bani sabuwar waya nabaki,"
Ɗan zaro ido sehrish tayi cikin mamaki tace "Who"? Murmushi azmee tayi tare da cewa, " i will let u know but not now, yanzu dae da anjima bayan magrib kina da baƙo,"
Waro ido sehrish tayi tare da cewa "baƙo kuma aunty azmee ? wurin wa zai zo? Tayi maganar cikin ruɗu,
Azmee ta dafa kafadarta tare da cewa "bakowa bane , fa ce wanda nace miki, yasan cewa ke maca ce !! yau zaku haɗu, na shirya muku haɗuwa a Garden, ki same shi immediately after magrib prayer,"
Murmushi sehrish tasaki tana jujjuya ido, ta ɗan jinjina kai kafin tace "shikenan aunty azmee Allah yasa naga alkairi," yanayin yarda tayi maganar taba azmee dariya,
"Ni zan wuce, maganar wayarki kuma, sai zuwa gobe zan baki ita, salon kuma in ga yarinya ta buɗe tiktok ko insta don na lura kan ƙanwar tawa rawa yake yi," ta ƙarasa maganar cikin zolaya da dariya a face ɗinta,
Itama sehrish dariyar take yi, duk da batasan menene tiktok da insta ɗinba, sunan kawai ta ta6a ji ana faɗa," .
Bayan azmee ta fita, sehrish ta daka wani uban tsalle sai saman gadonta, tsananin murna ne ya bayyana a fuskarta, rawa ta dinga yi tana tsalle tsalle asaman gadon jin an mallaka mata waya, gashi kuma zata haɗu da wanda yasan cewa ita maca ce acikin gidan, addu'a take yi Allah yasa koma wanene acikinsu yakasance mai sauƙin kai kamar hafsat bature,

😇😂

Yini tayi tana zullumi acikin ranta,wanene wannan dayasan cewa ita maca ce ba namiji ba, wayyo Allah yasa junaid ne don yafi su sauƙin kai, ko ba komai wannan wani mataki ne nasara arayuwata, ga kyautar waya kuma an bani, wayyo daɗi bisa daɗi yanzu ya'azayi na rinƙa waya da ƴan uwana? ta faɗi jiki a mace,.
Zama tayi saman gadon ta janyo pillow tare da rungumesa jiki amace, taso ace lokacin da zata riƙe waya, ta rinƙa samun su Hosana da jahad, amma kash tun time ɗin da junaid ke ara mata wayarsa, ta daina jin ɗuriyarsu kullum switch off, sehrish ta jima tana tunanin menene yasa ba'a samun wayar tsohuwa ne ? What's happening wit them?


💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞
..............AMANI........................
tunda taji dirar motoci acikin gidanta, kuma dama Cg abbas ya sanar da ita cewa, Rafayet yace masa zai zo gidansa ya kawo masa ziyara, hakan yasa sai faman rawar kai take yi, shiri na musamman tayi, ta ɗauki wankar less maroon colour wanda akayiwa ado da stones doguwar riga ce tabi shape ɗin jikinta, ko mayafi bata sanya ba, ta zubo da gashin kanta har gadon bayanta, dama fa akwai kyau abun saiya bada Citta, kai kace ba matar aure ba, ƙanin miji zai zo an dage ana ta zabga uwar kwalliya,"
fitow tayi daga bedroom ɗinta, tana saukowa daga saman stair, cikin tafiyar rangwaɗa da yanga, dama legs ɗinta nasanye cikin highheels launin kayanta, ta fito fess abunta Balarabiya
Ƙamshin turarenta ya gama gauraye falon, tunkan ta idasa isowa ta zuba mishi ido yana a zaune saman 3 seater, ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana daddana wayar hannunsa cikin natsuwa,
gaba ɗaya ya tafi da imanin Amani, saboda tagaza janye eyes ɗinta daga nashi, daker ta iya samun natsuwa har tace mashi "sannu da zuwa Babban yaya, ashe kaine nayi mamaki wlh, ban ta6a tunanin zan ganka ba agidan namu," tayi maganar tare da samun wuri itama tazauna suna facing ɗin juna,
Ya jima bai bata amsa ba, kusan 5 minutes sannan yace "Yawwa ya nasame ku,"?
Cikin kashe murya tace "lfy lou Alhamdulillah,' .
shiru su kayi ba magana aranta tace "tabɗijan can ! Wai dama haka yake da miskilanci? Ko kallo babu balle magana,'? ta tambayi kanta acikin zuciyarta,




Just managed ba editing,

~HafsatBatureBossLady~

In kina so ki gode mun kiyimun share na novel ɗina, shine first novel ɗina don haka ayimun share ɗinsa ko'ina 🪄🤗

*Page 77-76*




*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*


*🪄Hafsat Bature Moh'd Boss Lady*🪄


~page 77-78~



*❤‍🔥Extraodinary Love❤‍🔥*

(Don't forget to share it everywhere) 🪩

Miƙewa tayi tare da cewa"Bari na kawo maka snacks da abunsha,"
dakatar da ita yayi da hannunsa yace"No need thanks"
Murmushi ta ɗan yi tare da komawa ta zauna, tana ci gaba da kallon fuskarshi, kafin ta mayar da idonta kan surar jikinsa tana haɗiyar yawu,
"Banason Kallo," ya faɗi yana ci gaba da dannar wayarsa, cikin jin kunya Amani ta janye idonta, tana mai mamakin taya akai haryasan tana kallonsa,
Cikin kashe murya tace " Babban yaya ae dole na kalle ka, kai fa abun kallo ne, kuma ni ban ta6a ganinka ba ido da ido, shiyasan ya,' ta ƙare maganar tana cizon pink lips ɗinta alamar ya cije ta,
shi kuwa ba ta ita yake ba, burinsa yayansa Abbas ya ƙaraso, su ga juna, yayi kewarsu sosai,
Muryarta ce ta ƙara ratsa shi "Babban yaya, ko dae baka farin ciki dani ne amatsayina na matar yayanku ishaq,'? ta yi maganar tana kallonsa,
"Why'? ya tambaya har time ɗin bai ɗago ya kalleta ba, gyara zama tayi tare da cewa "to naga u don't even want to look at me, atlease u should put ur eyes inside mine,"
Amani ba ƙaramin takura masa tayi ba, ji yake tamkar ya tashi yabar gidan, don baisan nacin magana,
"Plsss babban yaya,"
dogon tsoki yaja tare da cewa "becareful with me," gabanta ne taji ya faɗi jin gargaɗin da yayi mata, tabbas mace bata gabansa,
Jiki a mace Amani tabar falon, cikin bedroom ɗinta ta koma, jiki na rawa ta ɗauki phone ɗinta dake ajiye asaman pillow ta dannawa AUNTY BABBA kira,
Ringing 3 ta ɗaga kiran bayan sun gama gaisawa cikin zumuɗi Amani tace "Aunty ko kinsa cewa SGR na cikin gidan nan yanzu haka? tayi maganar da murmushi a face ɗinta,
A can 6angaren kuwa cike da mamaki aunty babba tace "Are you serious? shi da kansa kuma"?
dariya Amani tayi tare da cewa "wlh kam,baki ji yadda naji ba dana gansa duk da rashin maganarsa, yaci ka ji dakai wlh,"
Aunty babba ta fashe da dariya ta cikin wayar tare da cewa "ki barshi zai zo hannu ne yanzu dai ya maganar Ziyartar wurin bokan nan baba ibliss? kin sama mana kuɗin?
Ajiyar zuciya amani tasaki tare da cewa "tukunna dae auntyna, ina nan ina tarairayarsa, ina so nabi komai a sannu, insha Allah nan ba da jimawa ba, zaki ji daga gare ni, da kaina ma zanzo kd na kawo miki ziyara,"
Aunty babba tace "To shikenan, Allah ya kaimu lpy, shiri na musamman zamuyi, domin ganin munci nasara akan waɗannan zafafan guda biyu,"
sun jima suna waya a tsakaninsu, agame da yarda zasu ziyarcin wurin hatsabibin bokan nan Baba iblisssss 👹
A can ciki kuwa, dirar Abbas kenan fuskar nan dauke da fara'a kamar gonar auduga jin cewa Sgr ya kawo masa ziyara da kansa, sanye yake cikin kakinsa na sojoji daga headquater yake,
yana shiga falon Rafayet ya miƙe fuska a sake suka rungume juna sosae, kamar karya sake shi haka Abbas ya ji,
"Am really glad to see u bros, nayi kewarku sosae kamar kamar me," abbas ya faɗi hakan cikin tsananin farin ciki, ruƙo hannunsa yayi suka zauna a mazauni ɗaya, suna kallon juna cike da kewa,
Cikin sanyin murya babban yaya yace"Nayi kewarku sosae, har ma bazan iya faɗa ba,"
ƴar dariya abbas yayi tare da cewa "Wake koya maka hausa ne? nayi mamakin jinta raɗau abakin ka duk da har yanzu da sauranka, last time da kazo daker kake fahimta in anyi magana,"
Jinjina kai Babban yayan yayi tare da cewa " bana so nazo ƙasar nan ne arinƙa gulmata bana ji, that's why na dage na koya saboda su Ammi,"
Dariya abbas yayi sosae jin abunda Rafayet yace, a wasa wasa shima ya iya zolaya in yaso , bayan abbas ya tsagaita da dariyar ne yace "Am wai baku gaisa da Amani ba? naga ko abunsha ma bata kawo maka ba,"
"No tazo mun gaisa, ni nace bana son komai shiyasa,"
Jinjina kai Abbas yayi tare da cewa "meyasa baka son shan abu ko cin abu in kazo gidan mutanene nifa ɗan uwanka ne jinin ka, shikenan nima duk ranar da kayi aure nazo gidan ka, matarka tayi mun tayin abinci bazan ci ba,"
wani kallo babban yayan yayi masa tare da ɗan ta6e baki kafin yace "NEVER," wato bashi ba aure har abada,
Murmushi abbas yayi yana kallonsa yace "hmmm haka dayawa irinka suke cewa but at the end sai ga lamarin ya sauya, irin ku ma mace tafi juya ku, sannan maza irinku da basa ra'ayin mata ko aure wlh basu iya faɗawa tarkon so ba, haukace wa suke yi idonsu ya makance lokaci guda," .
Abbas ya ƙare maganar da zolaya yana kallon fuskar Sgr, wanda ya tamke fuska yana sauraran bayanin yayan nasa," .
Miƙe wa yayi tare da cewa "Ni zan wuce,"
"Haba Babban yayansu, nasan magana tace tayi hurting ɗinka am sorry 4 that, it was a joke,"
Abbas ya faɗi tare da miƙewa shima ya ruko hannunsa cikin lallami,'
"Ba abunda kake tunani bane yaya abbas, time ɗin tafiyana ne yayi, saboda ko wane lokaci na rayuwata yana da amfani, kuma a ƙirge yake"
Murmushi abbas ya saki yana jinjina kai yace "kuma fa hakane, na tuna da wannan, ae nama gode ssae da ziyarar da ka kawomin, Allah yabar zumunci," ya faɗi hakan a yayin da ya matsa suka sake hugging junansu, sannan su kayi sallama,
........................SEHRISH............................
Bayan sallar La'asar wuraren ƙarfe 5 na yamma, suna kitchen ana ta faman girke girken abincin dinner, ƙamshi ya gauraye ko'ina,
tana tsaye tana yayyanka kayan lambu a saman chopping board, fuskar nan a washe abubuwa biyu na mata yawo aranta, na farko shine wanene wannan wanda xata haɗu dashi yau a garden wanda yasan cewa ita maca ce, na biyu kuma shine new phone ɗin da aunty azmee tace an bata kyauta, bakomai take ɗauki da wayarnan ba fa ce shegen son kallon fina finai dake gare ta, ga son sauraron music gata mayyar selfy kamar hafsat bature 😇
"Ji mana, ki dubamin girkin nan , ynx zanje na dawo," azmee ce tayi maganar a yayin da take fi ce daga kitchen, ..
Cikin sauri sehrish tace "To aunty azmee,"
Ajiyar zuciya tasaki tare da cewa "ko ƙarfe nawa yanzu i ave to check the time, ina da baƙo fa," ta faɗi cikin zumuɗi tana kallon agogon dake manna a bagon kitchen ɗin, shida saura murmushi tasaki tana faɗin "lokacin haɗuwa ya kusa Ya Allah ka bani ƙwarin guiwar tunkarar koma wanene wanna,"
ta faɗi tana nuni da knife ɗin da ke hannunta,
Azmee kuma da ta fice bedroom ɗin junaid ta wuce, domin ta ƙara tunasar dani haɗuwar da ta shirya musu da sehrish,"
Sai faman knocking take yi, amma sam baiji ta ba, yana tsaye riƙe da ƙugu gaban closet ɗinsa ya buɗe yana kallon jerin kayansa, yama rasa wanne zai sanya domin haɗuwa da sehrish ɗinsa for the first time, sai zabga murmushi yake yi ba magana, tun da azmee ta sanar mishi da haɗuwarsa da sehrish yarasa tsaye ya rasa zaune, sai rawar kai da zumuɗi yake, kamar sabon ango 😌
daga shi sai short ajikinsa, sai da azmee ta ɗaga murya da cewa "Junaid ka buɗe aunty azmee ce inason magana da kai,"
Ae yana shaida muryarta a kunnansa jiki na rawa, yayi hanzari zuwa ya buɗe mata kopan, yana sakar mata murmushi,
"Ango kasha ƙamshi," azmee ta faɗi cikin zolaya,
"Ka ce ka shirya haɗuwa da amaryar taka kenan,"?
Cikin ɗan jin kunya yace "Kai aunty azmee, nifa kunya nake ji,"
DOWNLOAD
DOWNLOAD

6 Comments On ABBAN SOJOJI
avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
muhammad-4-3-8

6 months ago

Reply

I want it

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
husaini

2 months ago

Reply

I love this novel

Please Login or Register in order to submit comment