Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

laifi suna da kyau,"
A fili kuma ta daka musu tsawa har sai da suka firgita Hosana ta ƙanƙame jahad don batason sauti mai ƙarfi,
"GET UP !!!! Maza a tasarmun daga gado na, ku sauko Mun haka nan ankawo mana mutane tsintattu cikin gida,' tayi maganar tana yi musu alama da hannu na su sauko,
Jiki na rawa suka miƙe tare da saukowa daga saman gadon jikinsu na rawar ɗari saboda sanyin A.c ne ya haɗu da sanyin ruwan da Hafsat ta watsa musu,
Tsayawa su kayi a tsananin tsorace suna faman shessheƙar kuka,
Tsoki aunty babba tayi tare da cewa "ku biyo ni,"

Bin bayanta su kayi ta fuce dasu daga ɗakin, sunyi mamakin ganin suna ta faman tafiya acikin wata Corner na gidan,

Adai dai ƙopan wani Room ta tsayar dasu, hannu tasa ta riƙe handle ɗin kopar tare da buɗewa tace "To ƴan matan mama ga fa makwancin ku daga yau,'
Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba domin kuwa, wani tsohon store ne na ajiyar kayan abinci, tarkace ne kamar hauka, jarkoki da galon aciki na manja dana mai da akai amfani dasu awargaje, Sun tsufa sunyi ƙura, ga buhun hunan Shinkafa dana gero dana fulawa duk gasunan, ƙasa kuwa sunkin doyoyoyi ne ajere da dankalin hausa dana turawa, da gunduwa gunduwar Albasa, babban tashin hankalin ɗakin ko fanka babu duk ƙura ga yanar girgizo har jikin bango, ga ƙwari kuma a ƙasan suna shawagi, Ga manyan drawers waɗan da ke a datse jikin bango da alama na ajiyar tarkace ne,'

"Uban me kuka tsaya kuna kallo kushi ga mana! Ko saina shigar daku ne !?
Basu yi mata musu ba jahad ta ruƙe hannun hosana suka shiga cikin store ɗin sannan aunty babba ta ƙara da cewa "daga yanzu nan ne wurin kwanan ku Kuma wurin zamanku, saboda baku da gurbi acikin gidan nan,"
ta faɗi hakan tare da turo kopan kuma tasanya Key ɗin dake ajiki tayi Locking ɗinta, ba damar fita kenan, ko taya mutun zai iya kwakkwaran Numfashi a ɗakin nan !? 😰

____________________________________________*ABBAN SOJOJI*
*Story by Hafsat Bature*
*BossLady*💞💞💞

Around 12 Abban su ya dawo cikin gidan time ɗin duk sunyi bacci, bai wuce ɗakinsa ba sai da ya fara zuwa part ɗin Marshal Omar domin yaga ɗansa kafin ya wuce nasa ɗakin, lokacin daya tura kopan part ɗinsa shima nashi sak irin na Sgr ne, akwai hamshaƙin ƙayataccen palor aciki sai bedroom aciki,
Wuce wa bedroom ɗinsa yayi ya shiga Ciki samun shi yayi saman shimfiɗeɗen gadonsa ya lullu6e da lallausan blanket ɗinsa,
Murmushi Abbansu yayi tare da cewa "Yawwa haka nakeso my son asha bacci lafiya," juyawa yayi zai fita Muryar Omar ta ratsa shi da cewa "Abbana idona biyu fa, i ave told u that i wll be waiting to ave ur hug, that's why i stayed awake,'
Omar ne yayi maganar a yayin da yasanya hannunsa yana janye Bargonsa ya miƙe zaune da murmushi a face ɗinsa,"
Ƙarasawa Abban yayi Omar ya tashi tsaye suka rungume juna ssae,
"Nayi missing ɗin Tiger ɗina ssae, " ya faɗi yana bubbuga bayansa, Omar yace "Abbana nima haka, ina fata nasame ka lpy,"
"Lpy lou Alhamdulillah Omar," ya yi maganar tare da janye jikinsa daga na Omar yana cewa "Ka koma ka kwanta Omar nima zan wuce ɗaki ynx,"
"Shikenan Abba, Mu tashi lpy,"
Sallama su kayi abban ya fice, kwanciya Omar yayi amma yana jin there's something missing a heart ɗinsa tabbas akwai wanda baisa a idonsa ba, tun da ya dawo cikin gidan ba kowa bane face "Junaid," ya bari ne kawai sae gobe ya neme shi su gaisa cos yyi missing ɗinshi,"

Sehrish fa sam ta gaza runtse eyes ɗinta tayi bacci, duk ta takure kanta ta tsani jikin ta, ta6awar da haroon yayi mata ji take tamkar raping ɗinta yayi, tana saman gadon daga kwance ta tashi zaune tsakiyar gadon, ta matse kanta baiwar Allah,

___________________________/___/
Time ɗin da Abban su ya shiga ɗakinsa, yayi tunanin zai ga junaid a kwance yana sharar bacci, amma sai yaga wayam daga blanket sai pillow asaman gadon, abun ya ɗaure masa kansa, aransa ya ce "meyasa Junaid bai zo ya kwanta bane wai, ko dae yana a bedroom ɗinsa bara dae na canza kaya naje na duba sa,"
Shaf shaf ya cire kakin dake jikinsa, ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito ya zura jallabiya fara, sannan ya fice daga room ɗinsa izuwa na junaid dake a upstairs,
Yana isa ya tura kopan ɗakinsa abun mamaki babu junaid babu alamarsa, har toilet ɗinsa ya duba babu Shi saboda tsabar ruɗu har cikin Laundry basket ɗinsa ya duba da cikin Wardrobe ɗinsa don yaga ko ya 6uya aciki 😂
Amma babu shi, aikuwa hankali atashe abban su ya fito ya wuce part ɗin sgr, ya shiga har ɗakinsa ya bubbuga masa jikin ƙoparsa,
Sgr dake kwance natse saman gadonsa yaji knocing ɗin da abban ke masa,
Janye bargon jikinsa yayi, sannan ya tashi zaune yana kallon Abban nasu daker yake buɗe Eyes ɗinsa saboda bacci,
A sanyaye yace "Abba me ya faru ne? Kai ne da kanka?
"Ina fa lafiya babu junaid fa acikin gidan nan"! Jin hakan yasa sgr yin saurin haurowa ya sauko daga saman gadon, jikinsa na sanye da night dress riga ce dai dai guiwarsa ta tsaya babu dogon wando sai dai shorts acan ciki,
Cikin ruɗu yace "Abba kamarya? How za'ace junaid baya cikin gidan nan!!!? ya tmby yana kallon abban nasu dake a tsaye,
"Nima bansani ba, dawowa ta kenan, gsky akwai matsala,'
Fito wa su kayi atare shida abban suka bi sauran bedrooms ɗin sauran saboda su duba su gani ko ya kwana a ɗakin sauran saboda yana yin haka in rigimarshi ta tashi sai ya za6i inda yake so ya kwana ko ɗakin waye kuma dole abarsa ya kwanta,
Duk wanda akayi wa knocing ya buɗe daga yaji cewa Junaid ake nema sai kaga ya wartsake daga baccin da yake yi, hankalin kowa ya tashi matuƙa,
Gaba ɗayansu duk suka hallara a babban falon in ka cire Marshal saboda basu tashe shi ba tunda shi ranar ya dawo baisan wainar da ake toyawa ba Sai haroon,

Duk sukayi tsaye cirko cirko sai faman hammar bacci suke yi,
"A cikin ku wayasan inda Junaid yaje !!? Abban su ne ya tambaye su,
Kowa sai faman murxa ido yake yana hammar bacci,
Haɗa baki su kayi wurin cewa "Abban bamu San inda yake ba wlh,"
Tsawa sgr ya daka musu har sai da suka ɗan firgita yace "wannan wane irin shashanci ne ace junaid yabar gidan nan batare da kun sani ba har yakai wannan time ɗin a waje baku lura ba,!"?
Murya na rawa Su twins suka haɗa baki wurin cewa "Junaid fa baya zuwa ko'ina kowa yasani yana cikin gida kullum sai dae wani abun daban,"
"Nima a iya sani na kenan gsky akwai matsala* acewar fawan
Jabeer da Irfan suka ce "mun fa lura baya cikin gidan nan, amma gaba ɗayanmu munyi tunanin yana ɗakin Abba yana bacci shiyasa mukayi shiru,"
Bin su da kallo kawai sgr yake yi suma kallon shi suke yi suna kora bayani,
"Yakamata ajaraba kiran layinsa mana aji inda yake" acewar Khaleed, cikin sauri kanal yusif ya zaro wayarsa dake cikin aljihun wandon baccinsa,
Contact ya shiga ya dubo numbar junaid wadda yayi saving da *Last Born* Ya danna masa kira ta soma ringing,

Gaba ɗaya koya ya saurara yana jiran amsa kira daga junaid, 3 times tana ringing junaid bai ɗaga ba,
Hakan yasa kanal yusif yin amfani da wayarsa wurin duba location ɗin Inda wayar take,
Gaba ɗaya kowa na jiran tsammani, kanal yusif yace "kai ! Location ɗin fa ya nuna cewa wayar tana acikin gidan nan that means junaid yana acikin gidan kenan ko yabar wayar tashi a bedroom ɗinsa ne,

cikin hanzari su fawan suka haye upstars shi da su twins domin su duba ɗakin junaid koyana nan,
A tsiyace suka tura ƙopan ɗakin suka shiga cike da tsammanin ganinsa amma sai suka ga wayam, sae wayarsa dake ajiye saman Pillow bisa gadonsa, hakan na nufin gida yabarta,
Duk basu ji daɗin hakan ba, jiki amace suka sauko down ɗin har haɗa baki suke keyi wurin tambayar Su ina junaid ɗin ? Suka amsa musu da cewa basu ganshi ba sai dae wayar shi kawai,
"I know u will not see him cos i ave checked his bedroom already ya Ilahi," acewar Abbansu ya faɗi cikin tsananin damuwa,
Hankalin kowa fa ya tashi, bazaman lpy ba Romeo ba junaid ba last born, ba shagwa6a boy Ba dole kowa ya rasa natsuwa,
"nasan inda yake ni,"
Atare suka ɗago don suga wanene haroon ne wanda fitowarsa kenan daga shi sai gajeran wando ajikinsa,
Har haɗa baki suke yi wurin cewa "Yana Ina!?
"Abada cin hanci a ɗauko muku shi," kai kana ganinsa kasan yasha ya bugu idon nan sunyi jawur kamar na mujiya sai tangyaɗi yake yi,
Tsoki suka ja atare,
Abbansu ya daka mishi tsawa "Haroon kadaina mun wannan wasan kasan inda yake ne ko baka Sani ba _"!!!
Haroon yace "Billahil Azeemu na tsarance da rabbus sama'wati wal'ard nasan inda junaid yake, in ku kayi haƙuri kuka sa salama azuciyarku yanzun nan zan ɗauko muku shi,"

gaba ɗaya mamaki ne ya kamasu su kace shikenan "Muna jira,"

Juyawa haroon yayi ya nufi hanyar ɗakinsa yana faɗin "saboda wannan ɗan shilan duk kun bi kun tashe mutane Fil laili..........
Shigewa bedroom ɗinsa yayi yana ƙunƙuni,
Su kuwa zama su kayi suna ta faman jiran haroon ya fito musu da junaid,"
Jimmm kaɗan sai gashi ya fito hannun shi ruƙe da Pillow yana tangal tangal,
Zuba ido su kayi suna kallon ikon Allah, haroon na ƙarasowa ya shiga ƙoƙarin tu6e rigar pillown yana cewa "Yawwwa ynx zaku ga shegen ya faɗo daga cikin pillown ae nan cikin ya 6uya ja'irin,'
Rai a6ace har haɗa hannu suka yi Babban yaya da Abbansu suka sharara mashi zafafan maruka , daga shi har filon kowa yayi ƙasa baje,
Ihu haroon yasaki tare da cewa "Eeeeeeee !!!huuu!!!huuuu !!! waman ƙadarallahu haƙƙa ƙadrihi yanzu abba daga abun arxiki zan nuna muku inda junaid ya 6oye sai kawai naji saukar maruka? Yaron nan fa akan idona ya shige cikin rigar filon nan ya 6uya amma shikenan bakomai,'
Abun haushi abun takaici, banza kowa yayi dashi suka shiga tattauna yarda za'a yi a nemo junaid,
Kanal yusif yace "ina ga bari naje na sanarwa Azmee wata'ƙil tasan inda yake,
"A'a bana tunanin hakan, kwarama wannan mai aikin tukur raina yana bani cewa suna shiri sosai da junaid wata'ƙil shi yasan inda yake tunda kusan shine tsaransa," acewar Abban su

yace hakan ne saboda abunda yagani wato da Junaid yyai ma sehrish magana ƙasa ƙasa lokacin da suna Cin abinci dama abbansu shine ya lura da hakan,
Cikin sauri Fawan yace "Bari naje na tambayesa,'
Yakama hanya da sauri ya nufi wurin ɗakin azmee don yana da tabbacin ɗakin tukur yana kusa dana Azmeee
Sehrish na zaune idanu duk sun kumbura, taji bugun ƙopa da ƙarfi jiki na rawa tace "Wanene," a tsorace ta tambaya,
Muryar fawan taji yana faɗin "Fawan ne, Fito maza ina son magana da kai,"
Cikin sauri sehrish ta kimtsa ta mayar da gashin bakinta, ta gyara ɗaurin kanta,
Sannan ta taso ta buɗe ƙopan cike da mamakin ganin fawan tabbas kam akwai matsala,
"Gani," ta faɗi a raunane,
Fawan yace "Kana da masaniyar inda JUNAID ! Yaje !?
Zaro ido tayi gabanta na faɗuwa aranta tace "Ina junaid yaje har daren ne bai dawo ba ake nemansa,'
Cikin sauri tace "a'a gsky ban da masaniya akan hakan,"
"Ka tabbata'?
"Eh wlh," ta bashi amsa
jiki a mace fawan ya wuce izuwa falon,

Shigewa cikin ɗakin tayi gabanta na faɗuwa sai lokacin ta tuno da cewa ɗazu junaid ya sanar mata da cewa su haɗu a garden After magrib,
. "to kodai yana can ? May be ya jira ni ne yaji shiru banzo ba bacci ya kwashe shi Acan, kai anya kuwa !? taya ma zai zauna tun bayan magrib zaman jira na har yanzu kusan ƙarfe 1:00 na dare bai shigo ba, gsky bana tunanin hakan,
Haka sehrish ta rinƙa tunane tunane aranta, har ta samu wuri gefen gadon ta tazauna zuciyarta ta saƙa mata cewa "Junaid fa rigimamme ne zai iya yiyuwa yana can ya dage akan in banzo ba ba zai bar garden ɗin ba, kai gsky fa haka nake tunani hankali na bazae kwanta ba har sai naje na duba garden ɗin can, tana faɗin hakan ta miƙe .................................................

Wannan kenan 🙌

Keep sharing it everywhere pls 🙏

Boss Lady 💝


Masu son yi mun Comment ba hali ga Phone no ɗina Only message kuma mata kaɗai (08103884440)*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*

*🔥The Father Of Soldiers🔥*

*Na*

*Hafsat Bature Moh'd*

~BossLady~


🔔🔔🔔

_nataƙaita littafin Abban sojoji yanzu yakoma part one and part two only duk mun yawansa zai ƙare a part 2, namai dashi yanzu muna a part 1 sai ya kai 100 pages cuf, sannan part 2 zai shiga, sannan kuma yanzu free pages ne_💔👌


Page 94-95


a hankali ta buɗe kopan ta fito cikin sanɗa, gabanta ne ya faɗi da ta hango su gaba ɗaya sun hallara a babban palorn cikin tashin hankalin rashin junaid, har sun fara yanke sha'warar fara kiran friends ɗinsa da sauran ƴan uwa aji koya je can,
Dafe zuciya sehrish tayi tabbas kuwa in tabi ta entry ɗin main palor zasu tambaye ta jin ba'asin ina xataje, don haka tayi deciding ta canza hanya cos there's many doors acikin gidan da zaka iya fita compound ɗin gidan,
Ja da baya tayi a hankali dama slippers ne a ƙafarta marasa sauti, cikin sanɗa ta lallaba, ta miƙi doguwar hanyar da zata sada ta da backyard ɗin gidan,
Taci sa'a akwai Key ajikin ƙopan jikinta na kerma tasanya hannu ta murɗa key ɗin kopan ta buɗe, ahankali ta zura ƙafa ta fuce,
tsoranta kada security guard ɗin dake strolling acikin gidan su ganta a daren nan tana shawagi tabbas sai sun tuhume ta, gashi ko'ina na gidan Haske ne 6ayau kamar rana saboda fitilun kwan da aka ƙawata shi dasu masu hasken da kyan gaske kamar rana,
A hankali sehrish ke tafiya kamar 6arauniya, har Allah ya shigar da ita cikin garden ɗin kai tsaye wurin da garden chairs ɗin suke ta tunkara,
tunkan ta ƙarasa ta Hango mutun a ƙanƙame saman kujera ya kifa kansa saman table ɗin gabansa, gaba ɗaya jikinsa sai kermar sanyi yake na tashin hankali,
Zaro ido sehrish tayi cikin tsananin tashin hankali ta watsa aguje inda yake gabanta na faɗuwa, tabbas kuwa Junaid ne, dafe kanta tayi tare da cewa "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un !!! Nashiga Ukuna ! Junaid meyasa !!!!!
Cikin tashin hankali tayi maganar tuni hawaye sunzo mata shar a face ɗinta,
Matsawa tayi dab dashi tasa hannu ta bubbuga table ɗin dake gabansa murya a mace take ambaton sunan shi "Junaid...junaid...,'
Wani irin dogon numfashi yaja hatta yatsun hannayansa kerma suke yi, ko eyes ɗinsa bai iya buɗewa tabbas yaji Muryar sehrish amma sam yagaza bata amsa, so yake yayi mata magana taje ta sanar da wani daga cikin gidan yazo ya taimaka mishi ya tashi amma ya gaza, saboda sautin muryarsa baya fita, Lips ɗin ma nasa rawa suke yi kaf kaf,
Bin ziraran yatsun hannun shi tayi da kallo ganin suna kerma kaf ! kaf !! Hakan ya tabbatar mata da cewa Junaid idonshi biyu, sanyi ne yakamashi ssae,.
Cikin sauri sehrish ta cire mayafin da take naɗe gashin kanta dashi ta rufa ma junaid abayansa, duk da mayafin bai da wani kaurin da zai masa magani,
Zubewa tayi saman guiwarta agaban table ɗin, saitin fuskarshi dake kwance saman table ɗin tace "Junaid meyasa? Why pls? meyasa zaka cutar da kanka har haka? dan Allah ka buɗe idonka junaid, ka tashi mu tafi,'
Daker numfashinsa ke fita sam sehrish batayi tunanin tana 6ata lokaci ba wurin agaza masa,
So yake ya buɗe idonsa ya kalle ta amma sam ya gaza, sai kerma eye lids ɗinsa suke yi,
Hawaye ne kawae ke fita a idon Reesh, tana cikin wannan zuƙunnan karaf idonta suka sauka akan Hancinsa da Jini ke ɗigo wa,
Waro ido tayi waje a firgice ta fashe da kuka tare da faɗin "Junaidd...!!! innalallahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga ukuna Wayyo Allah !!!
A zabure ta miƙe ta juya da gudu don taje ta sanarwa Aunty azmee wata'ƙil ta taimaka wurin sanar dasu halin da Romeo yake ciki don azo ataimake shi karya mutu,
Har Tayi nisa da gudun nata muryar shi ta ratsa kunnan ta "Sehrishhhhhhhh," cikin wata irin matacciyar murya wadda ta galabaita yyi maganar,
A razane ta dakata tare da juyo tana kallon shi, samun shi tayi ya buɗe idonshi waɗanda suka rune jawur daker yake ƴunƙurin tayar da jikinsa da dukkan sauran ƙarfinsa,
Cikin tsananin tausayi sehrish ta koma da gudu wurinsa tana faɗin "junaid,' tashi yayi zaune yana fidda numfashi a hargitse muryarsa na rawa yace "ki taimaka mun numfashi na zai iya ɗauke wa, ki goyani ki kaini wurin Abbana,'
ɗan zaro ido tayi tana kallonsa can kuma tayi tunanin ae junaid bazaiyi nauyi ba, ba wani girman jiki gare shi ba, duka nawa yake
daddagewa sehrish tayi ta tsugunna masa tare da cewa "hau muje," daker junaid ya sauko ya faɗo bayanta tare da ƙanƙameta yana numfashi a sama sama,
Jigumm sehrish tayi saboda wani abu da taji ya yi mata yawo ajikinta,
"Ki tashi mana so kike na mutu ko," junaid ne yayi maganar daker cikin shagwa6a, bawan Allah,
Da iya ƙarfinta na ƙarshe, daker sehrish ta miƙe tana tangal tangal zata faɗi amma ta hana hakan, ta dake ta cije ta miƙi hanyar fita daga garden ɗin da junaid goye abayanta kamar wani ƙaramin yaro, ya lafe abayan sehrish ɗinsa, tana jin numfashinsa a gefen wuyanta saboda nan hancinsa yake, tana jin yarda junaid ya ƙanƙame mata stomach ɗinta saboda ta nan ya zagayo da hannayensa,
Cikin sa'a ta fuce dashi daga garden ɗin kuma ba wanda ya ganta har ta shige dashi cikin ƙopan da ta fito, yanzu tunaninta shine yarda za'ae ta haɗa junaid da ƴan uwansa batare da wani ya ganta ba, tsayawa tayi tana wannan tunanin aikuwa junaid ya fashe mata da kuka mai sautin gaske yana cewa "wai bazaki shiga dani ba so kike na mutu ko,' duk yarda sehrish taso ta hana junaid magana abun ya faskara sai ma ya ƙara sautin kukan wanda hakan ya janyo hankalin Mutanen gidan dake a falo,
. gaba ɗayansu sunji kukan junaid da muryarsa, har haɗa baki suke yi wurin cewa "Kai wannan ae kukan junaid ne !!,'
gaba ɗayansu suka nufi hanyar da suka jiyo muryar junaid yana kuka yana yima sehrish faɗa akan taƙi ta motsa takai shi ɗakinsu,
Jin takon takalmansu alaman sun tunkaro wurin yasa sehrish shiga tashin hankalin, gashi ta cire mayafinta, hular kanta ta karkace dogon gashin kanta duk ya barbazo waje, ae kuwa a firgice ta saki Junaid ya faɗi ƙasa tumm !tayi saurin zame mayafinta dake jikinsa, kamar aljana tayi Wuff ta boye a wani saƙo hannunta dafe da saitin zuciyarta,
Junaid kuwa ganin sehrish ta jefar dashi ƙasa ta gudu yasa shi ƙara sautin kukan nashi ya karaɗe ko'ina yadinga burgima a ƙasa yana faɗin "wayyo Allah na, ta jefar ni !! bazaki zo ki goyani ba ki maida ni wurin Abbana ba, Wlh saina tona miki asiri tunda kikai mun hakan.......' sam junaid fa baya cikin hayyacinsa yake waɗannan maganganun, sehrish kuwa saboda ruɗin abunda junaid yace, tuni futsari ya kufce mata ta cikin wandonta ya soma zuba zirrrrrrrrrr ! Mai zafin gaske cije le6enta tayi tare da runtse idanunta,

Isowa su kayi gaba ɗayansu sunyi mamakin ganin junaid baje a ƙasa yana burgima sai faman sambatu yakeyi yana faɗin "wlh saina tona miki asiri kowa ma yasani Allah,' cikin kuka da shagwa6a yake maganar,
Atare suka haɗa baki suna cewa "Junaid ! ina ka shiga muna ta nemanka? Kai da wanene ? Ta ina ka shigo,'
Jin muryoyinsu yasa shi dakatawa yana kallonsu idonshi biji biji sam bai gane su wanene akanshi,
Murya na kerma yace "ita ce ta shigo dani, ta goyani kuma ta jefar dani ƙasa ta boye acan wurin,' yayi maganar yana nuna inda sehrish ta 6oye,
Tuni temperature ɗin jikin sehrish ya ɗau wani irin mahaukacin zafi, nan take wani futsarin ya sake zubo mata na tashin hankali, tuni zufa ta gama wanko mata sharkaf wandon jikinta kuwa ya jiƙe sharr,
Babu abunda take furtawa Acikin zuciyarta fa ce "La'ila ha illah anta subhanaka inni kuntu minal Zalimin,'

Gaba ɗaya idonsu ya kai inda junaid ya nuna musu,
"Ah Wannan Fa aikin shaiɗanun aljanu ne kubarmin kawai A ya neh nayi maganin ƴan Iskan," acewar haroon
Yana maganar ya nufin wurin,
Sgr bai tsaya jin bayanansu ba, hannu kawai yasa ya ɗago junaid dake kwance, ya ɗauke sa kamar wani ƙaramin yaro ya aza shi a ƙafaɗarsa, ya juya batare da ce musu komai ba ya wuce dashi part ɗinsa,
Shi dae abbansu ajiyar zuciya kawai yake saki tunda Allah ya dawo masa da Baby junaid ɗinsa lafiya, kallon sauran yayi tare da cewa "Kowa yaje ya kwanta, koma mekenan gobe zamu duba,"
Juyawa su kayi gaba ɗayansu kowa na faman sauke ajiyar zuciya suka wuce rooms ɗinsu, ban da haroon wanda ke faman sakin murmushin mugunta, domin kuwa ya hango ƙafafun sehrish masu sanye da wannan slippers ɗin nata na ƴan gado,
Bayan kowa ya bar wurin, sehrish tayi tunanin ta lalla6a ta wuce ɗakinta, dama idonta na runtse a hankali ta buɗesu gaf taga fuskar haroon a kusa da tata, wage baki tayi zatayi Ihu yayi saurin sanya hannunsa ya toshe mata baki yana faɗin "Ƴar shila, ae dama nasan kece ja'ira, na hango waɗan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

6 Comments On ABBAN SOJOJI
avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
muhammad-4-3-8

6 months ago

Reply

I want it

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
husaini

2 months ago

Reply

I love this novel

Please Login or Register in order to submit comment