Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yayansu da marshal omar to ina mai tabbatar maki da cewa gabadaya zamu rinka juya kowa na family dinnan, sai yadda muka so za'ayi"
ta idasa magabar tana kallon Amani, wadda tayi tsuru tsuru,
ajiyar zuciyata tasaki har zatayi magana wayarta dake saman saman pillow ta soma ringing, da sauri takai hannu ta duba sunan "Babyna" ya bayyana
Aunty babba tace "halan Abbas ne ? Amani tace "eh shine,'
"Yawwa maza ki daga, ki rinka kashe masa murya kina masa ladabi ko mun ci nasara akan kudin da muke bukata,'
amani ta amsa da to, tare da picking call din ta kara a kunne tare fadin " baby na y kke? nayi kewarka sosae,"
Saurara wa tayi tana sauraran muryar abbas dake cewa "nagaza bacci ne, na fito daga wanka ne, naji ba abunda nake son ji face muryarki,"
Murmushi Amani tasaki tana kallon aunty babba data kura mata ido, cikin sanyin murya tace "nima haka babyna, ynx haka maganarka nake ma,'
"Are u serious ? Zamu yi video call ne inaso naganki cikin sleeping dress din nan naki, '
Kallon aunty babba tayi taji me zatace saboda wayar a handsfree take, da ido tayi mata alamar tace masa eh,
"Eh babyna a shirye nake , nima a kagare nake dana ganga, "
Murmushi aunty babba, tayi tare da mike wa ta fita daga dakin tana ji aranta cewa burinta zai cika,

Dare yayi sosai Junaid na dakin abbansu , ya addabe shi ya hana shi sakat, shi ala dole ga auta, suna kwance atare saman king size bed dinsa, junaid ya aza masa kafarsa a saman jikin abbannasu, zallar rigima yake ji,
"Junaid dan Allah ka barni na huta, ka tafi bedroom dinka ka kwanta mana, ko kaje Wurin yayyen ka kwana mana," abban nasu ne yayi maganar cikin jin bacci,'
cikin shagawaba yace "nafi jin dadin kwanciya ajikin ka abba, In kuma kana so nadaina zuwa kwana nan, tam ka je ka dawo da mommyn mu, "
rai a dan bace abban nasu yace " kada na sake ji ka kira min sunanta Allah,"
Cikin zolaya junaid yace "kaifa kace kana so Abba, ba wanda yayi maka dole, saboda dadin soyayya ko su Ammi basu sani ba kaje har us ka aurota, wato kaga kyakkyawa, doguwa fara mai dogon gashi ko ?
Yunkura wa abban yayi tare da fadin "bismillah" ya janyo pillow, ya shiga bugun junaid dashi, dama sun saba ya maida shi tamkar tsaransa, kuma Abban ba karamin dadin hakan yake ji ba, cikin kukan wasa junaid kecewa " Abba dan Allah kadaina ae gsky na fada, wlh momyn mu akwai kyau, shi ya rudaka ma,
Cikin mamaki abban yace "wai junaid ko dan muna kwana shimfida dayane yasa ka raina ni?
dariya suke gaba dayansu, duk yadda yaso junaid ya rufe bakinsa ya daina masa maganar Alexandra (Alekzandra) amma yakiya, dakyar bacci ya kwashe su, su duka,


Insha Allah za'a samu Lunch ko dinner, in Allah ya yarda amma ✨
*💋💋SURGEON GENERAL RAFAYET & MARSHAL OMAR💋💋*


*Welcome to Nigeria* 😍

*finally our Stars Sun bayyana* 😂


*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*


*ku kaddara cewa page 1 ne wannan domin kuwa yanzu labarin ya soma*



Page *57*


Writer *HAFSAT BATURE* ~BossLady~


Bayan ta kammala cin abunda azmee ta kawo mata kitchen ta mayar da kayan, sannan ta dawo ta shiga toilet ta daura Alwala, ta zura hija bi ta shiga jera salloli, bayan ta kammala ta rufe da zafafan addu'o'i tana nema ma rayuwarsu sauki, tasha kuka ayayin da ta daga hannunta sama tana rokon ubangiji, hawaye na gangarowa a idonta,
Ba ita ta kwanta ba sai cikin dare ya taba, sannan ta kwanta, tare da rungumo pillow a chest dinta kamar yadda ta saba, tabbas ranta na bata cewa Babban yaya bazai wuce gobe ba bai dawo ba, saboda taji wani sanyi aranta, amma bata da tabbacin hakan , sai in Allah ya kaimu da rai da lafiya sai kuma in hafsat bature ta so hakan, dayake wuka da nama suna hannunta, 😜😜😜
****************************************
Mutum biyu ne suka san da zuwan su Abba da junaid sbd sunyi receiving call dinsu in d midnight, a time din mu na nigeria jirginsu zaiyi landing around 9:00am,
A Wani irin haɗaɗɗen katafaren privet jet ne ya ɗauko su, wanda ya kasance mallakin Surgeon general RAFAYET, ya haɗu fiye da tunanin mai tunani, cikinsa bai da banbanci da hamshaqin parlour wanda yaji tsadaddun furnitures, saboda an ƙawata shi da jigunannun furnitures,
Wato Aljannar duniya ce, acikinsa ya ƙawatu, 👌
Wasu hamshaƙan leather seats ne acikinsa jigunannun gaske, wanda ko a ido ka kallesu kasan zasu yi tafshi da daɗin zama, masu numfashi irin waɗanda kana zama zasu lumbutse dakai ciki,
A jere suke biyu suna facing ɗin biyu zungura zungura, a tsakankaninsu wani ƙayataccen table ne haɗaɗɗen gaske, mai ɗauke da travel cups wanda abunsha ne acikinsu, tukunna ma shin su wanene acikin jirgin ? 😒
tunkan na fara zayyana su zan fara da faɗin tabarakallahu ahsanul khaliqin 😇
Haɗaɗɗiyar sura, dogaye ne masu cikakkiyar ƙira irin ta zakuna, irin ta mazan gaske sadaukai kuma jarumai, ƙerarrun gaske, duk inda namiji yakai to su sun zarce nan, komai nasu na kece raini ne ba wasa a tattare dasu babbar harka ne, duk iya haɗamar mace bazata wuce waɗannan handsome stylish guys ɗin ba, buri kowace ƴa mace nesu, a fage na kyau kuwa ba'a magana, ƙarshe ne su, a bangaren wadatar arziki kuwa basai an faɗa maka ba, kana ganin su kasan cewa sun wanku da pawns da dollars, fatar jikinsu kaɗai abun kallo ce, su huɗu ne zaune kowa ya hakimce, jirginsu kawai suke jira yayi landing,
3 daga cikinsu suna sanye cikin expensive dress na suits, biyu launin nasu blue ne ɗayan kuma black ne,
Mutun ɗaya ne baya sanye cikin suits ɗin nan, shin wanene shi? Jikinsa na sanye cikin V-neck shirt , tayi tighting ɗinsa, white colour yayin da yake sanye da army trouser,
Yana da wata irin sura mai matukar rikiɗarwa mai razanarwa mai matukar jan hankali da ƙayatarwa, saboda a halitta dogo ne, mai wani irin faffaɗan ƙirji a buɗe yake, ga wannan six pack din nasa baro baro, ya cika vest ɗin kana ganin zanen ƙirjinsa ga breast ɗinsa sunyi 6ul-6ul ata ciki kana hangensu, daga gani yana gym (motsa jiki) sosai, in ka kalli damtsen hannunsa sai ka tsorata, kana gani kasan cewa yana da matuƙar ƙarfi kamar ɗan wrestling (dambe) haka surarsa take, mutun ne mai ji da ƙarfi,
Idan muka je wurin tommy dinsa kuwa a shafe yake ba alamar tumbi ko kaɗan, yayi flat, tamkar baya zuba abinci acikinsa saboda ɗamewarsa,
Launin fatarsa fari ne sol irin hasken fatar ƴan korea, natural white kasancewarsa half cast (ruwa biyu) mahaifinsa hausa fulani, mahaifiyarsa baturiya, ya kuke ganin abun zai kasance?
A wurin kyau kuwa sai dai muce tubarkallah, domin Allah yayi sa da wani irin ƙayataccen kyau mai matuƙar razanarwa, ko namiji jinsin sa ya kallesa sai ya ƙyasa balle mace, yadda kasan shi ya zana kansa, don duk mun haɗamar bil'ama aka basa damar ya tsara yadda kyansa zai kasance, bazai wuce nasa ba sai dai ma ƙasa da nasa 😯
Komai na halittar jikinsa dogo ne, kakkarfa domin Allah ya wadatasa da duk wani abu da mace zata buƙata ajikin ɗa Namiji!
Idan muka koma kan haɗaɗɗiyar suman kansa kuwa mai tsayin gaske wadda ta sauko masa har saman kafadarsa , tasha gyara na musamman ya ɗaure ta, dark brown ce Allah kaɗai yasan nawa ake kashe ma wannan suman wurin gyara,
Hatta gaban forehead ɗinsa sumarce a kwance, ga wani kwantaccen saje mai shegen kyau, eye brows ɗinsa kuwa tamkar an zana ta, tayi wani irin shape ga gashi cike da ita, kiris ya rage jagirarsa su haɗe da juna saboda yawaitar suma a wurin, idan muka koma kan idonsa kuwa yana eyelid (kwarin ido) wadatacce wanda ke lullu6e da eyeballs ɗinsa, yana da dogayen eye lashes masu cukowa da tsari, ga kyan gaske
Allah yabasa kyawawan idanuwa ga girma ga su so sexy, farare tass tass masu ɗauke da kwayar ido, blue colour masu shining masu ɗaukar ido,
daga ƙasa kuwa dogon hancinsa ne, ba wai irin ziƙau ɗinnan ba, a'a mai tsari dai dai wa daida, daga nan kuwa sai pink lips ɗinsa tamkar ya shafa jan baki, ga skin din la66ansa irin mai squeeze ɗinnan ce,
Cikin natsuwa yake daddana laptop ɗin dake gabansa saman table, ƙirar Luvaglio wadda price ɗinta yakai $1 million ne (dala miliyan ɗaya) a naira kuwa yakai 600millions, miliyan ɗari shidda, cikin natsuwa yake daddana ta da zira ziran yatsunsa, hannunsa na sanye da wrist watch kirar piaget emperador temple ce, farashin ta yayi $3.5 million a naira kuwa ba'a magana billions ne ke magana,
Zan iya cewa duk macen da zata so shi ba don Allah bane, zai yi wuya asamu macen da zata so shi hakanan kawai ba don wani abu nasa ba, kamar kyansa, tarin dukiyarda shi kansa baisan adadinta ba, surar jikinsa ga kuma ilimin addini dana zamani, komai ya haɗa komai nasa is Extraordinary,
Basu kadai bane acikin jirgin akwai wasu gabza gabzan soldiers wadanda suke a matsayin security guards nasu, mostly dinsu black americans ne, ba wasa a tare dasu, basa ji basa gani umarni kawai suke jira su aiwatar 😳
Bakowa bane wannan face SURGEON GENERAL RAFAYET 😘 wanda kowa ke zumuɗin ganinsa, wanda hafsat bature da sehrish suke kwakwar ganinsa, tare da mamee da kuma readers😂

BABBAN YAYA wanda kowa ke shakkarsa ko sunansa aka ambata sai an girgiza, baya wasa da aikinsa, kaifi ɗaya ne,babu mai iya tankwara shi, sam mace bata gabansa a tsarin rayuwarsa baya da burin yin aure gaba ɗaya, cos bashi da interest akansu, mata bibiyarsa suke kamar hauka, ƴa'ƴan manya yayan shuwagabanni ya'yan sarakuna, amma ko kallo basu ishe shi ba, 😂
yadda yake kallon namiji haka yaje kallon mace ba banbanci, sam bai da shauƙin soyayya a tare dashi,
Tun saura 30 mins jet dinsu yayi landing , manyan motoci suka isa airport din jibga jibga na sojoji, baka jin komai sai tashin jiniya kamar ana yaki, a cikin motocin akwai na gayu tsadaddun gaske kirar mercedes benz da aka zo daukarsu da ita,
Time din da jirgin yayi landing, cikin isa kowannansu ya fito, yana saukowa daga matattakalar benen, a jere suka sauko gaba daya ido na akan Babban yaya tare da marshal omer, cika ido suke kamar kamar me, a bubbude suke tafiya irin tafiyar nigogin nan, wadanda suka ji karfi, shi marshal omar sam bai kai rafayet tsayi ba amma fa akwai kira ta mazajan gaske,
Masha Allah,
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
Su wa ke farin ciki da zuwan *BABBAN YAYA*😍
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
*page 57 to 58*

Ci gaban page 57 cikin nan


Not edited like always 👀

..............SEHRISH.........................................
Bacci take ta faman sha, hankalinta kwance batasan meke wakana ba, time din da azmi ta shigo ta same ta, tana ta sharar bacci bata yi yunkurin tashe ta ba, saboda tasan halin da yarinyar take ci, akwai damuwa atare da ita sosai, tana bukatar hutu brain dinta ma ta huta ko ta samu natsuwa, hakan yasa ta juya ta koma kitchen domin gudanar da aiki ita kadai, sbd dama an sallami su chef ummu ynx aiki ya rage daga ita sai sehrish,
Azmi bata gajiya da aiki, maca ce mara kyashi, in dai tana girki tana tazbihi a cikin zuciyarta shaf shaf take kammala komai, Ita a tsarinta ma bataso Sehrish na aiki, tafi so ta zama kamar yar masu gida saboda son da take yi ma yarinyar, tana jinta kamar yar cikinta, ❤
bayan ta kammala, da kanta tabi ta jera a dining, a hankali su ka fara fito wa, wadanda yunwa ta koro, lokaci guda duk suka hallara kowa ya zauna,
Abba na kusa da junaid dama suna atare, kanal yusif, da irfan da jabeer da khaleed duk suna a right hand yayin da suke facing din, Aunty azeema, Amani da aunty babba, sai bg Abuhaisam na kusa da Fawan, kowa sai zuba wa cikinsa yake a natse, mutun biyu ne ke basu hallara ba a dining din ba,
sai faman wurga ido junaid yake yaga ko zai ga fitowar sehrish amma babu alamarta, hakan yasa shi jin wani yanayi tsoransa kar ace bata da lpy, dago wa yayi ya saci kallon aunty Azmee dake saving dinsu daga tsaya, a hankali yake motsa lips dinsa yana tambayarta ina Sehrish ba tare da sauti ya fita ba,
Murmushi azmee ta saki tana dan kallonsa, da hannu tayi masa alamar cewa bacci take yi, lumshe idonsa yayi alamar jin dadi aransa, maida idonsa yayi akan Chips din dake gabansa cikin plate,
gyaran murya Aunty azeema tayi tare da cewa "uhm ana ta kulu wash rabu, su yusif ba baka sai kunne,"
murmushi kowannansu yayi, dan dagowa yusif yayi ya kalle ta cikin sanyayyiyar muryarsa yace "Aunty azmee bakyau ana da'amin ana magana," .
murmushi aunty azeema tayi tare da cewa"dadi na da yusif akwai hankali ga natsuwa komai nasa na bin ka'idar addini ne masha Allah,"
Abba yace "ae ina ji duk cikinsu shine ya biyo halin ummansu komai nata, hatta kyan fuskarsa in ka cire Marshal omar,"
"gsky abba ka tara kyawawan samari masu ilmin addini dana zamani ya kamata ace kowannan su iyanzu ya fidda matar aure tun da aun mallaki komai,"
Aunty babba ce tayi mgnr, wani irin kallo yusif yabi ta dashi sbd baison yaji ana masa maganar aure bama shi kadai ba hada bg Abuhaisam,
"Aunty babba matan ne basu da tabbas, mutun na bukatar tsawon lkc kafin ya fidda wadda ta dace da rayuwarsa, aure baya bukatar gaggawa kuma shi lokaci ne"
Bg abuhaisam ne ya bata amsa, jinjina kai tayi, yayin da yusif yace "you're right yaya haisam, we're waitin for the time, in yayi zamu yi ne,"
dan murmushi aunty babba tayi ita burinta tafara tunzura abba akan Babban yaya da marshal omar saboda abun yazo mata da sauki,
"mgnar ku gasky ne, amma abun da nake so ku sani, shi lokaci baya jira ! lokaci tafiya yake yi, this is the right time daya dace ace kunyi deciding akan sama ma kanku abokiyar rayuwa, its very hard to find a righteous partner in this situation of life, rufe ido kawai mutun zai yi ya canka,"
tayi mgnr tana kallon yusif dake facing dinta, kafin yusif ya bata amsa abba ya katse masa hanzarinsa da cewa "kwara ki fada musu, ynz ni ba abun kwatance bane a wurinku ? ina da 20yrs akayimun aure dayake na mallaki komai na rayuwa, in Allah ya baka dama ka damata alokacin daya dace, gashi ynz Allah ya albarkace ni da ya'ya da karfi na ban tsufa tukuf ba, naji dadin hakan sosai, ada ina jin haushin anyimun aure wuri, amma at the end naga amfanin abun,'
Jinjina kai su kayi kanal yusif yace "pls muna barar addu'arku aunty azeema aunty babba and aunty Amani atayamu da addu'a Allah ya bamu mata salihan mata na gari masu koyi da matan Annabi muhammad (S.A.W) Ba shaidanin zamani ba,"
Gaba dayansu suka amsa da (S.A.W.) kafin suka bi da ameen, suna dariya jin maganarsa ta karshe da yace shaidanin zamani,"
Junaid ya kalli abbansu tare da yin kasa kasa da murya yace "Nima abba atayani da addu'a mace tagari,"
Dariya su kayi gaba dayansu don sun ji shi, fawan yace kama cire batun aure a ranka, domin kai da yin aure sai nan da 20yrs lkcn ka kara hankali,"
Harara junaid ya watsa masa tare da cewa "Yanzun ma da hankali na, abunda dan shekara 30 zaiyi in an masa aure nima zan iya fiye da haka ......."
Bai ida maganar ba bg abuhaisam yayi masa dakuwa da hannu tare da cewa "gidanku ! Ja'iri ina maka kallon ustaz ashe kaima dan duniya ne,"
Abbansu ko murmushi kawai yake yi sbd yasan cewa sarai junaid yayi maganar ne batare da yasan me zasu fahimta ba su,
Aunty azeema tace "yaro ya girma abun sai addu'a'
Dariya su kayi gaba dayansu ,
Ba zato ba tsammani suna cikin wannan nishadin, kwatsam su kaji dirar motoci a tsiyace, ba kakkautawa da gudun gaske suke shigowa cikin gidan, lokaci guda jiniya ta karade ko'ina, hankalinsu ba karamin tashi yyi ba Abun kamar a filin Yaji,
Antayo wa suke ciki ajere suke kurdadowa,



Sehrish sai faman toshe kunnata take da pillow saboda jin tamkar za'a fasa mata kanta, ga nauyin bacci tana ji sam ta kasa kakkauran motsi ta tashi, jiniyar motocin dake shigowa har tsakiyar kwalwarta, sai faman matse ido take ta ciccije lebe,
Kamar daga sama taji sautin harbin bindiga mai karfin gaske kamar fashewar bomb haka taji, a wani irin firgice ta wuntsilo daga saman gadon izuwa kasa gefensa, daga ita har pillow kowa ya ware gefen, bargon ne kawai kankame a hannunta, gaba daya dukkan ilahirin jikinta rawa yake yi, sai faman zazzare ido take yi, tuni zufa ta soma wanke mata fuska, da karfi take breathing in har mutun sai natsuwa tsaf zaiji bugun zuciyarta,
Wani harbin da aka sake yi nan take ta fashe da kuka, sbd dama a tsorace take da mafarkin da tayi,
Acan ciki kuwa, lokacin da jiniyar motocin nan ta karade ko'ina nan take fawan ya saki cokalin dake hannunsa, idonsa akan junaid sbd yasan cewa sarai junaid yasan da zuwan bazatan da Babban yayan nasu yayi bai sanar dashi ba, su kam sauran musamman aunty azeema da Abban nasu su bg abuhaisam da su kanal yusif farin ciki a wurinsu ba'a magana, juyawa aunty babba tayi ta kalli Amani wadda itama kallonta take wani shu'umin murmushi suka sakarwa junansu jin wadanda suke hari sun karaso,

Su irfan da jabeer kuwa da khaleed kallon kallon suka shiga yiwa juna kowa na sauraran jiniyar motoci yayin da zuciyoyi ke beating

Duk ba wannan ba ina maganar su twins wadanda ke kwance kankame da juna suna cikin shan soyayya suka jiyo sautin nan, zuba wa juna ido su kayi ba tare da kiftawa ba, hankali a tashe Ayaan yace "Maganarka ta tabba jahan wlh shine ya dawo," shiru jahan yayi sam ya gaza cewa komai, gaba daya jikinsu ya gama mutuwa ,

Cikin sauri wasu gabza gabzan sojoji sanye da kaki ga manyan bindigu a hannunsu suka diro daga saman motarsu,
Cikin hanzari suka karasa tare da bude masu mota, fitowa marshal omar yayi yayin da babban yaya ya fito ta other side din, abun gwanin burgewa, haka suka bude wa major general tare da Captain adams motarsu wadda ke bayansu ta Omar, suma suka fito
With respect sojojin nan gaba dayan su suka buga kafa tare da sara musu abun sai wanda ya gani, mu da akayi a gabanmu 😍😂

Sehrish dake a tsorace jiki na rawa ta lallaba ta taso, daga ita sai yar shirt wadda takai mata dai dai guiwa, ba dogon wando jikinta, sai santala santalan kafafuwanta,
Jikin window ta karasa tasa hands dinta dake ta faman kerma ta janye labulen tare da zuge glass din windown, zuba ido tayi tana hangen Zugar sojojin dake a cikin gidan kai kace yaki ne ya taso,
A hankali take lumshe idonta tare da budesu tana kare wa mutanen dake wurin kallo, sam sojojin da sukayi masu kawanya basu bari tagansu ba,
Sai da soldiers din suka dare biyu tare da bude masu hanya sannan sehrish ta samu damar hangensu, Marshal omar ne a gaba sai Mg osman a bayansa sai Captain adams ne, a hankali take kallonsu a ranta tana fadin "wanene babban yaya acikinsu, inaji araina cewa tabbas shine ya dawo,"
Bata idasa tunaninta ba eye balls dinta suka sauka akanshi, kasancewar duk yafi su tsayi nesa ba kusa ba, Allah yayi mishi tsayi, sumar kansa ce tafara hangowa wadda ke kwance luf a bayansa da gefen forehead dinsa, zuciyarta ta dinga ji tana mata wani irin mugun bugu, bata da tabbacin cewa shine, amma ba karamin razana tayi ba da irin kyansa, duk da bata samu damar ganinsa da kyau ba, amma irinsu ko daga nesa ana shaida kyansu, kamar tauraro haka yazama acikin taurari 💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞💞
duk yadda sehrish taso ta kare ma wannan da ta hango daga nesa kallo hakan baiyu ba, bakomai take tunawa ba sai wannan hoton na cikin wayar junaid datake yawan gani, tabbas wannan shine na cikin wayar wato BABBAN YAYA,"
zuge glass din tayi tare da janyo curtains din ta rufe, murmushi kawai take sakarwa kanta tare da ajiyar zuciya at same time,
Tarasa ina zata sa kanta don farin ciki, sai faman sakin fara'a take kamar wacce aka ma Albishir da gidan Aljanna 😂
Tarasa tsaye tarasa zaune tarasa ina zata tsoma ranta, tsilli tsilli haka take yawo da yan kafafuwanta cikin room din nata,
A can ciki kuwa lokacin da suka shigo, hankalin Amani ba karamin tashi yayi ba ✨✨✨✨•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·
_Warning ❗❗❗ko da gigin wasa banyarda wani ya ta6amin littafine ba kamar canza wani sashe na labarin nan ba , ko haɗa document ko makamancinsu, in hakan ta faru kuma wlh mutun bazai ji da daɗi ba, duk inda yake a faɗin duniyar za'a samomin shi koda aljani ne ba mutun ba_😡


*page 59 to 60*




A can ciki kuwa lokacin da suka shigo, hankalin Amani ba karamin tashi yayi ba data fara cin karo da marshal omar, duk tabi ta zuzuce, a hankali tace ma aunty babba wadda ke kusa da ita a tsaye tace "Shine "? girgiza kai aunty babba tayi tare da cewa "wannan Shine marshal omar, ki zuba ido kawai bama saina fada maki gashi ba kina ganinsa zaki gane sa da kanki,"
tun kan Amani tace wani abu Babban yaya ya shigo cike da wannan tafiyar tashi ta Qasaita, wani irin bugu taji zuciyarta tayi juyawa tasake yi ta kalli aunty babba wadda idonta ke akansa ko kyaftawa basuyi,
Cikin tsantsar farin ciki kanal yusif yayi sauri zai hugging din omar, dakatar tashi omar yayi da cewa "bari na fara kwasar Albarka wurin Abbana tukunna," murmushi su kayi gaba dayansu especially Abban nasu, karasawa yayi tare da rungume abban nasu, so tightly hannu abban yasa yana bubbuga bayansa yace "I really really missed u my guys" omar yace "i missed u too my daddy,'
Mg osman kam wurin su Bg abuhaisam ya karasa suka shiga rungume juna ana ta faman gaishe gaishe, bayan omar ya gama da abbansu ya koma yana rungume sauran,
gaba daya idon abbansu ya koma kan Rafayet wadda ko kallo bai ishe su ba, kawai bedroom dinsa yake kokarin tunkara,
Cikin sauri bg abuhaisam yace "kai ina zuwa........? dakatar dashi abban yayi daga yi masa magana, kowa binsa da ido yayi,
Cikin sauri junaid ya shiga gabansa don ya riga sa isa sbd key din na hannunsa, can upstairs katafaren bedroom dinsa yake mai hade da palour, Aljannar duniya ce aka shimfida,
tunkan ya karaso Junaid ya bude masa, ya shige ciki, an kawata shi sosai sehrish ce zata fada mana ya haduwarsa yake, 😝
"Amma abba anya Rafayet bai fara shaye-shaye ba? Kalli yadda yabi ta gabanmu ko kallo babu, atlease ko kai ae ya kamata ya tsaya ya gaisar ko,"? abuhaisam ne yayi maganar ransa ya baci sosai,
Aunty azeema tace "kada ku damu indai rafayet ne dakansa zai fito,"
Zama su kayi a saman royal sofas din suna kara gaggaisawa da juna, hankalin Omar bai kwanta ba da yanayin abban nasu, kuma yasan duk akan babban yayan ne, ya kwalfa rai akansa yasaran daya shigo shi zai fara runguma amma sai yaga akasin hakan,
Aunty azmee ce ta shigo musu da abunsha itama da fara'a a fuskarta, tabi su tana musu sannu da zuwa, tare da mika musu abun sha,
Cikin rashi kwarin jiki abban nasu yace "am really glad to see you, ina godiya ga Allah daya dawo mun daku
DOWNLOAD
DOWNLOAD

6 Comments On ABBAN SOJOJI
avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
ibrahim-5-3

7 months ago

Reply

Ina son abban sojoji complete

avatar
muhammad-4-3-8

6 months ago

Reply

I want it

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
hauwa-said

6 months ago

Reply

Please Ina so

avatar
husaini

2 months ago

Reply

I love this novel

Please Login or Register in order to submit comment