Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karfin halin cewa gsky wannan ba adalci bne dazaka kamata kadaketa sbd..wata wawar fincika yah Suleiman yyi masa had'e da makasa jikin bango atake bakinsa yafashe.
Cikin isa yah Suleiman yace yes na mareta sbd na isa ne kuma kaima yanxun zan Nuna maka isata ta hanyar yimaka hukunci da laifinka duk da nasan.bakasan wanene niba!
Tuni yasaita bindigarsa zai harbi Abbas ....da sauri baby dke tsaye dafe da kunci tana kuka tamatsa gaban Abbas cikin dakiya tace ah ah ni zaka kashe bashiba ,ta fad'a had'e da tare Abbas d'in kafin yah Suleiman yyi wani abu yaji Abba abdullahi na masa tsawa had'e da cewa kada kasake kayi Harbin nan....tuni yah Suleiman yyi wurgi da bindigar ya finciko baby da hannu daya ,hannudaya yakaiwa abbas wani wawan punch a fuska tuni hancinsa yafashe yyinda Abba ya iso afusace ya wanke yah Suleiman da mari had'e da cewa me yamaka ?"

Beyi mgn ba idanunsa sunyi jajir jijiyoyin kansa duk sun mik'e rad'o rad'o, yanajin zafin hanasa da Abba yyi yama Abbas hukunci......sai botsare botsare take tanaso yacikata ta taimakawa Abbas ganin halin dayake kuma sbd ita"amma yarik'e ta gam.

"Abba ne daya lura yah Suleiman bazaiyi bayaniba sbd dokin zuciyar dayahau " yasa Yakama Abbas suka nufi get .
https://2gnblog.blogspot.com/
Shikuwa gogan ganin abinda baby keyi yasake bata masa rai azafafe yadauketa da bindigarsa yyi part d'in sa da ita tanata ihu da kiran sunan Abbas din.

Abba kuwa suna fita saiga motar yah Yusuf tuni yatsayar dashi suka shige hade da nufar asibiti.

Bayan duk anbasa treatment d'in da yadace aka samasa drip had'e da yimasa allurar bacci sannan Abba yakira abbu yace su had'u a asibitin.

Shikuwa yah Yusuf yanufo gd yana tambayar kansa wanene wancan saurayin ?"kuma waye yajimasa ciwo haka acikin gidan?"

"Xuciyarsa tace yah Suleiman ne"

Shiru yyi had'e da yin parking yafito yanufi part d'in su...zubaida dke kallonsa ta window tana Dakon zuwansa tun dazun ,jitake kamar ta bisa saidai zuciyarta nace mata hmmm kije kici dukaba....

**********

Abbu kuwa byn yaje asibitin nan Abba yyimasa bayanin iya abinda yasani game da abbas,ajiyar zuciya yyi yace hmmmm wannan Yaro ALLAH yarabasa da Wannan zafin zuciya tasa! Yanxun dabakazoba fazai iya kissan kai "oh ALLAH yakyauta ,amma yanxun mujira asallamesa muwuce gd naga Suleiman din yyimun bayani meye hujjarsa na zubarwa da wannan Yaro jini.

Abbu yyi ajiyar zuciya afili yace gsky yaya Wannan karon zan yadda kwallon mangwaro na huta da kuda..

Abbu da mamaki yace mekake nufi?"

Abba yyi masa bayanin abinda yafaru da mm zulai dg karshe yace datadawo takardar sakinta zanbata nagaji wlh bazan iyaba ,mace daya nasan samun hawan jini da bacin ciwon zuciyar data samun...

Cikin rarrashi da ban baki abbu yace ah ah bazaa yi hakaba kodan sbd y'ayanta,kak'ara hkuri dan ALLAH kaje kabiyasu ayo Belin nata....katsesa yyi da cewa ah ah wlh kokai ban amince ka biyaba gwara abarta can kotasaduda da duniya....

Kiran sallar laasarne yasa suka fita masallacin , kafin sudawo ya farka ancire masa drip,bbu laifi jikin yyi masa sauki saidai yasha alwashin bazai koma gidan su baby ba yanxun zai koma kauye ko da dare ne ya isa"sbd yatsorata da sojan nan dan yatabbar mutumin bashida imani,inbachin yanada sauran shan ruwa da sai dai wani bashiba ,saidai yasha alwashin daya sauka gd zaije gun mlm yyimasa bayani ,wanene sojan nan?"meye matsayinsa agun nah nah? """""

Saurin tashi yyi ganin bbu kowa a room d'in dan beso ma su had'e da Abba daya taimakesa yakasa asibitin, yyi saurin ficewa yyi tasha yahau motar garinsu...


Su abbu nadawowa suka sami room d'in wayam,bbu Abbas bbu alamarsa ,nan suka tambaya a reception akace ai ya fita ,abbu yacewa Abba to shikenan ALLAH shi kyauta muje yanxun gd ni naga Suleiman din dolensa yyimun bayani da haka suka nufi gd...

-----------------------------------

Bangaren mm zulai kuwa tun amota take hawaye tana gayawa Laure saita d'au fansar abinda Tamara,dariya Laure tayi tace hmmm wlh zakijawa kanki natona abinda kika binne....cikin ko inkula mm zulai ta ce eh ai harda ke ,baki daya zaki tonama asirin .....police guda yace malamai kuyimana shiru,tsit sukayi harsuka iso aka saka mm zulai cell,aciki tasami wasu mata 8itace ta Tara ta tsorata ain in dan bata taba zuwa police station ba sai yau jiki bbu kwari ta zauna aka rufesu ciki.
Sai kallon su take tana Dade hanci sbd wari da zauri da gurin keyi,tuni tafara jin tukar amai sbd ko break batayiba aka taho da ita.
Kakarin amai ta fara ...cikin matan dake cell din wata tantiriya y'ar tasha ta watsawa mama zulai mugun kallo had'e da cewa ke karamar y'ar iska! Zakixo Okinawa mutane iyayi d hura hanci ke mai tsabta harda yunkurin amai ko?in har da gske ke me tsabtar zuciya ce bazakiyi laifi akaiki police station....afusace mama zulai tace ke matsiyaciya karamar y'ar bariki me ruwanki dani dazakizo kinamun halin dabbanci...

Azafafe tayi gun mm zulai had'e da mata wawar fincika tacigaba da jibga ,tun mm zulai na iya ramawa harta tagayyara sbd batayi break ba,tuni matar ta kumbura mata fuska ,sukuwa sauran dama tsoron matar suke basuce komai ba harta gaji ta kyale mm zulai din ta yi kwance yashe kamar kayan wanki.

Zuwa 12:00 har jikinta yyi zafida zazzabi da ciwon kai, mace daya ce mai dan tausayi tasanar da Wanda yakekae musu abinci ,yaje yakarbo magani yakawo ,byn taci abincin da ko almajiri bazata iya bashiba tasha maganin ,tana tuna yayanta da gd tana hawaye...


Yah Suleiman kuwa..



Share..


📚📚mmn fareesa ce✍✍
*_Typing📲_*



*_Haske writer's asso...._*💡




*_♦RAINA KAMA......♦_*
_{Kaga gayya}_



*_Bilyn Abdull Ce_*🤙🏻



~Book 2~ 👉🏻6⃣
https://2gnblog.blogspot.com/

............Har ya fita ya dawo, laptop da wasu takardu ya d'auka a falonsa ya fita, zai zauna a falonta saikuma wata dabara ta fad'o masa, bedroom d'inta ya nufa yana wani ciccijewa (kaida zaka karoro, miye na fuska to yalla6ai?🤔😂).
Munaya Na tsaye tana ninke hijjab d'in data rama sallolin dasuka risketa a hanya sai kawai shigowarsa tagani da sallama ciki-ciki. k'ok'arin warware hijjabin tafarayi tana masifa ita kad'ai a zuciya, haka kawai aita shigoma mutum d'aki babu izini, wannan wane irin rayuwane.
https://2gnblog.blogspot.com/
Shikam Galadima kallo d'aya yamata ya d'auke kansa, Dan daga ita sai zani d'aurin k'irji. Laptop d'in hannunsa da takardu ya ajiye a bakin gadon, sannan shima ya zauna, batare da ya kuma kalllon Munaya ba yace, “kinajin yunwa ne?”.
Ba yunwar takeji ba, amma dan Neman magana kawai tace “eh”.
Kallonta ya sakeyi, bata yarda sun had'a idoba, yace “Saidai kisha fresh milk kuwa, dan bani da abinci”.
Manyan idanunta ta waro masa waje, kamar wadda akace tasha wuta, cikin dafe k'irji tace “yalla6ai fresh milk?”.
Da mamaki ya kalleta, danshi bai fahimci ma'anar razanar tataba, yace, “uhmmm”....
“Na yafe wlhy”.
Tafad'a da saurinta.
“To mine nawani birkicewa haka? fresh milk d'in wani abune dashi?”.
“Humm”. Munaya tafad'a tana ta6e baki, tace “yalla6ai nikam idan kaga nasha fresh milk d'in data fito daga d'akinka saidai idan bana a hayyacina”.
Da tsantsar mamakin furucinta yake kallonta, da yake basuda nisa saiya mik'a hannu ya rik'o nata, zatayi magana ya fizgota ta zauna kusadashi, kad'an ya rage ta hau masa laptop, amma yay saurin janyewa da d'ayan hannunsa.
“wash hannuna”. Munaya tafad'a tana matse baki.
Banza yamata, yakuma matsa hannun da mugunta. tasaki k'aramar k'ara tana fad'awa gefen kafad'arsa.
Ya d'an kalleta ya janye yana ta6e baki “ban fahimci zancenki daga nesa ba, maimaitamin”..
Cikin tunzuro masa baki tace, “yoni babu abinda nake nufi fa, nidai bazan sha fresh milk d'in data fito daga d'akinka ba wlhy. haka kawai aje asakama mutum abinda zai halakashi”. ‘k'asa-k'asa ta k'arasa maganar, amma yajita sarai’.
Shifa saima yanzu yagane inda zancenta ya nufa, wani miskilin murmushi yasaki yana danne dariyarsa datake shirin kufcewa, amma dukda haka saida taji sautin fitar murmushin nasa.
Munaya dake satar kallonsa idonta harya cika da kwalla, a zuciyarta tace mugu d'an masa, dole fa kamin dariya.
Saida yayi dariyarsa a zuciya ya gama ya kalleta, itakuma saiwani mar-mar takeyi da idanu wai zatayi kuka.
Murmushi ya kumayi, sannan yace, “wannan bakin dakike tunzuromin ko, hummm.....”. ‘yak'are maganar da cije lips nashi’.
Yunk'urawa tayi zata mik'e, tace, “yalla6ai ni wlhy barci nakeji fa”.
Dawo da ita yayi ta fad'o jikinsa shima yana fad'in “nikuma gadinki zanyi ko? yalla6iya!”.
Tace “wayyo innarmu kice ya fitarmin a d'aki please”.
“ko waya zan baki ki kiratane”. ‘yay maganar cikin d'age gira d'aya’.
Munaya tai saurin janye idanunta daga Kansa ga k'amshin turarensa ya gallabeta, barci takeji, amma takula mugunnan soyake ya hanata ma.
Kamar zatayi kuka tace, “yalla6ai wai mikazo nemane please? Wlhy barci na keson yi?”.
Shiru yamata, saida ya mula dan kansa sannan yace “jikina fa”. ‘yay maganar yana kallon k'ugunta’.
Da sauri Munaya ta sauka daga jikinsa tana k'unk'uni da tura baki.
Medical glasses d'insa ya d'auka ya saka, tareda cigaba da aikinsa a laptop, a zuciyarsa yana fad'in yarinyarnan akwai ruwan tsiwa, amma duk randa Na kama bakin tsiwarcan sai yamin bayani dalla-dalla kuwa.

Ganin ya shareni ya cigaba da sabgarsa a System, nima sai ban kuma bi ta kansa ba Na d'auki kayan barcina nashiga bayi domin Na sanya. Sai dai zuciyata cike take da fargabar miya kawoshi d'akina?. haka na fito kamar wata munafuka ina lallak'ewa jikin bango.
Duk yana kallona ta gefen idanu, amma yay kamar baima San dani a d'akinba.
Sai zuwa can ya d'ago yana kallona, yana wasa da pen d'in hannunsa kan la66ansa, “idan bak'yajin barci zokimin wani d'an aiki nan”.
Saida gabana ya fad'i, a raina nace aikin mi kuma?, a fili saina aro jarumta na yafama kaina, Dan nakula tsoron daya fara gani a idona ne yake neman fara rainani da samin fargaba (🤣ho munayan shagali).
Takowa nayi inda yake, ina niyar zama bakin gadon sai ya nunamin tsakiyar gadon, shima laptop d'in ya tura sosai kan gadon ya haye tsakkiya yana gyara zamansa. kuma had'e fuska nayi ina wani dojewa na hau nima na zauna, cigaba yayi da danna laptop d'in, kusan mintuna 3 ya jehomin tambaya.
“shin kinsan minene aikin Abba?”.
Da mamaki na kallesa, nace “wai Abbana kake magana?”.
“uhmm”. ‘yafad'a batare da ya d'agoba’.
Shiru nayi alamar tunani, harya d'ago ya kalleni bance komaiba, maida kansa yayi ga laptop d'in yacigaba da aikinsa, zuwa can nace, “ma'aikacin gwamnati ne kawai tawani fanin kuma aikinsa yanada Nasaba da jarida”.
Tunda nafara magana ya tsuramin idanu, bakina kawai yake kallo yana taune lips nashi, saida nakai aya sannan yace, “jarida?”.
Nace, “eh, wani abune ya faru?”.
Kansa ya girgizamin, “innalillahi” yashiga maimaitawa a zuciyarsa, baya fatan zarginsa yazama gaskiya, cikin dakiya yakuma cemin “kokin san abokansa? ina nufin cikin manyan mutane haka?”.
“eh to, akwai senator halluru garba, sai kuma wani anacemasa Alhaji Mamman k'afur, last year yafito takarar shugaban k'asa......”
Caraf ya kama hannuna, “kina nufin Alhaji Mamman k'afur abokin Abban kune?”.
Ni tsoroma yabani, yanda yay maganar cikin rawar jiki, na jinjina masa kaina a hankali.
Gani nai ya taune lips nashi da masifar k'arfi, ya kaima iska naushi. da sauri na matsa baya Dan karya nausheni, ganin kamar na tsorata sai yay murmushi, cikin k'asaitacciyar muryar nan tasa yace “my Friend! Yanzu ne zamu fara aiki tare da gaske ni da ke”.
“kamar ya yalla6ai? wane irin aiki kuma?”.
Murmushin takaici yayi, ya kalleni ido cikin ido, kasa jurewa nayi nai k'asa da nawa. shima lumshe nasa yayi yana fad'in “zaki gani”. daga haka ya janye laptop d'in gefe ya zame ya kwanta.
Binsa nayi da kallo tamkar wata sokuwa, gaba d'aya ya kulle magudanar tunanina da wadda ke kaima kwakwalwata sakonni.
Medical glasses d'in idonsa ya cire ya ajiye, sai kuma ya juyo gareni, hannunsa d'aya ya mik'amin yanamin alamar nazo gareshi.
Idanu na d'an zaro, sai kuma na nok'e kafad'a alamar nak'i din.
Wani murmushin da bako yaushe yakeyinsaba ya sakarmin, ya juyamin baya yay kwanciyarsa. bai sake juyowa gareniba har kusan 6minutes. nagaji da kallonsa da nazarin murmushinsa da tambayoyinsa na janye idanuna, waishi guy d'innan mike damunsa ne? gaba d'aya ya canjamin daga saukarmu zuwa yanzun, dubana nakai ga agogon d'akin. 3:27am, “ya salam” na fad'a a hankali, muna Neman kwana a zaune. can k'arshen gadon na koma na kwanta, zuciyata cike da tsoron ALLAH yasa bawani Abu ya shiryaminba, babu dad'ewa barci 6arawo ya saceni.

Numfashina dake sauka a hankali yasaka Galadima gane nayi barci, juyowa yay yana kallona, yayinda zuciyarsa keta cud'a amsoshin dana basa yanzun, tabbas mahaifin yarinyarnan akwai abinda yasani, kwarai da gaske zaiyi amfani da ita wajen gano ko wanene mahaifinta?, minene alak'arsa da case d'ina?, sannan minene alak'ar Muftahu da ita?, Dan tabbas akwai manufar sako yarinyar acikin wannan tak'addamar, kuma Muftahu dashi aka shirya komai. yasaki wani murmushin mugunta tareda nuna kansa, a fili yace _MAK'IYAN MAHAIFINA SAINA ZAME MUKU_ *RAINA KAMA KAGA GAYYA* tabbas lokaci yayi dazakuga wannan *Gayyar*.



Tofa masu karatu, ana zaton wuta a mak'era🤔, mikuna yasako Abban munaya a rikicin masarauta? Kodai ba masarautar kawai bace keda alhakin ciwon tsohon Sarki Saifudden Abubakar🤔?, shin tsakanin Galadima da Munaya & munubiya, innarsu Munaya. Wanene RAINA KAMA...... d'in🤗?.

Kumuje zuwa kudai my Guy's😁, duk nisan jifa👆🏻, k'asa zai fad'o👇🏻🤗


★___________________________★


Bayan shigewar su Galadima Muftahu ya fito daga mota shima yana murmushin dashi kad'aine yasan fassararsa, jiyay kawai handkerchief ya rufe masa fuska, yay saurin cirewa yana waige-waige dan dunba wanene ya jeho masa, wayam babu alamar mutum a wajen, bai gama dube-duben ba yay luuu zai fad'i, saigashi a hannun mutum, idanunsa sunriga sunyi nauyi, dishi-dishi yake kallon Wanda ya tareshi d'in, dama gashi ya rufe rabin fuskarsa ba'a gani, wasu samarine su biyu sukazo suka kama Muftahu tareda wancan suka danna a mota, tun yanajinsu sama-sama har idonsa da jinsa suka rufe baki d'aya.


🙆🏻tofa suwaye?.


★__________★_________★


Tun kusan around 8pm Nuren yake k'ofar wajen, a dukkan bayanan daya samu daga majiya mai k'arfi yarinyar Minister ta shigo gari yau, kuma zatazo shan ice-cream wajen, wayarsa ya d'auka yay wasu 'yan danne-danne, murmushi yayi ya maida wayar ya ajiye tareda dasama k'ofar wajen idanu, dolene kafin tashiga ciki zai saceta, dan bincikrnsa ya nuna masa cctv camera d'aya ce a cikin wajen kawai, a waje babu, dan haka bama ya buk'atar ta Shiga, murmushi yayi saboda ganin motar da driver d'inta yamasa kwatancen zasuzo aciki, saida driver n yaga motar Nuren sannan yazo kusada ita yay parking, bud'e murfin gefen mai zaman banza Nuren yayi, hakan kuma yay dai-dai da fitowar zankad'ed'iyar budurwa daga motar datai parking kusada ta Nuren d'in, murfin ne ya daki gefen hannunta kad'an.
A fusace ta kalli motar Nuren, shikuma yay mata murmushi, wani haushine ya kamata, banda rainin wayo ya bigeta amma yamata murmushi saboda wulak'anci, yau saitaga wanene ubansa a garinnan?. da k'arfi tabuga saman motar tana lek'a kanta ciki, “kai wawa bakaga abinda kayi bane?”.
Maimakon ya bata amsa saiya jefa mata handkerchief d'insa saman fuskarta, janyewa tayi da sauri zatayi magana kanta ya sara mata, da lalube ta dafa kujerar motar ta shiga ta zauna, sai faman lumshe idanu takeyi. murmushi Nuren yayi, ya taimaka mata ta ida shigowa Sannan ya rufe motar, komai akan idon driver n ta ya faru, bashida damar hanawa, dan Nuren yasashi a tsaka mai wuyane. Agaban idonsa Nuren yaja motarsa yabar wajen yana murmushin samun nasarar tafiyar plan d'insa yanda ya tsara. a wannan daren yanufi gidan Galadima dake can bayan gari inda aka ta6a kai Munaya.


😱humm yau 'yar kidnapping akeyi kawai😂🤪.


------------(((★)))--------------



Galadima yariga Munaya farkawa, dama bawani isashshen barci yayiba, tunani da damuwa suka taru suka hana idonsa rintsawa sai gabannin Asuba. Ana kiran sallar farko kuma yana farkawa, tashi yay zaune dafe da kansa, kusan mintuna biyu ya juya yana kallon munaya data juyo tana fuskantar inda yake yanzun, da gani kasan barcin bamai dad'i takeyiba, dan sai yamutse fuska takeyi a cikin barci. matsawa yayi kad'an ya d'ora yatsunsa biyu gefen fuskarta, sai yaji zafi jikinta, ya janye yana mamakin wai mike damun yarinyar nan kwana biyu haka? dolene yau yasata taga doctor idan sunje ganin Abba. gabansa yad'an fad'i daya tuna har yanzu itafa batasan komai ba, shi baima San ta yadda zai sanar mata abbanta yana cikin mawuyacin hali ba, ya dafe kansa yana ambatar sunayen ALLAH kozaiji sassauci a ransa. Da k'yar ya samu ya mik'e domin yin rakata ainul'fijir kafin akira assalatu.

Bayan ya idar ya tadani, da k'yar na iya tashi dafe da kai, dan barcin bai isheniba, muryarsa da alamun shima rashin isashshen barcin yace, “time d'in salla yayi”.
Idona dake bud'ewa da lumshewa Na kad'a masa alamar amsawa, yay saurin janye nasa saboda wata fad'uwar gaba da tsirgawar wani Abu dayaji lokaci guda tun daga Kansa zuwa yatsan k'afarsa, bai sake magana ba yafice. nikuma nakoma Na sake kwanciyata.

'Dakinsa ya shiga ya tada Sauban dansu tafi massalaci.
Babu dad'ewa Sauban ya kammala alwala yafito ya iskeshi a falo yana jiransa, harara ya antayama Sauban, shikuma ya kauda kai gefe yana had'iye dariya (yo daga taimako saiya zama laifi?).

Sarki yayi mamakin ganin Sauban, dan yaron bawani zuwa k'asar yakeba saida dalili mai k'arfi, bayan yagama k'ar6ar gaisuwa wajen jama'arsa Galadima da Sauban sukabishi zuwa sashensa.
Kasa 6oye mamakinsa yayi, ya kamo hannun Sauban d'in dake d'ayan 6arinsa zaune kamar yanda Galadima yake, “yarona ne yau ak'asarsa ba biki ba ba bikin salla ba?”.
Dariya Sauban yayi, yace “Abba nazo gaidakune kawai”.
Sarki ya Murmusa yana kallon Galadima, “Galadima kodai akwai abinda ke faruwane kuke 6oyemin?”.
Galadima ya d'ago kansa cikin damuwa yace “babu abinda muke 6oyewa ranka ya dad'e. Mahaifin Munaaya ne yay Accident shine suka taho da Sauban d'in”.
“mu bamuda muhimmancin da zamu Sani kenan ko?”.
“ALLAH ya huci zuciyarka ba haka nake nufiba, bayan barina wajenka jiya nima aka sanarmin, lokacin dana shigo kuma dare yayi”.
Ajiyar zuciya mai martaba ya sauke, yace “ALLAH yabashi lafiya, zuwa anjima sai su waziri suje dubashi ai, tana ina ne ita d'iyar tawa?”.
“tana nan cikin masarauta”.
Jin jina kai kawai Sarki yay bai kuma cewa komaiba, sai zuwa can yacigaba dayima Sauban tanbaya akan jikin Abie, shikuma yana bashi amsa. Galadima dai Na jinsu bai saka bakiba.


*************

Saida gari yafara haske ALLAH yabani ikon tashi, dan zazza6in kuma ya sauka, yanzu kuma haka yakemin, da dare yayi zan fara zazza6i, lokacin da gari zai waye saikiji ya sauka. Sai dai ciwon jiki.
Saida nayi wanka da ruwa mai zafi sannan nayo alwala, sallar asubahi data kwacemin nayi, Na jawo handbag d'ina danazo da ita Na d'akko wayata, sim card d'ina Na 9ja Na d'akko shima Na saka akan wayar, massage suka turomin Na adadin awannin da suka bani sim card d'in zai d'auka kafin ya cigaba da aiki. ganin haka saina ajiye wayar natashi domin gyara d'akin, ina cikin kakka6e gado idona yakai bisa wayar Galadima. dad'ine ya kamani, koba komai nakira wani d'an gidanmu Na sanar dasu nazo 9ja.
Wayar Na d'auka Na saka number Abbana, dan yanzu nafi kwad'aituwa dajin muryarsa fiye da kowa, kodan mafarkai marasa dad'i danakeyi a kansa, Mtn d'insa nafara kira amma a kashe, saina kira glo d'in, shima switch up, ban kawo komai a rainaba na maida kiran kan innarmu, bugu biyu aka d'aga, wani dad'ine ya kamani, cikeda d'oki nace “innarmu I miss you”.
Aiyaan daya d'aga wayar yay dariya, aunty ba inna baceba. Nine, Nima Na iya waya yanzun”.
Dukda naji dad'in jin muryar d'an uwana, hakan bai hana zuciyata shiga fargaba ba, nace “Aiyaan Kaine? ina innarmu d'in?”.
“Tana wanka ne zamuje asibiti wajen Abba”.
Da sauri Na dafe k'irji, nace “Asibiti kuma? miya sami Abban?”.
“Lah Aunty baki saniba? Ai accident yayi fa, kuma innarmu nata kuka, hakama innaro dasu daddy”.
“Aiyaan!!...” nafad'a da k'arfi, kafin nace wani Abu naji an rik'emin hannu ta bayana an zare wayar daga kunnena.
Kuma rikicewa nayi, Na juyo da hanzari, cikin kuka naketa fad'in “abbana! Abba da gaske Aiyaan yake yi? Yalla6ai da gaske Abbana yayi accident?”.
Wani tausayina yaji ya tsargashi, ya dafa kafad'una, cikin sigar lallashi yace “cool down mana my friend”.
“to ka fad'amin da gaskene Abbana yayi accident d'in?”.
Rasa mizaice min yayi, sai bin fusakata da idanu yakeyi, ya cije lips nashi yana fad'in “inhar kinason na kaiki ki gansa toki nutsu”.
Share hawayena nayi da sauri nace, “to na nutsu muje”.
Yaja hancina, a hankali ya furta, “good girl”. Sai ya juya kuma ya fita.
Binsa nayi da kallo hawaye na zuba a kumatuna, kenan da gaske Aiyaan yakeyi Abba yayi Accident d'in, “hasbinallahu wa'ni'imal wakil”. Na dafe kaina tareda zama a bakin gadon nacigaba da raira kukana.

Shikam yana fita ya dunk'ule hannunsa yana cije lips, yama akayi yabar wayarsa harta d'auka tayi kira dashi, ko kad'an baiso hakaba. Baiso tajiba kai tsaye.

Saida naci kukana na gode ALLAH sannan natashi na hau shiryawa, atamfa na saka zani da riga, bawata kwalliya nayi ba, na shafa fauda kawai da lips gloss, turarema kad'an na shafa. ina cikin Neman mayafi ya shigo, kamshin turarensa yasani juyowa na kallesa, sanye yake cikin oxblood d'in shadda, hularsa takalmi agogo duk black, link d'in hannun rigarsa yake sakawa, sai alk'yabba pink da ratsin milk a hannunsa.
d'auke kaina nayi naci gaba da neman gyalena a cikin kayan lefena.
Baimin magana

Please Login or Register in order to submit comment