Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

 5:33 PM] ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️: 🌼🌼ARMAN MALEEK🌼🌼


*DAGA ALƘALAMIN*

SALMAJI ƳAR LELEN ROYAL STAR CE

Sadaukarwa ga Aminiyata Sadiya Abbakar Maru (Ƴar gatan royal star)

*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*



PAGE 1..



Cikin Natsuwa jerin gwanon Motoci kusan guda biyar kirar Mercedes Benz , farare ne sol gwanin sha'awa, suke tafiya, duk in da motocin suka wuce ɗaga musu hannu da jinjina ake, wanda hakan ma ya isa ya shaida maka, ba ƙaramin mai daraja da ake ganin mutuncin shi bane a motar, sai da suka zo gurin wani Babban hospital kafin su fara rage gudu, a hankali suka fara sulalawa cikin Asibitin, sai da suka shiga cikin tafkeken parking space din cikin Asibitin kafin su tsaya.


duk fitowa mutanan da suke cikin motocin suka yi, sai wata mota daya da go budeta ba'ayi ba, a hankali aka bude murfin motar, kamshin turaren Huge Boss da ya daki hancina ne ya tilasta min ɗago da idanuna, hankan kuma yy dai-dai da zuro fararen ƙafafunshi fararw tass, wanda suke cikin takalmi half cover fari mai kyau, yana yin zubin takalmin kawai zaka kalla kasan cewar na Sarakai ne.



tun daga ƙafafunshi na fara ƙarewa kallo, har izuwa kwaurinshi wanda farar Alƙyabba mai torch din Golding da ta mammaye gaba daya jikinshi, wanda har fuskarshu ba'a iya gani, sai dai hannayenshi da ya zuro, wanda ya ke gyara igiyar Alƙyabbar jikinshi.


A hankali ya sanya kyawawan fararen hannayenshi, ya dan jaaa hular Alƙyabban da yake jikinshi, Masha Allah, kyakyawa ne sosai, duk kuwa da ban ga fuskarshi da take nannaɗe da rawanin da yake a kanshu ba, idanubshi kawai da gefen fuskarshi na samu nasarar gani, idanunshi manya ne dan kai tsaye za'a kiransu da Lu-lu Eyes ko ace Oil Eyes, dan har wani mai-mai ko in ce ruwa-ruwa ne a cikin idanun nashi, farare ne tas, sai dai maimakon back eyes ball , sai nashi y kasance royal blue.


lumshe idanun nashi yy, wanda hakan yy nasarar bayyanar da zara-zaran Eyes lashes dinshi, da suke baƙaƙe sidiƙ, idanunshi y bude tare da dan juyasu a hankalin, kafin ya fara tafiya, cikin yalwatacciyar natsuwa da kamalarshi.


Sauran Fadawan da suke bayanshi ne suka fara take mishi baya, cikin natsuwa duk suka nufi cikin Hospital din.
shigarsu kuma tayi dai-dai da shigowar motar Ambulance da take ta ihu, cikin gaggawa gaba daya nurses din da suke cikin Asibitin da Drs duk suka nufi waje in da Ambulance din ta tsaya.

cikim gaggawa aka fara fitowa da Majiyatan da suke cikin Ambulance din wanda kallo daya zaka musu kasan cewar Haɗarine Hadarin ma mugun haɗari wanda baya kalluwa, daga gaba dayan su bb wanda bai rasa wani sashe na jikinshi ba, duk jini jikinsu bb kyan gani, masu rauni zuciya ma daga cikin nurses din sai kuka suke, Drs din kuwa dama su sun saba gani, hakan yasa abun bai wani ɗaɗarasu da ƙasa ba, sun damu amma bawai kamar nurses din ba.fiffito dasu aka yi, amma sai suka yi cirko², ba'a shiga da su ciki ba.

Mutanan da suka shiga ciki ne suka fito , gurin da mutanan suke tsaya suka nufa,
abin ya mugun ɗaga musu hankali, wanda yasa da damarsu suka fara zubar da hawaye,daya daga cikin Drs din ne ya ce "wannan sai dai ku shiga dasu Amma bb alamar rai a jikinsu", ya fada yana niyyar juyawa, hannunshi mutumin ya kama, idanunshi da dago tare da tsurasu akan mutumin da sauri cikin ƙanƙan da kai yace "Allah ya taimaki Sheikh Arman wannan Haɗarin ya munana, bashi da kyan gani, bana tunanin za'a iya fitar da mai a ciki", ya fada cikim zallar jimami.


sakin hannunshi yy ya ƙarasa gurin motar, yana zuwa idannshi ya sauka akan wata Yarinya da take sharɓe gaba daya jikinta jini ne, wanda yasa bama a iya ganin fuskarta sa boda jinin da ya wanke gaba daya illahirin jikinta, ga wani farɗeɗan ciwo da ya zagayo tun daga kanta har tsagin fuskarta ɓangaren haggu, gaba daya Yarinyar ba zata wuce 7years ba, royal blue eyes din shi, ya juya a kam Yarinyar da kallo daya yy mata ya gane tana numfashi, a hankali ya furta "Yah Subhanallah", ya fada yana kutsa kanshi cikin tarin Jama'ar gurin.

yana zuwa bai ɓata lokaci ba ya dauketa chaak tare da nufar cikin Asibitin da ita, cikin wata Golden Voice mai dadin gaske, wadda kamar ana busa sarewa ya fara kiran "Doctor! Doctor!! Doctor!!!", ya ƙarasa faɗa cikin gajiyawa da rashin son magana, Dr din da ya mishi mgn Ɗazun ne y fito da sauri jikinshi na rawa, miƙa mishi Yarinyar yy , da ido ya mishi alama da a duba ta, da sauri ya karɓi Yarinyar da bb alamar rai a jikinta, Accident and Emergency room ya nufa da ita da sauri.


Yana shiga ya shimfiɗeta kan gadon da aka tana da domin masu rashin lpy mai tsanani ko haɗari, gaba daya gadon yana kewaye da na'u'o'i , na ceton ran Dan Adam, da sauri Dr din ya dauki
stethoscope da yake ajiye a saman wani dan table in da anan ne ake ajiye duk wani abu mai muhimmanci da Drs suke buƙat amfani da su domin ceto ran marar lpy.

cikin Sauri ya juyawa Yarinyar baya tare sa zage zip din yar rigar jikinta, ya ajiye a gefe, kwantar da ita yy tare da daura stethoscope din a kirjinta ɓarin dama, domin jiyo sauti bugun numfashinta, a hankali ya jiyo bugun numfashinta da yake chan ƙasa sosai wanda in baka saurara ba ba zaka iya jiyowa ba, da sauri ya dauki ya matsa gurin Ventilator, (Na'urar hura iska ita ce injin da ke shaka wa mutum yayin da huhu ke samun waraka. Yana aika iskar oxygen ko iska zuwa cikin huhu ta cikin bututu mai bakin ciki kuma yana ba da damar carbon dioxide ya tsere. Ana sanya bututun a cikin bututun iska ta hanci ko baki), cikin Jaddada wannan lamari ya ci gaba da gyara mata jikinta, sai dai irin manya-manyan rauni kan da suke jikin Yarinyar ya bashi tsoro, domin raunika ne wanda ba lallai in mutum ya jisu a jikinshi ya iya rayuwa ba.

jinin da yake ta zuba a tsakiyar kanta ya fara tsayar mata, ganin wani kwasheshen ciwo yasa, ya dauki scissor ya fara iske mata gurin da taji ciwon, tsorata yy lokacin da yy arba da ciwon da yake kanta, wanda yasa har ya matsa ba, yanka ce sosai wadda ta shiga cikin kanta, wanda har naman kanta ana iya hangowa.

bai san lokacin da kwalla ta zubo mishi ba, sa boda zallan tausayin Yarinyar, a hankali ya shiga mata ɗinki a kan, har ya gama yana hawaye, duk in da ta ji ciwo ya wanke mata, ya gyara mata karayar da tayi, kafin ya fara gofe mata jinin fuskarta, bayan ya gama da ya kalli fuskarta, sai da zuciyarshi tayi wani kyakywan bugawa, sa boda ganin yarda fuskar Yarinyar take, wadda jini duk ya dan bubushe mata, Fara ce sosai, yana yin zubin halittar fuskarta da farin fatar jikinta kaɗai ya isa shaida maka cewar ba cikakkiyar yar Ƙasar Nigeria bace, dan tafi kama da Larabawa ko Turawa.


bayan ya gama ya shiga duddubata, domin ganin in ta samu wani Internal Injury, abun da ya gani yy bala'in girgiza mishi tunaninshi, wanda yasa sai da ya dago ya kalleta,na wasu minutes kafin ya ci gaba da aikinshi, bayan ya gama, ya fidda sakamakon Gwaje-gwajen da aka mata, tare da fitowa yana goge idanunshi da fuskarshi da suka yi jaaazir tsabar tashin hankali.


ko da ya fito wayam yaga ƙofar, ko ha'a faɗa ba yasan Sheikh Arman-Maleek Abdul-azeez Sarki ya tafi , domin lokacin Sallar Juma'a yy wanda kuma yana da tabbacin duk lokacin da ya shigo Ƙasar shine yake Limancin Central Mosque din da yake cikin Abuja .

da sauri ya shiga cikin Office dinshi domin shirin tafiya shima, sai da ya gama kafin ya fito, kiciɓis yy da wata nurse cikin harshen turanci ya fada mata ta kula da Patient din da take ER(Emergency room), jinjina mishi kanta tayi, kafin ya wuce
, yana hawa kan titin da sai kai shi Asokoro Central mosque da yake cikim Abuja, ya fara jin daddar muryar Sheikh Arman-Maleek tana tashi ta cikin abun ƙara karfin saurin maganar da yake cikin Masallacin wanda ya ƙaraɗe gaba daya Unguwar ta Asokoro, cikin dadda kuma sanyayya tattausar muryarshi yake huɗuba , tare da nusar da jama'ah da baiwar da Allah ya bashi ta iya magana.

har ya ƙaraso harabar tankamemen Masallacin da yake cike da Al-umman Annabi yana jin Muryar Sheikh din na ratsa cikin kunnuwanshi, a hankali cikin natsuwarshi shima ya nufi cikin Masallacin in da ya fara tara jama'a, sosai wanda da ka kalli yawansu ma zaka san ba mutane ne kawai ba, dole ma akwai ƙarin wasu jama'ar.


Cikin Masallacin da ya kusa cika ya shiga, kusan gaba daya Masallacin ta kusa cika da mutane, hakan yasa sai kusan sahun karshe ya samu , yana shiga bai fi sa 2 minutes ba aka kabbara Sallah,cikin tsari da tausasa harshe yake karatun Al-qur'ani mai girma a cikin Suratul Khafi, cikin zaƙi da dadin muryarshi yake karatun har aka idar da Sallah, mutane ne suka fara fita, bayan idar da Sallah Juma'an, kusan kowa da yake cikin Masalacin sai da ya fita, kafin Sheikh Arman ya fara takowa domin fita, ta wata ƙaramar kofa da take gefen kusa da gurin da Liman yake, bakishn dauke da Tasbhi yake tafita, yana yi yana lumshe idanunshi, har ya fito daga cikin masallacin.

Escort dinshi da suke a waje suna jiranshi je da Fadawa suka take mishi baya, har gurin motarshi,, bude mishi akayi, sai da ya tattare Alƙyabbar jikinshi kafin ya shiga, rufewa aka yi,bayan duk tarin mutanan da suka rakoshi sun shiga mota , kafin aka fara tafiya , a jere cikin tsari.


Direct Hanyar Garin Gombe suka nufa, idanunshi na lumshe bakinshi bai gushe da Ambaton Allah ba har suka yi nisa sosai suka raba dai-dai tsakanin Abuja da Gombe, A hankali ya fara bude Royal Eyes dinshi, tare da kallon wayar da take gefenshi wadda take ta vibrating , ga kuma haske da take kawowa.

a hankali ya kai zara-zaran fararen yatsun hannunshi, ya dauki wayar tare da yin Receiving call din, a hankali ya kara wayar a kunnenshi ba tare da sanin mai kira ba, Wata Muryar ce mai sanyi da dadi ta daki dodon kunnenshi wadda tasa ya dan lumshe ido, yarda ya dan saki jikinshu ne kawai zai fahimtar da kai wanda yake kiran nashi yana da matuƙar muhimmanci a gareshi,a hankali cikin halin rashin son magana yace "l'll call you late ",yana fadar haka ya kashe wayar .

ko Ajiyeta a in da take bai yi ba, wani call din ya ƙara shigowa cikin wayar tashi, ```Jaddi``` sunan Mai kiran nashi ya bayyana a kan screen din wayar, sai da ya lumshe idanunshi kafin ya dauki kiran, A hankali yace "Assalamu alaika", daga cikin wayar muryar wani tsoho ta fara magana cikin harshen turanci , sai da na ƙarewa fuskar wayar kallo kafin na gane ashe number bata Nigeria bace, number ƙasar waje ce.

shi din ma da ya dauka ba wata maganar kirki ce ta haɗashi da shi ba, daga uhmm sai uhumm, shi kenan abun da yake ce mishi, har suka yi Sallama.


4hours ne ya kai su Gombe daga Abuja, direct titin Abdul-azeez Arman-Maleeek Sarki roaud suka nufa, basu tsaya ko ina ba, sai gaban wani tankameman get din gidan Sarauta wanda gaba daya gidan fenti ne irin na daɗɗiyar masarauta, fentin da ba'a samunshi a ko wace Masarauta sai masarautar da ta Haura shekara ɗari biyu da wani abu, tsarin gini da shigar mutan gidan ma ya isa kara tabbatar maka da dadewar Masarautar, a hankali ya bude idanunshi da suka dan zurma sa boda wahalar tafiya, dan tunda ya shigo ƙasar bai samu ya huta ba.


Get din gidan aka bude, in da motacin suka fara shiga a hankali, suna shiga ƙaramin get wanda zai sadaka da cikin gidan in da mutane suke, aka saki wani Algaita da busa wanda ba ko wace Masarauta ake yinshi ba, sai Masarautar da suke da Kambun Sarauta, sanan Algaitar nan da Busar ba wani ne yake yinsu ba, suna busa kansu ne a duk lokacin da wani wanda yake da Haƙƙin Mulkar Sarauta idan ya biyo ta ƙofar wanda bama kowa ne ake budewa ita ba.

matse idanunshi yy sosai, dan baya son busar nan da Algaitar dan a duk lokacin da za'ayisu to gaba daya tsikar jikinshi na zubuwa ne, sai ya rasa Natsuwarshi har sai yata Addu'o'i, yanzun ma hakan ce ta kasance, har suka ƙarasa parking space aka bude mishi mota bai bude idanunshu ba, kuma bai yi wani abu da zai nuna cewar zai fito daga motar ba.



kusan 10 minutes da bude mishi ƙofar motar kafin ya fito, A hankali, cikin kamala da cikar Zati yake tafiya, yana babbazar Alƙyabbar da take jikinshi, hannun na rike da wani dan sada irin na sarakai ko kuma wani gawurtacce a cikin gidan Sarauta.


Ƙofar Fada da ta fi ko ina tsaruwa da shan Ado a cikin gidan Sarautar ya nufa a hankali, kafin ma ya iso, har an shiga An mishi iso da Sarki, yana zuwa ya shige, duk sauran mutanan da yake tare da su , suka tsaya a waje.


Laɓɓansa dauke da Tasbhi da Addu'o'i ya shiga, yana mai yin Sallama ciki-ciki, wata sanyayyiyar murya ce ta Amsa mishi Sallamar daga ciki , a hankali ta ci gaba da tafiya zuwa ciki, Kishingiɗe ya samu Sarki akan kujerarshi, yana shiga ya tashi ya zauna, har ya ƙaraso cikin Fadar idanunshi na cikin kanshi, shi kuwa idanunshi na ƙasa dan baya kallon mutane, kullum idanunshi a ƙasa........
[2/22, 5:33 PM] ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️: 🌼🌼ARMAN MALEEK🌼🌼

*DAGA ALƘALAMIN*


SALMAJI ƳAR LELEN ROYAL STAR CE🧚‍♀️🧚‍♀️🧚‍♀️.

SADAUKARWA GA AMINIYATA MASOYIYATA SADIYYA ABBAKAR MARU (ƳAR GATAN ROYAL STAR )


```WANDA YAKE SON A TALLATA MISHI HAJARSHI. ZAI IYA TUNTUƁATA TA NUMBER NA KAMAR HAKA.

07033371851


ZAMU TALLATA MAKA HAJAR KA CIKIN SAUƘI DA RANGWAME```



*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*




PAGE 2.


A hankali ya ƙarasa gurin kujerar da yake zama a kullum da ko Yaushe in ya shigo cikin Masarautar, zama yy tare da dan Zamowa with full respect yace "Sannu da hutawa Lamurɗe", ya fada a hankali cikin natsuwar da ta zame mishi jiki, dan murmushin da ya tsaya mishi iya kan fuskarshi yy tare da cewa "Sannu da sauka Arɗo", jinjinw kanshi yy bai ƙara cewa komai ba,sai da suka nisa kusan 5 minutes kafin Ahmad Arman Maleeq(Ƙanin Mahaifin Arman Maleeq), yace "Ya Barkindo da jiki ?", ya fada maganar na tsaya mishi iya laɓɓanshi.


a hankali cikin natsuwa da kamala ya bude laɓɓansa tare da cewa "Alhamdulillah", ya fada tare da mayar da idanunshi ya lumshe, tsureshi yy da ido na dan wani lokaci kafin ya juya idanunshi, ya dade sosai a gurin Ahmad Sarki kafin ya miƙe, A hankali yace "zan shige", bai ji Amsar da Allaraini ya bashi ba ya fice a binshi.


har ya shige ta gaban wani side mai kyau da tsari, sai kuma ya dawo baya, a hankali ya doshi cikin palon sashen, tura ƙofa yy a hankali yy Sallama, cikin palon yana tura kanshi ciki.


cikin Kaɗuwa da razani Hamshaƙiyar tsohuwar matar da take zaune nannaɗe cikin wata ƙasaitacciyar shiga, mai kyau irin ta Masu fada a ji, ƙarasowa yy cikin palon, ya zauna fuskarshi bb walwala ko kaɗan, fuskarta ta haɗe fiye da Yarda take baya, kyakyawa ce fara tasss da ita, tana da manya idanu, da hanci har baka, sai dan ƙaramin bakinta, yana yin kallon da take bin Sheikh Arman maleeq kawai zai gamsar da cewa akawai wani abu mai kama sa ƙiyayyaeshi a cikin ranta.


Cikin Yar isa da taƙama tare da jin kanta a Sama tace "sannun Isasshe Saukar yaushe ?, yau kuma daga wata duniyar ?, Ya Ubanka yaji da jiki?", ta fada cikin gatsali , idanunshi ya bude ya watsasu akan fuskarta a ƙaro na farko tun da ya shigo cikin palon.


Harshen shi ya taune kafin cikin ƙarfafa harshenshi da kumbura bakinshi, ya ce "Uhmmmm", abun da ya furta kenan bai ƙara kallon in da take ba, ita ma din bata damu da maganar tashi ba, bata kuma damu da lafiyar Mahaifin nashi ba.


a Hankali ta miƙe tayi cikin bedroom dinta ba tare da ta ko kalleshi ba, Sheikh kuwa haka ya gaji da zama ya miƙe tare da barin palon, zuwa sashenshi da bayan na Sarki da Sayya(Mahaifiyar Ahmad Sarki , tsohuwar da ya fita daga sashenta) bb sashen da ya kai shi kyau a cikin Masarautar.

Fadawan da suke a ƙofar shiga cikin sashen ne suka bude mishi, ya shiga cikin palon bakinshi dauke da Kamilalliya kuma cikakkar Sallama kamar yarda Addini ya tanadar, bb kowa cikin palon, sai dai hakan bai hana komai da yake cikin palon yin aiki ba kama daga kan Fankokin da suke kunne da AC har kan hasken da ya mamaye gaba daya palon , wadda ya haska ko ina tanwar kamar rana.



kuma ko ina ƙal-ƙal bb alamar ƙazanta ko wani najasa, a hankali ya fara taka ƙafarshi tsakiyar palon, idanunshi a dan janye, har ya ƙarasa kan kujera 2 siter ya zauna , a hankali ya ƙarasa jaanye idanunshi gaba daya ya lumshesu, yana sauke numfashi a hankali cikin natsuwar da ta zame mishi jiki, a hankali ya dan sanya hannunshi ya fara zare half cover din da suke ƙafarsa, yana sauke numfashi a hankali,har ya gama zarewa a hankali yajaa numfashi tare da furta "Subhnallah wal-hamdulillah waa laaa'illaha'illalahu wallahu Akbar, Suhbanallah", ya furta yana ƙara rumtse idanunshi.

nauyin da ya ji kanshi ya fara mishi sakamakon ciwon kan da ya riskeshi, yasa ya sa hannunshi tare da fara zare farin rawanin da yake kanshi ,bakinshi na kiran sunan Allah har ya gama zareshi.


kyakyawar sumar kanshi da take a barzaze mai kala biyu, ƙasa baƙiƙƙirin irin sumar Asalin Fulani, sai kuma Sama Brown kalar sumar turawa, wadda ta kasance kamar an rinata, sai dai ba rinatan akayi ba, zallar sumar kanshi ce a haka , a hankali ya dago kanshi, tsura mishi idanu nayi , sai dai na kasa ganin fuskar tashi, wadda sumar kanshi ta sauko ta rufe mishi gaba daya fuskarshi, sai dai kyakyawan cute lips dinshi da suka ƙasance pink irin na mata ake iya gani, da kyakywan sajenshi wanda ya haɗe da gumenshi, mai mugun yawa, san har kusan kirjinshi , baƙi sosai irin gemun larabawa.


a hankali yasa hannunshi ya fara zame gashin kanshi da ya zubo mishi akan fuskarshi, da sauri na matsa dan na mugun firgita da yana yin zubin tsarin fuskarshi, dan kallo daya in ka mishi baza ka gamsu cewae mutum bane, abu na farko da Zuciyarka zata fara raya maka shine ba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On ARMAN MALEEK
avatar
batula-yahaya

6 months ago

Reply

08139693951

avatar
daiy

6 months ago

Reply

Replying to batula-yahaya

Me yasa kika ajjiye nambarki kuma

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to daiy

Thanks for tuni

Please Login or Register in order to submit comment