Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya yi tagumi yana zufa.

Maganar zuci ta fito fili, "Oh Allah kusan wata kenan ina kokarin haɗa part din motar nan amman na kasa kash."

Bai san maganarsa ta fito ba sai ji ya yi Zeeyter na, "Mu gani."

Tsaki ya yi afili yana, "Dalla matsa mun ni da gani me zaki iya."

Bata kula shi ba ta fisge Laptop din tana dubawa ta hada mai bangaren da ya kasa kafin ta ajiye masa.

Da mamaki yaga tayi aikin da ya kasa yi awata guda amman ita cikin minti ɗaya tayi ta gama, kallonta ya tsaya yi can kuma ya kawar da kai yana kara jin mamaki.


Ita kuwa takardun ta hada waje guda, har taje kofa zata fita,ta dawo mintsilinsa tayi kafin ta fice da gudu shima ya bita.

Ya ma manta ba a gida suke ba, sai da sukaje tsakiyan compaynin suna guda kafin ya ankare ganin an fara kallonsa.

Kunya yaje ya koma office.

Ita kuwa Dariya tayi tana, "Ai da kazo Wallahi."

Gidan mai ta koma,ta samu Halliru zai je masu visan tafiya singafur saboda za su tafi da wuri ana saura kwana biyu ko ɗaya kan taron domin tsara yadda Shagalin zai kasance.


Kafin ita ta shige ciki domin karasa haɗa takardun waje ɗaya.


Tana gamawa ta kira Deejerh ta fada mata cewa tana bukatar wasu kayayyakin domin za ta yi tafiya na kwana biyu.

Da farinciki ta kunna data ta fadawa Farouk cewa ai abokin aikinta ya cika masu Humanitarian Award kuma sunyi nasara zasu tafi singafur.

Ba karamin farinciki Farouk ya yi ba, ganin yadda Zeeyter take Farinciki,domin hakan shine burinsa a kullum.

"Iyeee kice zamu singafur, Ma Sha Allah na miki murna ko zanzo nima a sakayani ne." Cewar Farouk.

Zeeyter tayi dariya tana, "Eh mana kazo ko a cinya nasaka ai."

Sai Dare Zeeyter ta kara komawa gida ta dibo wasu abubuwan bukatan saboda anan bobiel takeso ta kwana domin kammala aikinsu yadda ko sun tafi singafur babu Matsala.

Har cikin dare Haiydar bai dawo ba,aiki ya masa yawa shi ma a Office.

Hakan yasata daukan takarda ta rubuta masa cewa za ta yi tafiya na kwana biyu ta aje kan table kan ta tafita a wannan tsakar daren.

Tana tafiya ana binta kamar yadda aka saba, tana kunna torchlight sai agudu.

Can kuma taji an damƙe mata wuya ana ƙoƙarin rabata da numfashinta.

Wani irin karfi ne yazo mata,ta mauje mai bin nata tana kokarin makuresa shima.

Fisgewa ya yi y gudu,ita kuwa da kyar ta seta numfashinta kafin ta ci gaba da tafiya.


Haiydar na zuwa yaga takarda dubawan da zaiyi azahiri ya ce, "Mtsw Allah sa ma karki dawo, mahaukaciyar banza da wofi."



Wani takaici ne ya ƙufulesa domin ya tawo da bukatarsa,haka ya shige ya yi wanka kafin ya yi barci kawai.

Ya shige ya ci gaba da aikinsa.

Kwanan Zeeyter biyu A bobiel kafin su tafi har an fara kanun maganganu ai ta kashe auren daman ba iya zama za ta yi ba,ya korota ne.

Wasu ma agaban idanunta suke fada ita kuwa ko a jikinta sai dai ta sake masu Murmurshi, tayi gaba.


Daren yau jirginsu na singafur zai tashi, hakan yasa suka shirya ita da Halliru suka nufi airport.


Haiydar kuwa gabadaya ya ƙosa hakan yasa a daren bayan ya dawo daga Office yaje ya dauko Meenoh.

Amman abun mamakin shi ne sam ta kasa gamsar da shi,tamkar totuwar masara haka ya jita.

Wani irin tsaki ya yi yana hankaɗata gefe.

"Dallah matsa mun kauce anan, abu sai kace rijiya, fita mun agida ki tafi karki ƙara dawowa wannan ba dai ki kawar mun ba sai dai ki zuba mun takaici."

Ya fada yana shigewa toilet.

Tagumi tayi tana mamakin wai ita ce yau Haiydar baya marari ,duk maganin matan da take amfani da su,duk yabonta da yake ya tashi a banza.

"Tabbas wannan munafukar matar ta shi ce sanadi kuma zan dau mataki." Ta fada cikin bacin rai.

Tattara kayan ta tayi ta maida jiki, haka ta bar gidan domin ta san halin Haiydar sarai indai ya furta baya son abu to fa baya so.


Yana fitowa ya fita waje ya siyo giya,ya dawo zai sha kenan har ya zuba a kofi ya kasa sha zeeyter kawai yake tunawa da maganganunta.

Daga karshe ma tashi ya yi yaje ya zubar.

Ya kasa shan giyar kuma ya kasa barci.

Gaɓadaya gidan yaƙi masa dadi.
Tunaninta da kewarta ya fara
Yana, "Ko ina wannan mahaukaciyar yarinyar ta yi oho."



SINGAFUR.....


08103080717
URS XAYYEESHARTHUO
[6/15, 2:06 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *YEL*🦅

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

*LABARI DA RUBUTAWA*
_Aisha Sani Abdullahi_
_*(Xayyeesherthul-humaerath)*_

_*TSOKACI:* Labarina Kirkirarrene ban yi shi don cin zarafin wani ba ko wata, sannan labarina yana dauke da yaruka uku ne zuwa huɗu:*Hausa, French, Turanci, Malay*, Haka Kuma ka/ki faɗi alkairi ko ka/ki yi shiru! Yadda ki/ka ga labarin haka tsarinsa yake kuma babu canji,Salon na Mussamman ne sannu a hankali komai zai bayyana🦅_

_R.I.J.F. Little Baba *(Suhaan)*😭_

*PAGE-29*
Bismillahir-Rahmanir-Rahim

*MILKY ICE*

Masu son koyan Ƙanƙarar madara ga dama ta samu.

Abun bukata.
Madara
Sugar
Filebo
Madarar kunun Aya
Food color (in kina da bukatar ya yi kala)

Zaki dama madarar da ruwan zafi kar ya yi gudaje,sai ta damu kamar zaki hada tea sai ki zuba ruwan sanyi daidai yadda gardin madarar ba zai fice ba.

Kisa filebo,da madarar kunun Aya daidai yadda zai fito kuma ba zai yi daci ba.

Sannan kisa suga shima daidai yadda zai fito, in kina son yin kala biyu sai ki raba ɗaya kisa food kalo ɗaya kuma ki barsa a kalansa milk kenan.

A sha kankara lafiya, in ta saidawa ne zaki siyar goma-goma.

★★★

Suna isa kai tsaye suka riski driver har ya iso yana jiransu .

Masauki ya kai su.

Zeeyter ta shiga toilet tayi wanka a hotel din,haka ma halliru dake ɗayan dakin.

Bayan sun fito ta duba riga acikin kayan da deejerh ta hado mata ta sa, duk da cewa ba ta yi wata kwalliya ba,amman ba karamin kyau tayi ba, Mussamman yadda rigar ta tafi da jikinta.

Abinci ta zauna ta ci kafin Halliru ya shigo kan cewa suna da interview da su kafin afara taron.


Gabadaya kowa ya halla illa su Zeeyter, suna shiga wajen kuwa sauran turawan suka fara binsu da kallon banza.

Wata a gefe suna haɗa ido ta gallawa Zeeyter harara.

Murmurshi tayi kafin daga baya ita ma ta bita da hararar tana mika mata hannu su gaisa.


Sai da ta gama gaisawa da sauran,su doctors ne, Engineers ba irin mutanen ba a tara agun ba duk suna cikin participant ita kadai ce Yar Afrika.

Bayan sun gama ta koma wajen alkalan suka gaisa.

Sai da akayiwa kowa tambayoyi kafin aka zo gun Zeeyter.

Da mamakinsu yadda ta tashi tana jawabi da confidence dinta sannan kuma tana zubo turanci tamkar ba Yar kasar Nijar ba, kai kace wacce tayi jami'a abun ya matukar birgesu ba kadan ba.


Ana gama tattaunawar wannan baturiyar na kule da Zeeyter hakan yasata zuwa ɗakinta ta kulle mata kofar ta baya sannan kuma ta dauke keyn.


Halliru yazo kiranta domin tafiya dakin taro amman ina sam ta kasa buɗe kofar domin wannan ba irin mutane wacce ta saba buɗewa bane.


Lokaci ya kure har an shiga dakin taro.

Cewa tayi Halliru yaje kawai ta zauna a dakin tana zubawa sarautar Allah ido.


Kamar daga sama halliru ya ga Farouk gabansa yana, "Ina Madame din? Lafiya dai ko."


Jiki a sanyaye Halliru ya yiwa Farouk bayanin komai.

Gashi har an fara kiran sunan Zeeyter Amman babu ita.


Cikin takaici Farouk ya shige ciki, wani ma'aikacin hotel din ya samu ya karbi wani keyn awajensa ya budeta.

Za a wuce kenan ganin cewa bata zo ba sai ga sautin muryarta tana, "Here Am I."


Tsaki wannan baturiyar tayi tana jin takaici tamkar ta kufule kanta.

Tashi tayi zata fita, Zeeyter ta karasa daidai kusa da ita a hankali ta ce, "Thank you Mah." Ta karasa tana sakin Murmurshi.


Kallon tayi tana sakin tsaki kafin ta wuce.

Abin mamaki kuwa Zeeyter ce ta cinye aduk cikin kimanin Mutane dari da dauri dake kasashen waje.

Farinciki ya sa ta gagara rufe baki,yan jaridu,gidan Tv gabadaya sun baibayeta,ba abun mamaki da ya wuce karancin shekarun ta da kuma kasancewar ta 'Ya mace amman
ta take manyan maza da manyan matan kasashen ketare.


An bata makuden kudade kimanin 3 thousand Dollars da wasu yan kyautuka, certificate da Award, gaba-daya abu ya gama karade duniya cikin kankanin lokaci
Sujjada tayi afilin tana mika godiyar ta ga Allah.

Farouk da Halliru ban da washe baki ba abunda suke, tsabar farinciki Zeeyter bata san lokacin da ta rungume Farouk ba.

Bayan an gama taro an watse Suka zauna Zeeyter ta kalli Farouk ta ce, "Ya akayi haka? Me ka zo yi ko kaima kana ciki ne?"

Murmurshi Farouk ya yi ya na nuna halliru , "Abokina ne ya fada mun kunzo ni ko na ce dole inzo in ga Gimbiyata."


Halliru kuwa a zuciyarsa ya ce, "Madame duk wannan nasarar ta mu shine sila,shine silar Murmushinki a yau,ban da kuma wasu abubuwan da baki sani ba."


Suna cikin hira Zeeyter ta miƙe zumbur tana, "Ni fa yau nake son komawa gida, ince zamu samu jirgin da zamu hau ai."


Farouk ya tashi yana, "Haba Gimbiyata ba za ko ki bari mu kwana muna hira ba, kamar ana korarki? Ko dai kina kewar Haiydar ne?"


Tsaki ta yi ta ce, "a kan me zanyi kewarsa? Shi baiyi tawa ba sai ni, lallai kunci kai kai da abokinka,ni dai ina son komawa gida idanuwana sunata saƙa mun wani abu mai mahimmanci da ya kamata inyi shekara da shekaru ban samu dama ba, Amman yau kam Alhamdulillahi In sha Allah kowa zaiyi Farinciki bani kadai ba,kuma ba mu kadai ba."


"Ban fa yarda ba,na san duk wannan damuwar taki bai wuce ace ki ga Haiydar ba, na san abokina da shiga rai."Farouk ya fada yana dariya.


"Eh din naji ma shi nake son gani,ko ba komai mun kwana biyu ba mu yi rigima ba, nayi kewar rigimarmu amman ban da shi,don haka ina komawa shi zan fara tsokalowa."


Zeeyter ta fada tana dariya.

Farouk ya ce, "alright tun da kin dage bara naje inyi magana mu ga ko za asamu."


★★★
"Zoe Wake-up, Wake-up Please Baby." Wata matashiyar baturiya ta fada tana dan bugawa Yarinyar ta ta filo a hankali.


Cikin Muryar Barci ta ce, "Mom Live me please I'm feeling Sleepy."


"Baby ki tashi Sorry wasu ne suke buƙatar Ki tukasu zuwa Nijar."


Zoe ta ce, "Mom su nemi wani barci nake ji sosai ku barni mana,hutuwa nake,ina bukatar hutu."

Jan filon ta kara yi ta Ci gaba da barcinta, sai da tayi mai isarta can kuma kamar an tsikareta ta tashi da sauri ta shige toilet tayi wanka ta fito.

★Zoe matashiyar budurwar mai shekara ashirin da shida cif aduniya. aduniya,babbanta Hamshakin mai kudine a singafur, bata da sha'awar komai da ya wuce tuƙin jirgin sama, wanda take ason ranta kawai ba wai don kudin ba,domin in dan kudin ne tana daga zaune sai dai tayi umarnin abata, Yar Gayace takin karawa sannan kuma kyakkyawa ajin farko,bata cika shiga sabgar mutane ba sai dai in taku tazo ɗaya,ita kadai mahaifinta ya haifa hakan yasa shi sakaltata ta kowanni bangare,sannan Christen ne su,tun tana karamarta take da burin zama matukiyar jirgi hakan kuwa ya kasance tun kan ta girma ta fara, tana karatu tana tuƙi har ya kai ga ta girma kuma ta gama karatu.


Zeeyter, Farouk da Halliru suna zaune a airport har Zeeyter ta fara ƙula.

Tawowar Zoe ne ya dakatar da su daga maganar da suke, tafiya take tamkar ba za ta yi ba, Farouk gabadaya ya tafi da kallonta,suna haɗa ido ta galla masa harara, maimakon ya maida mata hararar sai ya sake tsaki.

Zuwa tayi ta karbi wani file ta nufi jirgin da kwarin gwiwarta zata tayar Amman ina sam jirgi yaƙi tashi,fitowa tayi tana ma ma'aikatan gun magana, "waya shiga cikin Jet din nan yau."

"Nobody Mah" suka fada.

Tsaki tayi ta koma ba inda bata duba ba, Amman sam ya gagara.

Zeeyter ce ta tashi ta bita Farouk ma ya bi bayanta.

Tana shiga jirgin ta ce, "taimake ni da box din cen naki."

Mika mata zoe tayi kawai ta tsaya.

Tana budewa ta fara gyara ashe wata waya ce ta harde, Farouk ya ce, "Gimbiyata ni kam mene ne baki iya ba arayuwarki?"

Zeeyter ta ce, "Kisa amman watakila shi ma zan fara akanka."


Dariya ya yi yana, "Ba matsala ai indai kece."

Zoe aranta take fadin, "Ina ga wa innan mata da mijine."

Zan kuma ta ce, "Mtsw to ma ni miye damuwata da su in ma mata da mijinne."

Ganin yadda Zeeyter ta duƙufa tana gyaran sai taji gabadaya ta birgeta,binta kawai take da kallo cike da mamaki, gata bakar fata.



Zeeyter na gamawa ta ce, " Ma sha Allah Madame xa ki iya tadawa yanzu mu ga."


Da mamaki tana tadawa kuwa ya tashi.

Dawowa tayi wajensu ta ce, "Sunana Zoe ni ce wacce zan tuƙaku zuwa Nijar can we be friends?"

Ta fada tana mika mata hannu.

Zeeyter ma ta mika mata, "why not? Nayi Farincikin haduwa dake ni kuma Zeeyter."

Karaf Farouk ya katse su da fadin, "Ni kuma fa? Anyi ƙawance da Gimbiyata saura ni."

Dariya suka yi duka zoe ta ce, "Kai ma Abokine daga yau."

Sai da suka yi exchanging numbers kafin suka yi sallama da Farouk ya koma hotel don shi ya ce sai washegari zai koma Malaysia.


Cikin kankanin lokaci zoe har ta sake jiki da Zeeyter sun saba.



Haiydar na zaune falo ya yi tagumi, Girmankai ya hanasa kiran wayar Zeeyter ga zuciyarsa fal take da kewa da muradinta.



Kamar daga sama ya ji an turo kofa, yana daga ido sai ga Zeeyter gabansa.

Kamar zaiyi magana kuma sai ya yi tsaki yana kokarin shigewa ɗaki.

Janyo shi tayi tana, "Kawu ko Oyoyo ba za amun ba,wai shin baka yi kewata bane?"

Fincike hannunta ya yi anasa yana, "Wane ne kawun? In rasa kewar wa zanyi sai ke,tur."


Zeeyter ta ce, "Oh ba ka yi kewata ba? Zanyi maganinka kuwa ni ce ai, bara inyi wanka inzo ."

Tsaki ya yi ya koma kujerar ya zauna yana duba wayarsa.

Tana shiga tayi wanka tayi sallah tukun tasa kayan barci ta fito.

Zama tayi daf da shi tana, "Har wani ramewa ka yi fa,ko dai da bana nan kayi ciwo ne? Ji goshin yadda ya kara fitowa kamar jirgi."

Karasa maganar tayi tana dariya tare da taba goshinsa da hannunta.

Bige mata hannun ya yi ya ci gaba da danna wayarsa.

Karaf ta fara yi masa kiss gaba-daya ta gama sakar masa da jiki, sai da ta gama tsokanosa ya sake yana mai da martani ta tashi da gudu ,bin ta ya yi,amman ina har ta shige daki ta kulle kofar.

"Ba za ki bude ba wai? Wannan wace irin mugunta ce, kin san......"

Sai kuma ya yi shiru.

Dariya Zeeyter ta fara tana, "ni ba sa'arka ba ce ai na faɗama daman zan yi maganinka,maza kaje ka kira wannan yarinyar nikam ma nayi barci."


"In baki bude ba wallahii sai na sa miki kadangare ta window na fada miki,kin san bana wasa da ke."

Zeeyter na jin hakan ta bude masa tsilif don tasan zai aikata Gwanda ta ƙara gumamai ta wani bangaren.


Gaɓadayan su cikin bagen juna suka raya wannan daren, Mussamman Haiydar.




Washegari da sassafe Zeeyter ta fita.

Zuwa tayi ta samu masu yin aikin titi,ta masu bayanin tana so ayi titi a bobiel da ƙauyuka biyu da suke cikin garin.

Nan take suka gama tsara yadda komai zai kasance suka yi lissafi sannan ta daura Yusuf a kan wanda zai lura da hakan.

Ta ce sam ba za ta ci wannan 3Thousand dollars din ba, sanadin al'umma ta samu,kuma su za ta yiwa aiki,hakan yasa bayan sun gama lissafi ta duba sauran ƙauyukan da ke fama da wahalar ruwa ta sanya a masu bohol.
★★
Zaune yake a office yaron da ya saba kawo masa jarida ya yi sallama kafin ya shiga ya ajiye masa kan table.

Daga kan da zaiyi Shafin Farko ya ga hoton Zeeyter dare dare.

Tashi ya yi tsaye cikin mamaki dauke da jaridar a hannunsa.
Kara kallo ya yi ya tabbatar dai ita dince kafin ya zauna ya fara karanta tarihinta.

Yana karantawa maganganun Farouk na mai yawo a azuciya, sai yanzu ya fahimci tafiyar da tayi da kuma inda taje. a zahiri ya furta , "YEL." nan take kwakwalwarsa ta fara tunano masa abubuwa da dama har ma ranar da suka fara faduwa suka bangaje juna,ranar da ta hau kan motarsa ta zauna,da kuma farkon zuwanta Compaynin sa.

"Ba musu Zeeyter ita ce wacce Farouk ke bani labari,amman Meyasa ban fahimci hakan ba?"


Ya yi shiru can kuma sai ya ci gaba, "To taya ma zan fahimci wannan mahaukaciyar yarinyar."

Murmurshi ya yi kawai ya dauke jaridar ya mai da cikin dirowa sannan ya ci gaba da aikinsa.



Dare na yi ya koma gida, tun daga bakin get yake jin sautin kiɗa na tashi, da hanzari ya shiga don atunaninsa ta tara masa mahaukata ne irinta a gidan.

Ita ɗaya ce tanata tikar rawarta.

A fusace ya karasa ya kashe yana, "ke wai Mahaukaciyar ina ne? Baki san cewa dare bane zaki sake wannan uban karan."

Tsaki tayi, "ina ruwanka dani? Ina ruwanka? Kai ma ka kunna mana kowa ya yi rayuwarsa ba matsi."

Ta karasa maganar tana kuma kunnuwa.

Kashewa ya kara yi

Ta kunna.

Ganin ba za ta fasa ba yasa shi shi ma dauko ɗayar speaker ya kunna ya ƙure volume din kamar nata.

*ZUCIYATA BA DADI WALLAHI SAM NA KASA KARASA TYPING DINNAN,KU MUN ADDU'A DAMA DUK WANI MAI DAMUWA ALLAH YA YAYE MANA YA BIYA MANA DUK BUKATUNMU NA ALKAIRY DUNIYA DA LAHIRA😭🙏🏼*

_*masu son shiga Group dina kumun magana ta number nan zan saku in sha Allah*_

08103080717

Xayyeesherthou
[6/16, 9:46 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *YEL*🦅

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

*LABARI DA RUBUTAWA*
_Aisha Sani Abdullahi_
_*(Xayyeesherthul-humaerath)*_

_*TSOKACI:* Labarina Kirkirarrene ban yi shi don cin zarafin wani ba ko wata, sannan labarina yana dauke da yaruka uku ne zuwa huɗu:*Hausa, French, Turanci, Malay*, Haka Kuma ka/ki faɗi alkairi ko ka/ki yi shiru! Yadda ki/ka ga labarin haka tsarinsa yake kuma babu canji,Salon na Mussamman ne sannu a hankali komai zai bayyana🦅_

_R.I.J.F. Little Baba *(Suhaan)*😭_

*PAGE-30*
Bismillahir-Rahmanir-Rahim

_*Jiya tsabar bana seti nasa page 29 maimakon 28 yau mu fiske hakan kawai anje 30😹*_


*TALLAH*
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._

★★★

Ita kuwa ko ajikinta rawarta ta ci gaba da tiƙa, daga karshe ya tsaya yana kallonta kawai.


Sai da tati mai isarta kafin ta kallesa tana gwalo ta nufi ɗaki.

Shiga ɗakin da zata wata irin gigitacciyar ƙara ta ƙwala wacce ba iya gidan ba sai da anguwar ta amsa.

Cikin sauri Haiydar ya ƙarasa kan kace miye har ta sume agun.

Ƙadangaru ne fal tsakar ɗakin irin jajayen nan manya-manya.

Daukanta ya yi ya nufi ɗayan dakin da ita kafin ya dawo ya kulle wannan.

A hankali ya shafa mata ruwa afuska,cikin razana ta farfaɗo tana,"Bana so na ce Wallahi bana so,ka daina samun wannan abun kasheni za suyi bana son su,bana so."

Ta fada tana fashewa da kuka tare da matsawa daga garesa.

Kokarin riketa yake amman ina sai rawan jikinta yake tana kara matsawa.

"Mugu bana son ganinka ka bar nan mugu kawai,bana so,ni nace bana so,kuma wallahi sai na rama."

Tsawa ya daka mata, "mahaukaciya kawai ki barni inyi magana ma ba za ki iya ba tsabar hauka? To sai kita yin, kiyi abun da zaki yi nasa miki din."

Ko kallonshi ba tayi ba, ta kara matsawa can karshen gadon,tana rufe ido ba abun da take gani sai wannan kadangarun gabadaya ta birkice ta fita a hayyacinta.

Tsaki ya yi ya tashi ya fita yana, "sai kita haukar taki ke ɗaya ai wawiya kawai."


Ta kasa sakewa sam, ko kyakkywan motsi ta kasa,ita kadai sai firgita take tana hawaye.

Ga wata irin yunwa da ta fara ji, har yaje ya zauna zai ci abinci sai zuciyarsa ta fara raya mai, "Yanzu haka wannan Mahaukaciyar ma ko abincin bata ci ba."

Kitchen ya shiga ya dibo mata,kafin ya bude kofar dakin ya wula mata Plate din ya fice abinsa.

A hankali ta rarrafo ta dauka tana murguda baki, "ai wallahii sai na rama nima, mugu kawai."

Zagewa tayi ta ci abincinnsn tamkar sabuwar kamu,tana gamawa kuwa barci ya kwashe ta.

Cikin daren Haiydar ya samo wasu maza suka kwashe ƙadangarun duka,yana mamakin yadda aka yi suka shiga dakin kuma da uban yawa haka.

"Dole akwai wani boyayyen lamari." Ya furta a zuciyarsa.


Ɗakin da take ya koma, ganin yadda ta kanƙame a karshen gadone ya matukar basa dariya.

Ganin baya jin barci hakan yasa shi bude data, yana budewa kuwa sai ga sakon Farouk.

"Hello Friend, Ya Gimbiyata ta isa gida Lafiya? Muna taya murna Allah kara daukaka."


"Gimbiyarka? Na bi gimbiya da gudu ka kiyayeni da gimbiyar nan fa tom." Cewar Haiydar dauke da emojin kashedi.


Dariya Farouk ya yi yana, "Eheen Gimbiyata mana,ko taka ce? Na ga business Marriage ne bare ace za a kafa mun sharadi."


"Oho dai,ni dai na fada ma ka kiyayeni da wannan sunan."


"Gimbiyata sai na fada fa,ba ma wannan ba,maganar da nake so muyi shine,tun da naga tana ta kokarin daga wannan ƙauyen nasu mai zai hana ka sai fili babba acen Khaleel ya tsara maku gida da makaranta aciki yadda komai zai wadata,ina tunanin hakan ba karamin faranta mata rai zaiyi ba,sannan kuma kun ƙara daga ƙauyen a takaice ka jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya."


"Kuma ka yi tunani mai kyau fa,don ni ƙauyen ya birgeni sosai ko da naje yafi wani cikin garin ma,basu da matsalar wuta bare kuma ruwa, Ma sha Allah,in sha Allah zan yi Magana da Khaleel din,amman kar ka bari ta sani ya kasance abun yazo mata ba zata." Haiydar ya rubuta yana kallon Zeeyter da ta jima da lulawa duniyar barci.



Farouk ya ce, "Owk As You wish."

Daga nan suka nufi Discussion group din su, gabaɗaya sai murna suke taya Haiydar da Zeeyter kasancewar abun ya karade duniya duk sun ji labari.


Daga nan yama Khaleel maganar yana son siyan fili a bobiel da kuma yanayin gidan da yake so a Private.


Khaleel ya ji dadi sosai hakan yasa da kan shi ya bada umarnin aduba masu babban fili wanda zai isheshi wajen fidda duk wani abu na bukata.


WASHEGARI

Kafin ta tashi har Haiydar ya ya yi sallah ya fice training.

Ita ma tana sallah tayi wanka tare da sanya kayan sport dinta ta fita.


Yana cikin gudu ya ji karaf an bangajesa.

Zeeyter ce tana sakin tsaki.
Ta ci gaba da gundunta.

Binta yayi shima da gudu zai bigeta,ta bangaje shi ya fadi a kasa sai da ya bige kai.

Dariya tayi ta tafi abun ta.

★tana komawa gida suka ɗaura kayan breakfast ita da mai aiki.

Sai da suka kammala ta ci kafin ta wuce bobiel abinta.

Haiydar ne yasa wani dan sanda yana binta a baya ba tare da ta sani ba,domin kwana biyu sam bai yarda da yanayin ba,ya fara fahimtar akwai wani boyayyen lamari.


Tana zuwa Bobiel suka fara shirye-shiryen taron wayar da kan da suka saba don ranar ne za aci gaba, tattaunawa kan mahimmanci sana'a, tare da karatu ga 'Ya Mace.

Madame Ayshe da Naddja sun gama tsara komai.

Don haka Malamar da aka kirawo ta fara jawabinta.

"Assalamualaikum barkanmu da kasancewa a wannan rana mai daraja, sunana Madame Surayyah sannan zamu tattauna kan mahimmanci sana'a da kuma karatu ga

'Ya mace ne, abun na matuƙar sosa mun rai ko ince bani mamaki wai ace karatun 'Ya mace bai da amfani ko kuma yin sana'ar ta baya da amfani,

a aurar da ita ta zauna tayiwa miji da 'Ya'Ya bauta Shikenan rayuwar 'Ya mace? Aa sam ban yarda ba,kuma ba zan taɓa yarda ba ko da kuwa acikin mafarki ne, don kina

'Ya mace baki zama bola ba,kuma ba ki zama baiwa ba,mutumce kamar kowa,nemi ilimi ta kowanni bangare yadda da an taɓaki zaki kare kanki,

babban kalubale da ke kanmu matan musulmai ya fi afkuwa a asibiti yadda ake wulaƙanta mu ake disga mu cikin jama'a don kawai bamu yi karatu ba,shin ba

Please Login or Register in order to submit comment