Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanzu bangaren ma'aikata fa? Ka tabbatar kowa bai da matsala? Ina so ka bincika duk wani mai Matsala a sanar dani, sannan a magance masa indai bai fi karfinmu ba,kada ka manta da wannan tsarin ma'aikatan mu tamkar danginmu ne,damuwarsu ta mu ce,haka matsalar su ta mu ce,a tabbatar kowa bai da damuwa domin yin aiki mai inganci cikin sauki."


"Yes Madame ban manta da wannan tsarin ba, domin duk wanda ya taso karskashinki dole ya karanci hakan, na kan tambayesu duk wani mai Matsala kuma ina magancewa kamar yadda kika saba akwai bayanan komai acikin wancen file din,dake kanune matsalolin yasa ban saki ciki amman indai da babba dole sai na sanar miki kafin yanke kowanni hukunci."

"Owk to Shikenan Allah yasa mu dace." Zeeyter ta fada tana tashi.


Haiydar na fitowa wanka ya duba ko ina bai ga Zeeyter ba.

"Oh My God,ko yaushe Yarinyar nan zata gama hankali tana nutsuwa oho, Shikenan tunda ta dawo seti ai na shigai abun da ba ayi da ba ma za a fara,Mutum ya dawo daga tafiya ta tsaya tayi wanka ta hutu ma aa bare kuma batun cin abinci,oho dai ita ta sani Let Me take my Food." Ya fada yana ƙarasawa wajen daining.

Sai da cikinsa ya ci yaji ya ƙoshi tukun ya dau wayarsa ya fara dannawa.

Zeeyter kuwa na fitowa daga kamfani ta shige cikin anguwar gani tayi duk anyi ruwa ya taru ga shara ta cika waje Cebur ta dauko tana jan ledojin da suka hana ruwan tafiya.

"Maddalla An dawo kenan,ni a tunani ma kin mutu ne ashe da sauran kwana,da na ji labarin gobara a gidan manki ai a tunani na harda ke cikin wa inda suka rasa ransu."

Dagowa tayi cikin mamaki tana kallon Dpo dake tsaye fuskarshi fal walwala.

Dariya ta yi kafin ta ce, "Ayyah ka san cewa mutum baya taɓa barin duniya ba tare da kwanansa ya ƙare ba,ko da za ata hankaɗasa kabari sai Allah ya nufa,gani kam da raina Alhamdu Lillah ina numfashi kamar kowa."

Wata irin dariyar Mugunta ya yi yana faɗin, "maddalla na ji dadin ganinki araye domin kuwa har yanzu burina bai cika ba,amman fa na miki murna kasancewar kubutar da kika yi matuka wannan ai babbar nasara ce, And ina kara miki murna karo na uku bisa kara gyara miki gidan mai da aka yi,tabbas kin samu miji ko ince kin samu kudi,hakan ya matukar birgeni."


"Godiya nake sosai,miji kam na samu mai jin kai da goyon bayana, Alhamdu Lillah, ko zaka iya ƙarawa gaba?."


Tsaki ya yi ya ce, "Hakan ya mun kuma zai ci gaba da mun amman ki jira wani lamarin da zai afku anan gaba,walwala,karfin gwiwarki da duk wata jarumta sai an nemeta an rasa bare kuma jajircewa."
Ya ƙarasa maganar yana kokarin sa hannu a jikinta.

Riƙon da aka masa ne ya sa shi saurin juyawa.


Haiydar ne cikin zafin nama yake magana, "da ka bari hannunka ya taɓata da kayi babban dana sani wanda baka taɓa ba arayuwa, MATATACE, tawa ce, Alhakina ce kuma rayuwata ce, kada ka kuskura ka yi kokarin shiga gonar da ba taka ba,ban san me ya hadaku ba amman ina mai kara sanar maka cewa ka tsaya iya matsyinka."


Fisge hannunsa ya yi yana, "Kasan ni wane ne da za ka zo kana fada mun magana son ranka? Na ce kasan ni wane ne? Kuma ma maganar ba akan kowa ba sai akan wannan watsattsiyar Yar Tasha mara gilihu yar Lingo? Ga dukkan alamu baka.....

Bai karasa ba sai jin saukar mari ya yi da duka ta ko ina.

Cikin fada Haiydar ke magana, "Zan iya hakuri ni a za geni in kyale,kuma zan iya hakuri ni aci zarafina in bari, zan kau da kai ko da dukana za ayi amman kada ka kuskura kai kokarin taɓata ko cin zarafinta ka nemawa rayuwarka salama ta hanyar kaucewa duk wata hanya da zai kasance ka kuntata mata." Ya fada yana nuna Zeeyter da hannu.


Dakyar Dpo ya samu ya tsare aguje,ko takalmi babu sai jiki na rawa kamar mai naguda amman duk da haka bai daddara ba yana gudu yana fadin, "Wallahi sai ka sha mamaki indai ina raye za ku sha mamaki sai na jefa rayuwarta cikin garari zan ga yadda za ka yi."

Tsaki Haiydar ya yi.

Zeeyter tayi kokarin ƙarasawa garesa tana rikosa bigeta ya yi ya wuce yana wuce kamar bijimin sa,tana mai magana ko ya tanka, direct ya je ya shige motarsa tare da yi mata wani irin figa ya tafi.


Mamaki ne ya kama Zeeyter ta tsaya kawai tana kallon ikon Allah,daga karshe ta shiga cikin gida, wayarta ta dauka ta kira Numbersa,amman sam yaƙi dagawa.

In yaga kiran ma tsaki yake ya kashe.

Tafiya yake cikin sauri ba abun da yake ganowa a idonsa sai Dpo dake kokarin sanya hannunsa jikin Zeeyter.

Da karfi yake maganar yana, "Me ya haɗata da shi? Me yasa take kula shi,har hannunsa a jikinta? Ba zan jure ba, sam ba zan jure hakan ba, Meyasa za ta bashi damar hakan?"

Tafiya yake kawai ba tare da yasan inda yake nufa ba.

Saura kadan ya yi accident ya tsaya.

Ganin dare ya yi Haiydar bai dawo ba yasa Zeeyter tayi wanka ta sa wasu fitattun kayan barci da Deejerh ta aiko mata.

Ba karamin kyau ya yi ba tare da fito mata da yanayin jikinta.



Tana zaune tana duban agogo har karfe 12 na dare ba Haiydar ba labarinsa.

Ta shi tayi tana kokarin shigewa ɗaki buɗe kofar da ta ji anyi ne ya dakatar da ita.

Haiydar ne dauke da kwalbar giya a hannunsa.

Kallo ɗaya ya mata ya kauda da kai,tare da zama kan kujera yana kokarin bude giyar.

Cikin fushi ta karaso ta kwace tare da fara yi masa kiss.
Sai da ta gama kashe masa jiki kafin ta ja shi, suka koma daki.

Nan take Haiydar ya manta da wani batun ɓacin rai tare da lulawa wata Duniyar.

*Masu nema daga farko da masu bukatar shiga group ga number nan dalilin da yasa nake ajiyewa kenan*
08103080717
Urs Xayyeesherthou
[6/23, 12:11 PM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *YEL*🦅

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

*LABARI DA RUBUTAWA*
_Aisha Sani Abdullahi_
_*(Xayyeesherthul-humaerath)*_

_*TSOKACI:* Labarina Kirkirarrene ban yi shi don cin zarafin wani ba ko wata, sannan labarina yana dauke da yaruka uku ne zuwa huɗu:*Hausa, French, Turanci, Malay*, Haka Kuma ka/ki faɗi alkairi ko ka/ki yi shiru! Yadda ki/ka ga labarin haka tsarinsa yake kuma babu canji,Salon na Mussamman ne sannu a hankali komai zai bayyana🦅_

_R.I.J.F. Little Baba *(Suhaan)*😭_

*PAGE-35*
Bismillahir-Rahmanir-Rahim


*TALLAH*

_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._
★★

Sai da suka farantawa ransu rai a wannan daren yadda ya kamata kuma ya dace.

Washegari
Haiydar ya gama shiri tsaf Zeeyter ta hada masu break da kanta.

Ci yake yana santi tare da yin godiya.

Sai da ya ci ya koshi tana gyara daining din yazo ya rike mata hannu tare da rufe mata ido da ɗayan hannun.

Sai da suka je filin gidan kafin ya bude mata ido yana, "Surprise."

Mota ce Sabuwar ƙira , wacce ya kasa haɗa bangarenta ta haɗa mai ranar.
Hakan yasa ya fara fito da biyu na shi da nata.

Bude baki Zeeyter tayi cikin yanayin mamaki tana, "Sunshine na waye ne wannan motar? Ta mun kyau sosai."

"Just For yhu My Bright Eye, I said Just For yhu, kiyi yadda kike so da ita." Haiydar ya fada yana mika mata keyn.

Kin karban keyn tayi ta ce, "Amman ni.......

Kafin ta yi magana ya rufe mata bakin da kiss, "Ki yi shiru bana son musun nan naki, na san kina da kudin siya Amman wannan kyauta ce daga gareni ban damu ba don kince ba za ki hau ba,amman motar nan da sunanki nayi kuma da sunanki zata kasance, kin ga cen?."
Ya fada yana nuna mata motar da hannu

Kafin ya ci gaba da Magana.
"Sunanki ne jiki, kamar yadda ɗayar tawa take dauke da sunana, karo na farko ki karbi kyauta daga gare ni ko zan ji dadi araina duk da cewa ban san ko kina sona kamar yadda nake sonki ba, kuma ba ki taɓa nuna hakan ba,amman Please ka da kice zaki maida mun wannan kyautar ina son kasancewar ki da ita,ki duba wayarki na tura miki App din Software din da za ki yi amfani da shi wajen driving."



"Sunshine." Abun da Zeeyter ta furta kenan da ya dakarta da shi daga shiga motar.

Da gudu ta karasa ta rungumesa tana fadin, "I love you, I mean I Really Love You, U mean D world to me,
How can I explain my feelings to you. Its pain, its numbness, its like I can see only one thing, hear one thing and think about one thing. That is you.
You know what?
U are the one who i can open up to. I feel so compotable in ur presence. And
Ban yi karyar cewa ba zan rayu ba in babu kai, amman ina so kasani cewa rayuwata ba za ta taba samun

walwala ba har sai da kai cikinta, ka rayu dani har ƙarshen numfashinka,daga yau gobe,anjima har ma da kullum kasa aranka cewa nima ina sonka."


Wani irin hamshakin Murmurshi Haiydar ya yi tare da saukar wani sanyi a zuciyarsa.

Ya kara rungumeta yana, "Love Yhu More Bright Eye,But Just Remember You Mine,Mine Only, ki kula mun da kanki, byee byee."

Ya kara sauke mata kiss a goshi Yana kokarin shiga mota.

Zeeyter ta yi Murmurshi tana , "Adawo lafiya, amman ka dawo fa sai munyi lissafi na biyaka kudin motarka ehee, kuma in zaɓa ma gun parking kowa ya dunga yi agunsa."

Dariya Haiydar ya yi yana, "Ciwon ya dawo kenan Ok what Ever bari in dawo ina daidai da kowani irin yanayinki ai kin sani."

Dariya tayi ta shige ciki tana, "Oho dai."

Driving yake amman gabadaya tunano maganar Zeeyter yake yana sake Murmurshi.

Ita ma din kamar haka har ta koma ta gama shiri inta tuna shi kawai sai dai tayi dariya.

"Mamaki nake,wai nice na fada tarkon soyayya? Imagine,ina son shi sosai fiye da zato ko tsammani na, rayuwa ke nan."

Sai da ta gyara gidan tsaf kafin ta nufi gidan mai.

Tana zuwa ba jimawa sai ga Halliru ya shigo tare da sanar mata cewa tayi baki.
Bada izini tayi kan cewa su shigo.

Maman Yusuf ce da wasu mata su biyu.

Ba karamin kyau tayi ba da ƙiba kana ganinta kasan cewa tana cin na kanta kuma zaune take cikin kwance hankali.

"Barka dai Madame kwana biyu ashe bakya kasar inata zuwa sai ace bakya nan sai jiya Yusuf yake sanar mun ai kin dawo."

Murmurshi Zeeyter ta yi ta ce, "eh wallahi mun dawo,ga waje nan ku zauna mana Bismillah."
Ta karasa maganar tana nuna masu wajen zama.

Bayan sun zauna an kawo masu ruwa sun sha zeeyter ta ce, "Ya kike? Ya sana'a ya kuma Baban Yusuf."

"Alhamdu Lillah Madame muna lafiya ya ma ce agaida ki shi ma yana nan tafe yi miki barka da dawowa yanzu ma kawaye na ne na rako Aminatou da Aishatou ."

Kallon su tayi tana, "Barkan ku dai Ameenatou da Mamana Ayshatou me ne ne matsalar ku? Allah sa ina da hali ko ikon Taimakawa."

Dukansu suka ce, "Barka dai Madame."

Kafin Ameenatou ta fara magana, "Matsala ce tsakanina da mai gida na dana fadawa maman Yusuf shi ne ta ce zata kawo mu gunki domin ita kam tunda kika bata shawara matsalar zamantakewar su ta kau kuma mu kanmu mun ga zahiri har sun zam abun kwatance a gare mu."

Zeeyter ta numfasa tana, "Alhamdu Lillah ina jin ki."

Ameenatou ta ci gaba da fadin, "Tunda na Aure shi bai fi wata gudu kacal bane muka yi rayuwar farinciki ta aure tun daga lokacin da abubuwan da iyayena suka kaini da shi suka kara komai ya sauya, komai a wulakanci kuma komai cikin tozarci,ya maidani tamkar baiwa sai dai yazo ya kwanta dani kawai ba batun wata soyayya domin har ma na manta da yadda ake yinta, sannan maganar abinci kuma kullum a Wulaƙance zai bamu kuma da wadatacce ba daga ni sai yarona karami shekarar mu ɗaya da aure amman komai a ƙaiyade yake ban isa in taba abu ya wuce kima ba,hatta magin da zansa a abinci guda biyune , Shinkafa kuwa rabin gwangwani ni da yarona,abun karyawa naira hamsin ne a kullum, ban isa in kusance shi da magana mai dadi ba,kullum cikin fada da hantara muke,in ina son abu sai dai in dau wani abu na kayan in saida,inna kai kara gida kuma sai dai ace in ci gaba da hakuri haka rayuwar aure ta gada,a kullum maganar kenan." Ta karasa maganar tana fashewa da kuka.

Cikin yanayin tausayi Zeeyter ta ce, "ba kukq zaki yi ba,kiyi shiru in sha Allah komai ya kau kuma komai ya wuce indai zaki bi shawarar da zan baki."

Ta kalli Ayshatou ta ce, "Saura ke ina sauraren ki Mamana."

Numfasawa Ayshatou ta yi kafin ta ce, "To nidai Alhamdu Lillah a bangaren tufatarwa da kuma ciyarwa, zai bani komai a wadace aurenmu Wata Bakwai kenan amman indai zai fita yaga kaya masu kyau ko amai tallah zai siyo mun,sannan abinci ma kan ya kare ya kawo wasu, inda gizon yake saƙa shine sam baya iya gamsar dani kuma ba zai taɓa yarda ya yi wasa dani kafin saduwa ba sai ya ce shi bai iya ba,kuma bai san wannan ba,sai dai kawai ya biya bukatarshi ya tashi bai damu da nawa biyan bukantan na gamsu ko aa ba, kawai dai kansa ko nace masa ni inada bukata sai ya ce ya gaji,wannan ce babbar matsalar zamantakewar gidan aurena."

Zeeyter ta numfasa kafin ta ce, "Tabbas tunda kuka kawo kukanku gare ni kun yarda kuma kun aminta da cewa zan iya magance maku matsala ne, Alhamdu Lillah zan yi iya bakin gwagwadon iyawata, abu na farko da nake so ku fahimta shine 'YA MACE BA BAIWA BA CE KUMA BA BOLAR ZUBAR DA SHARA BA CE,MUTUM CE KAMAR KOWA, gudun saki ko tsoron rabuwa da miji ba naki bane don inganta rayuwarki, zawarci ba tozarci bane, kada ku taba sa hakan aranku wai kuna gudun miji ya rabu da ku baza ku iya rayuwa ba, Ameenatou matsalar ki bangare biyu ce amman babbar masahar ta guda ɗaya ce, shi ne ki tashi ki kama sana'a ki dogara da kanki,nuna masa cewa ko ya baki ko bai baki ba za ki iya kuma za ki inda hali ma har shi ki kyautata masa,tsaya da kafafunki za ki ga canji arayuwar gidanki ba zai taɓa tunanin wulaƙanta ki ba ko nuna miki halin ko oho atakaice ma za ki ga tarairaya da soyayya fiye da zato ko tsammaninki, sannan ki cire tsoro ko shakkar sa abu mafi girma shine ki guji abun da zai iya janyo maku matsala a tsakani amman daga nan kada ki taɓa yarda ya takaki kan gaskiyar ki, fito da asalin ke wace ce, kasancewar ki mace ba shi ke nufin za a tauye miki hakki kiyi shiru bane, fi karfin kanki da bukatun ki ba wanda ya isa ya taka ki,in makaranta ce ma ba kiyi ba koma kiyi , in Kasuwanci ne baki da jarin yi zan baki gwagwadon iyawata in sha Allah na miki wannan alƙawarin."

Ta numfasa ka fin ta dubi Ayshatou ta ce, "Aishatou matsalar ki babba ce amman kuma karama ce awani bangaren ko addinance ba a haramta neman saki ga wanda baya samun bukatar aure yadda ya dace ba, Amman kafin nan zauna da shi ku fahimci juna ,cire tsoro fito a yadda kike kuma a yadda kike son kasancewa, nuna masa hanya mafi bullewa domin inganta rayuwarku, in yaki fahimta ba dole ba kashe kai, nemi takardar saki,in yaki kai shi kara daga nan Allah zai baki wanda zai iya dake,domin muddin bai canja ba,kuma kika ci gaba da zama da shi a haka watarana neman wasu mazan zaki fara, kuyi magana ta fahimta ku fahimci juna, sannan dukanku ina so ku rike wannan ba batun cewa zaman aure zaman hakuri ne,komai ma na duniya sai anyi hakuri ai amman kada ka yi hakuri agun da za a tauye ma hakki sam! Wannan ba yi bane kashe kanki za ki yi a banza,ba wai nace karku nunawa mazajenku soyayya bane aa in lokacin soyayya yazo ayi amman in an kauce hanya nuna masa cewa da kai ko ba kai zanyi rayuwa kuma mai inganci da yardar Ubangiji,wani zubin nuna soyayya fiye da kima kan janyo mana wasu matsalolin, ina fatan kun fahimta kuma kun aminta da zantukana."


Ameenatou ce ta fara girgiza kai tana, "Hakane Madame na yarda da batun ki ɗari bisa ɗari kuma zan yi amfani da su in sha Allah, Allah saka da alkairy."


"Nima na Aminta kuma na fahimci dalilai da dama dake sawa maza ke wulakanta mu a rayuwa da ace za mu cire tsoro kuma mu dogara da kanmu ba abin da zaifi karfinmu, mun gode sosai Allah ya saka da alkairy." Cewar Ayshatou.

Maman Yusuf ma ta ce, "Mun Gode Madame Allah biya bukatu na alkairy duniya da lahira , Allah ba da 'Ya'ya na gari."

Murmurshi Zeeyter tayi tana fadin, "ba komai, Allah ba mu ikon aikata alkairi."

Daga nan ta kira Halliru ya ba da Ayshatou da Ameenatou 50000f
(Cinquante mille francs) domin su ja jari.

Gaɓadaya cikin farinciki suka rabu.

Sai da Zeeyter ta raka su har bakin get suka tafi kafin ta dawo.

Su Harira da Hurera na lekenta.

Hurera ta ce, "Ikon Allah ina jin wannan fa ba za ta taɓa karaya ba,da kamar bata nan tayi sanyi amman kuma yanzu ta kuma dawowa da karfinta,ina mamakin shin wace iri ce Zeeyter."

Tsaki Harira ta yi tana, "Aljana mana,in ba Aljana ba wa zai iya hakan ni ki bar ma mun maganarta wallahi takaici nake ji inna ganta sai inji kamar in kasheta."


Hurera ta ce, "nikam tun ranar da ta kaini asibiti ta fara birge ni Wallahi ita muka ma Amman ya koma kaina kuma karshe ta taimakeni wanda da ba ita Shikenan sai dai inyi rayuwa ba kafa don nasan ruɓewa zata yi kuma ba mai kudin kaini asibiti."

Wani irin tsaki Harira ta kara tana, "kyaji da shi dai, kima sota ba birgewa ba."

Ta fada tana tafiya cikin sauri.

Zeeyter kuwa na komawa office ta yi tagumi ban da tunano matsalolin rayuwar auren da su Ameenatou suka fada mata ba abun da ke yawo akanta.

Jiki a sanyaye ta koma gida, afalo ta kwanta kawai tana kallon sama,har haiydar ya shigo ya yi sallama ba ta ma ji ba,bare ta lura da zuwan shi.

"Madame I'm back , I'm Back oh oh, ba za amun maraba da dawowa bane?"

Ina Zeeyter ko jin sautin muryarshi ba ta yi ba ta jima da nisa cikin duniyar tunaninta.

A hankali ya ƙarasa kunnenta cikin raɗa ya ce, "Sunshine I'm back."

Da Murmurshi ta juyo tare da tashi tana, "Welcome yaushe ka shigo."

Zaunar da ita ya yi,shi ma ya zauna yana, "Aa, Is Something Wrong?,Meya ke faruwa? Gaɓadaya fuskarki ba walwala bare annuri ba yadda kika saba kasancewa ba,na shigo ina ta sallama da magana ba ki ji ba har sai da nazo kunnenki fa,mene ne yake faruwa? Just Let Me Know Please da ganin Murmushin fuskar ki na san na boye damuwa ne ba asalin wanda kika saba ba."


Jiki a sanyaye Zeeyter ta ma haiydar bayanin komai da su Ameenatou suka sanar da ita.

Girgiza kai ya yi, yana, "Maddallah da mata da gari yadda kika shi ne dai-dai ,zan yi alfahari da ke aduk inda za ki kasance And kuma in baban Yusuf ya zo ki ce ina nemanshi akwai bukatar mu tattauna da mazajen nasu suma, ina so muyi magana akwai abun da dole sai namiji da dan uwansa na miji kamar yadda kuma kuka yi magana muma za mu yi in sha Allah komai zai daidaita ki daina damuwa kin ji, yanzu ki mun asalin Murmurshi bana bogi ba."

"Thank you,Thank you so much,a kullum kana bayana kuma kana karfafa mun gwiwa ban san ya rayuwata zata kasance in babu kai ba, i can't love you less Sunshine, amman fa ba zan yi Murmushin nan ba yau I'm hungry kuma kai nake so kamun girki irin tuwon ranar sai inyi Murmushin har ma da dariya."ta karasa maganar tana taɓe baki.

Tashi Haiydar ya yi yana daga hannu kamar dan sanda yana, "As You wish Madame."

Shiga daki ya yi ya cire kayan ya dauko kananu yasa sannan ya daura rigar girki asama ya shiga kitchen yana, "Ki bani mintuna kadan yanzu zan cika miki ciki,har sai kin gaji."


Cikin minti talatin ya mata tuwon semo din da miyar vegetable.

Ajiyewa ya yi a daining table , kan ya dawo ya rike hannunta yana, "Komai ya kammala."
Zaunar da ita ya yi,yana kokarin diba ya bata abaki.

Dariya tayi ta karba tana, "Thank you, zan ci da kaina yanzu kam sai aikin yama yawa ai, je ka yi wankanka sai ka dawo kai ma ka ci."

Har ya tafi ya dawo.
Kin tabbata ba abun da za a kuma miki.

Wata irin dariya Zeeyter tayi tana, "Eheen je ka yi wankanka Ni dai na san wannan ladabin ba a banza ba da biyune."

Dariya ya yi ,ya tafi yana waƙa.

Wayarsa da ke kan daining din ne ta fara ringing,lekawan da za ta yi ta ga Meenoh ce ke kira.

Tsaki tayi ta ci gaba da cin abincinta.

Ganin kiran yaƙi ci bare cinyewa yasata katsewa.

Ta ci gaba da kiran, cikin ɓacin rai Zeeyter ta dauka tare da kasawa a kunne...


*Alhamdu Lillah,hannu da sauki sosai bai tashi ba, hakanne ya bani damar yi maku Typing na gode da kulawa sosai son so fissabillah.*

08103080717
Urs Xayyeesherthou
[6/24, 10:18 AM] Xayyeesherthul-humaerath🥀: *YEL*🦅

*NOBLE WRITERS ASSOCIATION✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.```
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*

*LABARI DA RUBUTAWA*
_Aisha Sani Abdullahi_
_*(Xayyeesherthul-humaerath)*_

_*TSOKACI:* Labarina Kirkirarrene ban yi shi don cin zarafin wani ba ko wata, sannan labarina yana dauke da yaruka uku ne zuwa huɗu:*Hausa, French, Turanci, Malay*, Haka Kuma ka/ki faɗi alkairi ko ka/ki yi shiru! Yadda ki/ka ga labarin haka tsarinsa yake kuma babu canji,Salon na Mussamman ne sannu a hankali komai zai bayyana🦅_

_R.I.J.F. Little Baba *(Suhaan)*😭_

*PAGE-36*
Bismillahir-Rahmanir-Rahim

*TALLAH*
_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._

★★★

"Hello Darling, Wato ka manta dani ko? Wai me matarka take da shi ban da shi ne? Ni fara ce, kyakkyawaa kuma doguwa sabanin ita baka ga muni, Haba Don Allah kasan fa ina sonka,ka amince muyi aure ni na yarda zan yi zaman kishi da ita."


Wani irin takaici ne ya dunguri Zeeyter a Zuciya, sai da ta ja numfashi kafin ta ce, "Tabbas bai zama lallai in Kasance miki mai kyau afili ba,amman ina fata tare da burin a kullum in ingata zuciyata ta kasance mai kyawun da bai misaltuwa,. Sannan kuma maganar Haiydar in baki fita harkar

Please Login or Register in order to submit comment