Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

DUBA MIN BAYA FAKON BIRI Complete Hausa Novel Document by DUBA MIN BAYA FAKON BIRI


DUBA MIN BAYA FAKON BIRI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 29840



DUBA MIN BAYA FAKON BIRI

Reading Time: 2 Hours

Added On: 04, Jul 2024

Author: Zainab Idris Makawa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08036959257

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 154.83 kb

File Type: txt

Views: 899+

Download: 599+

Last download: 15 hours ago

Description/Story: DUBA MIN BAYA FAKON BIRI,,,,,,,,


ZAINAB IDRIS MAKAWA

1️⃣

GA MAISON BANI HAKKINA ZAI IYA TURA KUDI DUBU DAYA KACAL A WANAN LAMBAN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO A KIRA WANAN LAYIN WAYAN 08036959257 NAGODE ALLAH YA BADA IKON BIYA MUN GODE NAKU HAR KULLUN YAR MAKAWA, , , , , ,

YAR UWA KADA KI RAINA NAUYIN HAKKIN WANI A WURIN ALLAH DON MIN AMANACE HAKKI, , , , , , ,


HAKKIN MALLAKAN JUYAWA AUDIOVISUAL S ZARIA TV KEDA WANAN HAKKIN KADA WANI KO WATA YAYI GANGANCIN JUYASHI ZUWA AUDIOVISUAL HAKKIN S ZARI NE WANAN.

Akori kura motar kauye ta kwashi kaya ta kwashesu takaisu gangaren yan ,,,,,
Wanan wakar da mukeyi da dare idan muna wasan hasken farin wata na dandali na tuna a yau da muke bayan wanan tsohuwar akori kuran motan data dauko mu muda kayan mu har yar akuyata durgu yar illori mai zuba min diya da inna ta saye da sunana .
Don inna na fadin hbakinsa
yana da albarkan kiyo ta fahinci hakan ne tun lokacin yayena da aka sake min kaza da sunana wanan kazan a yau itace ta rikede ta zamo min akuya dan nake kiyo mai sake min diya tasowan namu mane aka sayar da mazan inna ta dunkule kudin tazo muna dashi nan katsina da zamu zo.
Asali kuma tasowan mu zuwa katsina shine dalilin fadan baba da matan gida wanda fadan yarane ya kawo wanan hatsaniyar dama gori muna shansa duk da muna yara amma haka za a sake muna magana da sunan diyan agolan gida.
Sukace damu idan dan magana ya hadamu dasu sani in fika angola da rabon gidan gidan gado tun bansan ma,anan hakan na har yakai na fahinci me suke nufi da kalman hakan a garemu.
Watau mu da mahaifan mu mun algaje gida baba yazo masu gida ya zauna yana yar mace yana kokarin fin masu gidan karfi shine habaicin nan ya hau kan mu dan abu kadan za,ace damu sani in fika,,,,,,
Ko asalin wanan fadan da har yakai muka bar kauye a yau ya samo asline daga mama tambaya matar da ta zamo masifafa a cikin wanan gidan kusan kowa na tsoron ta gidan bama gidan ba ince kaf kauyen kusan kaf suna tsoron mama tambai don haka wasu ke kiranta dashi asalin sunan tambaya.
Don irin matan nam ne da iyayye ke tambaya wurin bokaye ko malaman tsubbu da sukan zo su addabi al,umma saboda suna da surki da aljannu ko wani saddabaru shine mutane ke mata lakani da tambai din a fahintar bahaushe.
Wanan matar itace dai silan barin kauyen da muke zaune a ciki inda mahaifan mu suka haifemu mu ukku yan mata wanda take muna lakani wani lokacin da haihuwan yuyuyu da babu gara daku don kunfi babu gun iyayyen ku.
Muna dai rayuwane naba dadi a wanan dajin don can yake surkukin daji tsakanin Jibiya da Niger inda ya hada mahada da kasashen biyu watau niger da nageria asali mu mahaifiyar mu yar niger ce mahaifin mu kuma dan Nageria don kusan rayuwansu dayane a wajen don haka alakan aurataya yake yawan shiga tsakanin mazauna wajen don kusan ko wani halakan zimunci na bahaushe ya samo asaline ta dalilin aurataiya a duniya.
Matan gidan mu basu kaunar mahaifiyarmu damu don kawai kishin saure da yawancin matan hausawa sukeyi tsakanin matan wa dana kani ko wani dan uwa a dauki kishin duniya anawa juna har yafi na kishiyar da kuke miji daya zafi wani lokcin ma abin yakan zamo harda jifa a tsakanin don basu kaunar mijin daya ya dara na daya samu wanan shine yakan jawo wanan bakin kishin a tsakani a koma ana jin haushin juna na ba gaira ba dalili.
To nagidan mu da akewa lakanin da babban gida a kauyen mu ya samo asaline ta irin albarkan noman da baba ke samu wanda har ya dara samun mazansu yasa suka dauki kishi da kyashi da hassada suka dorawa iyalin baba watau mu ke nan a yanzu.
Don baba ya dara mazajen nasune kuma ta hanyar dan aikin da yakeyi na likitancin dabbobi a kauyen kasancewa shivyayi karatun shi don mahaifinshi bai yarda ya barshi cikin yan uwa ba ilimi ba don yan uwan baba na haihuwa da suke uba daya suna garin katsinane da zamasu.
Hanyar uwace nan a kauyen dan shi kusan hannun mahaifiyarshi yayi rabin rayuwanshi ko zaman mu a kauye gadonta yakeci yasa yake zaune a gidan da suke ganin kamar zaman banza yakeyi shi agolan gidane ba dan gida ba.
Amma mazajensu sun sani kason mahaifiyarshi ya gada a gidan yasa yake zaune dasu a cikinsu har yakai ga tara iyalin kansa da suka dauki karan tsana suka saka muna .
Don duk sun hade muna kai ko dayan mu ya dan fita by mistake yanzune za a hattaroshi don hakane bamu fita ko ina muna sashen mu dake can karshen gidan wanda yakai har baba ya bude muna hanya ta baya amma duk da hakan bamu tsira ba a wajensu.
Don don gulma zaki gansu sun biyo wai hanyan yafi saurin fita idan tafita ya kamasu kwatsam muna zaune zamuga sun fado muna ba ko magana wani lokacin hakan zasu tatsamu su wuce zuwa inda zasu.
Dan dama dama in yan arzikin na a kai wani lokacin zasuyi muna magana kansu fita din amma ido na aikin gulma suna rabashi wurin kallon wani bakon abu da idan anshiga gida za a karas wa sauran jama,an gidan da cewa muga kaza munga kaza a sashensu wace ai ko kuma a ailo inna ta sam masu abu kaza da suka gani.
Saboda mahaifinmu yana shiga daji a kullun wajen yin sana,an sa don hakane baka raba sashen mu da kayan marmari irin na kauye harma dana birnin don yana yawan shiga katsinashi sosai ya saro kayan amfaninshi ya dawo kauyen don hakane muka dan bambamta da sauran mutanen gidan da suka dora kyashinsu a kan mu.
Fada akayi akan mama tambai ta aiko inna ta san mata dankali hausa data gani shine inna tace bata aiko da wuri ba ta sulala ko saidai dafafen ta diba mata yan kwarori wanan ya kawo fada har yakai ga gama na tsawon wata da watani a tsakaninsu wanda dole kowa ya bita don tsoronta da akeji muka koma rayuwa mu kadai a gidan da mun fito kuma su bugemu mu koma da kuka lungun mu.
Har yakai sai babane zai fita yayi fadan hakan don inna kan gaskiya tana tsoronsu sosai ita kan sun manna mata tsoronsu kuma tanayin hakan.
Yasa bamu shan ruwa ya sauka muna a ciki ba,a dawo dashi ba abin yana bakantawa baba rai yasa da zaran karfe hudu yayi baba na gida da iyalinsa yana hada yan kayayakinshi ko yana wani abin don idonsa yana kan mu ko yaushe.
Kanwata habibi da aka aika shago ta biyo ta cikin gida don yafi kusa nan dan mama tambai ya maketa kuma ya zubar da gishirin a kasa ya turmuze da kafa anyi dace koda ta shigo da kuka daidai lokacin baba na gidan don dawowanshi ke nan yana aje tsohuwar mashin dinsa suzuki yana kokarin baiye dan kulin buhun kayan shi daya dauro a baya mukaji kukanta tashigo ga baki ya fashe yana jini.
Nan ya tashi ya bisu ya samu dan mama din ya doka ita kuma ta dauko tabarya tayi masa rotse a kai Allah ya gyara a ranan da baba ya mutu don jini ya balle a goshinsa daidai inda ta buga masa tabaryan saida akaje kemis aka gyara masa.
Wanan yasa abin yai tsanani don yace sai ya halaka mama ita kuma tace kafin ya halakata sai tayi sanadinsa har iyalinsa sun bar duniya hakan yasa mazan gidan suka shiga cikin zancen.
Ganin abu yaki ci yaki karewa yasa baba yaje birni gidansu na gado ya tayar da wa yanda ke haya a part dinsa ya gyara da sunan zamu koma ciki da zama.
Rana daya bai fadawa kowa ba sai ji sukayi wanan akori kuran ta tsaya kofan mu ana loda yan kayan mu a ciki labari ya kai masu suka dauki tafe da shewa mama har guda ta rangada taci gari dole uwar naki baba zai bar mata gida don dole.
Yan uwanshi maza basuso hakn ba don mutum yana da ranansa saboda zaman baba a cikinsu akwai taimako mai karfi a tsakaninsu
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download DUBA MIN BAYA FAKON BIRI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album