Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

MINISTER ASHRAF Complete Hausa Novel Document by MINISTER ASHRAF


MINISTER ASHRAF

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 42600



MINISTER ASHRAF

Reading Time: 3 Hours

Added On: 26, Apr 2025

Author: Yusrah Musa Abubakar ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : ANNURI WRITER'S ASSOCIATION

Author Phone : +234 8160983083

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 232.55 kb

File Type: txt

Views: 8+

Download: 17+

Last download: less than 1 second ago

Description/Story: TYPING 📲Fri, Dec 13/24 4:51pm YUSRAH MUSA ABUBAKAR✨✨✨.





💕MÏÑÏSTËR ÄSHRÄF💕





WHATSAPP NO:+234 8160983083
yusrahmusaabubakar@gmail.com



A*W*A
ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫
Home of hospitality and harmony gidan karbar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan.

____________________
____________________________
___________________________________




STÔRY WRITTEN ND EDITING
YUSRAH MUSA ABUBAKAR
✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë.




¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶¶
I'm here to make you happy educated domin nifa I have no girman kai if you fushi dani to wallahi you are just 6atawa kan k lokaci.




THINK BEFORE YOU DO
Always be watchful don't take risk don't try to get lost try to protect your life always, be good be helpful people will like u to be a happy child like my daughter Fatima Zarah Ilham little Zarahn Aunty people will like u.



°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
📿BISMILLLAHIR RAHMANUR RAHIM📿


In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE we love our NABI no success without him he's the light of every darkness he's the mirror of our life he's the answer to every question he've no limits, ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya muna sonka fiye da dukka muradi na zuciya ANNABI mu mu ganka shine buri na zuciya lamince mu ganka ya mai salsabil da khausara.

÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷
SHORT STÔRY
÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷


💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG____01&02
Zaune wani kyakkyawan farin mutum yake a wani office da takardu a gabansa yana dubawa a shekaru zai Kai shekara arba'in da biyar fari ne kamar ka ta'ba jikinsa jini ya fita a saman sa akwai katon photon sa banne a jikin bangon yana tsaye kamar ka kirashi ya amsa a qasan photon an rubuta sunansa da manyan ba'ki ASHRAF AHMAD da kyakkyawan murmushi na kwatance akan kyakkyawar fuskarsa sa, aiki kawai yake baya ko d'auke hannunsa ya huta sai lokacin da akai Kiran wayarsa sannan ya d'ago yana kallon wayar tasa ganin me kiran yasa yadan ja tsaki batare daya d'aga ba ya mayar da hankalinsa kan abinda yake yi har Kiran ya katse wani ya shigo amma ko inda wayar take bai sake kalla ba balle ya damu da ya d'auka saima saka wayar dayai a silent dan kada ringtone d'in yasa yayi mistake kawai yaci gaba da aikinsa.

Tsaye wata cikakkiyar mace take tasha ado ta soke d'aurin kwali kallo d'aya zakai mata kasan yar duniya ce ranta a'bace tana kallon wayar dake hannunta gashi Kiran yana zuwa amma ba'a d'agawa Kuma tasan yana gurin yana ganin kiran huci ta fitar daidai ta sake Kira ya katse tai jifa da wayar tana zama akan kujera tare da dafe kanta tace.

"Wai meyasa Alhaji Ashraf yake min haka wannan ai wulakanci ne nasan yana ganin kiran amma ya'ki d'agawa dan ya 6ata min rai meyasa zai min haka kodan yaga na damu dashi humm dole zan dau mataki a kansa kafin ya haukata min 'kwa'kwalwata haba wacce irin masifa ce wannan"?.

Ta'be baki hajiya Bilkisu dake gefe tai tana kallon yadda fuskar qawar tata take dan'kare da ba'kin ciki da damuwa tace "kema wallahi Hajiya Sadiya kina da abun mamaki dole dan zamuyi tafiya saikin sanar masa kamar wani mijinki ina ruwansa da wannan harkar ki share shi mu tafi idan mun dawo koma menene saiki je har office din nasa ki same shi".

Kai Hajiya Sadiya ta girgiza tare da furzar da huci tana cire glass d'in idonta tace "amma dai Bilkisu ke kanki sheda ce irin son da nakewa Ashraf ji nake kamar nayi hauka taya bazan damu da halin ko in kular da yake nuna min ba yadda nake binsa sau da qafa dan ya aureni ko ubana iyakaci kenan amma baya gani kullum labarin daya ne taya kike tunanin zan samu nutsuwa idan bai saurare niba"? Rausaya kai Hajiya Bilkisu tai tana cewa.

"Humm kece fa kika d'au abun nan da zafi wallahi yadda Alhaji Ashraf yake bazai ta'ba sauraron kiba a haka kinsan meyasa? Ta fad'a tana kallon Hajiya Sadiya wacce ta zuba Mata ido jiran amsa cigaba hajiya Bilkisu tai da cewa "saboda kina yawan zubar da kimar ki a gabansa kina nuna masa kamar baki da aji kin zauce kin susuce da ace zaki iya da kin d'auke masa wuta kona wata biyu zuwa uku ne ki daina kiransa ki daina zuwa nemasa wallahi Ina fad'a Miki da kansa zaki ji ya kira wayarki yana tambayar kina lafiya amma kullum kina kiransa kina zarya a office dinsa taya kuwa bazai Miki wulakanci ba"?.

Sauke numfashi Hajiya Sadiya tai tana kallon hajiya Bilkisu tace "amma taya kike tunanin zan iya share Alhaji Ashraf na wata uku batare Dana kirasa ba? Humm aiko kwana uku bazan iya ba balle wata uku so kike na mutu? domin ko sati nayi ban ganshi ko naji muryarsa sainayi rashin lafiya to kuma me kike zato idan aka ce yau rana ta fito ban daga waya na kirashi ba saidai a d'auke ni zuwa asibiti Bilkisu ni kaina bansan wanne irin so nake yiwa Ashraf ba hankali bazai kwatanto shiba misali bazai iya musalta shiba sannan kalmomi bazasu iya fad'ar saba kawai ki kyale ni nayi gwagwarmaya ta na samu soyayyar sa kuma burina a kansa shine na aure shi" tana rufe baki hajiya Bilkisu ta she'ke da dariya tana tafa mata tace "gaskiya ne saida ke qawata to Allah ya taimake ki ya soki nikam ina ganin hakan abu ne mai wuya domin kina kallon yadda naci ba'kar azabar soyayyar Alhaji Mukhtar amma qarshe ya barni ya auri wata balle ke da Alhaji Ashraf bai baki goyon baya ba ina tunanin yadda abun zai kasance da kamar wuya fa" ta karasa maganar tana yiwa Hajiya Sadiya kallon babu nasara a gabanta Kuma hakan zahiri ne a bayyane yake abunda take yi Mata hasashe gaskiya ne Alhaji Ashraf yasan Hajiya Sadiya da irin kalar rayuwar barikin da take na zaman kanta sannan dama gata babbar yar siyasa ce ko ina da ita ake shiga a fita dukkan wasu halayenta saidai ya baiwa wani labari shiyasa ko kad'an bai sake mata balle tayi tunanin zata samu fuskar dazai amsa mata gaisuwarta ma ko tayi zaton a gaba zata samu shiga a gurin sa inaaa!!! Never in history...............

Ganin yadda tayi nisa cikin tunani yasa hajiya Bilkisu dafa kafad'arta tana d'an girgiza ta da sauri Hajiya Sadiya ta dawo daga tunanin da take tana kallon Hajiya Bilkisu wacce ta d'age mata gira tana cewa "wato kema kin fahimci hakan bazai ta'ba kasancewa gaskiya ba ko? To yanzu ya kamata ki daina wahalar da kanki a kansa ki tsaya ki saita rayuwarki ki kama kasuwancin ki kawai".

Kai Hajiya Sadiya ta girgiza jikinta yana qara yin sanyi da karya mata gwiwar da hajiya Bilkisu take yi cikin rashin jin dad'i da walwala tace "a'a dan Allah Bilkisu kiyi shiru haka ki daina fad'a kar kisa zuciyata tai bindiga ko hawan jini ya kama ni abinda nace zai kasance alkhairi muna nan dake saina auri Ashraf ko yana so ko baya so ta hanyar halak ko haram tunda ni Ina sons........ shiru Hajiya Sadiya tai bata karasa ba sakamakon jin qarar takalmi ana saukowa daga upstairs tasan maybe Husnah ce ta shirya zata tafi school Kuma bata so ta ri'ka riskarta tana irin wad'annan maganganun juyawa tai tana kallon budurwar data sauko tasha kwalliya da handbag a hannunta bata rataya a kafad'a ba karasowa cikin parlon tai itama tana kallon Hajiya Sadiyan tace.

"Momy zan je school".

Kaita d'aga mata tana cewa "ok Husnah sai kin dawo".

Bangaren da hajiya Bilkisu take xaune ta juya tana cewa "Ina kwanan Momyn Meelat"? Da fara'a hajiya Bilkisu tace "lafiya kalau Husnah ya kike"? "Ina lafiya Momyn Meelat" ta fad'a daidai zata wuce Hajiya Sadiya ta dakatar da ita da cewa "am Husnah zamuyi tafiya yau nida hajiya Bilkisu idan kin dawo daga school ki wuce gidan Hajiya Maryam ki zauna tare da ita idan mun dawo next week zan Kira ki a waya saiki dawo Kinga babu dad'i ki zauna a gida ke kad'ai" jin abinda Hajiya Sadiyan ke cewa yasa Husnah ta juyo fuska ba walwala tana cewa "Momy Ina Kuma zakuje har sati guda baku dawo ba dan Allah Momy ki rage fita da wannan yawace yawacen".

Tana rufe baki Hajiya Sadiya ta sakar mata wata zazzafar harara tana cewa "kinga Husnah ki kiyaye ni akan irin wannan tambayar taki mara tushe Ina ruwanki da inda zanje wato abinda nake fad'a miki dabam kema wanda kike fad'a min dabam ko? Humm Husnah ke 'yata ce bana son ki ri'ka nuna kamar kina zargina dan haka ki kama kanki! ki kama kanki!! ki kama kanki!!! Sau uku na fad'a miki ko?
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download MINISTER ASHRAF

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album