Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dashi, na tsiyaya a kofunan na dauki daya na mika mishi guda, murmushi yayi ya amsa ya min murmuring din thanks cikin murmushi, ya kafa kai ya shanye tas ya miko min kofin, daga nan ya rufe computer. Ya tashi ya shiga toilet yayi brush ya fito ya saka kayan barci, nima na tashi na shiga na wanke bakina da mouth rinse mai kamshin inibi. Marwan na kaunar duk wani abu da aka sarrafa da inibi, hatta da yawancin turarukan da yake amfani dasu masu kamshin inibi ne, shi yasa nima na lazimci amfani da Ire-iren su domin faranta ran mijina.

Lokacin dana fito daga bayi har ya riga ya kwanta ya rage wutar dakin zuwa mai matsakaicin haske, na cire kayan jikina ya rage daga ni sai brazier da dan karamin siket, ire-iren wadannan kayan su duka zame min kayan barci shekaru biyu da suka wuce, wani lokacin ko na saka kayan barci masu nauyi bana feeling comfortable a cikinsu. Na fesa body spray a jikina da humra masu sanyin kamshi, nima na hau gadon na kwanta. Sai naji ya kashe fitilar gami da jawo ni jikinsa yasa bargo ya lullubemu, nayi whispering 'good night!' a cikin kannensa na kara shigewa cikin jikinsa, dumin jikinsa da kamshin da jikinsa ke fitarwa suka suka sanyani cikin wani yanayi wanda ban san sanda na kara lafewa a jikinsa gami da kara kwantar da kaina akan kirjinsa......




©Jeedderh🐾


[5/2, 11:00 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•32•°🐾


Ya nutsa kansa a wuyana yana fitar da wani zazzafan numfashi, hannunsa kuma na karade gabadayan bayana, wuya, da gefen cikina cikin wata irin shafa mai tada tsigar jiki.
Ba haka ya saba min a sauran daruruwan kwananmu da suka shude ba, don haka ne jikina ya fara wata irin kakkarwa amma na kasa tabuka komi. A hankali kuma da kyar na samu na iya furta Marwannn...!! Sakamakon hannunsa da naji yana kokarin balle min maballan brazier, ya dago fuskana ba tare daya bari na kara furta uffan ba naji ya manna bakinsa kan lebbana, ya kamo harshena ya fara tsotsa passionately, naji numfashi na yayi yajin aiki na wucin gadi, kafin in dawo hayyacina daga shock din abinda ke faruwa da lebba na Marwan ya zare min rigar mama yayi jifa da ita. Ya maido ni kan kirjinsa yana matsa da shafar breast dina cikin rawar hannu. Wani irin yuuu na dinga ji a cikin kaina, gabadaya na rasa inda kaina yake. Ina jin sanda hannunsa ya dinga shafar fatar cikina, yatsunsa suna circling din cibiyata, ina so in hana shi abinda yake yi mun amma na kasa. I can't lie, I was enjoying what he was doing to me. Cikin yanayin fita hayyaci na rike hannunsa daya saka yatsansa a center na, na fara kokarin zare jikina amma saboda irin rikon daya min na kasa ko motsi. Muka dinga hada wani irin numfashi mai tsananin nauyi da wahalar fitarwa, ni dai na rasa a duniyar da nake na kuma rasa inda zan sa kaina ko abinda nake ji yana yawo a magudanar jini na zai daina yawo. Na samu na cire bakina daga nashi, bai yi wata wata ba ya maida bakinshi kan nipples dina.....

A karon farko a tarihin rayuwar aurenmu, muka raba dare cikin nuna tsananin kaunar da son da muke yiwa junanmu ta hanyar romance. Washegari sai na kasa hada idanu da Marwan, haka kawai wata irin kunyarsa take lullubeni a duk lokacin dana kalleshi. Tun baya ganewa, har dai ya kula yau dai kunyarsa nake ji, gashi kuma ya kasa ya tsare yaki ya fita daga gidan.

Yana kwance akan lallausan carpet din tsakiyar falon yayi matashin kai da filon kujera, ni kuma ina ta kokarin shirya mana lunch akan dinning, ya saka hannu ya janyo ni na fada kan kirjinsa. Nayi saurin kulle idona gamm kamar wadda ta ga dodo, dariya ya saki a tausashe, "wai Meenah na zama surikin kine kike ta wani sunke fuska tun dazu?" shiru ba magana kamar mai magana da dutse, sai ma kara nutsa kaina da nayi a faffadan kirjinsa, "ok.... Tunda haka ne ba zaki yi magana ba to bari in dora daga inda na tsaya jiya....." ai a sukwane na dago kaina tare da sauke idanuna fess akan fuskar shi, cikin shagwaba nace "kai don Allah!" me zaiyi kuwa in ba dariya ba? Da kyar ya sake ni bayan na mishi alkawarin zan daina dari-dari dashi.

Muna gama sallar La'asar yace inje in shirya mu shiga gari yawo, naje na tsalo wankana da sabulai masu kamshi. A daddafe na gama wankan saboda yadda nipples dina suke min wani zogi. Yana zaune akan gado a shiryansa tsab, ganin fitowa na ya mike ya taroni ya zaunar dani akan stool, mai ya dauka wai zai shafa min. Yana fara shafar ya dora daga inda ya tsaya kamar yadda yace dazu, na kasa daurewa azabar da nake ji musamman kan nipples dina wadanda yafi takurawa da tsotsa, kuka na sakar masa a saitin kunnenshi a shagwabe, sai dai bai saurara min ba kamar yadda nayi tsammani. Sai da yaji ya gaji don kansa sannan ya kyale ni, ya gama shirya ni muka fita.

A sati uku da suka biyo baya, rayuwar aurenmu ta canza akala zuwa wata nahiya ta daban, wannan canjin rayuwar ya saukar mun da wata irin natsuwa da jin dadi wadanda basa misaltuwa. A bangaren Marwan kam abun was quite different, en wasannin da yake yi dani basu kare shi da komi ba sai ma kara mishi wahala da matsananciyar sha'awa ta, gashi shi tsakaninshi da Allah gani yake nayi kankanta da irin wadannan abubuwan, gani yake ba zan iya daukar lalurar shi ba....

Wannan Kenan!!!



•{Kuyi hakuri da wannan zuwa anjima plsss....}•




©Jeedderh🐾
[5/2, 11:01 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•33•°🐾


Rayuwa taci gaba da juya mana a haka. To me, Marwan yasa naji a raina cewa yes, ni mace ce! Cikakkiyar mace., ya kuma nuna min cewa shi cikakken namiji ne, gwarzo. Wannan dan takaitaccen lokaci da muka yi a tare, nayi treasuring dinshi fiye da sauran lokutan da suka wuce mana a baya.
Cikin haka muka riski daren wata juma'ah, daren da muka kira FARIN DARE! (Zulfa Aliyu), daren da muka yi ittifakin bamu taba riskar daddadan dare mai tattare da alkhairi irin sa ba, daren da Ni da Marwan muka zamo daya, ya zama ni na zama shi, ya zamo babu wata hijabi da tayi saura a tsakaninmu....
Muna cikin gudanar da wasanninmu kamar kowanne dare, sai dai na fahimci cewa yau wasannin na Marwan sun fi zafi ya kuma fi kowane dare rikicewa da fita a hayyacinsa. Hankalina ya dauke cikin wasannin da yake yi min, kamar daga sama na tsinci muryar sa a tsakiyar dodon kunnena, "Meeenahh.... Ki lazimce, ki yarda a wannan daren in karya alkawarin dana daukar miki don Allah! Wallahi-Tallahi bana jin zan iya tsallake daren yau ba tare da nasan ke din, wanka ce ce ba, plsss kinji???".
Ni kaina zan so hakan ta faru, ina son mijina kuma bana kaunar abinda zai saka shi cikin rudani, don haka nasa hannuwana na kara rungume shi tsamm a cikin jikina. Duk da cewa banyi magana ba, ya fahimci cewa na bashi hadin kaina. Cikin wani irin rawar jiki ya juya ni kasan sa, ya lalubo bakina yana tsotsa cikin wani irin salo.....

A wannan dare Marwan ya kawar da budurci na, ya mayar dani cikakkiyar 'ya mace cikin lallashi da so da qaunar juna marar misali, sai dai na sha azaba bata kadan ba saboda yanayin zuwan daya min. Amma duk da hakan banyi nadamar mallaka masa kaina ba.
Shi ya taimaka min na samu na kimtsa jikina, da asubahi ya jamu sallah da muka gama muka koma muka kwanta barcin gajiya. Lokacin dana farka karfe goma sha biyu da kwata na rana, jikina yayi wasai ba ciwo sai dai ba karfi. Marwan baya dakin, nayi wanka na shirya cikin doguwar riga mara nauyi don jin jikina nake yayi min nauyi sosai, ina fita falo na tarar har ya hada mana abinci, ya zaunar dani muka ci abincin ina jikinsa yana tattalina. Yinin ranar a gida yayi shi bai leka ko nan da can ba.

Cikin watanni biyu kacal, idan ka ganmu ni da ango na ba zaka yi fatan dauke idanu daga garemu ba. Munyi wani irin kyau da fresh, a yanzu ne muke cikakkun amarya da ango. Son Marwan ya bi jinin jikina, babu inda so da qaunar shi basu kewaya a jikina ba, zuwa extent din da nake ganin idan har babu shi ba zan iya rayuwa ba.

Ranar nan na dawo daga makaranta da yake wasu lokutan ni nake kai kaina, na samu dogon go slow a hanya don haka na canza hanya, sai gani a unguwar su Hindu nace bari in biya mu gaisa. Suna tare da wannan abokiyar tata na same su a falo suna hira, cikinta ya fito haihuwa yau ko gobe. Cikin mamakin yadda na bude cikin dan lokaci na kara yin kyau suke kallona, rabon data ganni tun ranar da suka je min dubiya. A tsaitsaye muka gaisa dasu suna ta wani yatsina suna jifa na da wani irin kallo wanda na kasa fahimtar ko na meye, ganin haka na mike tare dayi musu sallama don banga fuskar zama ba.
Ina bada baya, Manjunath kawar Hindu ta fara kitsa mata muguwar shawara, ita kuma ta hau kai ta zauna.....

Ina isa gida kiran Marwan ya shigo wayana da yake yaje Najeriya kwanansa biyu acan, kanwarsa Iklimah ta haihu yaje barka. Nan yake gaya min cewa washegari zai dawo, dariya kawai nayi na mishi fatan a dawo lafiya muka yi sallama. Washegari kuwa tun dana tashi da safe ban koma barci ba, gabadaya tsarin parlour na canza har da bedrooms. Ban samu kaina ba sai gab da La'asar, nayi sallah sannan na shiga kicin na dora girki. Ina gamawa na fada wanka na cude jikina da sabulai masu kyau da inganci da ruwan dumi, na shirya cikin material ash riga da siket da suka min cif a jiki, na bi duk wasu gabobin jikina na shafa humra mai sanyin kamshi sannan na zira hijabi na sallaci magriba.
Sai karfe tara ya shigo gidan, na tare shi da murnata na taimaka mishi yayi wanka ya shirya cikin jallabiya. Sai wani bina yake da kallo kamar zai cinye ni. Muka fita falo nayi serving dinshi duk abubuwan dana dafa mishi. A dokance yake dani sosai don haka ko hirar da muka saba yi bai bari munyi ba ya ciccibeni sai kan gado.... Wayar shi data fara kara ne ta katse mana hanzari, ya saki tsaki tare da daukar wayar., Hindu ce!!




©Jeedderh

[5/2, 11:01 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•34•°🐾


"Kana gari??" abinda ta tambaya kenan, ya danyi jim kafin yace "A'ah, menene?" Tace "ok, dama ina son ganin ka ne, amma shikenan sai da safe!" ya amsa da Allah ya tashe mu lafiya, suka kashe wayar.
Ya sake janyo ni jikinsa na janye, nace "me yasa zaka ce mata haka? Ka sani ko haihuwa ce ta taso mata ko kuma wata matsalar?" ya danyi tsaki, "ki kyale rigimar Hindu kawai ai ke kin san halinta, abinda bai kai ya kawo ba zai sa ta katse min jin dadi na. Kin san idan nace mata ina gari kuma ba zan je inda take ba rigima ce zan daukowa kaina. Don haka malama matso maza naji dumin nan naki mai gusar da hankali ko na samu natsuwar dana jima ban ji ta a raina ba...." murmushi nayi cikin jin dadin kalamanshi na matsa na ra6u da jikinsa.....

Ba mu muka samu muka rabu da juna ba sai da dare ya tsala, na tursasa mishi sai da muka yi wanka sannan muka koma barci. Garin yayi shiru kamar babu wani mai rai a duniyar, ya kara janyo ni jikinsa, yanda naji yana goga jikinsa da nawa ya tabbatar min da cewa shi fa bai gaji ba. Na janye jikina daga nashi a shagwabe ina cewa ni dai don Allah ka bari mu runtsa mana, dare yayi sosai pa. Yace to ni ina ruwana da daren? Nace wai kai baka gajiya ne? Yayi shiru, na matsa na kwanta a jikinshi ina shafa kirjinshi nace kayi hakuri har zuwa gobe don Allah, kasan a gajiye nake kuma ya kamata in tashi da wuri gobe kaji?? Ya kwantar da kaina akan kirjinsa yana shafa tattausar sumar kaina a hankali, "it's okay Meenah, sleep tight!!" nayi chuckling kadan na kara shigewa cikin jikinsa, barci mai dadi ya dauke mu.

Cikin tsakiyar kaina na dinga ji ana buga kofa, na bude idanuna cike da barci da mamakin waye wannan da tsakiyar dare haka? Barci yaci karfina sosai, na sake komawa ban san lokacin da Marwan ya fita ba.

Bayan kamar minti biyar da fitar shi sai na dinga jiyo alamun kamar ana rotse a falo, a sukwane na diro daga kan gado na duba babu Marwan a dakin. Na duba agogo ya nuna min karfe uku da kwata ne na dare lokacin, na fita falo ina kiran sunan Marwan amma ban ji ya amsa ba sai wani kakari dana dinga ji kaman nashi. A gigice na kunna wutar dakin, nan naci karo dasu cikin mummunar shigar bakaken kaya suna ta dukan Marwan har sun kaishi kasa yayi jina-jina, na kwala ihu na nufe su da gudu na kankame mijina ina kuka na dinga tambayar me ya musu? Basu kula ni ba. Wani daga cikinsu ya kama ni ya watsar gefe, kaina ya bugi wata makings, ina dagowa naga ashe intercom ce ta security din unguwar da suka makala a kowane gida saboda emergencies irin wannan..... A haukace na shiga danna makunnar ganin irin mummunan bugun da suke mishi, na kasa daurewa na kara komawa inda suke, cikin kuka da tashin hankali na rukunkume shi ina rokon su kyale shi zamu basu duk abinda suke so. Daya daga cikinsu yasa kafa yayi jifa dani gefe har sai da bakina ya fashe, ban san sanda na zuciya ba na wawuri kwalbar mayonnaise na bugawa daya a kai da karfina, take nan ya sulale kasa sumamme.....
Dai-dai nan sai ga jiniyar security, suka yi duru-duru cikin tunanin abin yi kafin suka arce suka bar dan uwansu anan, ai kuwa na take musu baya sai dai tuni suka kama katanga suka dira, daidai lokacin en sanda suka shigo gidan nan wasu suka bi bayansu, wasu kuma suka matso suna tambayana abinda ya faru. Ina kuka na zayyana musu duk abubuwan da suka faru, muka juya cikin gidan tare dasu. Marwan da wanda nawa rotse suna kwance shame-shame a kasa cikin halin kaka-ni-kayi, nan aka ciccibe su zuwa cikin mota. Kamar wanda ya diro daga sama, muka ci karo da Muhammad Kabeer kanin Marwan a kofar gidan. Saukar shi kenan daga states yayo gidanmu ashe da rabon zai ga tashin hankali, tare dashi muka dunguma zuwa asibiti.




©Jeedderh🐾
[5/2, 11:01 PM] ‪+234 816 492 9724‬: 💕🐾•°•° *BAYAN*•°•°🐾💕
💕🐾°•°• *RAI...*°•°•🐾💕




🐾°•35•°🐾


Babu wani bata lokaci aka amshe mu a asibitin kasancewar akwai en sanda, aka wuce dashi emergency suka barmu tare da en sanda suna kara min tambayoyi. Muna nan har aka kira sallar asubahi, sam na kasa zaune na kasa tsaye sai kai da kawowa nake yi, sai ga Hindu ta iso hankalinta a tashe ban san waya fada mata ba amma nasan kila Kabeer ne, ni kam tashin hankali bai barni nayi tunanin kiran kowa ba. Sai lokacin na kira uncle na fada musu abinda ya faru da kuma asibitin da muke, ba a jima ba kuwa sai gasu hankali a matukar tashe. Sai karfe goma na safiya sannan aka fito dashi, jikinshi yasha nadin plaster da bandeji kamar wanda yayi hatsarin mota. Muka bisu har zuwa wani daki aka kwantar dashi, daga nan likita ya nemi ganinmu muka bi shi zuwa ofis dinsa.

"Magana ta gaskiya wannan patient da muka gama akan shi yana cikin mawuyacin hali da rayuwar kila wa kala a sakamakon irin mugun duka da aka mishi na keta, bayan haka anyi amfani da takalmi mai nauyi sosai an bugi kirjinsa musamman saitin zuciyarsa, don haka ina bakin cikin sanar daku cewa zuciyarshi ta kumbura sannan yanayin fitar numfashin sa ya canza don haka muka mishi allurar hutu ta tsayin kwana uku domin mu ga yadda jikin nashi zai kasance. His chance of living is very low, but i promise you that things will not go out of hands In shaa Allah.....!!"

Bayanin da likitan ya mana kenan, kafin ya gama rufe baki Hindu ta durkushe kasa dafe da kugunta tana kuka, nan da nan nurses suka dora ta akan gado suka yi labor room da ita. Muna fitowa muka ci karo da mahaifiyar Marwan, jin abinda kenan sai ta zube kasa sumammiya aka kwashe ta zuwa wani dakin, kai ranar na ga tashin hankali irin wanda ban taba gani ba a rayuwa ta.

Awanni biyu curr, sannan aka fito da Hindu daga labor room ita da kyakkyawan babynta a nade cikin wani lallausan towel sai tashin kamshi suke yi. Zo kaga rige-rigen daukar baby ko ta kan uwar bamu bi wadda take ta shaqar barci. Jikina har rawa yake lokacin da Maah ta miko min babyn, na kura mishi ido ina kallo hawaye ya ciko min ido, gashi nan dai kamar Marwan yayi kaki ya tofar, babu abinda ya dauko na Hindu. Cikin dauriyar da nake ciki tun dazu na kira sallah sannan na tada ikama a kunnuwansa, sannan na tofa mishi addu'o'i na tsare kai daga zina a al'aurar sa. Na rungume jaririn a jikina wata irin tsabtacciyar kaunar yaron ta dinga tsirga jikina, kawai na fashe da kuka. Imagining if Marwan was fine irin murnar da zai nuna na dinga yi. Daidai nan en sandan nan suka zo suka mana sallama suka ce zasu je su dawo don har zuwa lokacin wanda na yiwa rotse aka bai farfado daga suman da yayi ba, muka musu godiya suka tafi. Uncle ya kawo zamzam da dabino na tauna dabinon na zuba ruwan dabinon a bakin baby na kuma shayar dashi ruwan zamzam. Yana tashi nurse ta amshe shi ta kaishi wajen mahaifiyar shi, amma sun hana mu ganinta. Muna asibitin nan har karfe bakwai na dare, daga Marwan din har Hindu babu wanda muka samu damar gani. Karfe bakwai suka ce mu wuce gida don basa barin en jinya, haka muka juya gida jiki a sanyaye babu kwari. A duk yinin ranar ba zance ga abincin kirki daya shiga cikina ba, gidana muka dunguma gabadayanmu har su Anti, sai dai basu shiga gidan ba suka mana sallama suka tafi gida, ni da Maah da Kabeer muka shiga cikin gida.
A gurguje na dafa sassaukan abinci nayi serving dinsu, yadda kasan wadanda aka takurawa haka muka dinga tsakurar abincin nan muna turawa a cikin mu. Na kaisu inda zasu kwana na musu sai da safe na tafi dakina, alwala na dauro na dukufa sallah ina nemawa Marwan sauki a wajen Allah.

Kwanaki uku suka zo suka wuce babu wani cigaba, na rame na fita a hayyacina kamar mai jinya koda yake bani da maraba da mai jinyar ma. Hindu ta warware an sallameta, ita kam har taso ta fini damuwa da halin da Marwan yake ciki. Gidana ta koma da zama gabadaya, don haka en zuwa dubiya da barka dangin shi ne ko na Hindu duk a gidana suke tarewa. Tare muke kwana da Iklimah kanwar Marwan, ita take tausa ta da kalamai masu dadi da kwantar da hankali.

A cikon kwana na biyar, mun je asibitin tun da safe kamar yadda muka saba zuwa, yanzu suna bari a shiga inda yake sai dai basa barin ayi hayaniya. Idanunshi a bude tarwai muka same shi a kwance, da alamun ya jima da tashi. Farin ciki ya mamaye mu, na rasa me zanyi a lokacin? Kawai na rushe da kuka, na ruga da gudu na fada jikinshi na rungume shi ina ci gaba da kukan, yasa hannu yana dan bubbuga baya na a hankali alamun rarrashi. Su Maah suka zagaye gadon da yake kwance kowa na furta kamar Alhamdulillah! Na koma gefenshi na zauna akan stool din dake gefen gado hannuna sarke cikin nashi kamar wadda take tsoron a kwace shi. Likita ya shigo ya duba jikin shi, Yanayin fuskar sa ya nuna alamun gamsuwa da yanayin jikin Marwan, don haka ne muka kara jin zuciyoyin mu sunyi wasai. Bayan fitar likitan na taimakawa Marwan yayi wanka da ruwa mai dumi kamar yadda likitan yayi umarni, ya sha madara marar sanyi ya biya bashin sallah da aka biyo shi.

Bayan ya gama ya zauna, aka kawo mishi danshi, ya amshe shi ya rungume shi a jikinsa, ya mishi huduba da Muhammad Al'Ameen. Ranar mun wanzu cikin farin ciki a asibitin nan, da yamma kamar kada mu tafi haka muka dinga ji.

Washegari da muka zo jikin nashi har yafi warwarewa, yana zaune a gefen gado da dan karamin qur'ani a hannunsa yana karantawa. Ganin cewa ba kowa a dakin lokacin na duka a gabanshi na bashi kyakkyawan sumba a kumatu, na gaishe shi sannan na taimaka mishi yayi wanka ya karya da abu mai dan ruwa wanda na dafa. Daga nan hira muka zauna muna yi, baby Al-Ameen yana hannuna yayin da nake zaune a gefen Maah da mahaifiyar Hindu, Hindu na zaune a gefen Marwan akan gado. Muhammad Kabeer kuma yana kan stool daga can bakin kofa. Kawai ji muka yi an turo kofar dakin an shigo, dan sandan nan ne da yake kula da case din wanda na yiwa rotse, ni na ma manta dasu ko don kwana biyu ban gansu bane? Muka gaisa dashi a mutunce ya duba jikin Marwan, ya dube mu daya bayan daya yace

Please Login or Register in order to submit comment