Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta sauke kafin ta ce "Fine, ita kuma mahaifiyarki zan kirata tana tina muku cewa ni yayarta ce, ni kadai take dashi a duniyarnan tinda ba uwa ba uba" Dariya tayi a hankali ta ce "Ai munsani Mum, tana kuma gaya mana, ni maganar aure ne banaso kina min wallahi" Mummy ta ce "Bari dai na dawo kasar kafin komai, aure ko bakyaso sai kinyi shi tinda ba zama zamuyi tayi dake ba" Rafi'ah ta yatsine fuska ta ce "Ai Abba is not in support, SS2 fa kawai nake Mummy, why not idan na gama degree" Mummy ta ce "Allah ya kiyaye, kina gama secondary school zakiyi aure, shiyasa nake tina miki ki tsaida miji, shi kuma Abban naki idan bazai aurar dake ba sai ya bani ke tinda shi gani yake kamar labari kawai nake, indai ina raye sai dai ki karasa karatunki a gidan miji" Rafi'ah ta dan ta6e baki a hankali ta ce "Ai iyayena ma ba yarda zasuyi ba" Cike da masifa Mummy ta ce "Yimin bori dan ban haifa ba, da ace ina da 'ya'ya mai zaisa na saka miki ido Rafi'ah, ai a rashin babu ne" jin mood dinta ya canza yasa Rafi'ah yin dariya sannan ta ce "Just joking fa Mummy, kiyi hakuri" Mummy ta ce "Sai anjima zan kira idan na koma gida" bata jira cewar Rafi'ah ba tayi hanging call din.
Wajajen karfe 3 na rana Rafi'ah ta tashi daga nauyayyen baccin da yayi gaba da ita, ta mike a hankali ta shiga toilet tayi brush sannan ta doro alwala ta fito, hijabi har kasa ta saka sannan ta hau kan sallaya. Bayan ta idar tayi addu'a sannan ta cire hijab din ta dauka phone dinta dake kan gado ta fice a dakin. Tafiya take cikin quick light step har ta karasa saukowa daga stairs din, ta karasa cikin falon tana kallan Ummi dake marking papers din gabanta, saam bata kula da luvly brother dinta dake zaune akan dinning ba, bayan ta zauna gefen Ummi ya taso a hankali ya cire scarf din kanta, tayi tsaki ta juya tana kallansa ta ce"Ka dawo kenan ko?" daga haka ta kwace hulanta ta saka, tana juyawa ya kara cire mata yana dariya, kamar zatai kuka ta ce "Ummi wallahi zan zane Abdul, kiga abinda yakemin" Ko kallansu Ummi batai ba bare tayi magana, Abduljalal ya zauna gefenta ya dora hannunsa a shoulder dinta ya ce "How are u Anty nah, yau a school anata tambayan ki nace kinje follow-up Clinic" a hankali ta ce "Ohk". Bayan Ummi ta gama marking dinta ta dago tana kallan Rafi'ah da gaba daya tayi collapsing jikin Abdul tana kallo, Ummi ta dalla mata harara ta ce "Tashi ki zauna" mikewa tayi da sauri tana turo baki ta ce "To Ummi kice ya tashi na kwanta, mu 3 akan sofa daya" Ummi ta ce "Ke ki koma caan mana" ta make kafada ta ce "Ni kusanki zan kwanta" tana rife bakinta Abdul ya tashi ya nufi dakinsa yana murmushi ya ce "Na kar6i girman". Daga haka ta koma ta kwanta tayi pillow da cinyar Umminta, bayan few minutes Ummi ta ce "What did u told Abba in the morning?" Tashi Rafi'ah tayi tana kallanta ta ce "I haven't told him anythi..." Kallan da Ummi ke mata yasa tayi shiru ta sunkuyar da kanta, Ummi ta ce "This should be the last zamuyi abu baya nan ki kirashi ki gaya masa, sau nawa ina kaiki Clinic muna kar6an magani?" Tayi shiru still kanta na kallan kasa, Ummi ta ce"Talk now, how many times? Ya kirani dazu yana ta fada na barki kin fita ke kadai, ba Mustapha nace ya kaiki ba? shekara 17 ace bazaki iya zuwa ki kar6a common drugs ba, i still don't like yadda Abba yake treating dinki wallahi, nayi magana harna gaji, wallahi Abdul ya fiki iya abubuwa, ya dawo kamar shine gaba dake, when will u change Rafi'ah fisabililliah?" Sai lokacin hawayen idanta ya sakko, wallahi har zuciyarta ba wai ta fadawa Abba dan yayi fada bane. Bayan hannunta tasa ta share hawayen idanta sannan ta dago ta kalleta ta ce "I'm sorry, and insha Allah i won't repeat such thing again" Ummi ta ce "Better, kin kira Anty Haliman ne?" Ta kara turo baki ta ce "Na kirata dazu, nifa wallahi kice mata ta dainamin zancen aure inba hakaba zan daina kiranta duka duka kowa ma ya huta" Ummi ta ce "To menene damuwanki da zancen aurenta? Wallahi koda wasa kar naji kin daina kiranta, banda shashanci irin naki auran za'a miki yanzu? Ki bita kawai a hankali" Rafi'ah ta share guntun hawayenta ta ce "Kuma harda cewa wai nafisan dangin Abba da ita, ni meye ruwana dasu banda gaisuwa daya zama dole" Ummi ta ce "Ki daina min hawaye dama, koma me zata fada u have to listen, ita kadai nake dashi duk duniya, bayan ni baku da wata uwar data wuce Anty Halima" a hankali ta ce "I know Ummi but ni banason yadda Mummy take abu sometimes, komai sai tayi magana haba" Ummi ta ta6e baki ta ce "And i asked u to cook kikaje kika nemi gado kika hau bacci ko?" ta yatsine fuska ta ce "Zanyi yanzu" Ummi ta ce "It's impossible in jira sai kin gama baccinki na jaraba kafin kiyi abinci, na gama rice kije ki rakasa stew din and if u like pls let it burn" daga haka Ummi ta mike ta dauka scripts dinta ta haura upstairs.
Kitchen ta wuce ta gauraya stew din sannan ta fito ta wuce upstairs zuwa dakinta, Hijabs dinta guda 3 ta dauko duk color daya sannan ta sakko, Abdul ta samu yana zaune yana cin banana, ta karasa kusanshi ta ce "Abdul pls help me and wash my Hijabs, kaga gobe zanje school kuma Thursday akwai hadda" ya juyo yana kallanta ya ce "Let me finish watching this match, i will wash ltr" ta shagwa6e fuska ta ce "Haba Abdul, kawai kaje ka zuba ruwa a washing machine kasa liquid detergent shine sai anjima that's all it's fah" ya ce "Anty banfa ce bazan wanke maki ba, wai ma meyasa ba kisa an kai laundry ba" ta zaro ido ta ce "Da Mustapha sai yayi sati bai kar6o kayanba ni inada Islamiyya jiranshi zanyi, just tell me idan baza kai ba" tashi yayi ya kar6i hijabs din yana kallanta ya ce "Is that all?" Ta bashi light hug ta ce "Thank u dan kanina me kama da Mummy" daga haka ta fashe da dariya, yaja tsaki ya ce "Ni bana kama da ita, kiba ne kawai kamar ita" bin bayanshi tayi har backyard tana ta dariya ta ce "Allah kuna kama" ya ce "That's what people said, amma ai ni bana fada irinna Mummy, jiya fa dana kirata we spent more than 1 hour muna waya, duk kuma complain takemin a kanki" a wani balcony dake wajen ta zauna ta ce "Na kirata ai yau, ta daiyi fada kam, ni dama idan ta gama Umranta ta dawo Nigeria ta wuce Bauchi mu huta" Abdul yayi dariya ya ce "Gidansu anan kice su wuce Bauchi" ta ta6e baki ta ce "To gidanta kam sai bayan wata wata zan ringa zua". Haka sukaita hiran Mummy har kayan ya gama turning ya tsaya, ta kalli Abdul ta ce "Dan Allah kayi spinning Abdul" ya ce "Komai zan maki ne wai" ta ce "Pls, kaga Salma Umar kaninta har nails dinta yake yanke mata idan yayi tsayi, kaga nima yayi tsayi zaka yankemin ko Abdul dina" Murmushi sosai yayi ya tashi ya fara kwashe hijabs din, duk duniya bayan Abbansu da Umminsu ba wanda ya keso sai luvly sister dinshi, he hate seeing her crying, he hate seeing her unhappy, duk wani abu a duniyar nan da zaiyi turning dinta upside down baya sonsa, wani lokaci ji yake inama lalurar da Allah ya dora mata ya dawo kansa. Ji yayi kawai ta tashi a firgice, ya juyo yana kallanta ta ce "What's that Aunty?" Kamar zatai kuka tana kallansa ta ce "Oh my God, it's burnt, it's brunt i know, Allah na manta dashi ne" daga haka ta zura da gudu tayi hanyar kitchen Abdul ya bita da kallo yana kyalkyala dariya.

*Attention pls 🙏🏻*

*This is to inform u that i may not be able to be updating everyday, I'm still in school so sai ranar da kuka ganni kawai, but i promise u that i will try my best to be entertaining u insha Allah, so expect no date of posting, u can see me any day/time. Sannan littafin bana kudi bane na wanda ke da ra'ayin karanwa ne 🥰*

*The page is dedicated to Fadila Madaki* 😍
[6/9, 11:00 AM] Teemarh: *_...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers_
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️

*BY FATIMA* _{Real~Teemarh}_

_5~6_

Anty Khadija ce zaune a babban parlon su da glass cup a hannunta tana shan exotic, lokaci~lokaci ta kan daga kanta ta kalli series din da ake a TV, bayan ta shanye na cikin cup din ta dago kanta tana kallan mahaifiyarta dake zaune a gefenta ta ce "Umma bafa kice komai ba?" Cike da damuwa matar da aka kira da Umma ta juyo tana kallanta, Anty Khadija ta ce "Dole ne fa Umma mu tashi tsaye, wallahi tallahi Yusuf ya kawomin budurwarsa har office dina, i'm still in a state of shock Umma, wai Yusuf da budurwa, lallai kam this is impossible wallahi" Umma ta ajiye remote din dake hannuna ta juyo tana kallan Anty Khadija, sai lokacin ta samu damar motsi, ta kirkiro murmushin takaici ta ce "Ba sai yayi auren ba idan shi yake da iko, indai ina raye rayuwar Yusuf ba zata ta6a kyau ba wallahi, sai dai ya kare rayuwarsa a haka, idan yaso ciwan zuciyar ya kashe shi" daga haka ta mike ta fara haurawa stairs, Anty Khadija taci gaba da chewing gum dinta ta ce "Atoh, indai ba'a dau mataki ba kam komai zai lalace" daga haka ta dora kafarta daya akan daya taci gaba da shan exotic dinta.
kasa dago kanta tayi tana ta wasa da fingers dinta, sai bayan Ummi ta gama mata fada ta ce "Pls don't let me angry again, wallahi zan manta da baki da lafiya na miki duk abinda naga dama" a hankali ta ce "Kiyi hakuri" Ummi ta ce "Ki wuce ki gyara kan dinning" tabi ta gefe a hankali ta wuce zuwa parlor ba tare data bari sun hada ido da Ummi ba. Karfe 8 bayan an idar da sallan isha Yusuf ya shigo parlor, milk shadda ce a jikinsa ta sha aiki, tayi masifar amsar jikinsa kamar dama saboda shi akayi ta, kallo daya Umma ta masa ta dauke kanta, ba yabo ba fallasa ya dan saki fuska ya ce "Sannu da gida Umma" a hankali ta ce "Sannu" Anty Khadija ta ce "Doctor sai yanzu?" ya ce "Wallahi Anty, nayi meeting ne shiyasa na dawo late" ya karashe maganar yana cire lab coat din jikinsa ya nufi dakinsa, Anty Khadija ta bishi da harara kasa kasa ta ce "Wicked man" Umma ta ce "Not only wicked" Anty Khadija ta ta6e baki looking into her mother's eyes ta ce "Ni wallahi Umma a duniya idan akwai wanda na tsana ya biyo bayan Yusuf, duk da nunawa nake ina san shi ina kaunarshi amma bakiga da yadda nasa ya kawomin budurwarta saba" Umma ta harari kofar dakinsa ta ce "Yanzu haka ma wajenta yaje zaice wani meeting yayi, indai ina raye kaida farinciki kunyi sallama, aure kuwa sai dai yaga anayi" Anty Khadija ta ce "Sai fa kinyi da gaske kin kara cusa masa tsanar rayuwar aure, ni dama i just wanted to know ko yana da budurwa yasa na matsa masa, kuma na ganta, fara sool, gata yarinya da ita" Umma ta ce "Ina nan dake shida kansa zaice baya santa wallahi, banda shi ba ma yaji da ciwan dake daminsa zai jajibowa kansa soyayya, ai insha Allahu wannan yarinya itace ajalinsa" Anty Khadija tayi murmushi ta ce "Allah yasa, kinga idan ya mutu ai wancen tsohon zai daina mana maganarsa kowa ma ya huta" Umma ta ce "A juri zuwa rafi dai" kiran daya shigo wayarta ne yasa tayi shiru ta dauka wayar ta kara a kunne, bayan ta gama answering call din ta ce "Wai yaushe Jiddah zata dawo ne Umma?" ta ce "Duk sanda kika dawo da ita, dama bake kikace ta tafi a gidan ba" Anty Khadija ta ce "I'm thinking about something, why not muyi amfani da Jiddah ta hanyar rushe soyayyar Yusuf da waccen yarinyar" Umma tayi murmushi ta ce "Haka ma yayi" daga haka Anty Khadija ta mike ta nufi upstairs tana dialing phone number din Jiddah.

Ranar Friday da yamma Rafi'a na zaune a dakinta tana tilawa Abdul ya shigo rike da phone dinsa ya na "Mummy want to talk to u" ta kar6a wayar ta kara a kunne hade da sallama, Mummy ta ce "I don't really know the essence of ur phone Fatima, why is it always off? Haka saurayinkin yake kiranki yaji ko yaushe a kashe" Abdul ya sheke da dariya harda kwanciya, turo baki kawai tayi kafin ta ce "Ni Islamiyya zan tafi ai mun gaisa" Mummy ta ce "Kika kashemin waya wallahi sai ranki ya 6aci, daga tambaya zaki taramin mutane wani wai islamiyya, Allah yasa Madina zaki taho" Qur'an din ta ajiye gefen bed side drawer ta mike tsaye, Mummy ta ce "To dama next week zan dawo, nace bari na fada da wuri dan ranar dana sauka dake zan wuce gidana" kallan wayar kawai Rafi'ah take with confusion ta ce "I will just go and see u Mummy, Abba ya hanani barin gida" Mummy taja tsaki ta ce "Sai na gani ai, na ta6a jin yadda ake hana diya taje wajen yayar uwarta, shekara nawa ina naci ya bani ke baiban ba na hakura, sai dan kwana uku zuwa hudun da zakimin zai hana, da anyi magana yace ba lafiya kike dashi ba, ai yanzu kam we have to drop a very big thank to God, Zainab tacemin bai fiye tashi ba yanzu ko?" daga mata kai tayi kamar tana gabanta sannnan ta mikawa Abdul wayarsa ta ce "To Allah ya kawoki lpy" Mummy ta ce "Alright sai anjima" daga haka tayi hanging wayar.
Dai dai lokacin Ummi ta bude kofar dakin, ta dinga kallan Rafi'ah dako uniform din boko bata cire ba, gashi har ana shirin islamiyya, Ummi ta ce "Why haven't u remove ur uniform Fatima?" A hankali ta ce"I slept off bayan na dawo, yanzu zanyi shirin islamiyya" Ummi ta ce"Hope u are not sick?" Girgiza mata kai tayi ta ce "Noo, stress ya sani bacci Ummi" ta ce "Ohk, Abba yana hanya fa" tayi wani tsalle hade da kara ta ce "Are u serious Ummi?" Ta daga mata kai ta ce "Sure, ya kiraki bai sameki ba" gaba daya she can't hide her happiness, ta rungume Ummi cike da shagwa6a ta ce "Almost 2 months fa banga Abba ba Ummi, amma dai muma 2 months zai mana ko?" Ummi ta zameta a jikinta ta ce "I don't know" Rafi'ah ta zauna gefen gado ta ce "Is he alone?" Ummi ta dalla mata harara ta ce "U can call him and ask" turo baki tayi ta tashi ta fara cire uniform dinta ta ce "Ai nasan waccen matar saita biyoshi" Ummi dai bata kula taba ta kalli Abdul dake kwance kan gadon Rafi'ah ta ce "Kai ba zaka je islamiyyan bane?" Ya mike yana kallanta ya ce "Zanje Ummi" ta ce "Oya do fast is after 4 now" daga haka ta fice a dakin yabi bayanta shima. Har Abdul ya shiya ya dinga jiran Rafi'ah a mota bata fito ba, ya kalli Mustapha dake kallan film din india a wayarsa ya ce "Let me check on her" daga haka ya koma cikin gida, a parlor ya samu Ummi tana tasa turaren wuta, ta juyo tana kallansa ta ce "Baku tafi bane, karfe 4 da rabi fa" ya tsaya yana kallanta ya ce "Anty isn't out fa Ummi" ta ajiye kwaskon hannunta ta nufi stairs ta ce "The only thing Rafi'ah can do fast is to sleep, in dai bacci ne tana kwanciya bata kara minti daya" tana bude kofar dakinta ta sameta a gaban mirror tana ta fama da trouser dinta ta kasa daure tazuge, dama mostly Ummi ke daura mata ko Abdul, itama ta koya amma yau gaba daya ta rasa kan abin ta masa kulli yafi hudu, dago kanta tayi tana kallan Ummi kamar zatai kuka ta ce "Help me pls Ummi, i can't do it, tin dazu yaki zama, my neck is even aching" Ummi taja tsaki ta karasa gabanta ta durkusa tana gyara mata ta ce "Keep shut now before i give u a dirty slap, when was the last time na koya maki daura abin nan" kamar zata fashe da kuka ta ce "Ummi ni kasawa nayi, I'm just trying my best but na kasa daurawa" mikewa Ummi tayi bayan ta gama daura mata ta ce "Wear your hijab and come out now" ta dauka zulelen hijab dinta har kasa ta saka sannan ta lankaya side bag dinta da qur'an ke ciki ta biyo bayan Ummi, bayan sun sauko ta bata light hug ta ce "Pls Ummi kiyi ma Abba hug dina kafin na dawo na mishi wani" Ummi ta dalla mata harara ta wuce kitchen, murmushi tayi ta fita a parlo'n ta wuce parking lot, bayan ta shiga motar Abdul ma ya shiga, Mustapha ya juyo yana kallanta ya ce "Wani film din india nake kalla Hajiya Rafi'ah, yarinyar yadda kikasan ke, komai naki take, ita fa har takalmin makaranta mahaifiyarta take saka mata" dalla masa harara Rafi'ah tayi ta shiga turo baki, hakan yasa yayi shiru yaci gaba da tukinsa, dan yasan yau babu me ta6a Rafi'ah tinda Abba yake hanya, in kwa aka ta6a ta har abinda aka mata tin tafiyarsa saita juye masa, shima Abdul shiru yayi ganin irin 6ata ran da tayi, bayan few minutes ta ce"Ai duk kaika fada mishi" Abdul ya zaro ido ya ce "I'm not the one sis, have u forgotten he said... " toshe kunnuwanta biyu tayi, cikin tsawa ta ce "I don't want to hear anything pls" shiru yayi ya juya kansa gefe, yasan by this time kam sunyi late kuma ana duka, shi kuwa tinda ta masa shouting bazai kar6a mata duka ba yau.
Mustapha na parking suka fita yaja mota ya barsu a wajen, Abdul ya nufi gate din ya tura, zaro ido tayi ganin students a compound ana ta dukan lattee, Abdul ya danyi murmushi ya shige ciki tabi bayansa, duk gaba daya ta gama tsorata sai numfashi take saukewa daki daki, ga idanuwanta da suka fito alaman tsoro, bayan an yiwa kowa Abdul ya mika hannunsa aka masa guda hudu ya wuce, Rafi'ah da duk ta rude ta ce "Pls don't leave me Abdul, pls help me kaji dan Allah" ko ya juyo ya kalleta ya shige ciki abinsa, Malamin ya daure fuska yana kallanta ya ce "Kawo hannunki" ta ce "Ai Abbana yazo ya fadawa Malam Ahmad kar ana dukana, bani da lafiya wallahi" wani kallan rashin mutunci ya mata ya ce "Ai kowa ma ba lafiya ce dashi ba, ki kawo hannunki na dakeki ki wuce aji an fara kar6an hadda" ta dukunkune one side ta ce "Pls let me go, i promise not to come late again, dan Allah kamin hakuri" Tinkarota malamin yayi ta fasa kara jikinta ya hau rawa, har idanta ya cika da kwalla ta dago tana kallansa ta ce "For God sake na roke ka". Muryar wani malami sukaji yana cewa "Wannan ai mahaifinta yazo tin shigarsu islamiyya ya sami headmaster, ai ba'a dukanta Malam Umar" ko kallansa Malam Umar baiyi ba ya ce "Su sauran 'ya'yan da aka daka ba mutane bane, dan meyasa zaku ware ta ace baza a ta6a taba, ni ba ruwana da ubanta koshi waye dukanta zanyi wallahi" Malam Sadeeq ya ce "Ba batun 'yar wani bace Malam, indan haka za'a bi ai rabi da quarter ba dukansu za'ai ba, ina maka bayani ne akan akwai dalilin da yasa ba'a dukanta" ganin ko kallansa baiyi ba yasa ya wuce ya barsu a wajen, sai lokacin hawayen idanta suka gangaro kasa, ya daka mata tsawa ya ce "Bani hannunki kona miki a jiki ki wuce" girgiza masa kai ta hau yi ta saita kofar gate ta fita a dari da sittin.
Cikin saurin ya taka birki yana fadin innalillahi, itama gaba daya ta tsoruta jira kawai take taji an kade ta, jin shiru yasa ta bude hijabinta a hankali tana kallan gabanta, sai kuma ta sunkuyar da kai ta kasa magana, Yusuf ya fito a motar sanye da lab court, daga gani yanzu ya tashi a clinic, ya dinga kallan Rafi'ah da kanta ke kasa ya ce "U again" ta dago da sauri jin muryarsa, suna hada ido ta saukar da kanta kasa, ya matso kusa da ita ya ce "U haven't forgot the other incident right?" Ta girgiza kai a hankali ta ce"It isn't my fault that time, shine yazo ya bigeni without me knowing and baiyi horn ba" ya danyi murmushi yana kallanta ya ce "Yau fa?" ya karashe magana yana shafa beard dinsa, ta kara sunkuyar da kai ta ce "I'm sorry it wasn't intentional, and dukana za'ai" Yusuf ya dan zaro ido ya ce "Who?" Ta ce "Malam Umar" ya kalli gate din islmiyyar sannan ya kalleta ya ce "Why?" Kamar zata fashe da kuka ta ce "Is because i'm late" ya ce "And why did u came late?" Sai lokacin ta dago kanta tana kallansa ta ce "Na kasa daura tazugen wandona shin... " zaro ido tayi da sauri taja baya, sai a lokacin ta lura saam bai dace ta fada masa haka ba, ya danne dariyar dake cinsa ya ce "Then what?" Ta fara kame kame ta ce "Noo i slept off.... Yes i slept and... And i woke up very late..Very late i swear"
[6/9, 11:00 AM] Teemarh: *_...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers_
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️

*BY FATIMA* _{Real~Teemarh}_

_7~8_

Folding hannayensa yayi yana kallan idanta ya ce "This is not strictly true" ta saukar da kanta kasa a hankali ta ce "It's true" murmushi me kyau yayi ya dan matsa gefe kafin ya ce "To ki shiga ciki" ta noke kafada ta ce "No, i'm going back home" ya ce "Why?" Ta ce "Yace zai dukeni to" ya danyi murmushi yana shafa tulin gashin dake kansa ya ce "To muje na kar6a maki" ta dan zaro ido ta ce "Are u serious?" Ya ce"Sure let's go" ta saki wani daddaden murmushi tabi bayansa suka shiga gate din. Ba kowa a compound din sai sound din karatun student, ya juyo yana kallanta ya ce "where is ur class?" Ta nuna masa upstairs da hannunta ta ce"A sama ne" bin staircase din yayi da kallo kafin ya fara takawa tabi bayansa. Suna hawa ta nuna masa class dinsu, ya shiga da sallama ya mikawa malamin hannu, ita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment