Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ba ya saki hannun Sultan ya mike tsaye.

“Raliya ki fadawa Umma na wuce”

“Okay”

Raliya ta amsa tana kallon Baturiya cike da jin haushin abun da yar'uwarta take yi a gabanta. Sai da ya fice sannan ta kalli Baturiya ta ce.

“Wallahi Rafi'a baki kyautawa, talauci ba fa ba hauka ba ne, baki san budin da Allah zai masa nan gaba ba”

Baturiya taja wani shegen tsaki.

“Ki dauki arziki ki ba shi, idan mun zauna mu kadai kin san iya abun da yake min ne? Kin san yadda yunwa take halaka mutum kuwa? Dan Allah karki kara min da wata damuwar ki bar ni na ji da wanda nake ciki”

Tana fadar hakan ta mike tsaye ta nufi dakin mahaifiyarta, Sultan ya bi bayanta.



Family house dinsu ya nufa cikin rashin jindadi, daman ta saba masa a gaban yan uwanta, yan'uwansa kam daman sun san irin zaman da suke, hakan yasa kanensa basa sha'awar zuwa gidan sai da wani babban dalili, domin bata musu tarbar arziki.
Mai achaba na sauke shi kofar gidan ya ciro kudinsa ya mika masa sannan yai sallama ya shiga cikin gidan, tun daga yanayin yadda ya ga gidan ya san ba su girka komai ba, domin murhunsu a bushe yake, a take ya ji ransa ya kara baci domin baya son ganin mahaifiyarsa a hali na yunwa, ga kuma damuwar halin da suke ciki na neman kudin aure. Da sallama ya shiga cikin dakin kanwarsa Aisha ta amsa ciki yanayi na damuwa. A bakin kofar dakin ya tsaya yana kallon mahaifiyarsa dake lullube da wani tsohon zanen gado tana ta rawar sanyi.

“Jikin ne?”

Ya tambaya da muryar dake bayyana tsananin damuwarsa.

“Haka ta kwana”

Aisha ta amsa.

“Miyasa ba a kira ni ba?”

“Ita ce kar a kiraka kar a tayar maka da hankali”

Runtse ido yai ya sauke ajiyar zuciya, ya dade a haka kamin ya bude idon ya nufi inda mahaifiyarsa take kwance ya zauna daf da ita, sai ta yaye mayafinta ta kalleshi da idanuwanta dake fassara irin tsananin zazzabin da take.

“Faruq”

“Mama damuwar nan ce kika dauka kika saka a ranki ko? Allah shi yake yin komai, kuma daman na yi tunani zamu hutar ta da kanmu da wani lefe ya bada kudin kawai a siya mata kayan daki da su”

“Ko ya bada kudin ai ba zai wuce 100k ba kuma ba zai isa a siye kayan daki ba, ko kujeru kanana yanzu sai an siye su 60k ko fiye ma”

“To ai sai a kara da wani abun idan Allah ya mana fatahi, dan Allah ki cire damuwa a ranki, Mama so kike ke ma mu rasa ki? Haba Mama”

“Damuwa dole ce Faruk bayan ta auren yaran nan akwai ta yau da kullum, yanzu ga shi abun da zamu karya ma ya gagaremu sai da na ba Asiya ta siyar da tufafina sannan zamu samu su karya, tun safe har la'asar ace bawa bai saka komai a bakinsa ba”

“Allah be manta da mu ba Mama, bayan wuya sai dadi, kuma idan ka ga tsanani yayi yawa sauki na tafe, Inshallah komai zai warware kamar ba a taba yi ba”

“Allah yasa muna da rabon jindadi ko kadan ne Faruq, lokaci tafiya yake baya jiran kowa”

Ta karasa tana runtse ido da karfi sakamakon bugawar da zuciyarta tai da karfi. Daga Aisha har Faruq hankalinsu tashi yai.

“Sannu Mama”

Kai ta daga musu cike da karfin hali har lokacin idonta na rufe saboda azabar ciwon da take ji. Ajiyar zuciya Faruq ya sauke ya mike tsaye ya bar dakin cikin damuwa, ji yake kamar ace yana da halin da zai magance damuwar mahaifiyarsa, kuma ya kaita asibiti a duba lafiyarta, amman ina? Talauci ya saka shi a gaba kamar wanda ya zagi arziki.



LEILA POV.

Rike da takardun Madina ta shiga dakin Momy ta zauna gefen gadonta.

“Momy Could you do me a favour?”

Momy ta aje plate din abincin dake hannunta ta kalli Leila dake sanye da doguwar rigar shadda ta sha aiki kamar sabuwar amarya.

“Minene?”

“Kin san kawata Madina ai...”

“Har sai kin sake gabatar min da ita? Madina ai ta zama yar gida”

“No Momy ina son ki gane cewar maganar da zan miki tana da muhimmanci ne, Wallahi ta min magana tana son aiki a kamfanin Daddy and i promise her zan saka a dauke ta”

“And....?”

Momy ta bukata tana tsattsage hakoranta na makka.

“So daman dazun na mata magana ta kawo takardunta shi ne ta kawo, da na zo naje na samu Daddy kai tsaye da maganar amman na san zai ce na bawa Talba ne, Talba kuma zai iya cewa ba zai dauke ta ba, kuma kin san be kamata na kasa yi mata haka ba, ko da ba ita ba ma a kamfanin mahaifina ya kamata ace zan iya yin komai ina da ikon yin komai”

Momy ta yi dariya.

“Leila kenan, kina abu kamar ke ce Amal, idan za a dauki wani aiki ta dalilinki har sai kin tsaya wani kame kame? Ki same yayanki Talba da maganar mana”

“No Momy ni fa bana son magana da shi sai idan wani babban abu ne, yadda yake jin kansa haka nakr jin kaina, kuma kin san zai iya amfani da wannan damar ya wulakanta ni ko ya fada min wata maganar marar dadi, idan kuma na rama ke da Daddy ni zamu dorawa laifi”

“Wannan ai da ne Leila, amman yanzu na fahimci halin da kike ciki, halin Talba sai mai hakuri da kai zuciya nesa ni kaina yanzu ya fara min ai”

“Shiyasa nake son ki saka shi ya dauke ta... ”

Tana rufe baki Talba ya kwankwasa kofar dakin sannan ya murda kofar ya turo ya shigo, juyowa tai ta kalleshi, a take annurin dake fuskarsa ya auri idanuwanta, duk yadda ta so ta dauke kai daga barin kallonsa sai ta kasa har ya karaso inda Momy take ya zauna a saman kujera, lumshe ido tai tana ta yaki da numfashinta dake ta kokarin sauya mata kamshin dakin Momy zuwa na turaren Talba da ya cika daki.

“Momy barka da dare”

“Yauwa”

Yanayin yadda Momy ta amsa masa ne yasa shi murmushi domin ya san har yanzu bata gama hucewa daga laifin da be aikata mata ba.

“Allah yasa dai ba fushi kike da ni ba har yanzu Momy?”

Uffan Momy bata ce masa ba, hakan ya saka shi kara yin Murmushi sai dai wannan karon be ce komai ba.

“Abun da kake dai ba abu ne mai kyau ba, mata aka sani da tsegumi ba maza ba”

“To ayi min afuwa ba zan sake ba, Leila...”

Ya karasa yana kiran sunanta, sai ta bude idonta a hankali ta kalleshi ba tare da ta amsa ba, daman shi ma he called her name ne kar Momy tace ta ganta be mata magana ba, duk kuwa da kasancewar ita ya kamata ta fara masa magana a lokacin daya shigo a matsayinta na kanwarsa kuma wacce zai aura, ko ba komai ai ita ce karama.
Mikewa yai tsaye sai Momy ta dauki takardun da Leila ta aje mata gefenta ta mikawa Talba. Sai da ya kalli takardun sannan ya mika hannu ya karba ya bude yana dubawa.

“Ba mu fara daukar ma'aikata ba, muna da enough”

Ya fada bayan ya dauke idonsa daga fararen takardun zuwa ga Momy.

“Na sani, saka iya replacement dinta da wani ai”

“Na dauka Madina tana aiki da ma'aikatar Alhazai ai”

“Tana yi, yanzu nan take so kuma umarni ne so nake ka dauke ta”

Ya hade yawun bakinsa, sannan ya kalli Leila da ita ma kallonsa take ya rufe takardun ya juya ba tare daya sake cewa komai ba ya fice, binsa Leila tai da kallo har ya fice sannan ta juyo ta kalli Momy.

“Thank Youu Momy”

“Karki damu, je ki samu abun da kika sakawa cikinki”

“Okay”

Ta mike tsaye ta fice daga dakin cikin jindadi. Ko da Talba ya fito Kabir na zaune kan center carpet tare da Amal suna shan kankana. Saman kofa Talba ya zauna rike da takardun yana kallon plasma.

“Malam bismilla karka ce mun maka rowa”

Kabir ya fada yana kallonshi, Talba kallonsa kawai yai ya dauke kai fuska ba yabo babu fallasa. Amal ta kalli Kabir sannan ya kalli Talba ta ce

“Ya Talba Momy ta maka fada dazun?”

Gira ya daga mata, wanda hakan yai daidai da saukowa Leila sai ya mike tsaye ya fice daga falon gaba daya.

“Strangers, ban taba ganin masoya irinku ba, wai a haka zaku yi aure?”

“Miye damuwarka ne Kabir? As long as yana so na miye ruwanka ne?”

Yayi dariya ya mikawa Amal hannu suka taba.

“Hi five Baby”

Dinning ta nufa ta bude manyan kulolin tana duba abun da Momy ta dafa, wayar dake hannunta ta aje a gefe ta dauki karamin plate ta dauka ta fara zubawa, abun ka da wanda baya son cin abinci sai ta zuba kadan ta ja kujera ta zauna. Kamar zaman ake jira tai sai ga sako ya shigo wayarta.

‘Good Night Dear’

Wani irin kasaitaccen murmushi tai bayan ta gama karanta sakon dake dauke da hoton zuciya.

“I love you”

Ta furta a zahiri, sannan ta aje wayar ta juya ta kalli Kabir dake ta rigima da Amal akan waye zai karasa shanye watermelon din da suka raga mai tawa, sai kuma ta juyo ta kalli abinci.

“Talba kana da wuyar sha'ani, wannan girman kan naka yana bani mamaki, ban taba ganin mai tsoro ko jin nakasu akan nuna soyayya ba kamar kai... But i love you..”

Ta furta tana kara jin shaukin kaunarsa na ratsa zuciyarta.


________

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.
  Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.


12

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa


_________


*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


Seven days later...

FARUQ POV.

A gabanta ya dire kofin dake dauke da koko ya dora mata suga a saman murfin.

“Ga abun da muka samu”

Wani banzan kallo tai ma kofin ta dauke ido tana turo baki gaba.

“Koko kuma? Ni bana son shan koko gaskiya”

Kallonta kawai yai ya dauke kai ya shiga dakin ya cire tufafin jikinsa ya daura wani tsohon tawul ya fito ya nufi inda ya jona ruwan zafi a electric a juye a karamin bokitin wanka ya fita waje ya sirka ruwan sannan ya dawo falon.

“Ni fa bana son koko”

“Wani yana can yana nema be samu ba”

“Wallahi babu, ba dai sa'ata ba, sai dai tsofafi sa'o'ina kyawawa kam suna can suna neman arziki”

Uffan be sake ce mata ba ya nufi hanyar dakin.

“Ni fa ba zan sha koko ba, waina nake so da nama”

Juyowa yai ya kalleta.

“Idan ina da halin siya miki ita kin sani, kuma babu abun da zai hana na siya miki, idan kuma babu sai ki yi hakuri har Allah ya kawo”

Sai ta mike tsaye.

“Tsakani da Allah Faruq kana cutar da ni, yanzu haka zan yi ta zama cikin matsi? Kamar mu muka fi kowa? Duk wani abun da nake so baka iya siya min sai idan na siyawa kaina ko kuma an aiko min daga gidanmu, ni gaskiya na gaji kana cutar nan kuma na san Allah zai saka min domin baya son zalinci”

“Gaskiya ne, Rafi'a baki da tunani ko kadan, kan mu farau talauci? Ko kuma mutum yana yi ma kansa arziki ne? Halin nan naki ya ishe ni..!”

“Da ya isheka da ka sauwake min, da ya isheka da ka samawa kanka mafita, tsakani da Allah Faruq idan ba kaddarar aure ba babu abun da zai hada ni aurenka, daman can na dauka zaka samu aiki rayuwa ta tafi mana da kyau, ashe hauka nake, gashi na gagara samun abun da zan ci ma”

“Saki kike so?”

“Eh saki nake so, ka sake ni Faruq ka sake ni idan ka haihu”

“Zan nuna miki na haihu”

Yana fadar hakan ya wuce cikin dakin da bokitin ruwan ya shiga bandaki ya watsa ruwan ya fito ya shirya cikin kananan kaya ya dauki makullin shagonsa ya saka aljihu, dayan aljihun kuma ya saka wayarsa, ko da ya fito tana zaune falon tana jiran ya mika mata takardar sakinta, tana ganinshi gabanta yai mugun faduwa.
Be kulata ya nufi kofar fita daga falon yai ficewarsa rai a bace.
Sai da ya fita sannan ta tashi ta fita ta rufe gidan ta dawo falo ta zauna, can kuma ta tashi ta fita ta dauko ludayi ta zo ta zauna ta bude kokon ta mutsa.

“Ba zan saka sugan ba”

Ta fada tana wurgar da kullin sugan ta fara shan kokon lami ba suga, ludayi biyu tai sai gata ta tashi ta nufi inda kullin sugan ya fashe ta kwaso a hannun ta nufo kokon ta zuba, ta zauna ta fara sha. Rabi ta sha ta bar ba Sultan dake bachi rabi, domin ta san bayan ya sha yanzu da rana ma zai iya nema.
Tashi tai ta koma saman kujera ta zauna, ta mika hannu ta dauki keypad din da Umma ta siya mata kamin ta siya mata smartphone, tsaki tai bayan ta shiga contact dinta ta fito ta shiga inbox dinta, nan babu komai domin sabun line ne da tai welcome back, hakan yasa ta ji babu dadi domin wanda ya saba rika babbar waya yana chatting idan ya rasata zai ji kamar ya koma a wata karamar duniya.

“Allah tsinewa Aljanin nan, ya dauke ni ya kai ni Kano kuma gashi nan ya rasa wayata da atm dina da yan kudina, Allah kasa min, Wallahi Faruq be da kashin arziki gashi nan na rasa komai”

Ta fashe da kuka. Kamar jira ake ta fara kukan sai ga kiran Ramlee ya shigo wayarta, share hawayenta tai sannan tai picking call din ba dan ta gane mai kiran ba domin number babu suna.

“Hello”

“Baturiya ya kike?”

“Lafiya kalau Ramlee ce?”

“Ni ce fa baki gane ni ba?”

“Number ba suna wayata ta bata ne na yi welcome back kuma numbers din ba su dawo ba”

“Garin ya? No wonder na yi ta kirankin number ki ban samu ba, na yi mamaki domin na san baki kashe waya”

A nan Baturiya ta labarta mata abun da ya faru, sai Ramlee ta saka mata dariya.

“Farin jininki yayi yawa Baturiya abun har da su Malam aljani? Shiyasa na ji muryarki wani iri kuka kike ne?”

“Ba dole ba Ramlee ina cikin matsala, ina son na ci da dadi na saka mai kyau amman abu ya garara, yanzu ko wayar nan tawa da ta bata ai daidai ne ya siya sabuwa amman sai da Umma ta siya min karama”

“Fee'at kenan, wannan fa duk kika so, da kin yarda da yanzu kin dangwali arziki har ma ki raba mijinki ciki, Wallahi Baturiya da zaki sake jiki yadda kike da kyau nan da har kyautar gida sai kin yi ma wasu”

“Ramlee ina fa da aure har da”

“Mace nawa ce mai yaya uku hudu har biyar take biyawa kanta bukatar da jikinta? Ke ko a unguwarku idan aka ce za a bude wasu matan auren ki ga sirrinsu zaki sha mamaki Wallahi, ba ki san cewa aure yana rufa miki asiri ba? Ko da kin samu wani abu ba za a zargeki ba? Yadda kike da kyau nan Baturiya ba ke ba ko ni da maza suke ganin hotunanki a wayata suna hauka sai na samu arziki, wai kin san ma dalilin daya saka na kira ki?”

“Sai kin fada”

“Wallahi wani ne ya sake ganin hoton ki yace kina cikin irin matan da yake so, na fada masa ke ba irin mu bace amman ya saka ni gaba wai na lallaba masa ke dan Allah, kuma babbar mutum ne dan siyasa, yanzu haka haka 100k ya bani wai na baki na wankan hoton da kika yi”

Baturiya ta mike tsaye tana dokan kirji idonta kamar za su fito.

“Dubu dari fa kika ce Ramlee”

“Wallahi ga su nan, tun shekaran jiya ya bani su jiya ma daker ya bar ni na yi bachi sai damuna yake da maganarki a waya kamar zai min kuka, shiyasa ma na kira ki da safen nan, Allah yasa ma mijinki baya nan”

“Baya nan ya aje min wani shegen koko ya fita”

“Kin gani yanzu da kina da kudi sai abun da ranki yake so zaki ci, idan kina free anjima zan zo na dauke ki a motata muje na siya miki sabuwar waya”

“Da kudin?”

“Aa da kudina dai, wacan kudin a cewa yai a baki kuma zan danka miki abun ki a hannu, amman ki yi tunani idan kika bada kai me kike ganin zaki samu? Bayan shi ma akwai maza da yawa musamman ace kina samun sakewa ana zuwa da ke hutu abuja ko kasar waje? Hmmmm Hajiyata ai kin take”

“To zunubin fa?”

“Allah gafurun raheem ne, kuma ban ce zaki dauwama a haka ba idan kin yi kin samu dan abun da kike so, sai ki daina amman ki yi tunanin future dinki dana yaronki koma nace yayanki na nan gaba Baturiya”

“Shikenan zan yi tunani”

“Yauwa Tawan haka nake son ji, ki yi tunanin kamin na zo kin ji? Yau ko wayar 500k kike so zan siya miki ita da yardar Allah”

Baturiya ta yi murmushin jindadi.

“Na gode kawata Allah ya bar min ke”

“Ameen Allah ya bar mu tare”

“Ameen”

Ta sauke wayar tana ta murna.

“Bari na yi sauri na gyara gidan kamin ta zo”

Ta dauki zane ta fara kabe kujerun, sai ta ji an kwankwasa kofar gidan, saurin saving number Ramlee tai sannan ta goge kiran da tai mata domin a tunaninta Faruq ne ya dawo. Sannan ta nufi kofar gidan ta bude sai tai arba da Malam Musa dilalin, cikin mutunci suka gaisa duk da kasancewar babu mayafi a jikinta sai hullar dake kanta.

“Mai gidan yana nan kuwa?”

“Aa ya fita”

“Oh dan Allah idan ya dawo ki ce masa na zo maganar kudin hayar nan, masu gida sun matsa, ko jiya da dare masifa yake ta min domin ganin yake kamar an bani kudin na kashe ne”

“Idan ya dawo zan fada masa, dazun ma yake cewa da ya ganka da ka saka masa number mai gidan domin yana son yai magana da shi”

“Indai maganar haya ne kar ma yayi domin Alhaji Sule be da mutunci ko kadan”

“Aa karka ce haka Malam Musa, bari na dauko wayar”

Kamin ya sake cewa wani abu ta juya da sauri ta koma cikin gidan ta dauko wayarta ta mika masa.

“Saka masa number a nan”

Be karbi wayar ba, ya ciro tasa wayar ya karanta mata number ta saka a wayarta.

“Idan ya zo zan fada masa sai na ba shi number”

“To yayi na gode”

Ta rufe gidan tana murmushi ta dawo falonta tana kokarin saving din number.

“Ba Alhaji Sule kake ba ko Alhaji lule kake sai na ci ubanka, talauci ya matsa shi ne kai kuma zaka kunno mana wata wutar dan kana da shegen tsohon gida”

Ta fada tana ƙwafa.


FARUQ POV.

Ya lalaba aljihunsa ya ciro naira 100 da ta rage masa ya mikawa Aisha.

“Je ki siyo koko ku sha”

Aisha ta saka hannu biyu ta karba.

“Yaya Wallahi ko jiya Mama ba tai bachi ba, yanzu ma jikinta zafi yake”

Ajiyar zuciya ya sauke.

“Jarabawa ce, ga rashin kudi, ga rashin mata ta gari, ga rashin lafiya Alhamdulillah”

Ya fada yana kallon mahaifiyarsa dake lullube bata ma san ya zo ba, karasa yai kusa da ita ya yaye mayafin data lulluba da shi ya taba jikinta sai ya ji shi da zafi sosai.
Mikewa yai tsaye ya fito daga dakin cikin wani irin yanayi na rashin jindadi. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya rike a hannu yana kallo, ya san ko siyar da ita yai kudin ba zai isa ya kai Mama asibiti ba, jinginar daya bada ma daker ya samu ya biya mutumen ya karbo wayar. Bakin kofar dakin ya zauna ya dafe kansa, yana mamakin lamarinsa wani lokacin shi kansa abubuwa suna daure masa kai, ga karatu yayi kuma ya fito da kwali mai kyau amman aiki ya gagareshi, wadanda sukai karatu tare wasu duk sun samu aiki har sun bar kasa, wasu kuma suna Abuja wasu a manyan mukana gobnati wasu a manyan bankuna da kamfani amman shi ya kare a shagon Barber, shi ma daker ya samu wani kawunsa ya bude masa shagon.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Allah ka kawo mana sauki”

Ya furta yana dago kansa ya shiga contact dinsa ya nemo number abokinsa kuma amininsa Nura.
Wayar bata dade tana ringing Nura ya dauka.

“Hello Faruq”

“Na'am Nura ya gida?”

“Lafiya kalau kwana da yawa”

“Sai godiya, ina su Sakina”

“Lafiya kalau”

“Wallahi Nura ina cikin matsala”

“Subhanallahi miya faru?”

“Abubuwa da yawa, yanzu dai wanda ya fi damuna rashin lafiyar mahaifiyata, kudi nake so rance idan zan samu na kaita asibiti”

“Kash.... Wallahi Faruq yau da 500 na tashi na basu su karya, ka san abu ga ma'aikaci idan ba albashi akai ba, ba mu da kudi, kuma gashi albashin na jihar zamfara sai a hankali anki a gyara mana, ga kayan masarufi sai tashi suke, abun da zaka siya da 20k yanzu sai 40k shiyasa albashin baya mana auki”

“Haka ne, Allah ya sauwake”

“Ameen, amman da zaka iya da kaje gidan Alhaji Mu'azu Shimkafa ance suna da Foundation na taimakon marayu da mabukata, amman idan baka jin kunya kasan wasu basa son zuwa irin abu na neman taimako”

“Haba Nura ina zancen kunya ga mai nema, suna nuna mutun a tv ne?”

“No babu ma wanda zai san an maka, amman ance Dattijon yana taimako sosai gaskiya, ban san yadda ake bi ba, amman dai idan kaje can gidansa ba rasa taimakon da zai maka ba, har aurarwa suna yi ga marayu su masu komai”

“Ai ban sani ba, ina dai jin ana fadarsa Tsohon Minister kudi ko? Ban san yana taimakom nan ba Wallahi, amman zan je yanzu Inshallah na gode sosai”

“Allah yasa a dace, ya bata lafiya anjima zan shigo na dubata Inshallah”

“Okay”

Ya dauke wayar daga kunnesa ya mike tsaye da sauri sai a lokacin ya tuna da be tambayi unguwar da yake ba. Hakan yasa ya sake kiran number Nura.

“Baka fada min sunan unguwar ba?”

“Shimkafi Road, kana shiga unguwar kace gidan Alhaji Mu'azu Shimkafi kake nema, za a nuna maka”

“Okay”

Ya saka wayar aljihu be ma koma cikin gidan ba ya nufi titi, da kafa ya taka tun daga gadar gaba har unguwar Shimkafi road, akwai tazara amman a haka yai ta cin kasa saboda babu ko naira aljihunsa.
Kamin ya karasa shiga cikin Quarters din wayarsa tai ringing, yana ciro wayar ya duba, a take gabansa ya fadi ganin number Malam Musa Dillali, hakan nan dai ya daure ya dauka.

“Hello”

“Hello Faruku haka ake daga karbar number sai ka ba matarka ta ciwa mutun mutunci?”

Tsaya yai daga tafiyar da yake fuskarsa da mamaki.

“Wane mutum kuma?”

A nan Malam Musa ya fada masa yadda sukai da Baturiya dazun sannan ya dora da abun da mai gidan ya fada masa.

“Wata kila kiransa tai ta ci masa mutunci, yanzu ya kira ni yana ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment