Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata.
Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers please, idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
https://www.wattpad.com/story/283871769?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_reading&wp_page=reading&wp_uname=KhadeejaCandy&wp_originator=ZCqcO2wXIv6pkkxIr3do4ng1%2BTHhzoVPTPFtpfDcb1ftHOVsldMflpG2lAwd5aYtrehJ12WEeerjWSVNDZunKAH9QpxhI0A%2BzJsYI6RrshbTOZsoLUXljeZDCPaDNtKr


*💔 BAKAR WASIKA 💔*


By Khadeeja Candy


Page -3️⃣

Shigowar Daddy ne yasa Momy ta cire farin gilashin idonta tana murmushi.

“Ranka ya dade an fito?”

Kusa da Amal ya zauna yana murmushi.

“Allah ya yarda”

Ya fada yana karewa katon falon kallo ganin Momy ce kawai sai Khadija da kuma Kabir, abun da ba kasafai yake gani ba, ya saba every weekend yana zuwa falon Momy ya zauna tare da ita da kuma yaransa, kowa ya fadi bukatarsa ayi hira a bawa juna shawara, ayi nishadi. Sometimes kuma shi zai kira su a bangarensa a tare a can.

“Daddy barka da wuni”

“Yauwa, Son”

Ya amsawa yana yi ma kowa kallon tsanaki, ciki har da yar autarsa Amal da ta wani hade rai.

“Hajiya ya ga falon ku kadai? Ina sauran yarana suke?”

Momy ta kalli Kabir dake kallonta sannan ta kalli Amal kamin tace komai Kabir ya tari numfashinta.

“Daddy yaranka biyu fushi suke da juna, kasan Angry Birds ne”

Daddy ya kalli Momy.

“Since when?”

Kabir zai sake magana Daddy ya dakatar da shi ta hanyar daga masa hannu, wanda hakan ke nuna kai tsaye Momy yake son ta amsa masa tambayarsa. Momy ta sauke ajiyar zuciya.

“Ni ma dazun nan na sani...”

A tsanake ta labarta masa abun da ya faru ciki har da fadan da tai ma Leila.

“Amman baki fada min ba? Taya zaki bar Mu'az ya fita ba tare da yayi breakfast ba? And baki dama ki san a wane hali yake ba?”

Momy ta lumshe ido ta bude tana murmushi.

“Wani lokacin kana maida Talba kamar wani karamin yaro, ya san yadda zai kula da kansa Alhaji”

“Ko da Mu'az zai shekara dari matukar ina raye to shi yaro ne a gurina, a shirya mana abincin rana tare”

“An gama ranka ya dade”

Ya mike tsaye sai Amal ta kalleshi.

“Daddy ni ma fa kaga ina fushin nan amman baka ce komai ba”

Sai a lokacin Daddy ya tuna da tana gefensa sai ya kalleta yana murmushi.

“Amal sorry wata taba ki?”

Ta nuna Kabir sai Kabir yai saurin daga hannayensa sama ya mike tsaye.

“Na ma bar muku falon”

Kamin Daddy yace komai ya nufi kofar fita daga falon da saurinsa yana murmushi.

“Mu yi masa uzuri amman yau kawai next idan ya sake tsokanarki zamu raba gari da shi”

Daddy ya fada yana kallon kyakkyawar yarsa. Sai ta sakar masa murmushi.

“Toh Daddy”

“Good”

Cewar Daddy yana ciro wayarsa ya kira Talba, ringing daya yai picking kamar daman can kiran yake jira.

“Hello Daddy”

“Mu'az kana Ina?”

Ya kalli katon office din da yake ciki kamar mai son tantance inda yake.

“Office Daddy”

“Me kake a office? Yau Weekend?”

“I don't know...Getting some fresh air”

“Baka fada min kana da damuwa ba, mu da kai ba abokai ba ne? Ba ma boyewa juna abu?”

Wani irin kasaitaccen murmushi ne ya bayyana a fuskarsa, ya mike tsaye daga inda yake zaune ya nufi windows.

“Daddy ba irin wannan ba you know dan crisis ne kadan”

Daddy ya tabe baki yana juya fuska kamar  Talba na gabansa.

“Uhm.. Ka dawo gida yanzu zamu yi lunch tare”

“Okay Daddy Allah kara maka lafiya, i love you”

Daddy yayi murmushi ba tare da yace komai ba ya sauke wayar, sannan ya nufi wata kofa a dayan bangaren falon wanda zata sadashi da bangarensa.

“Ita Leila ba ya bace kenan? Da ba zaka kirata ka tambayi inda take ba?”

Daf da zai wuce Momy ta yi wannan maganar sai ya juyo ya kalleta, sannan ya dauke kai ya bude kofar ya fice.
Sai da ya rufe kofar sannan Momy ta tabe baki ta kai hannunta ta dauki wayarta ta kira Leila, sai da wayar ta kusa yankewa sannan Leila ta daga.

“Leila kina ina?”

“Gidansu Madina”

Ta amsa murya can ciki.

“Ki dawo da wuri, and make sure kin ci abinci”

“To Momy”

Momy ta sauke wayar sannan ta mike tsaye ta nufi kitchen.

Misalin 2:30pm Talba ya daka motarsa harabar Daddy, ya fito ya nufi bangarensa kai tsaye hannayensa duka biyu zube a alhaji, tafiya yake kamar wanda baya son shiga bangaren, haka yake idan yana fushi be cika son ya rabi mutane ba ko kuma mutane su rabe shi, a tunaninsa tare da kowa zasu ci abinci, domin Daddy ya saba zuwa bangaren Momy ya zauna a ci abinci rana tare ko na dare wani lokacin har da na safe, sai dai yana yin haka ne kawai ranar kun Assabar da Lahadi. Domin ranar weekend ba ya fita ko'ina sai idan fitar mai dalili ce kamar daurin aure ko wani abun, wannan al'adar ba shi kadai ba har yaransa sun saba da ita, every weekend zaka samu kowa a gida sai mai dalilin fita yake fita.
Ya samu kusan dakika 40 zuwa 50 sannan ya danna door bell din kofar falon Daddy, babu bata lokaci Amal ta bude masa kofar.

“Ya Talba”

“Lil Sis... Waye da waye a ciki?”

“Just me and Daddy”

Ya sakar mata murmushi sannan ta shiga cikin falon, tun da ya hango dinning din babu komai a kai ya tabbatar daga shi sai Daddy za su ci abincin. Kai tsaye ya wuce karamin Falon Daddy inda ya saba zama. Yana shiga ya samu Daddy zaune saman kujera yana amsa waya, sai ya zauna a inda aka jera manyan kuloli ya dauki plate biyu ya zubawa Daddy shimkafa, ya zubawa kansa a dayan plate din sannan ya bude miyar dake ta kamshin naman kaji ya zuba ma kansa kadan domin ba ya son miya tai yawa a abinci ya zubawa Daddy ta jera kofuna biyu ta zuba musu lemu ya hada komai sannan ya dauki na Daddy ya dora masa a dan karamin center table dake gefen kujera da Daddy yake kai. Sannan ya koma ya dauko na shi ya dawo kusa da Daddy ya zauna a kasa, ya soma cin abinsa yana kallon katuwar plasma dake karamin falon, Bayan Daddy ya gama wayarsa ya kalli Talba.

“Na lura har yanzu baka san ka girma ba Mu'az, ya kamata ka koyi hakuri da iya danne fushi, idan ina kiranka na damu da inda kake, wata rana bana nan, domin akwai rayuwa akwai mutuwa, na san kana kokarin ganin ka kawarda damuwa a zuciyar wasu musamman yan'uwanka, amman kai baka san yadda zaka yi ka cire kanka a damuwa ba, sai dai ka karawa kanka”

Talba ya dakatar da cin abinci da yake yana sauraren Daddy ba tare da ya kalleshi ba.

“Ka daina fushi da abinci idan ranka ya bace, And su mata ba a fushi da su, lallabasu ake, idan ka san wahalar da na sha kamin ya auri Amina sai ka ji ka tsani matar nan, amman haka na daure dan marayan Allah da ni har Allah ya ba ni ita”

Talba ya kalli Daddy yana murmushi mai sauki.

“Haba Daddy”

Daddy ya kalleshi yana dariya.

“I'm telling you my friend”

Daddy ya kai hannunss ya fara cin abinci.

“So haka zaka yi hakuri kai ta lallabata, mata soyayya suke so da kulawa, no matter how rich they are, anya ma kana kiranta da safe ka ji ya ta tashi? Like hello Baby how was your night?”

Talba ya saka dariya sosai har yana kwantawa jikin kujerar dake bayansa. Daddy ma Murmushi yai.

“Yes... Gida daya muke da Hajiya kuma a guri daya muke kwana amman kana gani kullum sai na gaishe, ni ban san abun da yake damun ku yaran yanzu ba, mu a da kunya da rashin wayewar addini ya saka iyayenmu da mu kanmu ba su yi wasu abubuwan na more rayuwar aure ba, amman ku a yanzu ga ilmin addini da na zamani a arha ga wayewa amman kuke ta zaman matsalar zamantakewar aure, ban san miye matsalar matasan yanzu ba”

“So that's mean nine mai laifi kenan?”

“Kai ne mana, taya zaka samu mace kai tsaye da irin wannan maganar, bana jin yadda kake zaunawa kai hira da ni kana yi da ita ma, kawai kai gaka boss, gaskiya you're not romantic at all”

Daddy ya karasa yana wani yatsina fuska, wannan karon dariya sosai Talba yai har muryarsa tana fita kamar ba shi ba, dariyarsa ce ta saka Daddy murmushi mai sauti.

“Trust idan baka canja ba, za a iya kasa ka”

Ya daga kafadunsa alamar be damu ba.

“Then ai zan samu wata da gudu ma”

“Hakan na nufin ba wani son Leila kake ba, because idan kana son ta you won't said that”

Ya dan yi shiru kamar mai nazari.

“No i love her Daddy kawai dai ina sonta, but i won't tolerate nonsense”

Daddy yayi Murmushi yana dafa kafardarsa.

“Idan so ya zurfafa a zuciyarka, baka san lokacin da za ayi maka nonsense ba kuma ka dauka, a lokacin zaka zama wani stupid, fool, za a fada maka baka ga tana maka kaza ba, kace ka ji amman kana sonta ba zaka taba ganin laifin abun da take maka ba, mark my words”

Talba yayi murmushi irin murmushin nan dake nuna ban yarda ba, ranar ma ba zata zo ba.

“Yanzu ka gama cin abinci kaje ka samu Leila duk inda take ka dauko ta ka dawo da ita gida, kuma ka bata hakuri”

“No no no Daddy kasan ni bana ba wanda yake kasa da ni hakuri”

“Ba sai kace mata sorry abun da nai ban kyauta ba, no ka mata abun da zata ji farinciki sai ta manta da komai simple”

Ya dan yi jimm yana jin kamar an dora masa katon aiki.

‘Maybe i can try’

Ya fada a ransa a fili kuma sai ya amsawa Daddy da.

“Okay Daddy, for the sake of you”

Daddy yayi murmushi yana jinjina lamarin dansa.

FARUQ POV.

A gidan Mahaifiyarsa yai wanka sannan ya fito ya nufi gurin abokinsa, dake unguwar. He got lucky yana gida, yana sallama masa ya fito, bayan sun gaisa Faruq ya gabatar masa da abunda ke tafe da shi.

“Shamsu, na zo neman wata alfarma ne a gurinka”

“Allah yasa zan iya Faruq”

Faruq ya busar da iskar bakinsa.

“Wallahi ina cikin matsaloli ba ma daya ba, kasan matsalar kasar nan, mutum zai yi karatu amman aiki shiru, ga dan shagon da na kama sabuwar unguwa ce ba mutane sosai”

“Wallahi kasar ce har ka rasa yadda zaka misalta ta, abubuwan sai a hankali, idan baka yi karatu ba abun ya dame ka idan kuma ka yi aikin ya gagara”

“Shine nake son na fara koyon irin sana'arku, duk da ba iyawa nai ba amman dai idan nayi tare zan iya da yarda Allah”

Shamsu ya masa wani kallo na mamaki, a tunaninsa zai ranci kudi ne a hannunsa, sai ya ji yana masa maganar sana'arsu, ba Shamsu kadai ba kusan duk wanda ya ji mutum mai degree zai yi sana'ar gini zai yi mamaki, domin muna a zamanin da masu degree da kuma mutane suke ganin ba ko wane irin aiki ne ya dace da su ba, wani abun ana ganinsa kamar kaskanci ne, ace kana da degree kuma kai yi shi.

“Faruq zaka iya sana'ar gini kuwa? Kai da kai karatu? Kuma jikinka be saba da aikin wahala ba”

“Shamsu kenan, wanda ya tashi a area kamar wannan kuma dan talaka zai ce be saba da aikin wahala ba? Ya kake magana kamar ba san gidan da na fito ba?”

“To abun ne da mamaki Faruq naga kai ka yi karatu ka ni ban yi karatun ba”

“Ka aje komai a gefe ka duba bukatata idan zai yiyu”

“Inshallahu, sai dai ka san aikin mu tasowa yake ba wai kullum ba ne sai idan ta samu, inshallahu da mun samu zan kiraka a waya tun da ina da number ka”

“To na gode sosai sai na jika”

Ya mika masa hannu sukai musabaha, Shamsu ya koma cikin gidansa cike da mamaki, Faruq kuma ya nufi titi cike da damuwa.

FEE'AH POV.

“Gaskiya kina da kyau sosai”

“Thanks”

Shine reply din da tai ma mutumen da facebook bayan ta tura masa hotunanta masu kyau, kamar yadda ya bukata.

“A ina kike da zama a Gusau?”

Wannan karon tashi tai zaune tana tunanin irin karyar da zata masa, domin bata fada masa cewar tana da aure ba, duk kuwa da kasancewar bata dora hotonta a profile picture ba, sai hoton sunan Allah data saka as her profile picture dinta.

“Gida dari”

Ta bashi amsa.

“Na san gurin idan na shigo zamfara inshallahu zan neme ki mu gaisa”

“To Allah ya nuna mana”

Ta bashi amsa tana murmushi, kamin ta sake shiga profile dinsa ta duba komai nasa, ciki har da gurin da yake aiki da kuma hotunansa, kana ganinsa ka ga wani hamshakin mai kudi mai connection da yan siyasa, domin yadda ake masa fadanci a profile ma ya isa ya sanar da hakan. Murmushi ta sake yi sannan ta dawo inbox din ta duba tambayar da yai mata ta biyu.

“Are you on whatsapp?”

“Yeah”

Ta bashi amsa da sauri tare da rubuta masa number wayarta ta tura masa.

“Okay Thank You so much Baturiya”

Ta sake fadada fuskarta da murmushi tana jin sunan har cikin ranta. Sannan ta fita facebook din ta shiga whatsapp, few massage ta samu ciki har da reply din da MD Saleh yai mata, shi ta fara budewa da sauri jikinta har rawa yake kamin ta gama karantawa.

“Subhanallahi, Allah ya wadata, turo account number dinki”

Mikewa tai tsaye ta daka wani uban tsalle ta dire tsabar murna da jindadi sannan ta tura masa account din tana masa godiya.

“Alhamdulillah”

Ta furta sannan ta shiga group chat dinsu na makaranta, ta fita ta leka na matan aure ta fita ta shiga na novels nan ma bata dade ba ta fita ta bude chat din Ramlee.

“Kawata kin yi ciniki, wani ya ga Hotonki a wayata ya matsa na nemo masa ke”

Tana gama karanta sakon kawarta Ramlee ta zaro ido tare da sakin baki a lokaci daya, domin ta san sana'ar kawarta, tana da connection da manyan masu kudi tana hada su da mata kyakkyawa kuma masu siga kamar yadda ita ma take hulda da su, sai dai duk iskanci Baturiya bata taba aikata alfasha ba, za dai hadu da mutum har su gaisa ko kuma ta yi masa nata wayon ta waya ta samu yan canji, amman bata san tai mu'alama da maza ba, bayan Faruq babu wanda ya taba saninta a ya mace.

“Gaskiya aa Ramlee ni dai ina jin tsoro ba zan iya ba, amman idan kin san irin wanda zan yi ma wayo ne na ci kudinsa ba sai mun hadu ba, ba matsala”

Ta mayar mata da amsa duk da kasancewar Ramlee tana Offline a lokacin, sannan ta kashe datan ta aje wayar ta mike tsaye ta fito waje.

“Sultan zo nan yau zamu ci kaza”

Ta fada tana zaunawa jikin kofar falon tana mikawa danta hannu fuskarta cike da murmushi kamar yadda zuciyarta take fal da farinciki saboda kudin da za a turo mata, Sultan din ya rugo da gudunsa yana murna.

“Abba zai siyo mana ne”

Ta shiga kabe masa riga tana fadin.

“Ba nace ka daina cewa Abba ba? Ka rika cewa Daddy, yayan talakawa ne suke cewa Baba ko Abba, yaran masu kudi kuma su ce Daddy ka ji?”

“To Daddy ne zai siyo mana?”

“Aa adashen zan kwasa yau sai na siyo mana, amman karka fadawa Daddy ka kaji? Har da lemun kwalba zan siyo mana”

Sultan din ya shiga murna yana jindadi yau za su ci kaji, rabon da su ci nama har ya manta.

AMINATU POV.

A bakin kofar shiga gidansu ta hadu da Sanusi tsaye yana latsar karamar wayarsa.

“Ya Sanusi”

Ya kalleta sai kuma yai dariya.

“Igee ai sai ki fada mana cewar kin fara fita zance, mu shirya yi miki aure”

Ta cinno baki gaba.

“Ni dai dan Allah ka daina, Allah yasa ba ka fadawa Inna ba ko Baba”

“Ban fada ba, amman dai zan fada masa, Baba ma baya nan”

“Ina yaje?”

“Gwaggo ta Makka aka aiko bata da lafiya sosai, shi ne suka je tare da Junaidu a babur”

“Yanzu?”

“No tun dazun”

“Allah ya bata lafiya shi kuma ya dawo da ita lafiya”

“Inna tace naje na dubo ki, idan kin shiga ki ce ni na zo da ke”

“Wallahi ba zan fada ba”

Ta fada tana nufar cikin gidan.

“Ni kuma zan fada mata cewar kin yi saurayi”

“To na bari”

Ta yi saurin fada har tana dawowa baya, sai ya saka dariya ya biyo bayan kanwarsa suka shiga cikin gidan tare. Kamar Kullum inna na zaune tsakar gidan tana jiran dawowarta, domin bata bachi sai ta saka yarta a ido.

“Oyoyo Auta yar albarka, an siyar ko?”

Aminatu ta aje kwallon tuwon da bokitin miyar da plates din roba a gaban ina tana sauke gajiya.

“Eh Inna wai Baba ya tafi gurin Gwaggo?”

“Eh an aiko bata da lafiya, aka ce mai rabon ganawa da ita ya zo”

“Allah ya bata lafiya”

Ta fada cike da damuwa, sannan ta ciro kudin cinikin ta mikawa Inna, sai da Inna ta kirga kudi ta ga sun cika sannan ta cire wadanda ta saba bata tana sakawa a asusu ta mika mata.

“Ga na ki”

“Na gode”

Ta fada bayan ta karba tana kallon Sanusi zuciyarta sai raya mata take zai fadawa Inna maganar, sai har sukai yar hira da zasu yi suka gama bata ci ya dauko zance ba, hakan yasa ta ji dadi sosai. Bata bude wasikar da Maniru ya bata, da fitilar da take zuwa talla ta haska wasikar da ya rubuto mata da hausar ajami, tana karantawa sai murmushi take tana jindadin yadda ya jera mata kalaman soyayya da kwantar da hankali.

Bayan ta gama karantawa ta rumgume wasikar a kirjinta, can kuma ta tashi ta saka a cikin littafanta na Islamiya kamar yadda ta saba, sannan ta gyara gurin kwanciyarta ta kwanta. Inna kam bata kwanta ba sai da ta gama komai ta kintsa komai kamar yadda ta saba sannan ta kwanta tare da rage fitilar kwai dake dakin, hasken ya rago sai dai bata kashe gaba daya ba saboda Aminatu na tsoron duhu sosai, bata bachi babu fitila a kusa da ita.
Misalin 12am gidan yayi tsit domin kowa ya nemi gurin kwanciya ciki har da yan awaki da tumakin da ake kiwo, can cikin bachi Inna ta soma jiyo hayaniya, tare da karar babura hakan yasa ta ta tashi zaune tana sauraren jikinta na bata ba lafiya ba, domin kowa ya san matsalar kasar a yanzu, balle kuma su da suke kauye. Aminatu kam sharar bachinta kawai take bata ma san ana yi ba, jin ihu da kuma fadar Innalillahi a makota yasa Inna ta nufi inda Aminatu take ta shiga tashinta.

“Auta Auta”

Ta fada murya can kasa kasa, a hankali Aminatu ta bude ido ganin Inna yasa ta tashi zaune.

“Inna...”

“Shiiiii”

Inna ta mata alama da tai shiru. Wanda hakan yai daidai da banko kofar gidan ta kwano a shigo, ga wata uwar fitila mai shegen haske da suke ta hasken gidan da ita.

“Innalillahi Wa'inna illahirraji'un”

Inna ta furta gabanta na bugawa da mugun karfi, Aminatu ta mike tsaye da sauri kamar wanda ta rude, Inna ta shiga duba dakin tana jin kamar ace akwai wata hanya da zata bi ta fita, a rikice ta nufi gadonta.

“Shiga nan Auta shiga shiga”

Da sauri Aminatu ta nufi karkashin gadon na karfe ta shige, zuciyarta na wani irin zillo kamar zata fito, Inna ta nufi kofa domin duba sauran yayanta sai dai kamin ta isa kofar suka shuri kofar da mugun karfi ta cire suka shigo cikin dakin kamar an aikosu. Baya baya Inna tai tana fadin.

“Innalillahi Wa'inna illahirraji'u”

“Rufe mana baki dan ubanki”

Yanayin yadda yai maganar da karayar halshe kadai ya isa ya sanar da cewar gayu ne suka hauro garin a yau, wato bandits abun da ba a taba ba, domin duk wani hargitsi da ake fama da shi sai dai su ji a makotan kauyukan ko kuma a hanya abun ya rutsa da yan garin, amman ba a taba shigowa cikin garin ba. Ba Inna kadai ba har Aminatu dake karkashin gado sai da ta saka hannayenta ta rufe bakinta. Ta ko'ina jikin Inna rawa yake, ganin manyan makaman da ke hannunsu.

“Ina mijikin yake?”

Kasa magana tai bakinta sai rawa yake kamar jikinta ga wani gumi dake karyo mata.

“Wato ke ce uwar yaran ga yan iska ko?”

Nan ma Inna kasa cewa komai tai sai ambaton Allah take a zuciyarta, hannayenta duka biyu rike da bakinta.

“Innalillahi”

Inna ta jiyo muryar yayanta a tsakar gidan, wani irin abu ne ya ziyarci zuciyarta sai ta ji kamar ace akwai abun da zata iya yi ta ceci yaranta.
Dun dun dun ta ji tashin bindiga kamin ta tantance komai ta ji muryar Sanusi yana kuka.

“Wayyo Allah na, la'ilaha illahu, Innalillahi”

A lokacin ne hawaye ya cika idonta, irin hawayen da kowace uwa take yi idan ta kasa taimakon yayanta.

“Wayyo”

Ta jiyo ihun matar Amadu, bata san da inda kuzari ya zo mata ba har ta iya tambayarsu kamar ta rikice.

“Me muka muku?”

“Tambaya ma kike? Ba kun aje yan sakai a gidanku ba, wai masu yaya ko? To yau sai mun kashe su sai mun muku wulakanci”

Inna ta hade hannayenta biyu tana kuka tana rokonsu.

“Ku dubu girman Allah ku yi hakuri, ku kashe ni kar ku kashe yarana dan Allah...”

Bata gama rokon ba, wani ya karaso kusa da ita ta fisgi rigar jikinta.

“Cire wannan rigar ai har ke da kike uwarsu ba zamu bari ba”

Sai a lokacin Inna ta kara firgicewa, ta fara bin fuskokinsu da kallo tana ganin komai kamar a mafarki.

“Cire cire”

Sai ta rika jin kamar ba hausa suke mata ba, gaba daya ta rasa gane abun da suke nufi, bata fahimci manufarsu ba har sai da suka barge rigar dake jikinta suka kama zanen shi na suka fisge suka jefar da shi can gefe, suka mata tsirara a gabansu. Aminatu dake karkashin gado ta yi saurin kara rufe bakinta wasu irin zafafa hawaye na sauko mata, saurin rumtse ido rai hango mahaifiyarta tsirara a kwance yaron da be wuce sa'ar danta na biyar ba ya fara keta mata haddi!!
Ba mutum daya yai ba, ba biyu ba, ba uku ba, ba hudu ba, haka suka jera su goma sha daya suka yi mata yadda suke so, sannan suka fita suka barta kwance kamar tsumma. Abun ka da uwa suna fita ta yi karfin halin rarafawa ta isa inda zanenta yake da idanuwan da take jin kamar kukanta ya kare a yau. Ta dauki zanen da hannunta amman yadda zata sarrafashi ta daura ta suturta jikinta ne ta manta sakamon jin ihun Sanusi, cikin rashin kuzari zuci da na jiki ta isa jikin kofar tana kallon yadda yan bidigar majiya karfi, suka danne Rilwanu a kasa, dayansu ya kunna babur dinsa ya hau ta kan wuyansa ya tsaya.

“La'ilaha Illahu”

Inna ta fada da wata irin muryar da bata taba sanin tana da ita ba, tana mika musu hannu. Ba su kulata balle su fasa abun da suke, ba su saukar da babur din a wuyansa ba sai da suka tabbatar ransa ya rabu da gangar jikinsa, daman haka suke ma irin su Rilwanu masu aikin sa-kai domin kare rayuwarsu da kuma ta al'ummarsu, idan suka halbeka da bingida suka ga bata tashi ba, sai su gwada adda, idan ita ma ba tai ba sai su saka dutse ko babur. Bayan sun kashe Rilwanu suka fashe rumbun hantsen dake gidan suka saka Iro a ciki suka kunna masa wuta, tare da hatsin. Wani irin ihu yake yana neman ceto amman babu wanda zai iya kawo masa dauki.

“Kaico Kaico kaico”

Inna ta fada tana kallon yadda danta ke ci da wuta, ga kuma wani a kwance, wani irin shiga da fita numfashinta ya rika yi da karfi, tana jin wani abu na mata yawo a ciki, gaba daya sai ta nemi dan sauran kuzarin nata ta rasa, a bakin kofar ta fadi kwance yawu da majina suna zubo mata a lokaci daya, cikin karfin hali ta dan dago kanta ta juyo ta kalli Inna Aminatu take boye, sannan ta juya tana kallon yadda suka dauko katon dutse suka daga sama suka saki a akan Amadu da yake da wasu barayin suka danne a kasa ko motsi baya iya yi, kamar yadda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment