Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

masifa wai wata ta kira shi Baturiya ta zage shi, ya baku daga yau zuwa gobe ku tashi ku bar masa gidansa”

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, Wallahi Malam ban san Matata zata yi haka ba, kuma Wallahi ban ce zan karbi number sa ba”

“To yanzu dai sai ku san abun ba, Baturiya ko balaraba ta ja maka”

Malam Musa na fadin haka ya kashe wayar, Faruq ya dafe kansa.

“Na shiga uku wai me ke damun Rafi'a ne? Ta sake janyo mana wata fitinar kuma? Ina ruwanta da mai gida?”

Wani irin kololon bakinciki ne ya taso masa, sai ya ji kamar na runtse ido ya bude a gansa a kabari ya huta, yana fama da wasu matsalolin yanzu kuma ta ballo masa wani.

“Wallahi yau sai na miki mugun duka, Rafi'a sai kin dawo hayyacinki in ma baki da hankali sai kin yi shi”

Ya fada rai a bace, duk abun da take masa na bacin rai bata taba mata masa rai irin wannan ba, domin be san inda zai je ba idan ya bar gidan haka nan ya cigaba da tafiya ransa a bace. Da tambaya ya aka nuna masa kofar gidan Alhaji Mu'azu Shimkafi, Gate din gidan kadai a abun kallo ne, balle kuma farar ginar da aka kawata da farin fenti ga shuke shuke itatuwa da fulayoyi, idan ka daga kanka kuma sai ka hango gidan sama daga can cikin gidan an kawata ko'ina da gilasai komai a tsare kamar ba za a mutu ba. Faruq ya girgiza kai.

“Allah man yasha'u, ka baiwa bawa ba dan kana son shi ba, kuma ka hana Bawa ba dan baka son shi ba, Allah ka bamu na mu arzikin na halal, yanzu nan gidan mutum daya ne”

Ya fa da yana mamakin tarin dukiyar dake gidan. Karasa yai bakin gate din yana kallon security cameras daka laka hagu da dama na gidan sannan ya kwankwansa kofar gate din. Ba dade wani police ya bude masa yana sanye da uniform dinsa.

“Malam Lafiya?”

Faruq ya mika masa hannu suka gaisa cikin mutumci.

“Dan Allaj ina son ganin mai gidan ne matsala ce da ni”

“To ganin mai gidan a yanzu ai, sai an jira domin be fito ba, idan zaka iya jira a nan wajen idan ya fito sai ka tare shi da matsalarka, duk dai baya son a ana mishi haka amman karka nuna masa na san da zuwan ka”

“Ba Matsala na gode sosai”

Faruq ya nemi wani gurin ya zauna a nan kusa da gate din, shi kuma police din ya koma cikin gidan ya maida gate din ya rufe. Be yi minti talatin da zama ba, aka sake bude gate din sai dai wannan karon gate din gaba daya aka bude ganin mota zata fito yasa yai saurin mikewa tsaye a zatonsa mai gidan ne sai ya nufi motar da sauri, ganin ya nufota yasa ta tsaya ta sauke gilashin motar tana kallonsa.

“Ya akai?”

“Daman na dauka mai gidan ne shi nake son gani”

“Saboda me kake son ganinsa?”

Ya tambaya tana kare masa kallon from head to toe.

“Taimako nake nema”

Hannu ta saka ta cire katon gilashin idonta.

“Okay idan ana neman taimako sai azo har kofar gidan mutum a takura masa? Baka san yadda zaka bi ta Foundation ba? Ba ma taimako a gida sai ta karkashin kungiya, kaje can ka samu kungiya karka sake zuwa nan, Talauci ba hauka ba ne”

“Haka ma Arziki ba hauka ba ne malama, karki nemi fada min maganar banza saboda na zo nema a gidanku, ni ba wulakantaccen ba ne”

“Really”

Ta bude motar ta fito tana masa wani banzan kallo.

“Dubi ka! Ka zo nema a gidanmu kuma kana cewa kai na wulakantacce ba ne? To waye kai? Kai kama isa ka zo nema a gidanmu kuma fada min maganar banza?”

“Maganar banza ana furtata ne a lokacin banza kuma ga mutanen banza irinki”

“Ni...”

Ta nuna kanta Faruq ya daga mata kai cikin bacin rai daman be gama wankewa daga na matarsa ba ita kuma tana neman kara masa wani, hannu ta daga zata mare shi sai ya rike hannun da mugun karfi ya jefar da shi.

“Kika kuskura kai hannunki a fuskata sai na illataki, dan ina neman taimakonku ba shi zai baku damar wulakanta ni ba”

Bata sake ce masa komai ba ta juya da sauri ta isa gurin gate din ta buga da karfi, daman Police din ya rufe gate din a lokacin daya bude mata ta fita, da sauri ya bude sai ta nuna masa Faruq.

“Ku rike mutumen can”

Da sauri ya fito shi da wasu Police din biyu suka nufi inda Faruq yake tsaye suka rike shi, ita kuma ta nufi cikin gidan da saurinta kamar zata tashi sama, Talba dake kokarin tashin motarsa yana kallonta ta danna door bell din kofar be kula ta ba ya ja motarsa zuwa gate ya hanna horn, dai dayan Police din ya dawo ya bude masa gate din ganin suna rike da Faruq ga kuma motar Leila dake bude a kunne yasa shi tsaya ya sauke gilashin motarsa.

“Lafiya?”

“Wallahi ba mu san abun da ya faru ba, Hajiya Leila ce tace a rike shi”

Talba ya kalli Faruq daga sama har kasa, be masa kama da yan ta'addaba, kuma ya san halin yar'uwarsa mafi akasari fadan da take da mutane ita ce bata da gaskiya. Hakan yasa shi tambayar Faruq dake kokarin fisge kansa daga rikon da Police din suke masa.

“Malam Lafiya?”

“Lafiya ce zata saka Police rike ni? Daman idan za ku taimaki mutum sai kun wulakanta shi”

Faruq ya fada cikin fusata, hakan yasa Talba ya bude motar ya fito ya nufo inda suke tsaye.

“Ku sake shi”

Ya fadawa Police din sai suka saki Faruq, Talba ya saka hannayensa aljihu yana kallon Faruq.

“Bari na fada maka wani abu, ba a min tsawa kuma ba a fada min bakar magana, amman na maka uzuri saboda na fahimci kana cikin bukatar taimako ne, and bana son na yi ma mutun wani abun ta dalilin taimako, da ace a hanya na hadu da kai da zan iya maka cin mutunci fiye da kima, now tell me miya faru”

Kalaman da Talba yai yasa Faruq sasautawa zuciyarsa domin ya fahimci ba fada Talba yake son yi da shi ba, idan ma sun yi fadan ba riba zai ci ba.
Cikin bacin rai Faruq ya fadawa Talba abun da ya faru, sai Talba ya girgiza kai ya lumshe ido ya bude, ba dan baya iya bawa kowa hakuri ba, da sai ya bawa Faruq, domin ya fahimci halin da
yake ciki.

“Ka manta da abun da tai maka yanzu fada min wani iri taimako kake so?”

“Mahaifiyata ce ba lafiya”

Faruq ya fada domin yana jin cewar shi ne kawai abun da zai iya fada a halin yanzu, kasancewar shi ya fi damunsa. Talba ya juya ya koma cikin motarsa ya bude ya shiga ciki ya zauna, wani karamin diary ya dauko yai rubutu akai, sannan ya bude wani guri a cikin motar ya dauko 100k ya fito ya nufo Faruq.

“Ga wannan Allah ya bata lafiya, and idan kana neman taimako a foundation din Mahaifina ka tuntubi wannan number, su za su tantance komai su sanar mana”

Ya mika masa number bayan ya bashi kudin. Faruq ya saka hannu biyu ya karba cikin jindadi.

“Na gode sosai Allah ya saka da alheri, ya kara sutura”

Uffan Talba be ce masa ba balle har ya amsa da Ameen, sai juyawa yai ya nufi motarsa, yana kokarin shiga yaji dayan police din na fadin.

“Hajiya tace a rike shi, ku rike shi”

Juyowa Talba yai ya kalli Police din, sai suka fasa rikon Faruq.

“Hajiya Babba ba Leila ba ita ta kira ni yanzu”

Da kai Talba yai ma Faruq alama daya wuce sannan ya shiga motarsa ya danna horn suka sake bude masa gate din yai ribas ya shiga cikin gidan. A harabar Entrance din ya faka motarsa sannan ya fito ya nufi kofar falon kamin ya karasa sabuwar mai aikin Momy ta bude kofar da sauri da alama fitowa za ta yi.

“Yauwa ranka ya dade Hajiya tace na kira ka”

Shiga yai cikin falon hannayensa zube a aljihu sai kamshi turare yake zubawa, tsaye ya samu Momy Leila na gefenta dayan mai aikin Momy Zulai tana tsaye nesa da su, domin wannan karon har masu aiki biyu Momy ta dauka. Yana kallonta ya san ranta a bace yake, can kuma ya kalli Leila da ke hawaye, kamin ya kalli Kabir dake zaune rike da waya yana kallonsa.

“Talba haka zamu zauna mutane suna ci mata mutunci kana daukar side dinsu”

“Ta fada miki Abun da tai masa?”

“I don't care, amman komai tai masa ai be kamata ya rike hannunta ba, har ya fada mata bakar magana alhalin shi yanzo nema a gidansu, har kuma ka bar shi ya tafi”

Talba be ce komai ba, har Mairo ta shigo tare da police din da Momy tasa ta kira daman shi da Talba ta ce ta kira. Yana shigowa Momy ta nuna shi da yatsa.

“Wannan ya zama na karshe da wani zai zo ya takura mana kofar gida, karka sake barin kowa ya shigo mana ba tare da saninmu ba, idan makamancin haka ya sake faruwa a bakin aikinka, ba wai a gidan nan kadai ba, no ka daina saka Police Uniform kenan har a bada mark my words”

“Ayi hakuri ranki ya dade Inshallah zan kiyaye”

Cewar police din sannan ya juya ya fita. Da ido Talba yai ma Mairo da Zulai alamar su fice daga falon sai suka fice da saurinsu.

“Wannan abun yayi yawa Momy, ya kike Leila ta zama? Ba fa Amal bace, taya Leila zata raini yara masu tarbiya idan tana wannan halayyar? Saboda wani ya zo nema daga abun da Allah ya wadata mu da shi sai ya zama abun wulakantawa? And ji yadda kike fadawa Police din nan magana kamar wanda yai wani babban laifi”

“To ya kake son na yi? Haka zamu yi ta zama Leila bata da yanci a gidan nan? Haka zaka rika mata idan kun yi aure ka bar ko wane kare da biri suna cin zarafinta? Shi ne jindadinka?”

Talba ya kalli Leila cikin yanayi na rashin jindadi.

“I wonder what kind of woman zan aura! Akwai karamci tarbiya a tare da ke, ba zan iya daukar wannan halin na ki ba kina bukatar ki canja rayuwa Leila...”

“Kai kake bukatar canja rayuwa ba ni ba...”

Ta fada mishi kai tsaye sannan ta nufi upstairs. Momy ta kara da nata.

“Kana fada min Leila bata da tarbiya ko? An maka dole ka aureta ne? Ko kuma kana son ci min fuska ne Saboda ba ni na haife ka ba?”

Talba ya kalleta da sauri, Kabir ma mikewa yai tsaye sai a lokacin ya saka bakinsa a maganar.

“No haba Momy... ”

Momy ta daga masa hannu.

“Na san abun da yake nufi, duk abun da kake kana yi ne saboda ba ni na haife ka, kuma na sani, daman tsintacciyar mage bata taba zama mage ba, amman karka manta ni na raine ka, ko da ka bude ido baka san mahaifiyarka ba ni ka sani, na raine kamar uwa, so weather you like it or not I'm still your mother, karka manta da wannan...!”

Tana kaiwa nan ta nufi upstairs ya bita da kallo kalamanta na ratsa kowane lungu da sako na zuciyarsa. Leila ma da bata karasa hayewa ba juyowa tai ta kalleshi cikin yanayin da ke nuna bata jidadin kalaman Momy ba, balle kuma Kabir da ya tsaya kamar hoto yana kallon dan'uwansa cikin yanayi na rashin jindadi.




<<<<<>>>>>

Na ce ba? Baturiya ko ba indiya ta taro mach da Faruq yau 🤔

Anya Leila zata ga Annabi kuwa? 😔

Momy ta kyauta a kalaman da tai ma Talba saboda Leila?

Wai ina Aminatunan mu ne?
13

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa

*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*



Juyawa Talba yai ya fice daga falon, sai Leila ta sauko da sauri zata bi bayansa, kamar wanda ta tuna wani abu sai kuma taja ta tsaya cikin yanayi n rashin jindad

“Yanzu ai kin jidadi ko?”

Kabir ya tambaya yana gyara shirt din jikinsa. Sai ta kalleshi cikin yanayin damuwa domin har ga Allah bata son Talba ya shiga damuwa duk kuwa da irin son da take ya canja bata son ace saboda ita Momy ta yi masa Wani abun bacin rai domin ba su saba haka.

“Wane irin dadi kuma? Kana jin kalaman da Momy ta fada masa fa”

“Eh ai ke kika ja, ke dai burinki wulakanta mutane”

Yana kaiwa nan shi ma ya nufi kofar fita falon cikin bacin rai, duk irin rashin jituwar da suke samu da Talba baya son wani abun bacin rai ko damuwa ta same shi, kamar yadda Talba ma baya son ganin bacin ran Kabir sai dai dukansu sun san cewa ba a komai na rayuwa suke shan inuwa daya ba, musamman ma Talba da yafi kowa girman kai a gidan.
Juyawa tai ta hau stairs din ta nufi dakin Momy, ko knocking bata tsaya yi ba ta tura kofar ta shiga kamar zata fasa kuka.

“Haba Momy wannan abun har ya kai ki fadawa Talba irin wannan maganar ne?”

Momy dake zaune gaban madubi tana kokarin cire awarwaron hannunta ta juyo ta kalleta da mamaki.

“Ba ki kalmar da yake jifata da ita ba?”

“Da ni yake ba da ke ba”

“No cewa yai baki da tarbiya, kai tsaye na fahimci inda kalamansa suka dosa, tun ba yau ba ai na lura da yadda ya canja kamar mai son yai kishi da ni”

“Haba Momy Talba ne zai yi kishi da ke?”

“Eh mana, bakisan wasu yayan suna tsanar iyayen da ba su haife su, Idan ba haka ba ai ba zai min kalaman banza ba, ko ba komai ni surukarsa ce right”

“Momy yanzu zai ji babu dadi Wallahi ransa zai bace”

“Ran nasa ya dade be bace ba, wannan wane irin so ne kike ma Talba wai? Shi fa baya son ki kamar yadda ke kike sonsa, kuma naga ke ma ai kina bata masa ran”

“Eh amman Momy wannan ai matsalar mu ce ta dabam ba wai akan ba”

“I don't care, idan ke baki san zafin abun da ya fada ba ni na sani”

Mikewa tai tsaye cikin yanayin damuwa ta fice daga dakin tana ta sake sake, ko ta kira ta bashi hakuri akan abun da Momy tai ko kuma ta kyale shi, sai dai idan ta tuna cewar saboda ita komai ya faru sai ta ji wani iri.
Dakinta ta shiga ta dauki wayarta ta kira Madina ta labarta mata abun da ya faru, daman komai na duniyar ba zata iya boyewa Madina ba, no matter how Momy ta kwatseta akan abu sai ta fadawa Madina.

“Amman Leila baki taba bata min rai irin yau ba, wai miyasa kike barin zuciyarki tana aikata abun da Talba baya so? Ke baki san yadda zaki faranta masa rai ba? Haba Leila ni kam da baki labarta min wannan abun ba da ban shiga damuwa ba Mtchssssss ”

Ta yanayin yadda Madina take mata responding kadai ya isa ya karantar da ita cewar Madina ta fita shiga bacin rai ma.

“Ni ma fa ban jidadi ba, that's why na kira ki ko zan samu mafita”

“Mafitar me? Ni Wallahi kin bata min rai, i don't think i can eat today, kin bata ran bawan Allah, na sha fada miki haka rayuwarsa take ki bishi a haka mana sai ku samu zaman lafiya amman kin gagara daukar shawarata”

“Look Madina na yarda a nan ina da laifi daya janyo aka fada masa magana marar dadi, amman maganar Allah ban ga laifi a abun da na yi ba, Talba yana shigar min hanci da yawa fa”

“Yanzu dai na ji, idan kina son mu shirya da ke kije ki bashi hakuri”

“Na bashi hakuri fa? Gaskiya ba zan iya ba”

“To miye a ciki, ke fa kika ja komai, kuma ba akan abun da yai miki fada zaki bada hakuri ba, akan abun da Momy tai masa”

“Zan ga idan zai yiyu”

“Please do this for me, tsakani da Allah ko kadan bana son na ji ran Talba ya bace, Mutumen yana son ki Leila kin kasa ganewa ne, kina raina yadda rayuwarsa mata da yawa suna can suna sonsa a haka, ki bi a hankali”

“Na ji”

Ta fada tana juya ido, bata tsaya jiran abun da kawarta zata sake fada ba ta yanke wayar ta wurgar saman gadonta, sannan ta fadi kwance.


TALBA POV.

A lokacin daya fita daga falon cikin motarsa ya nufa ya zauna, ba karamin taba shi kalaman Momy sukai ba, duk yadda ya so ya ga laifin kansa kan abun da yai ma Leila sai ya kasa, zuciyarsa nata raya masa a daidai yake, hannu ya kai ya dauki wayarsa ya kira Ali.

“Hello”

“Kana ina?”

“Office ya akai?”

Iskar dake bakinsa ya busar ya kashe wayar ya aje gefensa sannan yai ma motar key yai reverse ya danna horn, tun kamin ya isa gate suka bude masa sai da ya fito ya ga motar Leila dake waje har lokacin sai dai wannan karon an kullenta amman motar tana kunne, horn ya danna har sau biyu wanda hakan ya saka Bello Police lekowa ya nufo motarsa da sauri, sai ya sauke gilashin motar ya nuna masa motar Leila, Bello na ganin ya nuna motar ya san abun da yake nufi na sai ya masa magana ba. Sai ya nufi motar Talba kuma ya hau titi, driving yake kamar wanda be san inda zai je ba, kadan kadan yake lafiya har ya isa asibitin FMC a inda ya saba fakin ya faka motarsa ya fito yana jin kamar ya juya ya tafi gurin aikinsa sai dai ya san he need someone to talk to, a duk lokacin daya shiga wata damuwa komai kankantarta Ali yake fara fuskanta ya fada masa damuwarsa duk kuwa da kasancewar wani lokacin za su rabu a fada ce ne. Kai tsaye office dinsa ya nufa and he got lucky Ali yana ciki sai dai office din ba shi kadai ba ne tebur biyu ne na dayan abokin aikinsa. Ko kallon gefen da abokin aikin na Ali yake be yi ba ya nufi teburin Ali ya zauna a kujerar baki. Ali na kallon abokinsa ya fahimci akwai damuwa.

“Leila ce ko?”

Talba ya dago ya kalleshi, sai kuma ya juya ya kalli teburin abokin aikinsa sai a lokacin ya lura da be shigo ba

“No”

Ya amsa masa cikin yanayin damuwa.

“Na san dai abu ne mai wahala yadda Daddy yake ji da kai abu ne mai wahala ya bata maka rai, sai dai idan wata damuwa ce ta dame shi a san zata iya shafarka”

Ajiyar zuciya Talba ya sauke, sannan ya labatawa Ali abun da ya faru. Ali ya kwanta jikin kujerarsa yana kallon Talba duk kuwa ya san kallo na daga cikin abun da abonkinsa ya tsana.

“Momy dai ta fusata ne, kuma kai ke da laifi”

“Amman Ali ban yi dan taji haushi ba, ba ina nufin bata bawa Leila tarbiya ba, kawai bata fahimci ni ba”

Yana fadar hakan ya mike tsaye ya nufi windows din office din.

“Kuma na ji babu dadi, na san ba ita ta haife ni ba, amman ban taba mata wani kallo na dabam na bayan uwa, ita ta raine ni a hannunta na tashi na girma”

“Kai ka ji zafin abun da ta fada maka balle ita? Yanzu dai ka manta da komai ka dauka cewar kuskure ne irin wanda kowa yake yi”

“And seriously ba zan iya zama da Leila da wannan halin ba”

“Kai da za a bibiya zata ce ba zata iya zama da kai saboda halinka ba, Talba dan adam duk tara ne be cika goma ba kowa ka ganin yana da inda be cika ba, abun da zai fi kawai ka dauke idonka daga gareta, musamman a yanzu da ka fahimci idan ka taba ta ran Momy yana baci, ka bita a yadda take sai a samu zaman lafiya”

“And... ”

“And ka koyi bada hakuri Talba, ba zaka ragu ba, mata rarrashi suke so, yanzu duk wannan abun daya faru idan ka koma gida ka yi kamar komai be faru ba, ka samu Leila ka lallabata ka bata hakuri”

“Ba a hallici wannan macen da Talba zai bawa hakuri ba, ba ayi mace da zan yi ma yar murya ina lallabata akan tai hakuri ba, matukar tana kasa da ni”

“Ya kamata ka sauke wannan nauyin daka dorawa kanka Talba life is very simple”

Talba ya juyo ya kalleshi.

“Ko?”

Sai Ali yai dariya domin ya san halin abokin nasa yanzu zata iya bare musu su fara siyar da hali.

“Yanzu dai forget about it, akwai maganar da nake son mu yi da kai”

Talba ya juya ya cigaba da kallon harabar asibiti da yadda mutane suka zirga zirga sai dai hankalinsa da ears dinsa suna gurin Ali.

“Akwai wata yarinya da aka kawo last week, tana cikin mutanen da yan bidiga suka raunata”

Yana tsaka da maganar sai kuma yai shiru yana duba wata takarda dake gabansa.

“To ta ina alakarta ta shafe ni?”

Talba ya tambaya ba tare da juyo ba, jin Ali ya dauko masa wata maganar da be san ta inda zata masa amfani ba. Murmushi Ali yai yana jinjina halin abokin nasa.

“Tana bukatar taimako ne sosai gaskiya”

Juyowa Talba yai ya rumgume hannayensa yana kallon Ali.

“Kai ina zuciyar taimakonka ta tafi ne? Ko baka taimako?”

Ali yayi dariya.

“Talba kasan irin taimakon da na yi mata? Tun da aka kawo su ba Gobnati bata sake waiwayarsu ba, babu wani tallafi da ake kawo musu, mostly yan uwa da iyaye ne suke daukar nauyinsu, sisin kwabo babu daga gobnati komai daga alijunsu dana yan'uwansu yake zuwa, wasu an sallame su sai dai wadanda albarushi ya shiga jikinsu ne kawai suke nan suna jinya har yanzu”

Ya hade yawun bakinsa sannan ya cigaba.

“But yarinyar har yau babu wanda ya taba zuwa nemanta, babu wani da yazo yace shi babanta ne ko yayanta, komai da ake biya daga aljihuna ya fita na taimaka mata saboda ta bani tausayi sosai”

Ganin Ali yana maganar babu alamar wasa a tare da shi yasa shi tambayar abun da yake son ji daga gareta.

“Miya same ta?”

“Na farko dai she can't walk, she can't talk tun da aka kawo ta bata taba magana ba, idan dare yayi sai na yi mata allurar bachi sannan take iya bachi, kuma na yi na yi da ita ta ki tai magana, babu wata alama data nuna yarinyar tana magana, idan ma kaga ta motsa to na matso kusa da ita ne da allura, sai ta fara kallon allurar tana hawaye, and the most sadness part is an yi mata fyade sun lalatata ko mai haihuwa iyaka kenan”

Kusan a lokaci daya komai dake aiki a zuciya da jinin Talba ya tsaya cak na dakiku. Kalmar fyade wata irin babbar kalma ce mai razanarwa da muni a kunnuwan tsabtattacin mutane irin Talba, shi din namiji ne ba mace ba, amman ya tsani jin duk wani abu daya shafi fyade balle kuma fyaden kansa, be taba ganin Aminatu ba, labarin wanzuwarta be taba ziyartar kunnensa ba, kamar yadda zuciyarsa da tunaninsa ba su hasaso masa mai irin rayuwarta ba, wani abu daga cikin cikin tausayinta ya kusa zuciyarsa ya samu guri a kusa da kirjinsa ya zauna, hankalinsa ya kara tashi sosai a lokacin da Ali yake kara fada masa halin da yarinyar take ciki.

“I don't think kurma ce, domin idan na
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment