Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

anfani dashi inamai tabbatar Miki zkg ynd jikinki zekoma luwai luwai😘
Soap:3k
Beauty kit:11k
Chat:08062991549
07046881166
07067210195
Call :07046881166
08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
amare inakara shaidamuku duk wacce tayi anfani d kayanmu Bata bukatar gyaranjiki sedai ra'ayi🥰
Masoya kunanan kauna yanda nakwashe aljihu domin nafarantamuku kuyi achieving goal dinku pls Nima kunanan kauna kufarantamin😪🤠aljihuna yafarfado hilis karnakoma kauyenmu🥲
Yar shawarmannan duk nasaba😤 hilis kugarzayo arabani da kaya🤝
Nd guest what🤩
Duk Wanda yy siya 10k zuwa sama zesamu Karin gift😃
Pamper your skin🧖‍♀️
Shine like a bride👰🏻
Glow
   

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*

Slowly ya shiga bangarensa ya zauna kan kujera, yana maida numfashi a hankali. Kokari yake ya gano laifinsa amman ya kasa, sai kokarin ganin ya hade maganar da Kabir ya fada masa nan ma ya kasa, abun is so painful. Sai da ya hade yawu sannan ya mike tsaye ya nufi windows dinsa. Ya jingina da windows din ya kai hannunsa ya bude curtains din kofar yana kallon harabar gidan, for the first time ya ji yana marmarin ganin kakarsa, rabonsa da ita tun shekara biyu da suka wuce ita bata zuwa shi ma kuma baya zuwa, sai dai ya san duk wata Daddy yana aika musu da kayan abinci, idan lokacin sallah tai kuma sai ya aika musu da abun layya da dinkuna, amman ko kiranta a waya sai ya kwashe watanin be yi ba, abun da ya damu ne da shi kawai rayuwarsa ta nan, sai kuma Daddy da Momy, ya manta cewar yana da wasu familyn na mahaifiya bayan na mahaifi, amman a yau ya tuna saboda Kabir ya fada masa maganar data hana numfashinsa tafiya daidai. Hannunsa ya saka aljihu ya ciro wayarsa ya shiga ma'adanar lambobi ya nemo number kakarsa, ya aika mata kira yana kallon wayar sai da ta dauka sannan ya kara wayar a kunnensa.

“Ashe ko yau za ayi ruwa, Mu'azu ya kira ni da kansa”

Yayi murmushi tare da kai hannu ya shafa kansa.

“Kaka kina lafiya?”

“Ina nan lafiya kalau, sai ciwon kafa ya matsa min har yanzu”

“Subhanallahi zan zo na kai ki asibiti Inshallah”

“Kuna can birni kuna ta kula da wasu kun bar mu a daji, kamar ba mu da kowa, sunayen ku ma sai a radio muke ji, idan ba mu dauki waya mun kira ba kiran ayi gaisuwa ma ba ku yi sai idan mu muka kira”

Talba ya runtse ido ya bude yana jin rashin kyautawa.

“Ayi hakuri Kaka inshallah gobe zan zo na duba ki, amman na san baki bukatar komai a yanzu shiyasa ban cika kira ba, kuma kin ga a nan aiki yana mana yawa”

“Ba ci da sha ne kawai abun da rayuwa take bukata ba, ba kai kadai na haifa jika ba, amman ka fi sauran kwanta min a rai, balle kuma ka tako kafarka garin nan, yau shekara daya da wata takwas Mu'azu, ni ma ai fushi na yi shiyasa na daina sakawa a kira min kai, kuma na ki na fadawa kowa na birni cewar ina fama da ciwo, idan na mutu ba sai ku zo ku tafi da gawata ba”

“Kaka ke din ce kin ki ki dawo a nan ki zauna tare da mu, kin da ciwon nan na ki zamu sani ai, gashi a nan muna ta bawa bare balle kuma ke”

“Ai daman haka masu arziki suke, ba kowa ne yake a cikin iyalansu yake cin amfaninsu ba, wani lokacin kamin na kusa ya ci sau daya sai na nesa ya ci sau dari, kuma ni ba zan baro kauye na dawo birni na zauna na ba, na fi son na mutu inda aka rufe uwayena da yan'uwana”

“Garuruwan ma babu kyau a yanzu bandits suna ta kai hari kauyuka”

“Toh mu dai har yanzu ba su shigo inda muke ba, kuma ina addu'ar Allah ya tsare mu”

“Ameen Kaka, Inshallahu gobe zan zo na duba ki, kuma zan dauke ki na kai ki asibiti”

“Toh Allah ya kaimu lafiya, Allah ya maka albarka ka yi marmarin matarka kenan”

“Allah ya kara miki lafiya”

Ya fada yana murmushi idanuwansa kuma suna cika da hawaye a lokaci daya, sai ya sauke wayar ya saki windows din ya juyo yana tafiya kamar wanda baya son taka kasa, bedroom ya shiga ya tube tufafin jikinsa ya daura tawul ya shiga yai wanka, sannan ya fito ya nufi wardrobe dinsa ya ciro jallabiya da gajeren boxer da vest ya saka sannan ya dauki wayarsa ya kira Line Leila ringing wayar tai har ta katse bata daga ba, saka wayar yai a aljihunsa ya nufi inda ya aje key din motarsa ya dauka ya saka aljihu tare da wallet dinsa ya nufi kofar fita yana ta sauri, kamar wanda ya manto wani abu a wani gurin. Bangaren Momy ya nufa kamin Mairo ta bude masa kofar ya danna door bell din ya fi a kirga.

“Sannu da zuwa yan ranka ya dade”

“Leila na ciki?”

“Aa tun kamin Magariba ta fita tare da kawarta Madina”

“Amal fa?”

“Ita ma ta fita tun dazun, Kabir ne kawai a gidan”

Kai ya daga mata ya juya ya nufi motarsa, sai da ya shiga ya zauna sannan ya kira sake kiran Leila, a yanzu kam sosai yake son jin muryarta domin ya san tana cikin damuwa, kuma be kamata ya kyale ta ita kadai tai ta fama ba, a nan ma ba ta yi picking call din ba, hakan kuma be han shi sake kiranta ba, abun da ba al'adarsa ba, idan yai ma mutun kira daya ba zai sake kiransa ba, not because saboda yana jin kansa no saboda ya san duk wanda aka kira be daga ba wata kila yana da uzuri ne. Sai da ya jera mata kira biyar sannan ya kira Amal.

“Hello”

“Amal kina ina?”

“Ina gurin Hajiya Yana”

“Gurin Momy kenan?”

“Eh”

“Amman kin san Daddy baya son kuna kaiwa waje da dare ko?”

“Ina tare da Momy ai”

“Leila tana tare da ke”

“Aa na bar ta a gida”

“Okay ki kula da kanki, kuma ki kira Daddy ki fada masa kina gidan Hajiya Yana”

“Toh”

Ya yanke wayar ya sake kiran Leila bata daga ba, sai ya yanke shawarar kiran Madina domin ya san suna tare a yanzu kamar yadda Mairo ta fada. Ringing daya Madina ta dauka tana wani irin kashe murya.

“Hello Ya Talba”

Be amsa ba, sai kawai ya gabatar mata da bukatarsa.

“Leila tana tare da ke?”

“Eh amman ni ina mota su kuma sun shiga vip”

Yayi shiru kamar ya tambaya ita da waye sai kuma wata zuciyar ta hana shi, sai dai hakan be hana Madina fada masa ba.

“Tare da Ali”

“Okay”

Ya fada a takaice ba tare da ya kawo komai a ransa ba, yana kokarin aje wayar ta dora masa da wata maganar.

“Ina ta son na kira na tambaya halin da yarinyar nan take ciki kuma ina tsoron kar na kira ranka ya bace, ka. Taimaka min dan Allah ka fada min ya lafiyarta take? Ko na samu hankalina ya kwanta”

“Lafiya kalau”

“Alhamdulillah, idan tana bukatar zama da ni ko kuma wani gurin dabam, zan iya sama mata inda zata samu aminci da kwanciyar hankali inshallah”

“No need”

Ya aje wayar feeling some how, ya aje wayar yana ta kallon screen din wayarsa dake dauke da hoton Daddy, sai ya sauke numfashi a hankali sannan ya kai hannunsa yai ma motar key ko kamin ya reverse mai gadi ya bude masa gate. Driving yake amman ya kasa natsuwa, sai ya rasa abun da ke damunsa, be yi nisa sosai ba ya faka kusa da wani masallaci yai fita yai alwala ya shiga masallacin yai sallah, after ya fito ya shiga motarsa ya sake daukar wayarsa sai dai wannan karon ba kiran Leila yai ba sakon kar ta kwama ya aika mata wato sms,

“If you need someone to talk I'm here”

Sai da ya tura mata sakon sannan ya kira Daddy.

“Hello”

“Daddy yanzu dai na san ka huce”

“Mace ne ni da zan yi yaji?”

Talba yayi murmushi.

“Daddy sarkin tsokana, ni dai yanzu na kira na sake rokon alfarmarka, kuma na tabbatar maka cewa dawowar Momy shi ne farincikina”

Daddy yayi shiru kamar ba zai ce komai ba.

“And Rashin Momy ya saka Leila da Amal za su kwana gidan
Hajiya Yana, ni ma zan tafi kauye gobe Inshallah”

Daddy ya tabe baki.

“Okay har da kai a masu yi min tawaye kenan”

“This time around Daddy bana tare da kai gaskiya, kuma abun da kai ya saka ni a wani hali”

“Karka damu komai zai wuce, amman ba sai kaje kauye ba saboda hanyoyin kasar nan basa da kyau”

“Allah shi ke tsarewa Daddy, zan dawo lafiya inshallahu”

“Sai mun hadu gida”

“Okay”

Yana aje wayar reply Leila ya shigo wayarsa.

“No need ina tare da wanda ya san darajata, wanda kukana yake zame masa damuwa, farinciki ya zama burinsa”

Ya karanta sakon sau daya sai ya ji kamar be gane ba har sai da ya sake karantawa. Yawu ya hade sannan ya aje wayar yai ma motar key, tafiya kadan ya tsaya ya shiga wani restaurant yai ma Aminatu take away na jalof da ruwa sannan ya dawo motar ya saka yi mata key, be faka ko'ina ba sai kofar gidansa, bude motar yai ya fita tare da takeaway ya rufe motar sannan ya doshi gate din ya saka key din hannunsa ya bude gate din ya shiga, kamar yadda ya saka key ya bude gate haka ya bude kofar ya shiga cikin falon silently.
  Har yayi kamar ya aje ledar hannunsa a falo sai kuma ya zarce dakin kai tsaye, a hankali ya tura kofar ya shiga, duk kuwa da ya san ba lallai ne ya same ta har yanzu tana bachi ba, sai dai be yi zaton zai sameta a halin da ya same ta ba. Ta koma can karshen gado ta rakube kallo daya zaka mata ka karamci tsoron daya cika mata zuciya, har ya rabawa wani bangare a jikinta domin idanuwanta hawaye suke jikinta kuma yana ta karkarwa. Ya dade a tsaye yana kallonta sannan ya karasa kusa da ita ya risina a gabanta.

“Shalele miya faru?”

Kallonsa kawai take hawaye na sauko mata, me zata fada masa? Yana bukatar ta maimaita masa cewar tana jin tsoro? Bayan ya rufe kofar fita kuma ya barta ita kadai a katon gida? Har yanzu kukan rayuwar baya take ta rashin uwa da uba da family da kowa ko kuma dai tana kukan kalubalen dake gaba ne? Ta yadda zata saba da rayuwa ita kadai ba tare da kowa ba?

“I'm sorry uzurin fitar ne ya kama ni shiyasa na fita, kin yi sallah?”

Ta girgiza masa kai alamar aa jikinta har lokacin rawa yake. Kallon jikinta yai kamin ya kai hannunsa ya kama hannunta wai ko zata samu hankalinta ya kwanta.

“You're safe now, babu abun da zai same ki, and na sama mana mafita, zan tafi da ke gobe a kauye can gurin Kakata na san za ki iya zama a kauye ko?”

Ta yi shiru bata ce masa komai ba, kuma bata bar masa wata alama da zai gane tana so din ko akasin haka ba.

“Tana da son mutane sosai, na san zata rike ki hannu biyu zaki jidadin zama a can Inshallah, abun nan is not easy arika passing passing da kai amman idan kika danne sai ki rayuwar ta zo miki da sauki”

Ban da hawaye babu abun da Aminatu take.

“Zaki iya yin kukanki, ba komai na fahimci halin da kike ciki, ni ma da ban taba jin kamshin mahaifiyata ba na ji wani iri balle da kika saba da su”

Kamar jira take sai ta fashe da wani irin kuka, zaunawa yai a gurin yana ta kallonta tun tana kukan da karfi har ta gaji ta daina dan kanta, mikewa yai tsaye tare da ita ya nufi bandakin da ita, ya kai dayan hannunsa ya kunna fanfo ya tara hannun nasa ya debo ruwa ya wanke mata fuskarta sannan ya fito ya barota tai alwala. A nan ta samu damar karewa kanta kallo a madubin dake gabanta, a zahiri madubin take kallo a badini kuma rayuwarta take hangowa? Har mutum dubu nawa zata gani kamin ta samu wanda zai zame mata uwa da uba? Har guri nawa zata zauna kamin ta samu muhallin zama na dindindin, kalaman da Umma tai mata sai ya suka dawo mata sabin, jin take duk duniyar nan babu wanda zai fahimce ta, babu wanda zai gane damuwarta, tana jin wani irin yanayi mai wuyar sabo, ta kasa sabawa da rashin kowa! A rayuwarta bata taba ganin zalinci irin wannan ba, a kashe maka kowa kuma a keta maka haddi sannan a raboka da garin da ka bude ido kai wayo a cikinsa, yanzu kuma a barta a wahale tana neman sabawa da rayuwar da bata taba mafarki ba, yau ga ta a duniyar da bata san da wanzuwarta ba, hannu ta kai ta dafa gefen kanta tana shafa kan a hankali dishes dishe ta fara gani jiri ya fara dibanta sai ta fisgi numfashi da karfi tai Sulale kasa tana ambaton Allah, da gudu Talba ya turo kofar falon ya shigo ganinta a kwance kasa ya saka shi furta.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Ya saka hannunsa ya dago ta ya taba kanta, ya bude ido be ga wata alama dake nuna tana motsi ba, ga fanfon daya kunna mata yana ta zuba, dankwalin kanta ya cire sai gashin kanta daya sha gyara a hannun Madina ya zubo, daukarta yai ya dawo ta ita saman gado ya koma ciki ya dauki dankwalinta ya jika da ruwa ya matse ya zo ya saka mata a gaban goshi amman be ji ta yi wani motsi ba, sai ya kai hannunsa jikin hancinta, ya ji bata numfashi a take hankalinsa yai mugun tashi sai ya girgiza ta.

“Amina.... Amina... ”

Nan babu alamar rai a gangan jikinta, sake komawa yai ya jika dankwalin ya sake zuwa ya saka mata a goshi, ya sake girgirza.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Ya furta gabansa na mugun faduwa, zuciyarsa na raya masa Aminatu ta mutu, saboda an fada masa zuciyarta zata iya bugawa ta rasa rayuwarta. Wayarsa ya ciro da sauri ya kira Ali, ya kara wayar a kunne yana ta safa da marwa sai yawo yake da hannunsa yana ala ala Ali ya daga, amman har wayar ta gaji da ringing ta katse be daga ba, aje wayar yai ya nufi Aminatu ya sake girgiza ta a karo na uku, sai dai babu alamun zata farka ya dauke ta gaba daya ya nufi kofar fita da ita kamin ya isa kofar falon numfashinta ya dawo da mugun karfi kamar an jefo mata shi, har sai da taja numfashin da karfi tana fito da ido waje, ita kanta ta san ta lula wata duniyar dake mantar da mai ita komai na rayuwa. Durkushewa yai bakin kofar ya sanda kansa kasa ya rumtse ido yana sauraren yadda zuciyarsa ke bugawa da mugun karfi. Dago ta yai ya rungume a kirjinsa.

“Kin zama daya daga cikin yan'uwana idan kika mutu a yanzu zan shiga wani hali, ki kasance mai karfin hali mana”

Ta hade yawu daker hawaye na fito mata har lokacin numfashinta da karfi yake fita bakinta har ya soma bushewa.

‘Ya kake tsammanin tsayuwar dakin da rufinsa ya yaye katangarsa ta zube? Taya zata iya yin karfi hali? Zata iya hana kanta tunani? Ko kuma zata mantar da kanta abubuwa da suka faru ne? Ko kuma dai zata daina hangen future dinta...?’

Ita da shi saka daya suke da kalar zare daya, domin tunanin da take a zuciyarsa irinsa Talba yake mata a zuciyarsa, bude idon yai sai ya yi saurin rabata da jikinsa ya ajeta kasa yana kallonta kamar yadda take kallonsa da idanuwanta dake wani lumshewa kamar mai jin bachi kana ganinta zaka san babu karfi a jikinta.

“Sannu...”

Ya furta, kallonsa kawai take ba tare da ta ce komai ba. Can kuma ta lumshe idon ta bude sannan ta fara yunkurin tashi kyaleta yai ta gwada tashin da kanta ko zata iya, cikin iyawar Allah kuwa sai ta tashi zaune sai dai ta yi ginshikai da hannayenta.

“Suma na yi?”

Ya dauki lokaci yana kallonta kamin ya daga mata kai alamar eh.

“Kin zufafa a tunani, kuma kin yi kankanta da haka, zuciyarki zata iya bugawa a ko wane lokaci kamar yadda likita ya fada”

Sai kuma yai shiru damuwa ta bayyana a fuskarsa.

“Kin tsorata ni sosai”

Ya fada yana mikewa tsaye.

“Zaki iya tashi ki yi sallah? Ga abinci can sai ki ci”

Ta yunkura ta gwada tashi sai ta kasa, dukawa yai ya dauke ta ya shiga da ita bandakin, wannan karon tsayawa yai bakin kofar har sai da ta gama tsoro yake kar ya barta ta ta sake yin na dazun.

“Ki gwada takawa mu ga”

Ba musu ta daga kafar ta fara dakawa a hankali, ciwon ya ragu sai dai jirin ne be gama sakinta ba. Yana ta kallonta har ta iso bakin kofar fitowa bathroom din sannan ya fito yana kallonta tana takawa a hankali har ta fito gaba daya, kamin ta isa bakin gado ya zauna har ta tsawwala saboda gajiya da tai da tafiyar, tana zaunawa sai ya nufi akwaitin kayanta ya bude ya dauko wani dankwali a ciki ya shimfida mata.

“Kin ga gabas nan”

Ya nuna mata sai ta kalleshi.

“Ban taba tsammanin mutane irinka suna da saukim rayuwa da arha har haka ba, ban tsammaci samunka a yadda ka zo min ba, na yarda Allah yana so na, kuma idan ya hana ka wani abun sai ya baka wani, shiyasa ya hada ni da babban mutum kamar kai kake ta hidima da ni, na gode Allah ya saka maka da alheri, ba ka dubi tazarar dake tsakanina da kai ba, kana ta hidima da ni kamar wata yar'uwarka”

Yayi murmushi sannan ya nuna mata hijabinta.

“Ki yi sallah a zaune idan ba zaki iya tsayuwa ba”

Bayan ya fadi haka ya nufi kofa.

“Ni kadai zan kwana a nan?”

Tsayawa yai sai kuma ya juyo.

“Aa zan zauna falo ne, a nan zan kwana, gobe da safe zamu kama hanyar Maradun zan kai ki gurin Kakata za ki zauna tare da ita, ina da tabbacin zata karbe ki hannu biyu”

Ya sakar mata murmushinsa mai matukar kyau da tsada sannan ya juya ya fice.



LEILA POV.

A tare suka fito da Ali, ba laifi ta samu sakewar zuciya ba kamar dazun da take a cikin damuwa ba. Da kansa ya bude mata mota ta shiga front seat ta zauna sai Madina ta dubeshi tana murmushi.

“Yayi kyau Aminin ango, lallai kasan ta kan amaryar nan ta ku, nan da nan har ka mantar da ita damuwarta”

Leila ta kalli Ali tana murmushi, shi ma murmushin yake yai yana ganin kamar da biyu Madina ta fada masa maganar nan.

“Dole ne na yi abun da zan iya na tare abokina kar ya fadi”

“Yayi kyau, ai ka fi abokinka sanin darajar mata shiyasa kake damuwa da kukansu, matarka da huta Ali, Wallahi da ni na aureka da more miji”

A zahiri da kanta take, sai dai a kasan zuciyarta tana ingiza mai kan tururuwa ne, saboda Leila ta soma dasa wani abu a zuciyarsa akan Ali.

“Kina da son zolaya Madina, yanzu dai kuje gida ku huta”

“Thank Youu Ali”

Leile ta fada sai ya gyada mata kai ya rufe mata motar, Madina ta tashi motar tana fadin.

“Angonki fa ya kira ni yana tambayar ina kike?”

“Ai ina ganin kiransa na share shi”

“Aa Leila be kamata ki yi haka ba ai sai ransa ya bace, kuma tun da har ya kira ai ya nuna miki kulawa”

Madina na rufe baki sakon Talba ya shigo wayar Leila, tsaki tai bayan ta karanta sannan ta nunawa Madina, Madina kam dariya tai ta rike wayar da hannu daya tana rubutawa Talba amsar da take ganin ta dace da shi, sai da ta tura sannan ta mikawa Leila wayar.

“Duba ki ga amsar da na bashi, ta nan zamu fara wana shi kuma mu gane irin son da yake miki”

Leila ta tabe baki.

“Ni yanzu ma ban sani ba, ina sonsa ko tsanarsa nake, bayan duk abubuwan da yake min, yanzu wannan abun da yai ya saka na fara jin tsanarsa a raina”

Madina ta yi saurin kallonta tana tukin motar.

“Da gaske? Wai kin bincika inda ya aje yarinyar nan kuwa?”

“Yace be san inda ya kaita ba, ki kai ni gurin Momy can zan kwana”

“Okay”

Daga haka bata sake cewa komai ba, sai dai a zuciyarta murmushin jindadi take, domin Leila ce kawai zata zame mata matsala a tarayyarta da Talba, idan kuma har Leila ta juyawa Talba baya burinta zai samu ciki, a tunaninta Talba zai iya neman maye gurbin Leila da ita ko dan ya batawa Leila rai, a iya tunaninta Aminatu ba matsala bace a gurinta, domin ta san waye Talba kuma ya dade tana karantar rayuwarsa fiye da Leila da suka taso a gida daya.



FARUQ POV.

Yana tsaye a tsakar gidan rike da yar karamar traveling bag, yana sanye da kananan kaya kansa a kasa yana furta

“Ameen”

Idonsa yar rine yayi ja sosai kamar wanda ya wuni ya kwana yana kuka.

“Allah ya baka abun da ka je nema Faruk, Allah ya shige maka gaba”

Mama ta fada tana fashewa da kuka, ji take kamar idan Faruq ya tafi gurin ginar zinari nan ba zai dawo ba, shi kansa yana jin wani yanayi na rashin jindadi wata kila saboda be saba tafiya mai hadari da nisa kamar wannan ba ne. Dukawa yai ya kama hannun dansa yana kallon fuskarsa sai ya ji kamar kar ya tafi ya bar Sultan.

“Dady yaushe zaka dawo?”

“Ba zan dade ba, kuma zan kira a waya na gaisa da kai ka ji”

“Momy fa yaushe zata dawo?”

Faruk yai shiru kamar mai tunanin abun da zai fada masa, ya san shi kansa dauriya kawai yake balle kuma Sultan da yake karami, an raba shi da uwarsa yanzu kuma zai tafi ya bar shi hannun Mama.

“Ita ma zata kira ka a waya ku gaisa, kuma idan zan dawo zan dawo tare da ita”

Sai kawai ya fashe da kuka, daman tun da ya bude ido ya ga Dadynsa na shirin tafiya yake ta son yin kukan, Faruk ya kama shi ya rumgume zuciyarsa tana sosuwa da kukan dansa.

“Dady zan bika, ka tafi da ni”

“Ba a zuwa da yara, amman kai ta ma Dady Addu'a, idan ya samu kudi zan siya maka komai kake so kuma zai dawo lafiya”

A take Sultan ya kara fashewa da kuka, sai Aisha ta zo ta kama hannunsa ta dauke shi ita ma hawayen ne kwance a idonta.

“Kyale Dady zamu je mu siyo minti mu sha ba zamu je da shi ba ka ji?”

“Dady zan bika zan bika Dady zan bika”

Shi ne abun da Sultan yake ta maimaitawa har Aisha ta fice da shi. Sannan Faruk ya mike tsaye yana duba agogon hannunsa, hudu da yan mintuna gashi kuma abokin tafiyarsa ya fada masa da biyar za su kama hanya. Karasawa yai gaban mahaifiyarsa ya risina gabanta yana rokon gafararta.

“Mama dan Allah ki yafe min duk abun da na yi miki na bacin rai wanda na sani da wanda ban sani ba, kuma yi min addu'a, Inshallahu da zarar na isa zan kira ku, ga Sultan nn na bari a hannunki kuma a karkashin kulawarki, ko da Allah be kaddara min dawowa ba, Mama dan Allah karki bari Rafi'a ta dauke shi, kara yai ta zama a nan tare da ku da talauchi da ya koma karkashin kulawarta, ban zan iya abun da zata aikata nan gaba ba, kuma zan rika yi miki aike ke da ita saboda cikin dake jikinta Inshallahu”

Ya karasa hawaye ya sauko masa, sannan ya mike tsaye Mama ta bishi da kallo tana hawaye kamar wanda aka cewa idan ya tafi mutuwa zai yi ba zai dawo ba, har ya fara tafiya bata ce masa komai ba sai da saka kafarsa daya a waje zai fita.

“Allah ya maka albarka Faruk, Alhamdulillah ko Allah be ba ni arziki ba ya ba ni ɗa mai tarbiya, ni da kai ba a san gawar fari ba”

Juyowa yai ya kalleta ita ma ta kalleshi sannan ya juya ya fice ba tare da yace mata komai ba.
30

Ko kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment