Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

driver, and this should be the last time da zaki umarce akan wani abu”

“Amman ni dazun ka cilasta ni na bawa Baaba hakuri bayan kuma bata cancanci haka ba”

Ta fada idonta na cika da kwalla.

“Me ka dauke ni ne Talba? Baiwa?”

Be amsa ta ba, ya juya motar zuwa gida, kamin su isa hawaye da ya wanke mata fuska ya fi a kirga, yana yin farkin ta bude motar ta fita tana share hawayenta. Sai a lokacin ya juyo da fuskarsa yana kallonta har ta danna door bell din aka bude mata ta shige, sannan ya maida dubansa gurin Daddy dake tsaye jikin motarsa yana magana da Momy da gaba daya hankalinsu yake kan Talba.
Bude motar yai ya fito ya rufe ya nufi gurin da Daddy yake tsaye yana wata irin tafiya kamar baya son taka kasa, kamin ya karasa ya zuba hannayensa aljihu kana ya sadda kansa kasa.

“Ranka ya dade baka burge ni ba, da baka tura Leila gida gurin Gwaggo ba”

Daddy ya fada yana kallon dansa, sai Talba ya kalli Daddy, kamin ya maida dubansa gurin Momy wanda hakan kr tabbatar masa da cewar Momy ta fadawa Daddy abun da yai ma Leila kenan.

“Momy ba zamu iya yin abu a tsakaninmu ba har sai Daddy ya ji?”

“Yes, ya kamata ya ji ne, saboda kana kokarin wuce guri”

“Just because...”

“It's just because? Tun ba yau ba Talba kana treating Leila kamar ba yar gidan nan ba, ya kamata ka sani ita ma tana da right fa!”

“Miyasa karamin Abu zai bata miki rai Momy?”

“Kai kaja komai, wacan yar aikin ma dana kora saboda kai na koreta Talba, saboda kana nuna kamar ta fi Leila gata a gidan nan, and now kana son na kori Baaba ko? Ka cigaba”

Tana kaiwa nan ta nufi hanyar da zata sadata da bangarenta, daga Daddy har Talba kallonta suke har ta shige, sannan Daddy Talba ya ce.

“Ka saba da halin Momy ka ba tun yau ba, kar hakan ya dame ka”

Talba yayi murmushi.

“Daddy fita zaka yi?”

“Yeah zan je gaisuwar Galadima ne”

“Lemme drive you”

“No tare da direba zamu je, go and rest”

Murmushi ya sake yi ya dan ja baya, ya budewa Daddy motar sai Daddy ya shiga yana fadin.

“Ance an kai hari Galadi, ya kamata A shirya wani abu a kai musu, mutanen nan suna cikin matsi”

“Inshallah Daddy, ban ji ba two days ban duba news ba”

“Sai na dawo”

“Allah ya kiyaye”

Ya fada yana rufe masa motar, sannan yaja ya tsaya har sai da driver ya ja motar Daddy suka fice daga gidan. Sannan ya nufi bangarensa, daga shi har Faruq da part dinsa yake kusa da nasa a kasa dakunansu suke, tsabanin bangaren Daddy da Momy da akai yi ma upstairs.
Dakin da yake aje tardunsa ya nufa ya bude ya shiga cikin natsuwa ya zauna a kujera ya bude system dinsa ya cigaba da wani aikin da be karasa ba, be bar dakin ba sai kusan 6pm.
Freezer ya nufa ya bude ya dauko ruwa ya zuba a cup ya surka da wasu sannan ya sha, bayan ya ajr cup din ya nufo kofar fita yana duba agogon hannunsa. Kai tsaye bangaren Momy ya nufa domin ya san izuwa yanzu ta huce fushin da take. Door bell din ya danna, yana dauke hannunsa Amal ta bude masa da sauri hawaye na sauko mata.

“Lil Sis?”

“Na'am?”

“Me ya same ki?”

Ya tambaya a yayinda ya saka kafarsa cikin falon yana dubanta.

“Baaba ce...”

Sai kuma tai shiru, shi dai kallonta kawai yake, as she knows ba zai sake tambayarta ba sai ta soma labarta.

“Tana mopping sai ruwa ya zame ta ta fado...”

Wani irin kallo tsoro yai mata.

“Ta fado ina?”

“Daga sama ta fado kasa!”

“You're kidding me”

“No Wallahi da gaske nake”

“Ina take? Ta ji ciwo?”

“Momy ta dauke ta sun tafi asibiti tare da Ya Leila tun dazu ba su dawo ba”

“Yaushe abun ya faru?”

“Lokacin da Daddy ya fita”

Ya juya da sauri ya fita zuwa bangarensa domin a can ya baro wayarsa, yana shiga ya koma dakin karatunsa ya dauki wayar ya kira Momy, ringing tai sai da ta kusa tsinkewa sannan ta daga.

“Momy kuna ina?”

“Gamu hanyar dawowa gida”

“Ina Baaba?”

Dan Jimm Momy tai kamin ta amsa masa.

“Yaranta sun zo sun dauketa, sun tafi da ita, daman ciwon ba sosai ba ne”

“Amman...”

Be karasa ya lumshe idonsa sosai jin Momy ta katse wayar, hakan nan jikinsa ya ba shi kamar ba iya haka ba ne. Idan har ba babban abu ba ne, babu yadda za ayi Momy ta kaita asibiti da kanta, kuma har Leila ta bi ta su tafi tare.



AMINATU POV.

Tun safe take ta wanke tufafin Baba da nata har kusan daya da tabi, abun ka da marar aiki da kuzari, bata da kuiyar aiki kam amman bata da sauri, sai wuni ta kwana tana abu daya.
Bayan ta wanke su fes ta matse ya daurewa ta soma sha shayawa, sannan ta bi tana kwashe wadanda ta shanya da farko suka bushe tana ninkewa, sai ta dora akai da haka har ta gama kwashe ta kai su daki, sannan ta fito ta shanya sauran. Ta dauke kayan da tai aikin da su cike da gajiya ta aje a inda suka saba ajewa.

“Inna tashi ki yi sallah”

Ta fada tana doso dakin, har zata shiga sai kuma ta juya ta dauki butar Inna ta cika da ruwa sannan ta nufo dakin, bata sake ce ma Inna komai ba har sai da jera tufafin Baba a inda ta saba saka masa sannan ta nufo inda Inna take zaune ta sadda kai kasa ta.

“Inna...”

Jin bata amsa ba yasa ta risina a hankali ta leketa, sai ta ga idonta a rufe, da sauri ta taba ta abunka da wanda yai nisan bachi sai ta zabura da karfi ta bude ido, da wanin irin karfi Aminatu ta hade yawu ta sauke ajiyar zuciya.

“Inna anyi sallah, yi hakuri na tashe ki da karfi tsoro na ke ji”

Sai Inna tai mata murmushi, sannan ta fara yunkurin tashi Aminatu ta kama ta ta mike tsaye, da taimakon Auta ta fito waje ta shiga bandakin, bayan ta fito ta rika mata butar tai alwala, sannan shimfida mata tabarma da abun sallah ta dauko mata hijabi.

“Allah ya miki albarka”

“Amin”

Ta amsa tana kokarin rikata ta zaunar da ita, domin a zaune take sallah, saboda bata iya dadewa a tsaye. Sai da Inna ta fara sallah sannan ta dauki butar ta shiga bandaki bayan ta fito tai alwala ta zo kusa da Inna ta yi sallah, babu komai a cikin addu'ar sai nemawa Inna lafiya, domin shi ne abun da yafi komai tsaya mata a rai a yanzu.

Kamar kullum bayan ta gama ta dora girki, sannan ta matsawa Inna furarta ta jiya ta bata. Baba be shigo ba sai bayan sallah isha'i.

“Sannu da zuwa Baba”

“Yauwa”

Ya amsa yana sauke gajiya, kamar wanda ya wuni yana aiki, daman can haka yake tun da tsufa ya kama dan abu kadan sai gajiya ta tarar masa. Aminatu ta tashi da sauri ta dauko masa abinci da ruwa ta aje masa.

“Allah ya miki albarka”

“Amin Baba”

Ta amsa tana jindadi albarka da suke yawan saka mata, ta san ko ba yau ba wata rana albarka nan zata bita.

“Baba na wanke kayanka fes na ninke maka”

“Eyeee Auta gayyar aiki, Allah kara miki albarka yar Baba”

“Amin”

Ta amsa tana murmushin data manta rabon da ya ziyarci kumatunta, Inna ma murmushin take tana kai hannu ta rage hasken fitilar dake kusa da ita.

“Yau da wuri za'ayi bachi ko? Dan a san akwai gajiya”

Cewar Inna tana kallon Aminatu, fuskarsa sai haske take duk da kasancewar dare ne, sai dai dan hasken farin wata daya haska ta da kuma fitilar dake kusa da ita yasa duk wanda ya kalleta zai yi arba da yadda fuskarta take ta haiba.

“Jikina yau Alhamdulillah ji nake kamar ba ni ba”

Baba yayi murmushi yana kallon Aminatu wanda ita ma murmushin take.

“Ai na ga alama ga annuri nan a fuskarki”

Ta sake fadada fuskarta da murmushi tana amsa sallamar da Isah yai, kusa da Baba ya zauna sannan ya aje mata ledar yalo a gabanta.

“Ga tsarabar kasuwa”

“Allah ya maka albarka”



“Amin”

Ya fada kamin ya dora da amsa tambayar da Baba yake masa.

“Wallahi kasuwa Baba taki ta koma kamar da, kowa a tsorace yake, saboda ana ganin mutanen nan kamar za su iya dawowa, kasan idan suka saka gari agaba sai sun ga bayansa, musamman garin da da suke da dade suna dafafe, tun da ba a taba shigo mana ba sai yanzu, gashi daman yan saka kai na yankin nan sun sha kashe mutane suna da haushin garin nan sosai”

“Allah dai ya tsare, abun da Bashiru yake ta ce min kenan kullum, ga shi tsohuwar ta ku ta ki yarda mu bar nan”

Cewar Baba.

“Ku bar ni na mutu inda uwaye na da kakanina suka mutu, ai ba a tsirewa mutuwa”

“Amman inna idan mu ka bar garin nan ke kanki hankalinki zai fi kwanciya fiye da nan”

Amina ta fada, a karon farko kenan da ta saka bakinta a maganar. Sai Inna ta girgiza kai.

“Babu inda zanje, kina ganina ko tafiya bana iyawa miya rage min Allah na tuba”

“Mai ciwo da mai lafiya, duk daya ne a gurin Allah, sai kaga mutuwar ta dauke mai lafiya ta bar mai ciwo ai”

Ta daga ma Baba hannu.

“Dan Allah ku daina min maganar nan, ni ban hana ku tafiya ba, amman ni kam ba zan bar garin nan ba”

“Allah ya kyauta”

Duk suka amsa da Amin har ita. Ko da goma tai duk sun kwanta Inna da Aminatu suna daki, Isah da Baba kuma suna waje saboda garin akwai alamun hadari hakan yasa zafi ya tsananta, sai dai hakan be saka Inna fitowa ta kwanta waje, Aminatu kuma duk inda Inna take tana nan. Kowa yayi bachi ban da Aminatu dake ta tunanin abubuwa da dama ciki har da wasikar ta ta karshe da ta bawa Maniru shi ma ya bata, babu yadda be yi ba akan yana son tai masa iso gurin iyayenta ta hana shi saboda tana jin tsoro, ashe ba rabon gaisuwa da shiga tsakaninsa da iyayenta. Sai a yanzu take jin zafin mutuwarsa, kuma take ganin laifin kanta na hana shi ganin Babanta da tai. Ba shiri tai firgigit ta tashi zaune sakamakon kara bindigar da taji, a da can yan saka na yanki su kan harba bindiga idan dare yai, shi ma kuma ba kullum ba, sai dai tun bayan harin da aka kawo musu aka kashe wasu wasu suka tarwatse sai aka daina harbawar, ba ta hadda karar wacan bindigar da kuma ta yan ta'adda ba, balle ta iya banbanci ta su da kuma ta yan sa kai, sai dai yanayin yadda take ta jin tashin bindigar babu kakkautawa yasa hankalinta ya tashi sosai.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Daga waje ta ji muryar Baba yana neman agajin Allah. Kamin su soma jiyo hayaniyar mutane da alama gudu tsiratar da rai suke, Baba ya shiga dakin da sauri ya haske fitilarsa ya bude inda yake ajiyar kudi ya kwashe su ya saka aljihu.

“Aminatu rikata tashi mu tafi yan ta'adda ne”

Kamar an zare mata lakka haka Inna ta ji, sai jikinta ya kara nauyi, Aminatu ta shiga kokarin rikata da sauri amman ta kasa.

“Tu tafi Malam, ku gudu ko dan saboda Aminatu”

Aminatu ta girgiza mata kai da sauri tana kuka.

“Ba zan tafi na barki ba Inna...”

Ta shiga kama Inna da dukan karfinta tana jin kamar ace tana da karfin da sata iya daukarta ta dora akai, sai gashi tsaye ma ta kasa mikar da ita sai da Baba ta rika mata dayan bangaren, sun mikewa tsaye suka ji harbin kamar a bayan dakinsu, wani kuma a cikin gidansu.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Baba ya fada yana sako fitsari a wando sai kuma ya fara rawa yana tsalle kamar wanda ya tabu.

“Allah ka batar da ni, Allah ka batar da ni kar su gan ni”

A take cikinsa ya murda sai zawo, abun ka da mai tsoro sai yai cikin tufafinsa na sakawa ya tura kansa sauran jikin a waje, ga wandonsa sharkat da zawo da fitsari. Inna kam gaba daya hankalinta yana gurin Aminatu. Da hannu ta nunawa Aminatu karkashin gadon karfi alamar ta shiga domin bata ko ina magana. Da gudu Aminatu ta nufi karkashin gadon kamin ta karasa shigewa suka shigo dakin rike da magayen makamai, ga wata uwar fitila mai dan karen haske da suke haska ko'ina da ita kamar gulub. Dayan ya turo Isah cikin dakin da karfi, sannan ya karasa karkashin gado ya daga daga katifar ya jefar can gefe, sai ga Aminatu dunkule.

“Fito ko na halbe ki”

Dayan ya fada, da Aminatu ake sai dai tsabar tsoro yasa Baba ya ji kamar da shi ake, sai ya cire kansa cikin jakar kayan ya rarafo kusa da Isah yana ta kuka da karanta addur'ar da ta zo masa.

“Yanarukuna bardan wassalamu ala ibrahim”

Daga nan ya dora ta ayatul kursiyu, kamin su daka masa tsawa ya kama bakin ya rike jikinsa ta ko'ina rawa yake. Wani irin rawa jikin Aminatu yake tana ganin komai kamar ba gaske ba, yadda take fita da shigar da numfashinta kadai ya isa ya bayyana irin tsoron da take ji.

“Dan Allah karku taba ta, ku kashe ni ita ku kyale ta”

Inna ta fada, sai dayan ya saka bakin bindigarsa ya buga mata a kai, take gurin ya fara zubar da jini.

“A kyale ta ita tafi sauran yaya ne? Kuna son ta kuka ja mata masifa ba kuri kuke ku kuna da jarumai a gari ba? Yayanka sai kashe mu suke duk inda suka ga bahillace sai ku kashe shi, Wallahi yau ko wa ba mu bari garin nan”

Cewar wani tsukaken a cikinsu yana rike da ak47. Ko kamin ya karasa maganar har wani ya fara yaga tufafin Aminatu, a take ta fashe da kuka tana kiran sunan Inna tana jin kamar ace Inna ko Baba wani zai iya taimakonta.

“Dan Allah ku kashe ni, ba zan iya ganin wannan abun ba...”

Inna ta fada a rikece tana kallon Aminatu take ta kuka suna kokarin rabata da zanenta.

“Kai bata giďa”

Wani ya fada a take na kusa da kofa ya dauke ta da bindiga har harbi hudu. Wani irin ihu Aminatu ta saka jikinta na rawa idonta kamar zai zubo tana kallon gawar Inna dake kwance tana zubar da jini ido a bude, tassss wani ya dauke ta da mare wanda ya saka ta a take ta manta inda take, duniya ko lahira? Ba suma tai ma, sai dai jinta yayi karanci kamar yadda idonta suke ganin haske wutar marin da akai mata, sai dai ko kadan hankalinta be yi nisa da jikinta ba.

“Bar shi ya fara yi”

Dayan ya fada yana nuna Baba da ke jiran ace masa mutu ya mutu. Baba ya kalli Aminatu dake kwance tsirara sai kuma ya kalli mutane kamar be gane yarensu.

“Tashi ka yi aka ce ko mu kashe ka”

“Ya... Ya... Ya...ya.... Ya... Ta ce... Ce.. ”

Daker ya furta, sai dayan ya saka bindigar ya halbe Isah dake gurfane kamar mai neman gafara yana kuka, halbi biyu yai masa a kai.

“Ko ka yi ko mu kashe ka, ina ruwanmu da yarka ce, mu be dame mu ba...”

Aminatu ta runtse idonta da sauri tana jin kamar ta bude ta ganta a wata duniyar...!




________

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe.
Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
*💔 BAKAR WASIKA 💔*


By Khadeeja Candy


Page -8️⃣

“Mutuwata zata fi min sauki fiye da aikata abun da kuka bukace ni da shi”

Abun da ya fito daga bakin Baba kenan. Wanda hakan ya saka Aminatu bude idonta duk kuwa da kasancewar bata da tabbacin idan ta bude idon zata ga mutane, domin kamin ta rufe idon haske ne kawai take iya gani.
Sai dai kallon be kare mata ma, domin ta yi arba da fuskar mahaifinta da suka haske da katuwar fitila mai haske.

“Kai ba shi giďa”

Idan suka ce aba wa mutum giďa yana nufin a halbe ka, take dayan ya daga bingida da zimmar harbin Baba sai bindigar ta ki tashi. Dayan ya sake daga ma ita ma taki tashi.

“Kaga wani tsohon shige... Sa mai wuka”

Dayan ya fada yana buga masa kan bindigar. Sai biyu suka kama shi suka kwantar da shi, dayan ya saka zabgegiyar wukarsa ya fara gagarawa a wuyan Baba, nan ma wukar bata kama ba.

“Shege, samo dutse yau ba maganin karhe ba ko maganin mutuwa ka kasha sai mun kashe ka”

Ban da kallon Baba babu abun da Aminatu take, ta kasa kuka hawayenta sun kafe, kamar yadda zuciyarta ta wanke tass, kwakwalwarta kuma ta zama fanko babu tunanin komai a ciki. Bata iya jin komai sai kalmar shahadar da Baba ke yi, duk yadda ta so ta kawar da kanta daga kallon yadda suke fasa kan Baba da katon dutse sai ta kasa ko da kwakkwaran motsi. Wani irin sanyi ne marar misaltuwa ya taso mata ya baibaye ilahirin jikinta, sai ta soma jin abu na mata yawo a cikin kai kamar hatsi.

“Baba...”

Ta furta daker tana kallon yadda suka rabe masa kai biyu a cikin dakin mahaifiyarta da suka harbe bayan sun kashe Ya Isah.

“Tashi ki saka tufafinki”

Dayan ya fada, sai ta kalleshi, duk da kasancewar hasken fitilar ba ya iya bari ya ta ga fuskokinsu, ba kuma dan ta fahimci abun da yake fada mata ba, sai dan hasketa da yai da fitila da yai, kana kallon kwayar idonta ka san bata cikin hayyacinta. Dayan ya kai mata mugun shuri a cinyarta.

“Saka tufafinki dan ubanki”

Maimakon ta saka tufafin sai ta juyarda fuskarta ta kalli inda ya shuri ta, ta kai hannu ta taba.

“Baba....”

Ta furta domin har yanzu tana jin sautin kalmar shahadar da yake a kunnenta, dayan ya fisgota sai ta mike tsaye sam ta manta a sirara take, yau ga ranar da bata kunyar siraicinta, ranar da dimauta da bakinciki suka saka ta manta babu sutura a jikinki.

“Wuce mu tafi”

Ta kalli inda mai maganar yake tana jin kamar ta taba jin kalmar. Tasss ya wanke mata fuska da wani irin mari mai zafi, sai ta rikice ta fara kuka.

“Inna.... Baba.... Wayyo Baba.... ”

“Saka tufafinki”

Ras ta ji abun da ya fada, kuma ta fahimce shi, hakan yasa tai saurin nufar inda tufafin suke ta dauka, sai dai a maimakon ta saka sai ta rike tufafin tana ganin komai kamar a mafarki. Dayan cikinsu ne ya fisgota ya turo keyarta waje, sai ta samu kanta da bin bayan wadanda suke gabanta, abun da bata sani ba ashe a sauran gidajen nan ma sun fito da sauran matan da suka rage, tafiya kawai take tana jin kamar ba kasa take takawa ba, hade ta sukai da sauran matan dake ta rawar jikin tsoro, domin sun kasu kashi kashi ne, suna shiga gidaje. Kamar wandanda suka fito yakin duniya, haka kowa ganinsu, karyar mutun yace ga iyakarsu sai dai ya kiyasta a kiyasinsa ya fadi iya abun da idonsa ya gane masa, babura ne ko wane da goyon mutum uku dauke da makamai, wasu kuma mutum biyu ne a kai, wasu kuma a kafa sun saka manyan samarin maza a gaba dauke da hatsin da suka kwasa.
Ba Aminatu ce kadai mace da suka tafi da ita ba, sai dai Aminatu ita kadai ce tsirara a cikin matan da suka kora zuwa daji, kamar sun kora dabbobi haka suka saka matan a gaba, wasu kuma suna daga gefe duk wanda yai kokarin guduwa daga cikin matan sai a halbeshi. Wasu mazan kuma suna bayan su Aminatu dauke da hatsin da suka dora musu, suna tafe suna dukan mazan a baya. Tafiya suke ta yi Aminatu na rumgume da tufafinta, bakinta kuma be daina furta Baba ba, da muryar da ita kadai zata iya ji, tana jin ta taka abu har ya huda fatarta ya shiga cikin kafarta, sai dai ko kadan tashin hankali be barta ta ji zafi ba, ko da ma ta ji bata isa ya tsaya cirewa ba, a cikin matan da suka tura gaba har da masu goyo, da kananan yan mata da matan auren, babu mai waiwaye balle ya taimaki wani, a cikin masu goyon wandanda yayansu suka fi takura musu da kuka sai su fige yaran su jefar, tsofafin da suka fara gazawa kuma sai su halbe su, masu sauran jini a jika kuma suna tafe suna dukansu. Zalincin da mutanen nan suke sai ka rantse da Allah ba zuciyar dan'adam ce a jikinsu ba. Ba su san wani abu tausayi ba, ba su ragowa ba, ba su san rai yana da muhimmancin ba, ba su wani abu imani ba, ba su san ragowa ba. Tun cikin dare suke tafiya a kafa suna ratsa wani irin jeji da Aminatu bata taba mafarkin gani ba, ba su isa inda za su je ba sai da hasken asuba ya fara ketowa.
Ba ita kadai ba mata da yawa idan ka duba kafafuwansa zaka tarar sun kumbura, saboda babu mai talkami a kafarsa, kuma da yawa sun taka kaya wasu kuma ice ya shiga kafar amman ba damar cirewa, sai dai kai ta taka kafar a haka.

Wani irin jeji ne da baka iya ganin iyakarsa, sai dai da alama mutanen kowa ne da dabarsa dabam, domin an raba matan ne wasu suka kora wasu zuwa yamma wasu kuma suka arewa, a cikin matan da aka kora arewa har da Aminatu dake rike da tufafinta.
  Har ga Allah ba zata iya fadar inda take ba, har yanzu bata yarda ba rayuwarta ba mafarki bace, har yanzu kisan da akai Baba da Inna gani take kamar ba gaske ba ne. A wani kebantaccen guri aka tsayar da su, sannan wadanda suke manyansu suka taso da manyan fitilu suka haska matan, kamin su kalli mazan da su ma sun gama galabaita.

“Wadanda ku kashe su kawai”

Aminatu ta juya a hankali ta kalli mazan da bata iya tantance fuskar kowa a cikinsu saboda tana cikin nata tashin hankali. Kamar umarni suke jira a take suka budewa mazan wuta suka musu mugun halbi, wadanda bindiga bata kamawa kuma suka takasu da babur. Faduwa Aminatu tai durkushe ta fashe da kuka, domin a yanzu ta tabbatar ya baro duniyarta, ta shigo wata duniyar ta azzaluman mutanen da babu digon tausayi a zuciyarsu. Kukan da tai ne ya saka dayan sake haskata.

“Wai iyakar matan kenan?”

“Aa an raba dai, Daba... Ba ruwana ba zan fadi suna ba🤐, sun dauki rabi, kai duk mun watse garin nan fa yau babu wanda muka bari, Wallahi yau mun aiki”

Dayan ya fada cikin mutanen da suka zo da su Aminatu, idan suka ce suna nufin gundu, domin akwai Babbar daba akwai karama, kuma daba kala kala ce, kowa da tashi, suna maganar yaron wata na kuka sai dayan ya ce.

“Kai wacan ya dame mu da kuka”

Wanda ke kusa da ita ya fisge yaron, sai ta rike masa kafafuwa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment