Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sai da aka gyara gurin, sannan tana zaman kadaici ne kawai babu kowa a tare da ita a nan”

Talba ya kalleta cike da tausayi, shi kansa ya san tana bukatar mai kula da ita, domin tufafin jikinta ma sun yi datti duk da kasancewar Ali ya saka an canja mata wasu tufafin tun a lokacin da take asibitinsa.

“And jiya ma ance bata yi bachi ba sai magana take ta yi da kanta tana kuka, be kama ace kullum sai an mata allurar bachi sannan zata iya bachi ba, domin ita kanta allurar yawan yinta yana haifar da wata cutar ta dabam”

“Ba ni da wanda zai kula da ita a yanzu gaskiya”

“Ko da a gida?”

Yayi shiru kamar mai tunanin abun da zai fada.

Aminatu ta kalleshi da idanuwanta da suka sha kuka har suka canja kala.

“A yanzu ba mu da gida, idan kun gaji da ni, to ku kai ni gurin da yan gudun hijira suke zama, ko kuma gidan marayu ko gidan nakasassu, ba ni da kowa...”

Talba ya risina kusa da gadonta yana kallonta cike da tausayi.

“Ba nasasa kika yi ba, ciwo kika ji, kuma zaki warke soon ko Likita?”

Sai likitan ya daga mata kai yana murmushi.

“Bata da kowa ne?”

“I can take care of her zan kai ta gida...”

Talba ya fada, sannan ya mike tsaye.

“Okay, idan zaka kaita gida, za ta fi samun kulawa gaskiya, domin a yanzu damuwarci kawai ciwonta sai kuma kafafuwan. Amman a shawarce zai fi kyau ka samu likitan da zai rika zuwa yana dubata, ko kuma ka rika kawota time to time asibiti ana duba kafar”

Talba ya daga masa kai alamar gamsuwa, Likitan ya kai hannunsa ya rika kan Aminatu ya bude idonta.
[3/7, 11:34 AM] Zatuuu🦋: “Ki daina yawan kuka kina daga idonki sama saboda kar glass din idonki ya samu matsala”

Ita dai bata sake ce masa komai ba har yai abun da zai yi ya fice. Sai da ya fice sannan Talba ya zauna a saman kujerar dake facing din gadon yana kallonta.

“Ki zama mai jajircewa da hakuri, komai da kika gani na rayuwar duniya baya zuwa da sauki, kuma kowa da kalar jarabawarsa, and ina tunanin Allah ya hada ni da ke saboda na taimakeki, wata kila da dace da wani kika hadu shi ba ni ba, da yanzu wani labarin ake ba wannan ba, so ki dauki haduwa ta dake a matsayin kaddara, akwai wani karon magana da ake cewar when life gave you hundreds reasons to cry, show life you have thousand reasons to smile, ina da tabbacin zaki zama jaruma, ki hade komai ki rayu ko dan iyayenki”

“Kuka ya zame min dole baka san yadda nake ji ba, rashin iyaye yan'uwa abu ne mai matukar ciwo, lokaci daya na rasa komai”

Ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta, hawaye nata wanke mata fuska kamar ba gobe.

“Na san yadda kike ji, ni ma maraya ne kamar ke ba uwa ba uba, banbancina da ke shine, ni ban taba kukan maraici ba, ban taba neman wani abu na rasa ba, ke ma kuma za ki samu kulawa Daga yanzu har karshen rayuwarki, kamin ki gane danginki, zan sama miki wasu dangin da zaki zauna tare da su, su rika debe miki kewa, na san ba za a rasa wani daga familynki da yake raye ba, From now on babu abun da zaki nema ki rasa Inshallah, babu abun da ya dace da ke a yanzu sai farinciki!”

Ta yi kasa da kanta tana hawaye.

“Da gaske na rasa kowa kenan! Da gaske ni kadai zan rayu? Taya farinciki zai zama a tare da ruhin da bakinciki ya zagaye, kuka da damuwa suka masa masauki? Har yanzu na kasa yarda a duniya na ke, an raba ni da kowa”

Ta fashe da sabon kuka tana jin wani irin bakinciki mai taba zuciya yana ratsata.

“Faranta ran mutane na daga cikin abun da yake saka ni farinciki, musamman irinki, ta ya mutum mai imani zai same ki a irin wannan halin kuma ya kasa taimakonki? Ki saka a ranki daman can haka Allah ya rubuta kuma akwai irinki da yawa”

Haka ya dage yana ta kokarin kwantar mata da hankali kamar na shi ba. So yake ta ji cewar ba ita kadai bace a cikin halin damuwa, so that ta kwantar da hankalinta, gudun kar abun yai mata yawa.

“Ki ci abinci yanzu sai na yi ma likitan magana, ya ba ku takardar sallama”

Wannan karon har dan guntun murmushi a fuskarsa.

“Bakina akwai datti da yawa”

Ya dan wara ido yana jin haka yasa mai tsabta ce.

“Okay bari muje gida gaba daya sai ki wanke bakinki a can ki karya”

Ta yi shiru bata ce masa komai ba, sai ya rufe abinci ya mike tsaye ya fice daga dakin. Be dade ba ya dawo rike da wata takardar sai wasu nurse biyu bayansa, su suka dauke ta suka saka ta a Wheelchair. Shi kuma ya dauki abincin kadai ba tare da ledar fruit din daya kawo ba sai kuma magani. Nurse din ce ta turo ta, shi kuma yana gaba har suka isa gurin motarsa, back seat ya bude musu suka saka ta sannan ya bude bayan motar suka saka masa wheelchair din, after ya rufe ya nufi driver seat ya bude ya shiga ya zauna.

“Yanzu zaki ga sabon gidanku da kuma yan'uwanki”

Ya fada ba tare da ya juyo ya kalleta.

“Na gode Yallabai”

Ta fada da muryar kuka, domin a yanzu ko kalma yan'uwa ta ji sai ta tuna da nata.

“Talba sunana, daga yanzu ni yayanki ne, kin zama kanwata gashi kina da sunan Momy kin zama Shalele”

Bata ce komai ba, har ya fara tukin motar ya fice daga asibitin, yana hawa babban titi ya fara gudu kamar yadda ya saba, sai jikinta ya fara rawa ta fara tsorata, abun da ya faru ya taba mata zuciya kuma ya shiga kwakwalwarta ya zauna, abu kadan sai hankalinta ya tashi.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Ta furta da karfi tana runtse idonta. Hakan yasa shi juyowa ya kalleta sai ya rage gudun da yake, sai dai be ce mata komai ba, ita kuma bata yarda ta bude idon ba har suka isa gidan da bata san yadda yanayinsa da tsarinsa ba. Harabar gidan ya faka ya motarsa sannan ya fito ya dauko Wheelchair ya aje ya bude back seat din yai ma daya daga cikin mai aikinsu hannu, sai gashi ya zo da gudunsa.

“Ka dora Wheelchair din nan a kofar falo, sai ka saka yarinyar nan ciki, ka dauko abinci yana ciki Motar”

Ya fada yana kallon motar Daddy dake fake, hakan ke tabbatar da Daddy be fita ba kenan. Wayarsa ya ciro daga aljihu da zimmar kiransa sai ya hangoshi ya fito direbansa na rike da jakarsa, da sauri ya nufi inda yake Daddy na hango shi sai ya tsaya jikin motar yana jiran karasowarsa.

“Daddy good morning”

“Morning Mu'az har na fita?”

“Yeah muna da meeting a office, amman ka rasawa na dawo na fada maka wani abu”

Daddy ya masa irin kallon nan dake nuna ina saurarenka. Tun daga biri har wutsiya ya fedewa Daddy komai, ba karamin tausayin yarinyar Daddy ya ji ba.

“Yarinyar tana ina?”

“Gata acan na zo da ita, ina neman amincewarka, idan kuma hakan be maka ba, zamu iya duba wani gurin sa zamu iya ajeta, saboda gida marayunmu yawanci kanana ne ba su kai kamar ta ba, idan ma na aje ta a can zata sake shiga kadaicin ne”

Daddy yayi murmushi jindadi ya kai hannunsa ya dafa kafadar Talba.

“Ina alfaharin da kai Mu'az ka ci sunana kuma baka rago komai daga halina ba, mu gidan nan ai kullum muna marhabun da baki ne, kuma ni uban marayu ne karka manta da wannan, ko da ace tana da kowa nata a raye ta so zama da mu zan dauke ta kamar ya balle ma tana marainiya, ka yi tunani mai kyau ka ga yanzu kun zama ku biyar, Allah ya muku albarka”

Talba yayi murmushi.

“Thank you Daddy, amman Momy ba lallai ta yarda ba”

Daddy yai masa wani kallo.

“Momy ke da gida ko ni?”

“For now ita ke da gidanta...”

“Really to bari mu ga idan kai aure kai ne da gida ko matarka”

Talba yayi murmushi.

“Wannanai dabam, ni Talba ne kai kuma Daddy ne”

Daddy ya girgiza kai yana murmushi tare da zolayarsa.

“Za'a min izinin ganin yarinyar?”

Ban da dariya babu abun da Talba yake, ya wuce gaba Daddy ya biyo bayansa, sai dai hakan be hana su isa kofar falon a tare ba.
[3/7, 11:34 AM] Zatuuu🦋: Talba ya danna door bell ba dadewa aka bude masa sai ya matsa Daddy ya fara wuce sannan shi ma ya shiga. A tsakiyar falon ya hango Aminatu zaune a wheelchair ta sanda kanta kasa hawaye na sauko mata, Kabir na tsaye gabanta. Momy kuma na zaune a kujera daya ita da Leila suna kallon ikon Allah.

“Ita wannan bata magana ne?”

Kabir ya tambaya yana kallon Talba.

“Ka dame ta da surutun ne ko?”

Cewar Daddy. Sai Kabir ya ce.

“Sunanta kawai na tambaya, sai ta rufe ido ta fara min kuka”

Daddy ya karasa kusa da ita yana kallonta cike da tausayawa.

“Sannu Allah ya baki lafiya”

Bata bude idon ba har sai da ta ji kamshin turaren Talba, sannan ta bude ido ta kalli inda take jin kamshin na fitowa, ido biyu suka yi sai dai nata idon cike suke da hawaye.

“Ya sunanta?”

“Sunan Momy”

Talba ya fada, sai Daddy yai murmushi ya kalleta.

“Yar gata ce kenan, sunan matata kuma uwar yayana kin ga babu wanda zai taba ki a gidan nan! Ki kwantar da hankalinki ki dauki kowa kamar dan'uwanki ni kuma na miki alkawarin zama mahaifinki da yarda Allah, duk abun da zan iya yi ma yayana zan miki Inshallah”

Talba yayi murmushi, sai Kabir ya wara ido.

“Ji wannan daga zuwanki zaki karbe mana fada, bari fitinanniyar ta zo zata zalzaleki”

Daddy ya girgiza kai yana dariya.

“Aa yanzu ita ce auta, daga gani Amal zata girme ta ai”

Ya fada sannan ya dago ya kalli Momy.

“Hajiya karaso ki ga yar da muka samu kyauta daga Allah”

Momy ta taso daga inda take zaune tare da Leila suka karaso inda Aminatu, sai da Momy ta kare mata kallo sannan ta ce.

“Ya kamata a nemi izini na kamin a kawo ta, amman sai ganin musaka nai a falona, saboda ban isa da gidan ba”

“Na fara magana da Daddy ne, kamin na yi magana da ke, ni ma ban yi zaton hakan zai faru ba sai da likitan ya fada min sai na ga kamar hakan ya dace”

“To be dace ba, be kamata ka dauko min wata bare can ka kawo min a gida ba, yarinyar da ban san daga inda ta fito ba”

A hankali Aminatu ta dago ta kalleta sai ta maida kanta kasa.

“Momy karki tsorata mana, ba nan ya kamata ku yi wannan maganar ba”

Kabir ya fada. Sai Momy ta watsa masa harara.

“Idan na tsoratata sai ka saka zane ka goya ta ai”

Daddy ya hade rai yana kallon Momy cikin rashin jindadi.

“Bana son maganar nan, Danki zai fada miki komai”

Sannan ya kalli Aminatu dake hawaye.

“Aminatu ki kwantar da hankalinki kin ji, mu iyayenki ne”

Ta kasa dagowa ta kalleshi ma balle ta ce masa komai, har sai da Talba ya kirata da sunan da Inna take kiranta da shi.

“Auta...”

Sai ta kalleshi da sauri tana jin wani tsam a jikinta.

“Ki cewa Daddy kin gode”

Ya fada yana mata murmushi kadan kamar na dole. Sai ta kalli Daddy da idanuwanta da ke zubar da hawaye.

“Na gode...!”

“Oh Really.. Zai ka mata umarni zata yi magana kenan”

Kabir ya fada yana kallon Talba, murmushi kawai Daddy yai ya nufi kofar fita.

“Zan tafi kar na yi latti, sai a gyara mana daya daga cikin dakunan da suke kasa nan”

“Da a BQ na so ta zauna”

Talba ya fada.

“Why BQ ga dakuna a cikin gida? A bar ta nan BQ ai na amsu aiki ne, sai na dawo”

A karon farko Momy ta kasa ce masa Allah ya tsare balle har tai masa rakiya. Bayan Daddy ya fice Talba ya risina gabanta ya nuna mata Leila.

“Sunan wannan Leila kanwata ce, kuma matar da zan aura, akwai wata Amal tana makaranta, wacan kuma Momy mahaifiyarmu, muna da masu aiki biyu Mairo da Zulai idan kina bukatar wani abu ki fada musu za su miki. Wannan kuma Kabir, shine likitan da zai rika dubaki shi ma kuma kanena ne”

Talba na ajewa Kabir ya tari numfashinsa.

“No no no Malam shekara biyu ka bani ba, sai wani ji kake da kanka wai kanenka kar ta dauka da gaske”

Talba be ce komai ba, daman ba komai yake saka shi dariya ko magana ba, sai ya kalli Momy.

“Momy ina son zamu yi magana”

Momy ta dauke kai daga kallon Aminatu ta kalli Talba tana jin wani irin zafi a zuciyarta.

“Har a bada dan wani br taba zama nawa ba, nawa kuma be taba zama dan kowa ba”

Kusan wannan ne karo na biyu da wata kalmar ta fito daga bakin Momy da bata masa dadi ba, bayan wacan karo da shigarwa Leila.

“Momy yarinyar nan marainiya ce, ba uwa ba uba, kuma ban daukota na kawo ta nan ba sai dan nasan zamu iya kula da ita, kuma kin san muhimmanci rikon maraya, and ko dan ni ya kamata ki daga mata kafa...”

“Saboda gaka Ubana? Ko kuma saboda mu muka fi kowa son lada? Waya sani ko karya ta tsara maka? Idan ma da gaske ne mu muka kashe iyayenta ne da responsible din ta zai dawo kanmu?”

Da mugun mamaki Talba yake kallonta jin irin kalaman dake fitowa daga bakinta, sai dai be ce mata komai ya kalli Aminatu ya dauke kai ya kalli Kabir da yanayinsa ke nuna be jidadin kalaman Momy ba.

“Kabir kira Mairo”

Momy ta ja tsaki ta nufi upstairs ta bar Leila tsaye tana kallon ikon Allah.

“Mairo...”

Kabir ya kwala mata kira, ya san daga muryar ne ba zai iya ba shiyasa ya saka shi kiranta ba wai dan yana nufin ya tafi yaje ya kirata ba. Da gudu Mairon ta fito daga kitchen hannunta da kumfa.

“Gani ranka ya dade”

“A wanke mata baki, a bata abun karyawa, sannan a gyara mata dakin kasa, ki taimaka mata tai wanka sai dai kafarta na ciwo sai kin yi a hankali”

“To ranka ya dade”

Ta amsa da sauri, shi kuma ya juya ya fice daga falon ya bar Aminatu sai Kabir da Leila.

“Let me help you with brush and toothpaste”

Kabir ya fada sannan ya juya ya nufi upstairs. Leila ta bishi da kallo sai da ya haye gaba daya sannan ta kalli Mairo tana yamutsa fuska.

“Idan kika mata wanka, sai Momy ta ci ubanki”

Mairo ta kalleta da duba na rashin jindadi.

“Haba Leila kina ganina kin san na yi kanwa ta uku da ke, be kamata ki ce min haka ba, ko da kuwa kin san Hajiya zata yi fada ne, amman be dace ki zage ni ba”

“Okay miya dace na fada miki? Ki zo aiki gidanmu sannan ki yi tunanin zan girmamaki? Koya min magana zaki yi ko mai”

Yanayin yadda Leila ta rufe Mairo da masifa ne ya saka jikin Aminatu rawa, sai ta fashe da kuka.

“Mtssss munafuskar banza”

Leila ta fada tana hararar Aminatu, sannan ta nufi kofar baya ta falon tana danna waya.


21

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


BATURIYA POV.

Sai da Ramlee ta shiga da ita har cikin falon sannan ta fita ta barta. Baturiya ta dade a falon sannan ta ji tsayarwar Mota harabar gidan, sai ta leka ta window ta hangoshi ya fito daga motar rike da wata karamar jaka, dayan hannunsa kuma rike da Makalle da waya a kunne. Babban mutum ne a haife ya haife ta kuma ya haifi yayunta, irin mazan nan ne da ake kira da sugar daddy.
Wani irin faduwa ta ji gabanta yayi, sai hakan be hanata daidaita natsuwarta, Ta gyara zamanta sannan ta kunna wayarta ta saka ta silent, gabanta ya tsanata bugawa ne a lokacin daya turo kofar falon ya shigo, abun ka da wanda be saba ba sai ta mike tsaye tana kallonsa, shi kuma ya kare mata kallon tun daga sama har kasa sannan yai mata alama data zauna, sai ta koma ta zauna tana kirkiro murmushi, a kujera dake kusa da kofar ya aje jakar hannunsa sannan ya karasa kusa da ita yana murmushi ya zauna. Ita ma murmushin ta sakar masa, sai ya kai hannu ya shafa fuskarta ya nuna mata fuskarsa alamar tai masa kiss, ba musu ta mika bakinta ta sumbanci gafen fuskarsa sai ya rumgumeta yana shafa bayanta.

“Yanzu dai Hajiya ki bari idan na dawo gida hankali kwance sai mu yi maganar, kisan Muhammad baya jin maganar kowa a yanzu so dole lallabashi za ku yi, idan yaji yana son ta ya amince daman abun da muke nema ne tun da yar'uwarsa ce, idan kuma yace sai wacan sai mu masa addu'a”

Ya fada yana gangarowa da hannunsa ya cire mata zip din atamfar ya fara murza fatarta ta baya dake cike da taushi da fari.

“Yanzu muna da meeting, idan mun gama kuma zan je na ga gwana saboda maganar kudin kwangilar nan, ba zan dawo da wuri ba sai dare”

Baturiya ta yi shiru tana sauraren yadda hannunsa ke ta yawo a jikinta, Sai wani abu take ji na rashin jindadi, ta saba mu'amala da Faruq balle tace ko dan bata saba bane, wata kila kuma saboda wannan sabo ne tsabanin wacan da take samu lada.

“Eh ya same ni da maganar ai, shiyasa muka taho tare sai kuma na buge wani mai acha, sun tafi da shi su kai shi asibiti, idan ya dawo nace ya same ni a gida mu yi maganar, so zamu zauna gani ga ki gashi sai mu yi maganar, sai anjima”

Ya kashe wayar gaba daya yana kallon Baturiya.

“Yan mata ya kike?”

“Lafiya kalau ya aikin?”

Ta amsa cikin rashin sakewa, shi kam sai murmushi yake abun nema ya samu.

“Alhamdulillah”

Ya fada yana kokarin cire mata dankwalin kanta gaba daya, ya fara shafa gashin kanta, sannan ya kamo hannunta ya saka a kirjinsa.

“Ba za a taya ni cire tufafin ba agajiye nake fa”

Sai da ta hade yawun bakinta sannan ta rika babbar rigarsa ta cire masa, da haka wasan ya canja salo, sai dai duk inda ya taba a jikinta sai ta ji wani iri musamman ma daya raba ta da rigar jikinta yana shafa kirjinta.

“Taso mu watsa ruwa yadda zamu jidadin bachi”

Ta dan yi murmushi ta mike tsaye, sai ya rika hannunta suka bathroom dinsa, a tare sukai wankan, yana ta labarta mata karamar haukar data same shi a lokacin da Ramlee take nuja masa honta a wayarta. Bayan sun gama suka fito sai kallon tsiraicin yake yana yabawa, tare da kai hannu ya taba inda yake jin ya masa. Kusan duk abun da Ramlee ta karantar da ita sai da ta aikata masa har abun da bata taba yi ma Faruq ba da sunan ya samu gamsuwa sai da tai ma Alhaji Haroon, sannan ta biyewa son zuciyarta ta budewa kanta babban file daga cikin manyan manyan files din zunubai. Ba shi ba ita kanta kanta ta samu gamsu irin wanda bata taba samu ba, sakamakon kayan matan da Ramlee ta bata ta sha, balle kuma shi da yai kamar zai haukace.
Nan da nan bachi yai gaba da shi, ita kuma ta tashi zaune ta daura tawul ta fito falo inda ta bar wayarta ta dauka tana dubawa sai ta samu miss calls biyu daga Fahat, jiki na rawa ta mayar masa da kiran daman can yana cikin ranta tun da ta shigo gidan take jiran kiransa. Ringing daya yai picking

“Na yi fushi yau duk ban ji muryarki ba kuma na kira wayarki na ji ta a kashe, na sake kira baki daga ba”

“Bana kusa da wayar ne, kasan idan ina kusa da wayar babu abun da zai hana ni dagawa, ni ma ai tun dazun nake ta jiran kiranka”

“Miyasa baki kira ni ba? Anyway yanzu dai bari na miki wani albishir na yi magana da Daddy, na fada masa cewar na samu mata”

Hannu ta saka ta dafe kirjinta, farinciki da faduwar gaba suka zo mata a lokaci daya.

“Da gaske? Amman me ya ce maka?”

“Me zai ce min kuwa, daman ai sun dade suna jiran ranar da zan fada musu na samu wanda nake so, even though akwai yan'uwa da ake son hada ni da su, amman ni bana son auren zumunci gaskiya”

“Allah yasa ya amince dai”

“Zai amince ma, fatar ba zan samu matsala daga bangarenki ba”

“Aa babu wata matsala Inshallahu”

“Haka nake son ji, ya kike?”

“Lafiya kalau, kai fa?”

“Ni ma kalau nake”

Sama sama take amsa masa duk wata magana da yake mata saboda bata son Alhaji Haroon ya ji tana waya da wani, ko da be nuna mata baya so ba ta san be dace tan a guest house dinta tai haka ba, domin maza suna da kishi no matter how old and young they are.
Bayan sun yi sallama ta kashe wayar ta koma cikin dakin ta hau gadon ta kwanta, ba jimawa bachi yai gaba da ita. Sai da aka yi sallah azabar suka farka kowanensu ya gabatar da wanka sannan suka yi sallah.

“Baby Fee'at me zaki ci na aika yarona ya siyo mana?”

“Shimkafa jalof”

“An gama gimbiyar mata”

Ya fada har wani kashe ido yake, ita kuma tai murmushi, tana sauraren wayar daya dauka ya kira yaronsa fada masa abun da suke bukata. Yana aje wayar ya mika mata hannunsa.

“Ta so zo nan”

Babu kunya balle tsoron Allah haka ta sake zuwa ta biye masa suka sake tarawa kansu wani babban zunubin, suna gamawa yaronsa ya kira wayarsa ya fada masa ya siyo.

“Ka aje a falo”

Ya fada masa sannan ya aje wayar ya tashi ya fita, ko da ya fito yaron ya aje abinci yayi ficewarsa, daukowa kawai yai ya shigo da shi ciki.
Jalof kawai ta bukata amman ya hado mata da farfesun kayan ciki da naman kai, ga kuma lemu mai sanyi da soyayyen naman kaza, zaunawa tai ta ci ta koshi nas, sannan ta tashi tana jindadi, rabon da ta ci abincin hotel har ta manta.
Bandaki ta shiga ta sake yin wanka ta fito, sai ya kalleta da mamaki.

“Wanka kika yi? Ai bamu gama ba, ni fa wuni ake min ba zaki koma gida ba sai dare, Ramlee bata fada miki ba”

“Aa bata fada min ba, amman tun kai ka fada min ai ya wadatar”

Murmushi yai ya bude nasa abinci ya fara ci yana yaba yadda ya sake me, da kuma irin gamsuwar daya samuna jikinta, ba karamin dadi ta ji ba domin Faruq ba mutum ne mai yaba mata ba idan ma ta gyara masa shimfidar, baya daga cikin mazan nan dake nuna jindadinsu a gurin matansu, ba dan komai ba sai dai be dauki yabon a bakin komai ba.

Kamar yadda ya bukata haka ta biyewa sharholiyarsa suka wuni suna raya sabo, sai bayan sallah Magariba ya rabu da ita tai wanka ta shirya cikin tufafinta, tana kokarin daura dankwalinta ta dauko jakarsa ya bude ya kirga dubu dari hudu ya aje mata.

“Ga wannan, sai kuma yaushe?”

Juyowa tai ta kalli kudin, a take gabanta yai mugun faduwa, sai dai bata yarda ta nuna matsa yawan kudin sun tsoratata ba sai tai murmushi.

“Sai kuma ranar daka tashi Alhajina”

“Ni kullum ai ban ki mun hadu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment