Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya fada masa komai, at first Ali dariya ya fara masa kamin ya biyo da addu'a sannan ya tabbatar masa cewar da shi za a daura auren nan.
Haka kuwa akai, kamin lokacin daurin auren ya iso garin tare da sabuwar shaddda mai masifar kyau da tsada sai kyalli take kana ganinta kasan ta ci kudi, fara ce sol zagenta ya fito kwar gwanin sha'awa, not just shadda hula da Talkamin da Ali ya siyo masa ma abun kallo ne.

Misalin karfe biyu da yan mintuna aka daura aurensa da Aminatu, ba zai iya cewa happy marriage ba ne, and it's not the sad one, sai dai ya samu kasa da farinciki marar misaltuwa, wani irin annashuwa da natsuwa suka saukar masa, fuskarsa sai haiba take kana ganinsa ka ga ango. Ko kadan fuskarsa ko dabi'arsa da mu'amalarsa bata nuna cewar baya son auren ba, domin shi kansa yana jin matsayinsa da kwarjininsa su karu.




BATURIYA POV.


Kamar yadda tai masa alkawari, a ranar ta same shi a gidansa na hutawa, suka aikata masha'arsu kamar wacan lokacin. Sai dai wannan karon bata yarda ta kai dare ba saboda tana son zuwa asibiti ganin likita kamar yadda ta fada a gida da karyar zuwa asibiti ta samu fitowa.
Wannan karon a account ya saka mata 450k a maimakon ya bata a hannu, saboda ta fada masa bata son kudin a hannu. Yadda yake santi yana yabonta har yafi na wacan karon, sai wani narke mata yake a jiki kamar zai shige ciki, daker ta kwanci kanta domin a ra'ayinsa ya so ta kwana a gidan ne, sai ta nuna masa tana a karkashin iyayenta ne za su iya zarginta idan ta kwana, sai dai bata yarda ta nuna masa cewar tana da aure ba, sai ma karyar da tai masa cewar mijinta ya rasu ya barta da yaro daya.

Misalin hudu da kwata ta fito daga gidansa, sai da ta shiga Napep sannan ta kira Ramlee ta sanar mata cewar yanzu ta fito daga gida, domin bada sanin Ramlee ta hadu da shi ba, kuma ta san idan har taji sun hadu ta bayan fage zata iya zargin Baturiya.

“To ki tsaya ta sokoto Road, zan zo a dauke ki”

“Okay toh amman karki dade dan Allah”

“Okay”

Baturiya ta sauke wayar tare da shafa cikinta tana jin irin abun da take ji a duk lokacin da tai yunkurin zubar da cikin, sai dai bata da mafitar data wuce wannan, domin idan bata zubar da cikin ba zai iya bata matsala tsakaninta da Fahat, wanda bata fatan haka.
A kusa da wani shagon mai Napep din ya sauke ta sannan ta fita ta ciro kudinsa ta ba shi taja gefe ta tsaya sai taunar cingan take tana wani kis kis kis, kamar wata tsohuwar karuwa, dan mayafin dake jikinta ma ba wani abun kwarai ba ne yadda kasan wata yar iskar budurwa haka ta fito, arzikinta daya abaya ce a jikinta ba Atamfa ko lace ba. Ta kusan minti talatin a gurin har ta fara gajiya ta fara takawa gafen titin tana tafiya sannan Ramlee ta kirata sai ta kwatanta mata inda take, tana sauke wayar wata Benz ta wuce gabanta sai kuma ya dawo baya ta faka daidai inda take tsaye. A hankali mai tukin motar ya sauke gilashin motar yana kallonta, suna hada ido sai ta sakar masa murmushi shi kam ya dade da yi ma fuskarsa ado da murmushin.

“Hajiya ke ce haka dai?”

Ta dauke kai tana fari da ido sannan ta sake kallonsa da kyau, shi din ne dai abokin Faruq da ta taba roka kudi ta WhatsApp a lokacin data saci numbersa a wayar Faruq.

“Ni ce dai ranka ya dade, ya akai ka gane ni?”

“Kyakkyawar mace irinki ai kowa ya gani zai tsaya, sai dai daga baya mutum zai tantance idan ya sanki ko akasin haka”

Ta yi murmushi.

“Ka dawo nan ne ko zuwa kai?”

“To gani nan dai, Ina zuwa haka? Ina abokin nawa ya barki a rana tana gasa ki”

“Abokin ka ai ya dade da yin tazara, duk kyau surar nan da kake gani ya zubar wata zai dauko”

“Subhanallahi, lallai da labari a bakin naki mai kyau, da zaki taimaka min da kin shigo motar nan”

“Wallahi kawata nake jira, zata zo nan ta dauke ni”

“Okay”

Ya dauko katinsa ya mika mata.

“Gashi a taimaka a kirani, duk dai na san ba a rasa number”

Ta yi murmushi bayan ta karba, sannan ta daga kai tana kallon Ramlee data faka a dayan gefen.

“Okay zan kira ka Inshallahu”

“Na gode kyakkyawa”

Ya fada yana kare mata kallon irin kallon nan na yan iska. Sannan ya rufe gilashin motar ya hau titi, ita kuma ta nufi gurin da Ramlee ta faka motar ta bude ta shiga.

“Waye wacan?”

“Wani abokin Faruq ne”

“Okay”

Sai da suka hau titi sannan Ramlee ta kalleta ta ce.

“Hope dai kin shirya?”

“A shirye nake, kawai dai ina gudun a samu matsala ne”

“Ba wata matsala, Dr KB kwararen likita ne, ba yau na saba aiki da shi ba, ki kwantar da hankalinki”

Ajiyar zuciya ta sauke tana jin kamar kar ta aikata.



________________

Inshallahu a nan zamu dakata sai kuma bayan sallah idan mai kowa mai komai ya amince mana ganin lokacin cikin koshin lafiya. Fatar Allah ya karba mana ibadar da zamu shiga ya yafe mana kurakuranmu.

Ina neman afuwarku. Sai mun hade a Book 2 bayan Sallah inshallahu. Happy Ramadam

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment