Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dace kai wannan ba, wannan ya dace kai, ban san maraici ba amman ina jin son ganin mahaifiyata ko da sau daya ne a rayuwata”

Yanayin yadda kalaman suke fitowa daga bakinsa kadai sun isar da kewar dake zuciyarsa.

“To ai Daddy yana raye, ka rika kallon dabi'unsa da kamaninsa kamar na mahaifinka, mahaifiyarka kuma sai ka nemi hotonta ka rika kalla”

Murmushi yake yana kallonta kamar ba shi ba.

“Kina da wayo Shalele, kin fahimci damuwata a take kuma kin sama min mafita duk da karancin shekarunki”

Ya fada yana kai hannu ya taba halshen gashinta. Sai ta kai hannu ta sanye gashin.

“Waya gyara miki?”

“Ya Madina, gata can”

Mikawa tai tsaye daga ita har shi suka koma kallon entrance din da Madina ta fito sanye da dogon Hijab ta nufosu da saurinta.

“Sannu da zuwa”

Ta fada a yayinda ta karaso kusa da su, sai ya daga mata kai alamar ya amsa.

“Ban san ka shigo ba sai yanzu bari na kawo maka ruwa”

“Ka ci abinci dazun ka ce min kana jin yunwa?”

Aminatu ta tambaya, sai ya kalleta ya girgiza mata kai alamar a'a. Sai Madina ta kalleshi.

“Ko na dafa maka wani abu? Zama da yunwa be da kyau”

“Ruwa kawai”

“Okay”

Ta juya da sauri sai ya kira sunanta.

“Madina...”

Ta juyo da saurin gabanta na faduwa a zatonta ko zai ce ya fasa shan ruwan ne.

“Thank Youuuuuuuu”

Suma ne kawai ba tai a gurin ba, amman ta yi mutuwar tsaye har ta kasa yarda da ita yake. Ita fa? Madina yace wa Thank you after celled her name kuma yace mata ya gode, godiya fa yake mata...? Murmushi ta sakar masa duk da kasancewar babu murmushi a tasa fuskarsa ta juya ba tare da tace komai ba ta cigaba da tafiya, tana jin kamar ta zuba ruwa kasa ta sha dan murna da jindadi, yadda ya kira sunanta ma abun alfahari ne a gurinta, sai ta ji kamar ba a taba kiran sunanta da lafazi mai dadi irin na Talba ba, lastly zai sha ruwan hannunta.
27

Ko kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*

Yana tsaye a gurin kusa da Aminatu har ta fito da glass cup dayan hannunta dauke da gorar ruwa. Tana isowa ta mika masa cup din ya karba sannan ta bude ruwan ta zuba masa, sai ya sha kadan ya mika mata cup din, ya juya ya nufi mota ba tare da yace da ita komai ba, haka ma be yi ma Aminatu sallama ba, daga ita har Madina binshi sukai da kallo har ya shiga motar ya fice daga gidan.
Sannan Madina ta kalli Aminatu.

“Idan kin gama ki min magana zan shiga dake ciki”

“Toh”

Ta juyo tana ta kallon gate din kamar ance mata Talba zai dawo, ta nufi kofar falon cikin wani irin farinciki, ta shigo falo, bata ko kula Hajiya dake falon ba ta nufi kitchen, cup din ta aje ta kara ruwan gorar hannunta sannan ta dauka ta saita bakinta a inda Talba ya sha, tana sha tana murmushi.

“Madina...”

Ta juyo da sauri ta kalli Hajiya hannunta rike da cup din.

“Na'am Hajiya”

“Waya zo yanzu?”

“Talba ne”

“Miyasa be tafi da yarinyar ba? Ba kin ce kwana biyu zata yi ba?”

Ta yi kasa da kanta.

“Hajiya gaskiya ba kwana biyu zata yi ba, kusan zata zauna a nan ne kamin abubuwa su daidaita a can gidan, yanzu haka Momy bata gidan sun samu matsala da Daddy har ya turata gida”

“Saboda yarinyar?”

Ta daga mata kai.

“Eh saboda abun da Momy tai ma Talba a kan yarinyar”

“Amman shi Talba ba yana da yan'uwa uba da uwa ba? Miyasa be kaita can ba sai a nan? Saboda mu ya raina mu ko kuma saboda me? Ke baki tunanin aje a nan zai lalata alakarku da Leila ko mahaifiyarta? Ni kaina sai ki ga abun ya shiga tsakaninmu da Hajiya dan mutuncin da muke ma mu daina”

“Bana fatar hakan Hajiya, kuma ba wai ya dauke ta kai tsaye ya ba ni ba ne, ni na bukata”

Hajiya ta yi mata wani kallo na mamaki.

“Saboda...”

“Saboda na faranta masa rai”

Ta amsa kai tsaye, sai kuma ta aje kofin hannunta ta karasa kusa da mahaifiyarta ta kama hannunta cikin yanayi na damuwa.

“Hajiya ke mahaifyata ce, na san ko ban fada ba kin fahimta, Wallahi ina matukar son Talba na rasa yadda zan yi”

Hajiya ta yi saurin janye hannunta daga rikon da Madina tai mata.

“Kul...!!! Karki yarda son zuciya ya debe ki ya kaiki ya baro karki, Aminiyarki? Kuma mijin da zata aura? Ki ce kina sonsa? To me kike tsammani zai juyo gurinki ya bar zabin iyayensa? Anya kin shirya yin takara da Leila? Hajiya bata has akan yayanta, karki kuskura dinke rigar kanki inda kai ba zai fito ba balle sauran jiki, domin wahala kawai zaki sha ki tashi a tutar babu kuma tutar kunya”

Hawaye ya cika idonta.

“Na yi iya yadda zan yi na yaki abun nan Hajiya, na yi iya yadda zan yi na kawarda idona daga Talba, amman na kasa, na yi ta hangowa kaina matsalolin dake tattare da hakan, amman zuciya na raya min zan iya dauka, na san kawance na da Leila mai zurfi ne, mun taso tare an girma tare mun zama kamar yan'uwa, be kamata na yi hakan ba, amman wata kila wannan ce kaddarata, Wallahi Hajiya ina matukar son Talba fiye da yadda Leila take sonsa”

Maganar take cikin kuka hawaye na sauko mata.

“Ki gaggauta cire shi a zuciyarki, kuma bana son yarinyar nan ta wuce yau, ki fada masa na ce ya zo ya dauke ta, daman ai na lura da take taken ki ba tun yau ba”

Hajiya na kaiwa nan ta juya ta fice, sai Madina ta durkushe a gurin ta fashe da kuka. Kuka tai sosai marar sauti sannan ta mike tsaye ta nufi dakinta tana shiga ta kulle kanta ta fara rusar kuka kamar wanda akai wa mutuwa, can kuma ya dauki wayarta ta shiga gallery wayarta ta kamo hoton Talba ta tisa a gaba tana ta kallo hawaye na yi mata sallama.
Wani irin abu take ji marar misaltuwa, da daske yanzu kam ta tabbatar sonsa take fiye da kima, tun da har sonsa zai saka ta kasa ganin Leila kuma kunnuwanta su toshe daga maganganun da mahaifiyarta tai mata. tashi tai ta shiga bandaki ta wanke fuskarta ta fito falon idonta har ya canja kala, sai da ta zauna sai kuma ta ji zaman baya mata dadi, sai kawai ta mike tsaye ta fice daga falon zuwa parking lot inda Aminatu take zaune. Tun kamin ta karaso Aminatu take kallonta da karantar yadda yanayinta ya canja daga far'a da jindadin da ta shiga da shi dazun, zuwa fitowa da damuwa da kumburarin idanuwa.
Zuwa tai ta tsaya akan Aminatu ba tare da tace mata komai ba. Aminatu ta tsayar da rubutun da take tana sauraren abun da Madina zata ce mata ammam shiru bata ce mata komai ba har na tsawo lokaci. Hakan yasa ta dago kai ta kalleta sai ta ga hawaye na sauko mata.

“Yaya Madina baki da Lafiya ne?”

Madina ta lumshe ido wasu hawayen na sauko mata.

“Ba ni da lafiya Aminatu, kuma ciwo ne da ba zan tana warke shi ba, ciwo ne da Allah ya dora min, kuma kowa ya kasa fahimtata”

“Me ke damunki?”

“Ciwon son, ciwon son wanda be san da wanzuwar son ba”

Aminatu kan kallonta kawai take ba dan ta fahimci inda kalamanta suka dosa ba, sai dai ta fahimci son wani take amman wanenen wanda be san da wanzuwar son ba? Dukawa tai gaban Aminatu kamar mai neman gafara.

“Hajiya tace dole ne na dauke ki daga gidan nan tsakanin yau da gobe, ni kuma bana son ran Talba ya bace, ban san yadda zan yi ba, daman na fada mata cewar zaki zauna na kwana biyu ne, bana son bata ran Talba, kamar yadda bana son tsabawa umarnin mahaifiyarta”

“Shine kike kuka?”

Ta girgiza kai.

“Aa abun da nake yi ma kuka dabam”

“Ki kirashi a waya Sai ki fada masa na ce bana son zama a nan”

“Zai iya zargin wani abu, bana son abun da zai nisanta ni da shi, ko ya saka ya ga kamar ni ce bana son zamanki a kusa da mu”

“Zan fada masa gaskiya ba amin komai ba”

Saaz  ta fada tana Kallon Madina, sai Madina ta hade yawun bakinta ta saka hannunta ta share hawayen da suka zubo mata. Sai da ta kira Talba sannan ta kara wayar a kunne.

“Hello...”

Ta fada bayan ya dauki kiransa jin muryarta sai yai shiru be ce komai ba, bata damu ba ta cigaba da maganar.

“Aminatu ce, ta dame ni da kuka na tambaye ta me ke damunta bata fada ba”

“Tana ina?”

Ya tambaya daga dayan bangaren.

“Gata nan kusa da ni”

Ta mikawa Aminatu wayar, sai ta karba ta kara a kunne.

“Hello”

“Shalele lafiya kike kuka?”

Ta yi shiru tana kallon Madina.

“Ko saboda na tuna miki da baya ne?”

“Aa bana son zama a nan ne?”

“Ba ki son zama kuma? Miya faru?”

“Ba komai ni dai bana son nan ka zo ka dauke ni”

“Ana miki wani abu ne da baki so?”

“Aa ni dai ka zo ka tafi da ni”

“Okay zan zo”

“Yaushe?”

“Yanzu ko anjima”

“Toh”

Ta mikawa Madina wayar. Sai Madina ta karba ta kai kunnenta.

“Hello”

“Akwai abun da akai mata ne?”

“Wallahi babu, amman ban sani ba ko ita tana da abun da take son fada maka”

Ne sake cewa komai ba ya kashe wayar yana busar da iskar bakinsa. Ali ya kalleshi.

“Ya akai?”

“Shalele ce, wai ba zata zauna a gidansu Madina ba tana son na zo na dauke ta”

Ali ya masa wani kallon na mamaki.

“Ka kaita ina?”

Sai ya daga kafadunsa ya jingina da motarsa.

“Wannan abun yayi yawa Talba? Sunan ma da kake mata ka daina domin Leila ba zata jidadi ba idan ta ji, kuma karka dauko ta daga can”

“Idan kuma ana mata abun da bata so fa? Wata kila suna musguna mata ne, ba zata iya fada ba ne a gaban Madina”

“Okay let assume that ana mata wani abun, idan ka dauko ta gidanku zaka sake maida ta saboda Daddy yace ka kawo ta? Kana ganin tunani ne mai kyau ka dawo da ita bayan Momy bata nan kuma saboda yarinyar komai ya faru?”

“Ba gida zan kaita ba?”

“To ina zaka kaita? Talba ka yi tunani please... Gidan wata gwaggonka ko yar'uwarka? No suma ba su maka kallon mai hankali da tunani ba”

Ya mike tsaye yana kallon Ali.

“Okay then zan ajeta a gidana i think babu wanda zai takura mata a can kuma ina da iko da can ai”

Ali yayi dariyar mamaki.

“Like seriously? Talba kana magana kamar baka san illar abun da zaka aikata ba?”

“Idan na kaita can fyade zan mata? Saboda gani dan'iska ko?”

“No don't take it serious, amman dai kasan idan mace da namiji suka ke be a guri daya shedan ne na ukunsu, yarinyar kyakkyawa kamar wannan, kai kuma gaka lafiyayyen mai bukatar aure? Duk abun da musulunci ya hane mu da shi ya kamata mu nisance shi, And aje wannan ma a gefe baka tunanin wasu za su iya amfani da wannan damar su yi blackmailing dinka? Kuma ya kake tunanin Daddy zai ji idan ya san ka aje ta a gidan ka yarinyar da ba matarka ba”

“Me kake son yanzu na yi? Kai ma fa kasan halin da yarinyar take ciki! Bata da kowa sai ni sai Allah”

“Bata da kowa dai sai Allah, kai din miye hadinka da ita? Kana kokarin bata alakarka da kowa saboda wata yarinyar da baka san asalinta ba? Ka bata hakuri daman ba zai yiyu mutum ya samu abun da yake so dari cikin dari ba, idan tai hakuri da zaman a can sannu sannu sai mafita ta zo mata, idan ta samu lafiya sai ka kaita gurin yan'uwanta, idan kuma ta ki yanzu ka dauke ta ka kaita gurin da yan gudun hijira suke zama ka siya mata abinci da dan wani abu mai dama ka bata”

Talba ya rumgume hannayensa yana kallon Ali.

“Karka zama marar tausayi Mana, abun da ya faru da ita zai iya faruwa da kowa, kuma ina ce kai ka gabatar da min da yarinyar nan saboda kana ganin tana bukatar taimako”

“Amman ni ban yi tunanin zata haifar da matsala tsakaninku da Leila da kuma Momy da Daddy”

“Babu matsalar data haifar, domin bata ce dole a taimake ta ba, kuma ba zuwa tai ta hada su fadan ba, daman na san damuna zaka yi da maganar Leila shiyasa bana son zuwa gurinka yanzu”

Ali yayi murmushin takaici.

“Allah sarki Leila baiwar Allah, yanzu har baka son maganarta? Ni daman shawarar da zan baka kawai ya daure ka sake yi mata maganar auren ka lallabata, idan ta aureka hankalinku zai kwanta zata samu natsuwa kai ma kuma zaka samu?”

“That's the only solution, gidan zan kaita kuma wannan ya zama a tsakaninmu, ni Wallahi kasa ma na kara jin tausayin yarinyar nan, bata da gata ko kadan”

Yana kawai nan ya nufi driver seat. Ali ya bishi da kallo.

“Ya ina maka maganar Leila kana maganar wata yarinyar? Talba lafiyarka kuwa”

“No ban da lafiya zo ka kai ni asibiti”

Ya fada bayan ya shiga motarsa sai da yai mata key sannan ya rufe, yai reverse ya ja motarsa ya bar Ali tsaye bakin kofar gidansa.
  Daga gidansu Ali family house dinsu ya nufa, sai da ya faka motarsa harabar gidan sannan ya soma jin wani yanayi na kadaici tunawa da Momy bata ciki. Ya dade cikin motar sannan ya bude ya fito ya nufi bangarensa, kamar wani bako haka ya shiga bedroom din ya zauna kan kujera yana maida numfashi, sai kuma ya dago wayarsa yana kallo kamar mai tunani, yawo ya fara yi da yatsunsa saman wayar har zuwa gurin number Madina sai dai be kira ba, kiran Amal ya shigo wayarsa saurin tashi yai zaune ya amsa kiran.

“Lil Sis”

“Ya ka yi magana da Daddy?”

Ya kai hannunsa ya shafa hancinsa zuwa kasan bakinsa.

“Yeah na yi magana da shi, kuma zai dawo da ita komai zai wuce, amman yana bukatar mu ba shi lokaci domin shi ma yana cikin bacin rai a yanzu”

“Amman dai ai zata dawo ko?”

“Eh dole ma ne Daddy ya dawo mana a ita, Ki kwantar da hankalinki”

“Toh”

Ya yanke kiran, ya mike tsaye ya fice daga idakin, motarsa ya nufa ya shiga tun kamin yai reverse ya danna horn, ko kamin ya isa gate din an bude masa.
Kai tsaye gidansu Madina ya nufa, sai dai wannan karon be shiga ciki ba ya faka bakin gate din, ya kirata a waya ya sanar mata yana waje.
Bayan kamar minti talati aka bude gate din ta fito rike da Aminatu, mai aikinsu kuma na rike da jakar tufafin Aminatu, daga cikin motar yake kallonsu har suka karaso sannan ya bude motar ya fito ya zagaya ya bude mata gidan gaba ta zauna ya rufe. Sannan ya juyo ya kalli Madina.

“Thank Youu, zan so wata rana nima n rama abun da kika yi min na karamci”

Murmushi take tana masa wani irin kallo mai cike da saukin so.

‘Ina ma zan iya buda maka zuciyata ka kalli irin kaunar da nake maka? Taya zan iya fada maka cewar kaunarka ita ce tukuicin abun da na yi maka?’

A ranta take ta wannan tunanin tana binsa da kallon da bata san tana yi ba, har ya bude back seat ya saka jakar tufafin ya rufe ya zagaya bangaren direba ya shiga ya ja motar, sai da yai horn sannan hankalinta ya dawo jikinta har ta zabura sai kuma ta lumshe ido tana maida mumfashi a hankali.
Sai da yai nisa sannan ya kalli Aminatu ya ce.

“Ana miki wani abu ne a gidan?”

“Aa”

“Miyasa baki son zama a can?”

“Ba komai”

Be sake cewa komai ba, sai dai duk bayan lokaci yana kallonta da karantar yanayinta.

“Yanzu zan kai ki gidana ki zauna, a can babu wanda zai takura miki”

“Gurin su Momy?”

Ta tambaya tana kallonsa nan da nan idonta har ya cika da hawaye.

“No gidana ni kadai ne a ciki nima kuma bana zama, yanzu ke kadai zaki fara zama a ciki”

Ta yi shiru bata ce komai ba, sai dai kuma bata gama fahimtarsa, ba mutane kamar ya? Gida ne da zata zauna ita kadai? Ko kuma da matarsa? Amman ai yace mata Leila ce matarsa kuma da alama be aureta ba. Haka tai ta jerowa kanta tambayoyi tana yi tana kallonsa har suka kusa isa gidan, each and every single kallo da take masa sai idanuwanta da na shi sun yi tarayya. Wata sabuwar unguwa ce mai dauke da manyan gidaje na Alfama, a gaban wani katon green gate ya faka, sai ya kalleta.

“Bari na bude gate din”

Bata ce masa komai ba, ya bude motar ya fita tare da keys din hannunsa ya saka ya bude gidan ya shiga ciki ya bude gate din gaba daya sannan ya dawo yaja motar ya shiga da ita ciki, kato gidane mai matukar kyau da tsari, ya fenti ko'ina da golde color, ga manyan itatauwa da ko'ina daga bakin entrance din kuma flowers har harabar gidan. A inda ya faka motarsa guri ne da aka tanada aka kawata domin aje motoci kawai, a kusa da inda ya aje motar akwai mota biyu dake lullube. Sai da ya kashe motar sannan ya bude ya fito, ya isa gurin gate din ya rufe, ya dawonya bude bangarenta ya miko mata hannunsa.

“Fito”

Ta rika hannunsa ta fito, ya rufe motar ya da taimakonsa suka isa entrance din, sai dai a nan be tsaya jiran ta taka da kafarta sai ya sake ta ta isa gurin kofar falon ya bude, sannan ya dawo ya dauke ta cak ya shiga da ita cikin falon, babu komai a ciki sai dai an ware gurin yin komai kama daga dinning har zuwa gurin saka plama. Sai dai ba a saka kujeru ba, ba a masa kwalliyar komai ba. Bedroom din ya nufa da ita shi ma ba yi masa wani gyara ba sai dai an saka gado da standing mirror.
A saman gadon ya sauke ta sai ta fara rabon ido yana karewa dakin kallo, ko'ina yayi datti alamar an dade ba a zauna a gidan ba.

“Bari na kunna miki inji”

Har ya juya sai ta mike tsaye tana jin tsoro.

“Ni kadai zan zauna nan?”

Ya juyo ya kalleta, babu komai a cikin idanuwanta sai tsoro da tashin hankalin da be san inda ya samu asali ba.

“Kina jin tsoro ne?”

Ta daga masa kai idonsa na cika da hawaye.

“Ba zan iya zama a nan ni kadai ba”

“Amman idan ba a nan ba, babu inda zan kai ki, duk inda zan kaiki za a takura miki ne”

“Ni dai ba zan iya zama a nan ba”

Ta fashe da kuka, tunani ya soma dawo mara, tana ganin kamar a nan din ma wani abun zai same ta.

“Dan Allah karka bar ni a nan tsoro nake ji sosai”

Ta fada tana ta kokarin takawa ta isa inda yake.

“Ba zai yiyu na kai ki wani guri ba, kuma ba ni da inda ya fi nan, kuma ba zai yiyu na zauna a nan ba, saboda ni ba muharramin ki ba ne, taba ki ma da nake Allah kadai ya san zunubin da zan samu”

Yana kai Aya saibta fashe masa da kuka sosai jikinta ya fara rawa, ta fara daga masa murya zata masa irin kukan da tai a lokacin da Leila ta mari Mairo. Sauri karasa yai kusa da ita ya rikata, sai ta fada jikinsa, nata jikin yana karkarwa numfashinta har rawa yake.

“Ya isa ya isa ba zan bari ki zauna a nan ke kadai ba”

Ta runtse ido sosai jikinta nata rawa numfashinta ma kamar zai fita ya bar jikinta. Sai da ya tabbatar ta samu natsuwa sannan ta taka tana a jikinsa ya zauna bakin gadon tare da ita.

“Tsoro nake ji, bana son zama ni kadai”

“Ba zaki zauna ke kadai ba, amman we have to plan, ba zai yiyu mu zauna sheidan ya rijanye mu, be kamata na yi kusanci da ke haka ba...”

Ya fada yana sauke ajiyar zuciya, sai kuma ya dago ta a hankali sai ta kalleshi idonta har ya fada.

“Zan zauna tare da ke, amman sai idan zaki yarda da wani sharadi da zan gindaya miki”

“Minene?”

Ta tambaya bakinta na rawa, jikinta na amsawa wani sanyi ya taso mata. Buaar da iskar bakinsa yai ya mike tsaye yana ganin kamar be dace yai mata wannan maganar ba, ya zata kalleshi? Ya zata dauki abun? Besides shi dai ya san ba sonta yake ba, amman dole yai haka saboda masa wa kansa mafita da kuma ita. Wayarsa ya ciro ya kira line Momy ringing biyu kamin tai na uku ta daga, da sallama.

“Talba”

“Na'am Momy kina lafiya?”

“Lafiya kalau ya kuke?”

“Momy kina ina?”

“Ina gidanmu, ina zan je?”

“Haba Momy ko da ace saki uku Daddy yai miki ai be kamata ki bar gidan nan ba, saboda kin tara mu sai dai shi ya tafi ya barki”

“Uhm... Indai kuna lafiya ai shikenan zan dan yi wani aiki”

Be ce komai ba har ta kashe wayar, sai ya juyo ya kalli Aminatu, sai kuma ya juya ya fita, kamin ya kunna injin din ya dawo har ta kawo bakin kofar falo tana hawaye, da tana dafa gini, har ga Allah tsoro take ji bana wasa ba, yanayin gidan da yadda yake shiru ga shi da girma sai yai mata kamar wacan dajin.

“Har kin kawo nan?”

Ya fada bayan ya bude kofar falon ya shigo, da mamaki ya kalleshi.

“Ba zan zauna a nan ba, dan Allah ka kai ni wani gu....gu... rin...”

Kamin ta karasa tai baya ta fadi duk kokarin da yai na riko be yi nasara ba har ta kai kasa babu numfashi.
28

MG'S COLLECTION.

"Saudatu ki shirya zamu je gaishe da su Baba, kasancewar azumi ya yi nisa ya kamata ace sun samu wani tagomashi daga arziƙin haihuwa"
Ta faɗa tana nufoni da ƙunshin kayan da ta soma zazzagesu. Galala yaro da wayau, haka na saki baki ina kallonta.
"Amma Raulatu baki kyautamin ba, haka zan je gaishe da su hannu na dukan cinya bayan ke kin gama shiryawa?"
"Ban fahimta shiri ba? Kina nufin ki ce min baki da labarin ƙayatacen wajen da suka sahalce mana yin Ramadan package?"
"Ina kenan?"
"MG'S COLLECTION mana. Wajan da ya tanadar mana da sauƙaƙiyar hanyar kyautatawa makusantamu ta hanya me sauƙi. Ingantattun kayansu masu sauƙi da kuma inganci. Ɗangin Turare, Darduma, Jallabiya, Agogo, Jaka da Takalmi. Har ma da Alƙur'ani mai girma"
"Eh lalai ki ce sa'a tafi manyan kaya, da hanau gara manau"
"Tabbas kuwa ba su tsaya iya nan ba, sun saida ingantatun kayan ɗa'a masu maida tsohuwa yarinya shar washar da ita.sannan munada set n gyaranjiki me matukar kyau yasakiyi haske meban shaawa,munasaida daddaya,kuma Akwai frams na ƙawata ɗakin amarya da uwargida"
"Tabbas zan garzaya ƴar uwa domin kashe ƙwarƙwatar idanuna"
"Za kuwa ki godemin, zaki same su a adireshinsu dake
Kunemesu ta WhatsApp number nasu 07046881166, 08062991549
kan waɗanan lambobi. Ga sauƙi ga inganci ga kuma mutuntawa.

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*

Momy ta aje wayar tana murmushin takaici.

“Waya kira?”

Hajiya Yana ta tambaya, sai Momy ta kalleta.

“Talba ne”

“Bawan Allah, bayan duk abun da kike masa har kiranki yake”

“Uhm Hajiya kenan, ke da Alhaji sai dora min laifi kuke”

“Dole a dora miki laifi mana Amina, yaron da zai girma a hannunka be san wata uwa ba bayan ke, amman ya kawo wata ki masa haka saboda kawai ba ke kika haife shi ba”

Cewar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment