Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tana kuka.

“Dan Allah kai hakuri yaro ne be san komai ba”

Ba su saurareta ba, sai suka aje yaron gefe suka halbeshi, da sauri uwar ta saka hannunta ta rufe bakinta saboda kar kukanta ya fito ita ma su halbeta.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Aminatu ta furta tana jin hawayen ya tsaya mata cak. Sai dayan ya haskata daga masa zuwa kasa.

“Ku daure wadanda”

Kamar dabbobi haka aka turasu zuwa wani gurin da babu wanda zai iya tantance shi, suka fara dauresu da sarka. Wasu kuma da igiya irin yadda ake yi ma dabbobi, idan an daure sai a saka igiyar a turke. Sauran da aka baro a garin suna da suke kan babura ba su iso ba sai kusan 6:30am daman can haka ake, idan za a saka mata to wadanda za su kura matan su zasu fara tafiya da su a gaba, su kuma sauran su biyo bayan idan sun gama na su aikin. Sai da haske safiya ya baibaye ko'ina sannan Aminatu ta tabbatar da ba ita kadai take ba, domin a gabansu wasu mazan ne aka daure masu yawan gaske, gafensu kuma akwai mata, gana ganin su kasan sun dade a gurin domin sun galabaita tufafin jikinsu sun yi datti sosai, mazan kuma wasu har gemu ya tarar musu, wasu gashin kai yayi musu yawa, a cikin wadanda suke daure akwai marasa lafiya. Sai dai wayewar gari zuwa karfe takwas an kashe mutun biyu a gaban idonta saboda sun cika tari, wai suna gudun kar su saka musu cuta, da zarar ka fara tari yayi yawa sai su ce a kashe ka kar ka saka musu cuta. A lokacin ne Aminatu ta samu kuzari da karfin zuciyar daura zanen dake hannunta ta suturta jikinta.
A wani kebantaccen guri aka fito da abinci, aka fara bin wadanda suka dade a gurin ana zuba musu 3 Spoon na shimkafa fara babu mai babu gishiri babu komai a ciki, kowa aka zubawa jiki na rawa yake cinyewa yana hadeye yawu, ba a baka abinci wadataccen, kuma baka isa ka yi magana ba. Bayan an gama da su aka biyo gurin su Aminatu aka zuba musu a hannu, ita kam rike nata tai a hannu tana ta kallon abinci kamar wanda bata san abun da ake kira da shimkafa ba. Suna zaune a gurin har rana ta fara dukansu, daga ita sai ireirenta ne suke ta murkususun zafin ranar da ya tsanata, sauran wadanda suka tarar a gurin kam da alama sun sab da zafin rana domin ko motsi basa yi. Wadansu mutanen ne dabam suka nufo inda Aminatu take suka kwance ta tare da wasu matan suka zaga da su zuwa bayan wata zana da aka kafa aka kare ta kamar katanga.

“Kwanta nan”

Ya nuna mata wani karamin duhu dake shimfide a gurin. Sai ta kwanta kamar daman can an halittota ne kawai dan ta bi umarninsa, da kansa ya kama zanenta ya cire, ya bude kafafuwanta, sannan ya kwance wando ya kwanto samanta ya ratsa cinyoyinta yana kokarin ratsa jikinta, runtse ido tai, ta ja wani dogon numfashi kamar zata shude, sannan ta fashe da kuka.
  Har cikin kwakwalwar kanta take jin yadda yake ratsa cinyoyinta yana kokarin shigarta da karfi, zabar da ta ji ne yasa ta fasa ihu, sai ya rika kanta ya buga da kasa, a take ta ji kan ya sara mata.

“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un”

Take ta maimaitawa tana tuna nasihar da Inna tai mata. Bayan ya gama abun da zai yi ya tashi, sai wani ya shigo ya saka zanenta ya shafe gabanta, sannan shi ma ya kwanta jikinta ya aikata irin abun da mutumen farko ya aikata, bayan ya gama wani ya shigo, suka suka bi layi, tun tana iya ambaton Allah tana kuka har ta kai bata iya yin komai, Wallahi sun keta haddi Aminatu tun tana cikin hayyacinta har sai da hankalinta ya bace gaba daya, babu komai a tsakanin cinyoyinta sai jini da fatar gabanta data zazzago tana rawa, bayan sun gama suka janyota kamar shara suka fito da ita suka kawo ta a inda sauran matan suke suka barta nan kwance galala sai zanenta da suka rufa mata a jikin.
  Ba Aminatu kawai sukai ma ba, kusan duk macen da suka dauko sai sun mata haka, suna yi ma mata fyade har sai sun fita hayyacinsu, ba matan kadai ba har da mazan suna keta musu haddi, sai dai ba kowa ce Daba ce suke haikewa mace kamar Dabar da aka kai su Aminatu ba, ta haka ne mazan da aka kama suke gane an ketawa mace haddi, ko kuma namiji, domin idan sun gama suna barin mutun a wulakance.


LEILA POV.

“So kike ki tonawa kanki asiri ne?”

Momy ta tambaya tana kallon Leila, sai Leila ta girgiza kai tana share hawayenta.

“To na ce ki yi shiru ya isa, babu abun da zai faru, amman wannan kukan da kike zai saka Talba ko Daddynku ya zargi wani abu, bana son tashin hankali kin sani”

Kai ta daga mata, sannan ta kai hannunta ta dauki tissue ta goge hancinta, a daidai lokacin da Momy ta faka motar a harabar gidan. Kusan a tare Talba da Amal suka fito har ma da Kabir da ya shigo bangaren ba da dadewa ba.
  Amal da Kabir suka karasa gurin Motar ban da Talba da ya tsaya jikin kofar yana kallon Momy da Leila da ta kasa hada ido da shi. Abun da Momy ta fadawa Talba shi ta fadawa Kabir, sannan ta nufo inda kofar falonta take wato inda Talba yake tsaye yana jiran karasowarsu.

“Sannu da zuwa Momy”

“Yauwa”

Ta amsa masa sannan ta ratsa gefensa ta wuce cikin falon. Yana tsaye a gurin har Leila ta iso, idonta yayi ja sosai kana ganinta ka san ta ci kuka ba kadan ba, uffan Talba be ce mata ba, bayan kallonta da yake har ta shige cikin Falon.

“Me Leila take yi ma kuka?”

Ba Kabir daya tambaya ba, har Amal dake tare da Kabir din sai da ta Kalleshi, sai dai bata ce komai ba ta wuce cikin falon. Kabir ya saka hannayensa biyu aljihu yana kallon Talba da mamaki.

“Really? Ina ce matar da zaka aura ce, miyasa ba zaka same ta da kanka ka tambaye ta damuwarta ba?”

Talba ya dan daga kansa sama ya sauke.

“Kabir Leila tana da matsala you know it”

“Tana da matsala ko kana da matsala? Simple tambaya ba zaka iya ba”

“No baka gane ba ne, ina son na san idan tana kuka ne saboda abun da ya faru da Baaba or not, saboda ban gansu da abun da Momy ta fada ba”

“So Momy ta yi karya kenan?”

Kabir ta tambaya yana masa wani kallo. Shiru Talba yai domin be san me zai sake ce masa ba. Ganin hakan yasa Kabir kai hannunsa ya tura kofar falon ya shiga ciki, Talba kuma ya sauke ajiyar zuciya sannan ya nufi bangarensa.

“Momy miyasa za ku dage sai Talba ya auri Leila ne? Ba ku tunanin kamar za ku takura masa ne?”

Momy dake kokarin yaye mayafinta ta juyo ta kalli Kabir dake tsaye bayanta.

“Ya maka wata maganar ne?”

“No kawai ina ganin kamar Talba ba sonta yake ba”

“Idan ba sonta yake ba wa yake so? Tun da kake a gidan nan ka taba jin ya yi maganar wata yarinya? Be taba yin maganar aure ba, sai da Engineer ya gabatar masa da Leila, kuma ya amsa yace yana son ta, idan kuma har baya son ta ai ba zai ce yana so ba”

Kabir ya kwanto jikin kujerar yana fadin.

“Ina ganin kamar ya amince ne saboda kar ya bawa Daddy kunya... ”

Momy ta daga masa hannu.

“Yana sonta baya sonta, saboda Engineer ya amince what so ever, ba damuwar mu bace, tun da ita Leila tana sonsa, daman shi ai be san so ba”

“Amman tsakani da Allah fa zai cutu nan gaba, kuma ita ma....”

“Kabir....!!!”

Momy ta daka masa tsawa, tare da mikewa tsaye.

“Ka daina yin abu kamar ciki daya kuka fito, kai yana tausayinka ne ko ya raga maka? Ba zaka gane hakan ba sai nan gaba, kullum maganar Talba kake baka duba yar'uwarka, baka tunanin idan aka fasa aure ita Leila zata iya shiga damuwa?”

“Kara ta shiga damuwa a yanzu, da wanda zata shiga nan gaba... Domin abu ne mai wahala Talba ya canja rayuwarsa, imagine yanzu fa ni yake tambaya miyasa Leila take kuka ba zai iya tunkararta ya tambaye ta ba”

“Zai canja, domin dole ya canja, dole ne mu gyara masa zama, idan ba haka ba zai wahala ne”

“Ko kuma ita ta wahala ba..”

Momy ta kalleshi da kyau.

“Wai Kabir ko so kake mu bar Talba ya dauko mana wata bare can daban? Bayan ga yar'uwarsa a gida?”

Ya dan tabe baki yana kallon Momy, domin ya san a yanzu ba zata fahimce ba. Daukar mayafinta tai da jakarta ta nufi upstairs rai a bace. Har zata shige dakinta sai kuma ta nufi dakin Leila ta murda kofar a hankali ta tura, sai ta same ta zauna tsakiyar gado hawaye shabe shabe a fuskarta wayarta makalle a kunne, da alama magana take da wani.

“Da wa kike waya?”

Momy ta tambaya with serious face. Sai da ta sauke wayar sannan ta kalli Momy.

“Madina”

Momy ta karasa shigowa cikin dakin gaba daya, tare da maida kofar ta rufe.

“Leila wannan sirrinki ne, duk amintar da kike da Madina karki fada mata sirrinki”

“Toh Momy”

Ta amsa tana share hawayenta.

“Ki dauka kuskure ne kowa ai yana kuskure, idan kina yawan kuka sai ki saka mutane su zargi wani abu”

Saukowa tai da kafafuwanta a kasa, tana kara share hawayenta. Momy har ta juya sai kuma ta juyo ta kalleta.

“And for the very last time, zan sake tambayarki kina son Talba?”

Leila ta daga kai.

“Wallahi ina son sa sosai Momy, ina son shi, miyasa kika tambaye ni?”

“Ba komai, ki kwantar da hankalinki”

Leila ta daga kai alamar gamsuwa, sannan Momy ta juya ta fice daga dakin zuwa dakinta. A hankali ta tura kofar dakinta ta shiga kai tsaye ta nufi gadonta ta sauke jakarta da mayafinta akai sannan ta zauna tana sauke dogon numfashi.

“Allah ka yafe mana...”

Ya furta tana lumshe ido, sai kuma ta busar da iskar bakinta.




FARUQ POV.

“Ina son anjima zan tafi kasuwa”

Ya juyo ya kalleta yana kokarin saka agogon hannunsa.

“Gurin me?”

“Tufafi zan siyo, kuma zan siyawa Sultan ma”

“Karki je ko'ina, kuma karki siyawa dana komai da kudin da ban san inda suka fito ba”

Yana gama fadar hakan ya saka talkaminsa ya fice daga gidan gaba daya. Wani dogon tsaki ta ja ta murguda masa baki.

“Wallahi sai na je, wato bayan talauci har da hassada tana damun talaka”

Ta fadi zaune saman kujera rike da wayarta tana tabe baki, Data ta kunna ta shiga facebook, sai da ta fara duba notifications dinta, ta shiga comments tana duba yadda maza ke yaba surarta kowa da yadda yake yaba sabon hoton da ta dora, murmushi take tana ta bin comments dinsu da like har cikin zuciyarta take jindadin yadda suke yabonta. Bata da fargabar komai domin ta yi blocking din Faruq da duk wani dan'uwanta na kusa da ta san zai iya ce mata ta gyara ko ta daina, daga familyn Faruq har nata yan'uwan. Bayan ta gama karanta comments din ta leka inbox dinta, sakonni ta tarar da yawa cikin har da bakin fuskar da basu saba mata magana ba, kamin ta yi ma mutun reply sai ta duba profile dinsa ta duba abokansa aikinsa hotunansa da kuma inda yake zaune, da zarar ta ga alamar mai rufin asiri ne sai ta sake masa idan kuma ta ga sabanin haka sai ta yi blocking dinsa a take.

“Ibrahim”

Ta furta sunan dake profile dinsa sai kuma ta shiga duba hotunansa, da inda yake aiki kana ganinsa kasan mai abun hannun ne. Komawa tai inbox din ta amsa masa da thanks akan yaba kyauta da yai. Kasancewar yana online a take ya maido mata da amsa.

“Babu godiya a tsakaninmu, wani ma yai rawa balle dan makadi”

“Uhmm haka kace”

“Haka ma yake, wani ya bawa mana matarmu balle kuma ni”

Ba shiri ta zaro ido gabanta ya fadi.

“Ya san ni kenan, ko kuma dai wasa ce”

Ta fada tana tashi tsaye.

“Matarku kuma?”

Ta tambaya domin tantancewa.

“Eh mana ba matar Faruq ba ce Rafi'ah?”

“Ka san Faruq ne?”

“Sosai ma tare muka yi makaranta da shi”

Ta kara zaro ido.

“Na shiga uku”

“Gaskiya abokinmu yayi dacen mata, kina da kyau”

Ya rubuto mata, sai ta koma ta zauna tana kokarin kwantar da hankalinta.

“Da alama shi ma shegen ne”

‘Allah sarki, ashe kun yi karatu tare’

Ta amsa masa.

‘Eh sosai ma, na zo har aurensa ai, kuma ko lokacin da kika haihu na so na zo ban samu dama ba, ya Babyn?’

‘Lafiya Kalau, ya naka iyalin?’

‘Ni kam da saura har yanzu ban yi aure ba, sai na samu mai kyau irinki’

‘Hmmm kana koda kyau na kamar gaske’

‘Da gaske ne mana, Faruq be taba fada miki kina da kyau ba’

‘Uhmmm’

Shine reply din da tai masa sannan ta kashe data ta aje wayar, ta nufi inda Sultan yake yana bachi ta tashe shi ta bashi ragowar kazar jiya ita ma ta ci ta koshi sannan ta shirya masa ita ma ta shirya ta dauki jakarta da mayafi ta riko hannun Sultan suka fito daga cikin gidan, sai da ta kulle gidan sannan ta nufi makontansu ta bada ajiyar Sultan ita kuma ta kama hanyar titi, ba yau ta saba satar hanya ta fita ba, wani lokacin idan ta tambaya ya yana ta ma fita take wani sa'in kuma bata ma tambayarsa, gashi idan ya fita baya dawowa sai dare, inda ba wani abun ya bijiro ba. Ko ma ya dawo ya tarar bata nan sai dai yayi hakuri ya danne abun a zuciyarsa.

“Malam tsohuwar kasuwa”

Ta fada bayan ta tsaya da mai adaidaita, kai kawai ya daga mata, sam bata lura da kofatun dake kafunsa ba ta shiga, sai da ta gyara mayafinta da face mask din dake fuskarsa sannan ta aje jakarta gefe. Kamar ance duba ki gani tana kallon bayan kansa sai ta ga kan kamar na tsuntsu har wani rawa yake kamar zai fado ga bayansa duk gashi kamar dabba.

“Malam tsaya na fasa zuwa...”

Ta fada da sauri tana runtse ido, sai mai Napep din ya faka gefen titi, tsabar tsoro yasa bata tsaya daukar jakarta ba ta fita da sauri tana haki, tana fita mai Napep din ya cigaba da tukinsa kamin ta rufe ido ta bude har ya bacewa ganinta, baya tai da sauri tana kara zari ido.

“Innalillahi”

Bata karasaba ta ji kamar ta taki abu, sai ta juya da sauri ta kalli Mahaukacin dake bayanta ya tara uban gashi ga tufafin jikinsa duk datti, wani irin tsalle ta daka ta ranta ana kare, wani irin gudun bala'i take mahaukacin na biye da ita shi ma da gudunsa. Wani shagon dake titi ta nufa kamin ta isa mutanen dake gurin suka watse da gudu domin sun san mahaukaci ba ya yi ma mutum da sauki, ita kanta bata taba sanin tana da gudu ba sai a yau, tana karya kwana ta samu wani gida ta shige ta turo kofar gidan da karfi ta rufe, tana ta haki kamar numfashinta zai fita. Mutanen gidan suka fito da sauri suna kallonta.

“Lafiya?”

Sun tambaya domin kama tai musu da mahaukaciya, kanta babu dankwali balle mayafi ga kafafuwanta babu talkami sai uban datti da suka yi, gashin kanta ma dake fake har ya yamutse, gumi sai sauko mata yake.

“Mahaukaci ya biyo ni....”

Ta fada daker tana haki, idonta har wani zurfin wahala sukai.

“Subhanallahi tsokanarsa kika yi?”

Dayar ta tambaya tana kokarin gyara goyonta, kamin ta amsa mata suka ji aka dukan kofar da karfi.

“Zai iya balla mana kofa fa”

Baturiya ya kauce jikin kofar da sauri ta dawo cikin mutanen tana kallon kofar.

“Ban tsokane shi kasuwa zan je sai mai Napep...”

Bata karasa ba tai shiru tsabar fita da numfashinta yake da karfi.

“Wallahi haka yake, ranar fa tun daga rijiyar zaki ya dinga bin Marwa har unguwa uku”

Baturiya ta kalli mai maganar, daman tun daga jin yanayin maganarsu ta ji ta banbanta data Zamfara, domin su kananci suke yi, gashi kuma an fadi rijiyar Zaki da unguwa Uku, wanda ta san ba a Zamfara unguwar take ba.

“Baiwar Allah nan kuma wani gari ne?”

“Kano... ”

“Kano....?”

Ta maimaita tana zaro ido, sai ta fadi a gurin zaune ta fashe da kuka.




________

Na zo muku da albishir guess what? A have alot of kayan mata masu kyau gaske, akwai na infection, akwai maida tsohuwa yarinya, akwai set din da ake hadawa for matan da basa gane kan mazajensu, akwai na mallaka kala kala, muna kaza mai magani, tantabaru, akwai kaza mai Yasin, akwai na mallaka sirrine mai karfin gaske. Ina masu son zama madubi a gurin mazanje su? Ina matan dake cewa na gwada ban dace ba? Muna da gumba da garin magani kala kala da na tsarki ga Humra da turarunka kala kala amman fa na kayan mata. Akwai dan wata bakwai, muna da kwalli mai karfin gaske (Mujarrabun sadidan) Akwai na farin jini for yan mata da Zaurawa. Akwai wanda ba a bawa mai kishiya, akwai na mazajen da kr neman mata, muna da rantse baki da kishiya, muna da back to virgin, for yan matan da kaddara ta fadawa, ko Zaurawan dake son zama yan mata, akwai jigida mai kyau, muna da man ayu 100% natural. Akwai na maza masu hannun Dambe.
Hajiya sai n gwada akan san na kwarai, ba cuta ba cutarwa, duk wanda kika siya sai kin dawo.

Ga masu bukata za su iya tuntubar number na 08036126660 zan saka miki a mota na aika miki har inda kike da yarda Allah.

Serious Buyers Please idan ba ki shirya ba kar mu batawa juna lokaci.
*💔 BAKAR WASIKA 💔*


By Khadeeja Candy


Page -9️⃣

If you're not living around these people, you will never know what they are going through, fiye da haka ma yana faruwa, kawai dai Allah ya tsare mu su kuma yai musu mafita.
Tun daga jin sunan Labarin kun san abun da ya kunsa. Ban san abun da readers suke so ba, idan an saka kudi da luxury life sai ace writers suna bude idon mutane, and when we're talking about reality kuma ba mu tsira ba, anyway if you don't like the story you can quit it.

                  ***        ***        ***

Har past 12am Talba yana zaune bangaren Momy doing nothing, haka nan kawai yake jin yanayinsa sai a hankali. Idan zaka tambaye shi damuwarsa ba zai ce maka ga matsalarsa ba. Mikewa yai tsaye ya isa gaban plasma ya kashe sannan ya wuce kitchen domin samu abun da zai sakawa cikinsa, rabonsa da abinci tun da rana, ko lunch din Momy ta hada be ci ba. Tea ya fara hadawa kansa sannan ya bude freezer dake kashe ya dauko cake ya kunna oven ya saka shi a ciki, sannan ya dauki tea ya rike a hannunsa yana ta kallon harabar gidan ta windows kitchen din, ko ina haske ne kamar rana.
Juyowa yai a hankali jin kamar shesshekar kuka a falo, aje cup din dake hannunsa yai ya tako a hankali zuwa bakin kofar kitchen din ya tsaya. Sai ya hango Leila zaune a bakin stairs din sanye da kayan bachi riga da wando sai kuma safar dake kafarta, kanta ba dankwali sai hawaye take tana kallon wani bangare na falon, sam bata lura da shi ba har sai da ta juyo tana cigaba da rera kukan a hankali. Suna hada ido sai tai sauri share hawayenta ta dauke kai sannan ta mike tsaye ta juya a hankali zata hau stairs din.
Har tai rabi ban da  kallon mamaki babu abun da Talba yake mata.

“Leila...”

Ya kira sunanta kamar wanda baya son magana, tsayawa tai cak gabanta na mugun faduwa, domin har ga Allah bata dauka yana zaune a falon har lokacin ba, da b zata fito daga dakinta ba, juyowa tai a hankali sai dai bata yarda ta kalleshi, sanin kanta ne ba zai tambaye ta me take yi ma kuka ba, kiran sunanta kawai da yai ya isa ya sanar da ita cewar tambayar damuwarta yake.

“Na yi mafarkin tsoro ne...”

Ta fada tana wasa da yatsun hannunta, bata tsaya jiran abun da zai ce mata ba ta juya da sauri ta haura sama. Da kallo ya bita har ta bace masa sannan ya juyo ya dawo cikin kitchen din, mamaki karara a fuskarsa.

‘Mafarki tsoro?’

Ya maimaita aransa, idan mafarkin tsoro tai me zai saka ta fito a nan ta zauna ita kadai?

“Ko dai saboda ni ne?”

Ya tambayi kansa yana kokarin kai hannunsa ya dauki tea, domin ya san abun da zai tashi hankalin Leila ba karami ba ne, and bayan shi ba ya ji akwai wani abu da zai saka Leila ta yi kuka ko ta shiga damuwa. Kamar wanda baya son bude baki haka ya kai cup din a bakinsa ya soma sha a hankali, dayan hannunsa ya saka a aljihu yana kallon oven din sai dai gaba daya tunaninsa ba a nan yake ba.
Sai da ya sha rabin tea sannan ya kashe oven din ya ciro cake din daya dumama ya aje, ya dauki tissue ya saka a hannunsa sannan ya fara daukar cake din yana ci. Bayan ya gama ya kashe wutar kitchen din ya fito falo ya kashe wutar sannan ya wuce bangarensa. Shirt din jikinsa ya fara cirewa wanda hakan ya bawa kyakkyawar surarsa da murdaden kirjinsa bayyana, a kafadarsa ya dora rigar sannan ya nufi wani madaidaicin daki dake hannunsa na dama, a hankali ya murda kofar ya bude ya shiga, kai tsaye ya nufi teburinsa ya ja kujera ya zauna ya bude system dinsa yana duba sakon da Jahid ya turo masa na adadin kudin da za a kashe wannan watan na gidan marayu.

“Okay”

Ya furta sannan ya rufe system din ya saka hannunsa aljihu ya ciro wayarsa ya kunna data ya shiga WhatsApp.

‘Zan rubuta maka cheque gobe, after that, ka bincika abun da yan gudun hijira suka fi bukata ka kirga ko nawa za akashe na mutun 300’

Bayan ya gama rubuta masaya kashe data ba tare da ya duba sako ko daya da yake shigo masa ba, balle har ya amsa. Fitowa yai daga dakin ya nufi Bedroom dinsa yana shiga ya aje rigar dake kafardarsa a muhallinta ya cire jean din jikinsa ya nufi bathroom ya jika jikinsa da ruwa ba tare da ya saka sabulu ba yai alwala ya fito, sai da ya tsane jikinsa sannan ya nufi closet din ya dauko kayansa na bachi.
Wando kawai ya saka domin abu ne mai wahala ya kwana da riga komai tsananin sanyi, sai dai ya rufa da bargo, riga na cikin abun da ke takura shi ta hana shi sakewa idan zai yi bachin dare.


BATURIYA POV.

“Wallahi tun da nake a rayuwata ban taba zuwa Kano ba, ni fa ban taba barin Zamfara ba”

Ta fada tana fyace hancinta daya cika da majina tsabar kukan data sha.

“To ya akai kika zo nan?”

“Agwagwa da buje na shiga nace ya kai ni tsohuwar kasuwa sai na ga kansa yan rawa kamar dan tsuntsu, bayansa kuma da gashi shine nace ya sauke ni yana sauke ni na fito da sauri, sai wannan mahaukacin ya biyo ni”

“Minene kuma Agwagwa da buje?”

Ta kalli wanda tai tambayar da idanuwanta da sukai ja abun ka da farar mace.

“Keke Napep”

“Oh Allah na wata kila aljanine ya dauke ki, kin san fa ance suma suna yin Napep din”

“Ga zahiri na gani, wata kila da bance ya tsaya ba da yanzu na tsinci kaina a Russia ko Iraq”

“Lallai kuwa abun na su ba wuya, to yanzu kina da waya a tare da ke?”

Sai a lokacin ma ta tuna da jakarta, domin wayarta da kudinta har da makullin gidanta suna cikin jakar.

“Na shiga uku Wallahi jakata na cikin napep din aljani nan kuma ya tafi da ita”

A take ta fashe da sabon kuka, domin ta san samun wata wayar ma agareta yanzu abu ne mai wahala.

“Subhanallahi, to kina da number wani akai ko mijinki ko Baba?”

“Babana ya mutu sai dai mijina kuma shi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment