Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Be jidadin abun da Leila tai mata ba, sai dai be nuna mata ba.

“Okay amman yanzu bari ki fara cin abinci ki samu kuzari, sannan muje ki yi sallah okay?”

Ta daga masa kai.

“Zulai zata zo ta tura ki bathroom ki wanke bakinki sai ta fito da ke ki ci abincin ki yanzu”

“Aa bana so yanzu wannan zata zo ta fara min masifa, kuma zata hana su yi min komai”

Ta fada kamar zata fasa kuka.

“Kina son na tura ki?”

Ta daga masa kai, sai ya mike tsaye ya dauketa ya dora a wheelchair din. Ya turata da kansa har bathroom din ta wanke bakinta.

“Zaki yi fitsari?”

Ta girgiza masa kai alamar aa. Sai ya turo ta ya fito da ita sai da suka kawo gurin kofar sannan ta kula da kofar a balle take, sai dai bata ce komai ba tana ta kallon hanyar har ya fito da ita falon. Iyakar abun da ta sani Leila ta rika kanta tana ja da karfin tsiya, bayan baka bata san me ya faru ba, sai ganinta tai ta farka daga bachi.

“Waya kwantar da ni kan gado dazun?”

“Ni”

Ya amsa mata a takaice sannan ya tura kujerar har gurin dinning, babu kowa a falon daga shi sai ita sai katon Plasma. Da kansa ya shiga zuba mata abincin, sannan ya mika mata. Sawun takun talkami da taji ne ya saka ta waiga ta kalli Upstairs din sai ta hango Madina da Leila suna saukowa a tare, suna hada ido da Leila tai saurin maida kanta kasa cike da tsoro. Kallo daya Talba yai musu ya dauke idonsa, kusan a tare suka kalli juna, ba Leila kadai ba har Madina ta ji zafin ganin Talba na zubawa Aminatu abincin da kansa, sai dai ta dannewa zuciyarta bata yarda ta nuna ba, duk da kasancewar Leila ta fada mata komai daya faru dazun.

“Amman wannan wulakancin ne, haba Talba? Taya zaka zuba mata abinci a irin plate din da muke cin abinci? Kuma ka kaita har gurin dinning?”

Madina ta yi saurin rike ta.

“Haba Leila miye haka?”

“Ai dole na yi magana, dazu fa har rumgumar ta yai...”

Tana kokarin kai hannu ta taba Aminatu data make guri daya Madina ta yi saurin rike ta da karfi.

“Leila miye haka wai?”

“Wallahi sai ta bar gidan nan, na rantse da Allah ba zata zauna a nan ba”

Ta fada da karfi kamin ta kwalawa Momy kira tana ihu. Uffan Talba be ce mata ba, ko kallonta be yi ba sai aikin zubawa Amina ruwa yake a cup. Kamar da gangan Madina ta saki Leila ta karasa gurin dinning.

“Karki taba yarinyar nan”

Furucin da yai mata ne yasa saka ta tsaya cak, domin bata ji wasa a muryarsa ba kamar yadda fuskarsa ma bata nuna wasan ba. Aminatu ta yi saurin sakin plate din abincin dake hannunta idonta cike da hawaye. Hango Momy na saukowa tare da Amal da Kabir yasa Leila ta dauki ruwan da Talba ya zuba a cup ta watsawa Amina.

“Haba Leila miye haka?”

Madina ta fada tana zaro ido tare da saka hannayenta ta rufe baki.

“You should apologize ki bata hakuri yanzu nan”

Talba ya fada yana nuna mata Aminatu.

“No Leila ta yi kuskure, amman ba zata bata hakuri ba, you're just hurting her”

Kabir ya fada, Momy na karasa kusa da ita ta maida Leila.

“Ya isa haka Talba, ba zan yarda ka wulakanta Leila akan wata banza ba”

“Momy kin san abun da ta yi”

“Be dame ni, amman ta duka ta bawa wannan musakar hakuri ne ba zata tayi ba!”

Nan da nan jikin Aminatu ya fara rawa, Talba ya kalli Momy.

“Wannan ba daidai ba ne Momy”

“Miye daidai tana yar riga kace ta bawa wata banza hakuri? Wai gata ka fi leila ne ko kuma miye?”

“Kuma na rantse da Allah ba zata zauna a gidan nan ba, Wallahi Momy sai dai ku zaba ni ko ita...!”

Leila ta fada tana buga kafa a kasa. Leila ta ji wani irin dadi, komai ya faru kamar yadda take so, duk da kasancewar bata yi zaton da wuri haka komai zai faru ba, daman ta zo gidan nan kawai saboda Leila ta kirata tana kukan rumgumar da yai ma Amina, sai dai a yanzu komai ya yafi kamar yadda take son ya tafi. Da sauri ta nufi Aminatu dake kuka taja kujerarta.

“Madina ki kyale yarinyar nan a gurin nan?”

Sai ta girgiza ma Momy kai.

“Dan Allah Momy ki gafarce ni, be dace ku yi wannan fada a gaban yarinyar nan ba”

Bata jira abun da Momy zata sake cewa ba, ta tura Aminatu zuwa corridor, a azaton Momy Madina ta yi hakan ne saboda bata son su yi fadan a gabanta kasancewar su yan'uwa.

“Abun da kake ba kyautawa ba ne, Talba, be kamata ba, ko a dazun ka rumgume yarinyar nan a gaban Leila kuma kasan dole zata ji ba dadi ba, and now kana kokarim feeding dinta for what”

Talba ya nuna Kabir da yatsa.

“Don't you dare tell me what is right and wrong, don't you dare judge me, this is my life waye kai da zaka kalubalanci abun da na yi?”

“So baka isa ka kawo wata a gidan nan just to hurt my sister in front of us? And now ba zamu zabi wata akan Leila ba, take her away”

Wani irin kallon kallo suke tsakanin shi da Kabir ko wane zuciyarsa ta kawo kamar ya rufe dan'uwansa da duka yake ji. Daker Talba ya samu hade numfashinsa ya kalli Leila dake tsaye sannan ya nufi corridor da zai sada shi da dakin da Aminatu take ciki. Bakin kofar dakin ya tsaya yana kallon Madina dake rumgume Aminatu tana share mata hawayenta da dankwalinta, ita ma tana kuka.

“Dan Allah ki yi hakuri ki daina kukan nan, ban taba rasa kowa ba, amman na fahimci yadda kike ji, akwai ciwo sosai ki kwantar da hankalinki Inshallah Talba ba zai bari ayi miki komai ba, ni kuma zan kula da ke kamar kanwata Inshallah”

Yadda take hawaye sai ka rantse da Allah kukan gaske take, zaka yi zaton da gasken gaske take tausayin Aminatu. A badini kuma tana yin hakan ne saboda ta ji kamshin turaren Talba ta san yana tsaye bakin kofar dakin ko ma cikin daki.
Aminatu na hada ido da Talba ta saki Amadina tana kuka.

“Dan Allah ka kai ni inda yan gudun hijira, ko wani gurin, bana son fada bana son fada dan Allah karka yi fada da su dan Allah...”

Karasowa yai cikin dakin ya risina gabanta yana kallon fuskarta, magana yake son yi mata amman ya rasa ta ina zai fara.

“Idan zamanta a nan zai kawo matsala, zan iya tafi da ita gidamu, Mamana bata da matsala kuma zan iya kula da ita, kamin Momy da Leila su sauko”

Madina ta fada muryar na rawa, a ranta tana ala ala ya amince, a hankali Talba ya juyo ya kalleta.

“You can trust me. Wallahi ba zan mata komai ba, tare na da Leila ba zai saka na cutar da wani ba, yarinyar nan ta cancanci rayuwa mai kyau...”

A nan ma Talba be ce mata komai, ya juya yana kallon Aminatu.

“Excuse us Madina”

Murmushi ne ya cika fuskarta, saboda ya kiran sunanta, kusan tun da take da Leila ba zata iya tuna rana daya ta taji sunanta a bakinsa ba.
24

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa

*Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*

“Kar abun da Leila tai ya dame ki, tana da zafi ne, amman a sannu zata fahimta ta daina”

Aminatu ta saka hannu ta share hawayenta, wasu a sauko mata.

“Komai be da sauki a rayuwar duniya, komai ka sara yana da wahala ka samu abun da zai maye maka gurbinsa, rayuwarmu da ta ku akwai banbanci, kuma tana da gaskiya, ni yar kauye ce marar gata wanda bata waye a komai ba, ba kamar ni ba talaka kuma yar kauye, be kamata na zauna a mazauninsu ba, ko kuma na ci abincin a inda suke so, muna da banbanci mai nisa a tsakaninmu”

“Ban taba ganin wannan banbanci ba, ban taba jin cewar Leila ko ni mun fiki ba saboda dukiya, ita ma kuma kurciya ce ke janta”

“Idan ita kurciya ce, Momy fa?”

Yayi shiru kamar mai tunanin abun da zai ce mata.

“Momy tana goya mata baya ne saboda bata son bata kunya a gaban mutane, ko da ni zan yi fada da Leila wani lokacin zata iya shigar min ta yi ma Leila fada”

Ta yi shiru hawaye sai sauko mata suke.

“Kalleni”

Ta dago, sai idonta ta sauka cikin nasa, a karon farko ta ji kwarjininsa ya cika sa, akwai kalama a fuskarsa kamar yadda natsuwarsa take kara fito da siffar zatinsa.

“Zaki iya zama a gurin Madina ko kuma na kai ki wani gurin dabam?”

Ta kawarda fuskarta tana tunani.

“Ban sani ba, wata kila ita ma iyalan gidanta kamar na ka ne, ba lallai ne su karbe ni, amman ka min wani alkawari dan Allah”

Kallonta yake, ita ma kamar tasan ba zai tambayeta minene sai ta fada tana yawo da idonta a dakin.

“Ka min alkawarin, zaka nema min gurin da zan zauna cikin yan gudun hijira yan'uwa, ko kuma ka nema min wasu daga dangina kamar yadda kai alkawari”

Yayi murmushi kadan.

“Kina tunanin yan gudun hijirar suna shan dadi ne? Suna wata irin rayuwa ne mai ban tausayi da tada hankali, abun da za su ci ma wahala yake musu, ba su da muhalli, wasu na fakewa a kangon makaranta ko tsohon gida, wasu kuma suna zaunawa inda yan'uwa ne, amman su suke ciyar da kansu, wasu bara suke su ciyar da kansu, wasu kuma surfe suke su yi wankakau ko wani aikin karfi sannan su samu ciyarda kansu, idan sun shiga wani gurin za a nuna musu kyara ana kiransu da mayu, sadakar ma sai wanda ya ga Allah ya ga Annabi yake ba su, ba rayuwa suke mai dadi ba, ya kamata ki daina wannan tunanin”

“Ba jindadi nake so ba a yanzu, jindadi abu ne mai wahala a gareni, so nake na samu sakewa ina sonnna zauna da irin mutanen dake rayuwa kamar yadda nake, mutanen da basa kyamata, ina ma kasance tare da mutane masu irin rayuwata, wadanda suka san zafin rashi...”

“Ina daya daga cikinsu ai”

Ya fada yana mikewa tsaye. Sannan ya nufi kofar fita wa kusa da kofar ya samu Madina ta jingina tana jiran fitowarsa.

“You should go and talk to your parents first, idan sun amince sai ki sanar da ni”

Ta dago a hankali ta kalleshi.

“Iyayena basa da matsala, amman zan je na sanar da su, sai dai ban san inda zan same ka ba”

Tsayawa yai kallonta sannan ya mika mata hannunsa, tana ganin haka ta fahimci wayarta yake nufi sai tai saurin cire password din wayar ta mika masa. Yana saka number ya mika mata wayar sai ta karba da hannu biyu tana godiya.

“Na gode”

Be kula ta ya juya ya koma cikin dakin, sai ta yi tsalle ta dire a hankali ta kai wayar a hancinta tana shinshinar kamshin turaren Talba kamin ta kai wayar a kirjinta. Sannan ya fito corridor tana boye jindadinta, Kabir ta samu tsaye yana fada Leila.

“Kishi ba hauka ba ne, kowa ya san akwai zafi amman ya kamata ki rika controlling kanki, idan ma wani abu ne ai shi yai miki ba ita ba”

Madina dai bata ce komai ba har Talba ya turo Aminatu kam wheelchair ya fito da ita falon, kanta a kasa tana tsoron kallon mutane, shi ma kuma kofar fita daga falon kawai yake kallo. Momy da Leila har ma da Kabir na tsaye ban kallonsa babu abun da suke har ya fita da ita.

“Aikin banza mtsssss”

Leila ta fada tana jan tsaki. Sai da Madina ta leka windows ta hango ya tashi motar yana kokarin yin ribas sannan ta kalli Momy ta ce.

“Momy zan tafi da yarinyar nan saboda anan zata haifar da fitana ne kawai, kuma idan tana tare da ni zata nisanta da shi ba kamar yanzu ba”

Momy ta kalli Leila sannan ta kalli Madina.

“Ke iyayenki za su yarda ta zauna ne?”

“Eh zan musu bayani kuma ai kin ga ba dadewa za ta yi ba, na dan lokaci ne”

“Shi zai yarda ki tafi da ita?”

“Eh na masa magana, amman yace min na fara zuwa na yi magana da iyeyena”

“Okay ba matsala”

Momy ta amsa ta tana kallon yanayinta, sai ta yi ma Leila sallama tana fadin sai sun yi waya. Momy ta bita da kallo har sai da ta fice sannan ta kalli Leila ta ce.

“Ki yi hankali da yarinyar nan, hankalina be kwanta da ita ba, idan b munafurci ba ta ya za ayi fada akan yarinya kuma ke ki ce zaki dauketa ki kaita gidanku?”

“Momy da sani na tai, sai da tai shawara da ni, plan ne muke hadawa, Madina bata da matsala, ba yau na santa ba fa Momy”

“Ki dai yi hankali, kuma ki san irin sirrin da kike fada mata”

Kabir ya mike tsaye yana kallon Leila.

“I hope plan din da kike hadawa ba cutar da yarinyar nan zaki yi ba, ba na goyi bayanki ba ne saboda ki samu damar wulakantata, no na yi hakan ne saboda na san kina jin kishin abun da Talba yake yi ma yarinyar nan”

“Ba wanda za a cutar kawai zan nisanta ta da shi ne”

“Dauketa za ki yi?”

“Haba Kabir? Idan ma na dauke ta zan yi ai shi ya ja mata...”

Uffan Kabir be sake ce mata ba ya fice falon. Ita ma tashi tau ta nufi upstairs aka bar Momy zaune tana kallon Leila har ta haye.

TALBA POV.

A entrance din ya bar ta, sai da ya fara isa ya bude motarsa sannan ya dawo ya saka hannunsa ya dauke ta ta saka a motar ya dawo ya dauki wheelchair din ya saka a bayan motar, kana ya zagayo ya rufe side dinta ya shiga driver seat yaja motar suka ce daga gidan.
A hankali yake tuka motar yana kallonta, ita kuma tana ta kallon titi, da motocin dake kai da kawo har suka isa super market din da yake siyen chocolate da sweet da yake kaiwa a gidan marayu, fakawa yai a harabar sannan ya fita ya shiga ciki be dade ba ya fito ya dawo cikin motar, yaja suka dauki hanyar by pass.
Har suka isa aka bude musu gate din ya shiga ciki ya faka motarsa Aminatu bata kalli inda yake ba, sai da ya bude motar ya fito, sannan ya zagayo gefenta ya bude mata.

“Ina kujerar?”

Ta fada tana kallonsa.

“Ya kamata ki fara takawa”

Ta bata fuska tana turo baki gaba kamar zata fashe da kuka.

“Akwai zafi idan na taka”

“Idan baki taka ba, then yaushe zaki taka kafar? Kullum haka zaki yi ta zama fa”

“Ni dai ba zan iya takawa ba”

A dole ya bude ya dauko mata kujera ya aje mata.

“Ta so ki zauna”

Ta kalli kujera ta kalleshi sai ta kara bata fuska.

“Akwai nisa ai sai na yi taku har hudu”

“Idan ba zaki taka ba, zan tafi na bar nan”

“Sai na yi ta zama a nan ina ruwana”

“Ni ma ina ruwana ki yi ta zaman to”

Ya fara takawa kamar gaske, sai ta fashe masa da kuka.

“Ashe kin iya kuka... Ya miki kyau”

Ya fada ba tare daya juyo ba, hakan yasa dole ta fito da kafafuwanta ta taka kadan.

“Wash wash wash...”

Tana fada tana hannunta rike ta ganbun motar har ta karasa gurin kujerar ta zauna.

“To na zauna”

Ta fada cikin kuka. Sai ya juyo ya kalleta yai murmushi.

“Daga yau ba za a sake turaki a keke ba”

“Ni kuma ba zan yi tafiyar ba, ai saboda kasan akwai ciwon a kafata ne, idan kai ne Allah kadai ya san yadda zaka yi kuka”

This time around murmushi yake mai sauti. Ya dawo kusa da ita ya tsaya.

“Wato kukan zan yi, an fada miki ni rago ne kamar ke?”

Ya fada yana kai hannu ya lasa kumatunta, sai ta kara turo bakin gaba. Murmushi yai ya bude back seat din ya dauko abubuwan da suka siyo ya dora mata saman jiki sannan ya koma bayanta ya fara tura keken.

“Yaran da zan nuna miki yanzu, basa da uwa ba uba, ba yan'uwa ba kowa, amman sun zama kamar iyalai a nan, kuma suna farinciki, ba dan yau yana ranar karatu ba, suna makaranta da yanzu sun zo sun zagaye mota suna murna da ganina”

“Waya kawo a nan to?”

“Na yi miki karya?”

“Aa ka fada min gaskiya dai, Babba ba ya karya karya ba kyau”

Yayi murmushi.

“Ni na kawo su a nan”

“Amman da zaka yi karya me zaka ce min?”

“Sai na ce Babana”

“Babanka ba ya rasu ba?”

“Yeah tun ina ciki mahaifina ya rasu, amman Daddy ai shi ne Babana gatan da yai min ko da ace Babana yana da rai ba zai min shi ba”

Ya fada sannan ya turata har gaban ajijiwansu, yaran na ganinsa suka  taso ta gudu suna masa oyoyo.

“Uncle Uncle”

Yayi murmushi ya duka yana tambayar lafiyarsu. Aminatu na kan kujerar tana kallonsu cike da burgewa, irin yadda yake sake musu ya saka suka saba da shi sosai har taba jikinsa suke wasu na tsokanarsa. Mikewa yai tsaye ya dawo kusa da Aminatu ya dauki ledar sweet din ya bude ya mika mata.

“Ki ba su”

Ta kalleshi kamin ta kai hannu ta dauka ta fara mika musu duk wanda ya karba sai ya koma gefe, wasu kuma sai su dawo a kara musu, shi ma ya dauki daya ya fasa ya saka a baki, bayan sweet din ya kare ya bude chocolate ya bata tana dauka tana ba su, sai ga murmushi a fuskarta. Sai da ya kare sannan yai musu sallama suka koma ciki, shi kuma ya turo Aminatu har gurin Motarsa.

“Yanzu ma ke zaki shiga da kanki”

Ta bata fuska.

“Wallahi akwai zafi tafiyar dazun ma daurewa kawai na yi”

“Yanzu ma daurewa kawai zaki yi”

“Yanzu ba zan iya daurewa ba”

Ta fara matsar hawaye sai yai murmushi kadan ya ciro wayarsa dake ring, sai da yai kamar kar ya dauka sai kuma yai picking.

“Ya akai?”

“Talba... Kana ina?”

Ya kalli harabar gurin.

“Ina wani guri”

“I need to see you akwai magana mai muhimmanci daya kamata ka sani”

“Idan na dawo zan kira ka”

Yana fadar hakan ya kashe wayar ya kalli Aminatu dake masa kallon tsoro.

“Momy ce?”

“Momy kike tsoro? Abokina ne”

“Wannan likitan?”

Ya daga mata kai, sannan ya duka ya saka hannunsa ya dauke ta ya saka a front seat ya rufe, ya nade kujerar ya saka ta a bayan motarsa, ya zagayo zai shiga motar wayarsa ta sake yin ringing, sai da ya zauna sannan ya duba wayar sai ya ga bakuwar number. Picking yai ya kara a kunne sai Madina ta yi masa sallama.

“Assalamu Alaikum, Madina ce”

“Ina ji”

“Ka kawota gidanmu Hajiya ta amince”

“Mahaifinku fa?”

“Shi ma ya amince, baya gidan amman na yi magana da shi ta waya”

Be sake cewa komai ba ya kashe wayar. Ya yi ma motar key yai reverse suka fice daga gidan. Be yi wata doguwar tafiya ba, suka iso gidansu Madina, horn daya yai aka bude masa gate din ko kamin ya faka harabar gidan Madina da kanenta biyu mata sun fito da saurinsu suna tarbonsu, ko wanensu fuskarsa a sake alamar suna maraba da zuwanta.

“Ina fatar dai kina ra'ayin zama, bana son na cilasta ki, kuma zan rika zuwa kullum ina dubaki, idan kin ga wani abu na daman ki fada min”

Ta daga masa kai, sannan ya bude motar ya fita kamin ya zagaya ya bude gefen da Aminatu take, har Madina ta ta rumgume Aminatu a gabansa, hakan da tai kuma ba karamin dadi yai masa ba, domin a ganinsa ko ba komai ta nuna mata rashin kyama. Da kansa ya fito da wheelchair din ya aje ta nesa da inda motar take, ita kuma ta riko Aminatu suka ta fito.

“A matso da kujerar”

“Aa ki taka a hankali, ki isa gurin kujerar, ya kamata ki rika takawa”

“Akwai zafi sosai”

Ta fada kamar zata fashe da kuka, Madina ta yi dariya.

“Aiko kara ki saba, domin ni ba zan yarda ki yi ra zama kan kujera ba kullum dole ne ki fara tafiya”

Da wash wash ta karasa gurin kamin ta zauna har ta kagu, Madina ta fara tura kujerar Talba kuma yana dagawa kanenta dake gaishe shi kai, sai kuma yai tsaye sai har sai da suka karasa gurin kofar falon sai ta juyo ta kalleshi ya sakar mata murmushinsa mai kyau, Madina ta ji gabanta yayi mugun faduwa, sai yanzu ta tabbatar Leila ta fita juriya, domin bata jin zata iya jurewa Talba ya rika kula Aminatu a gabanta, saboda shi, yanzu ma ba dan tana neman kusanci da shi ba da ba zata yarda ta karbi Aminatu ba.

“Maraba maraba”

Hajiya ta fada da fuskar dake nuna dole Madina tai mata ba dan tana so ba.

“Ina wuni”

“Lafiya Kalau”

Tana amsawa ta kalli Madina sai kuma ta dan yi murmushi.

“Yanzu bari mu fara cin abinci sannan ki yi wanka, ki huta”

“Ina son zan yi sallah”

“Okay”

Ta turata har zuwa dakinta.

“Nan zamu zauna, nan ne dakina so yanzu mun zama mu biyu”

Aminatu dai bata ce mata komai ba, har gaban gadonta ta kaita ta fita ta debo mata abincin da aka girka shinkafa da miya. Da kanta tai feeding dinta sannan ya kaita bandaki ta hada mata ruwan wanka ta fito ta baro ta a ciki, bayan ta gama ta koma ta turo ta suka fito, wata doguwar rigar ta dauko mata ta taimaka mata ta saka sannan ta nuna mata gabas ta bata hijabi.
Haka tai ta wuni tare da ita a dakin tana kunna mata tv can kuma ta jata da hira.

Da dare ma a tare suka ci abincin dare, sannan ta dauko mata daya daga cikin tufafin na kwana ta bata ta saka. Sannan ta dauko wayarta ta rike.

“Ko na kira miki Talba ki masa sai da safe?”

Aminatu ta yi shiru kamar mai tunani.

“Aa”

Sai Madina ta kai hannu ta dafa ta.

“Ai kara ki saba da gaisawa da shi, ai zai jidadi kuma zai ce kin damu da shi, kamar yadda shi ma ya nuna miki kulawa”

“Toh...”

Sai Madina tai murmushi ta nemi number sa ta kira shi.

“Idan ya dauka ki ce kina son ki ji muryarsa ne kamin ki kwanta”

“Toh”

Wayar ta yi ringing ta katse be daga ba, tasan Talba baya son hayaniya, hakan yasa bata sake kira ba.

“Be daga ba wata kila baya kusa da wayar”

Aminatu ta daga mata kai sannan ta kwanta saman gadon. Tara da yan mintuna Madina ta sake kiran Talba, rejecting call din yai ya kira jiki na rawa ta dauka.

“Hello”

“Madina bana son yawan kira”

“Ka yi hakuri dan Allah, ni ma ban so kiran ba, Amina ce tace tana son na kira mata kai”

Yayi shiru be ce mata komai ba, sai ta saka wayar a hands-free ta mikawa Amina.

“Fada yayi?”

Amina ta tambaya kamin ta karba.

“Ban yi fada ba, Shalele ba ki kwanta ba?”

“Eh”

“Akwai wata matsala ne?”

“Aa kawai ina son na ji muryar ka ne kamin na kwanta”

Yayi murmushi ya.

“Shalele sleep tight”

“Miye haka nan?”

“Ba ki san abun da hakan ke nufi ba?”

“Eh ni bana jin turanci”

“To za a koya miki, ki kwanta yanzu ki yi bachi da kyau”

“Toh sai da safe”

“Sai da safe”

Yanke kiransa yayi daidai ta sauke ajiyar da Madina tai yi, domin har ga Allah bata dauka tana kishin Talba har haka ba sai yanzu. A take yanayinta ya canja, ta kwanta ba tare da tace cewa Amina komai ba.
Washe gari a dakinta ta kawo mata komai a karyawa, sannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment