Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yasa naje ko na siyen fili na samu ai na samu”

“Haka ne, amman kudin motar zuwa can fa?”

“Har cin abinci da komai zan iya kashe 20k haka Yusufa ya fada min, kuma yace ana kwana uku kamin a samu isa, wannan kudin da ban biya haya ba zan iya cire na mota ciki sai kuma sauran kuma na siya ma Rafi'a abinci na bar mata kamin mu tafi kuma mu ga abun da Allah zai yi”

“Toh Allah ya shige maka gaba”

“Ameen”

Ya fada yana mikewa tsaye sai kanwarsa ta kalleshi.

“Ya Faruq ance fa rame ake shiga, ko. Kwanan baya na ji ance rame ya rusga da wasu”

Murmushi yai.

“Allah shi ke tsarewa ai, ku dai kui ta mana addu'a”

“Toh Allah ya tsare, yasa arzikinka na can”

“Ameen ya Rabb”

Ya amsa sannan yai musu sallama ya fice, ko da ya isa gida har ta gota, a bude ya samu kofar gidan, sai ya shiga da sallama ya maida kofar ya rufe sannan ya shiga falon, sai ya same ta tana waya sai dai ganinsa yasa ta sauke wayar ta kalleshi.

“Sannu da zuwa”

“Yauwa, ya gidan?”

“Alhamdulillah”

Sai ta tashi ta nufi inda abincinsa yake ta dauko masa ta aje masa tare da ruwa.

“Ina Sultan?”

“Yayi bachi”

Ta amsa sannan ta zauna kusa da kujerar da yake zaune, kallonta yake har ta zauna din, gaba daya yau ta canja, daman can fara fes amman haskenta and yau ya karu sai wani sheki take tana ta kamshin hummura mai tsada. Dauke kansa yai ya maida dubansa gurin abincin data aje masa yana hade yawu, rabon da wata mu'amalar aure ta shiga tsakaninsu har ya manta, domin bata yarda idan ma ya neme ta, idan ya matsa sai tace ga ciki ba zata iya ba, shi kuma baya son yi mata da karfi hakan yasa ya dauke mata kai ta wannan bangaren ba dan baya bukata ba sai dan ba zai iya ja'inja da ita ba.

“Rafi'a ina ta shawara da kuma neman zabin Allah”

Ta kalleshi da sauri a tunaninta ko zai fada mata cewar daya faga cikin aikin da yake Applying ne wani ya fito.

“Na me? Aikin ka samu ne?”

“Aa, ina shawarar zuwa nijar ne?”

Wani irin yatsine fuska tai kamar wanda tai arba da abun kyama.

“Nijar fa kace? Ba dai gurin ginar zinari ba ko?”

“Can mana”

“No nonono, Wallahi ba zan yarda ba, so kake ka ja min abun magana a gari? Ace mijina ya tafi gurin ginar zinari? Talaucin har ya kai nan? Aa Wallahi ba zaka je ba”

“Shi zuwa ginar zinari zunubi ne? Wace irin magana ce wannan nan?”

“Kana tafiya za a ce talauci ya matsa mana har ka bar gari ka tafi nema nijar, ka ja min abun magana, kawaye na mazajensu daga masu aiki a kamfani sai banki sai ma'aikatun gobnati, ni kam ba zan iya ba Wallahi”

“To sai na fasa saboda ke nan? Ni na riga na yanke shawara, kuma na zo na fada miki ne saboda na baki hakkinki”

“To Wallahi ba zan yarda ka je ba, Wallahi sai dai ka sake ni ka tafi na san ba mu tare”

Dubanta yai irin duba na mamaki.

“Rafi'a me kike son ki zama? Ke kin isa ki yi ma kanki arziki ne, da abu kadan zaki fara cewa talauci?”

Sai ta mike tsaye domin ya fahimci da gaske take.

“Wallahi Faruq, na rantse da Allah ba zaka tafi nijar ginar zinari da aurena ba, sai dai idan tafiya ce zaka yi ta har abada, wanda babu dawowa, wai kai baka da zuciya ne? Baka san Annabi ya faku ba, na gaji da abun kunya Faruq, na gaji, aurena dole ne? Ni kadai ce mace a duniya nan ne? Ba zan iya ba, ga danka nan yayi wayo amman ka kasa saka shi makaranta, wannan da zan haifa ma na san dan taure zaka yanka min”

“Sai ki saki kanki ai, ba saki ba? Ba zan saki ba kuma sai na tafi nijar din ki mutu, ina hakuri ne dake kawai saboda Mama da kuma mahaifinki”

Ya fada yana mikewa tsaye, sai ta sa gabansa.

“Wato ka fito gurin bakar tsohuwa ta kitsa maka abun da take so a kai...”

Bata karasa ba ya wanke mata fuska da mari sai da ta fadi zaune. Ta fashe da kuka.

“Faruq ni ka mara?”

“Har abun da yafi mari zaki samu, matukar iskancinki da rainon wayo ya kai ki ga taba mahaifiyata, ai ko da ba ta hada komai dake ta cancanci girmamawa saboda tana sarakuwarki balle tana a matsayin kanwar mahaifinki”

“Ita bata san da zumuncin bane ta barka kana ta cutar da ni? Ba zan iya ba, na ce bana so ka sauwake min mana”

Har yayi kamar Ya bude baki yace na sakeki sai kuma wata zuciyar ta hana shi. Be sake kulata ba ya shiga bedroom din, bakin gado ya zauna yana kallon Sultan dake ta bachi ya kai hannu ya shafa shi, makomar dansa yake zubawa idan har ya sake ta rayuwarsa zata zama abun tausayi, domin zaman zai zame masa a tsakanin gida biyu, gidan mahaifinsa da kuma inda Mahaifiyarsa. Tsabar bacin rai da tunani be ci abincin ba ya kwanta kusa da dansa, Baturiya kuma ta kwana a falo.
Washe gari waina ya siyo musu abun kari kasancewar aljihunsa da dan nauyi irin na masu nema yau da gobe, bata gaishe ba tun da garin Allah ya waye, sai dai hakan be hana shi ce mata zai fita ba, da harara ta bishi babu Allah ya tsare balle addu'ar alheri.

“Allah yasa kai hadari ka mutu..”

Ta fada bayan ta ji karar rufe gidan, sannan ta tashi ta bude wainar ta zubawa Sultan, ita kuma ta nufi wayarta ta dauka ta kira Fahat, ringing biyu ya dauka.

“Fee'at”

Sai ga murmushi a fuskarta kamar ba ita ba, bata kula da Sultan ba ta cigaba da wayarta tana masa kalaman soyayya kamar yadda shi ma yake mata. Sun kusa awa daya suna abu daya sannan sukai sallama tana masa kiss a wayar, duk abun da take Sultan na kallonta sai dai ita bata lura da hakan ba. Fitowa tai waje ta fara gyara gidan domin Ramlee ta fada mata karfi goma za su hadu. Ko da tara tai Baturiya ta gama komai har ta shiga ta yi wanka. Sai da ta shirya sannan ta kai Sulta makota ta dawo gidan ta kara daukar wasu kayan matan ta sha daman Ramlee ta nuna mata wadanda zata sha idan tana kusan tafiya.
Tara da rabi kiran Ramlee ya shigo wayarta, jiki na rawa ta dauka kamar ba ita ce ta gama jin tsoro ba a jiya.

“Madam hop kin shirya”

“Na shirya, ke kawai nake jira”

“Haka na ke so, ba wasa ganin nan nima na kusa karasowa”

“Sai kin iso”

Ta aje wayar tana murmushi, ita ma kanta ta san ta yi kyau, sai kamshi take zubawa kamar sabuwar amarya, kamin Ramlee ta iso ta shafa hoda ya kai sau shida, turare kan ba adadi irin feshin da take masa.
Tana jin sallamar Ramlee ta dauki wayarta da jakarta ta fito waje da sauri.

“Wow yanzu kika fito da sunanki n Baturiya, amman mutumen idan ya ganki sai ya rude”

Baturiya ta yi dariyar jindadi.

“Da gaske”

“Wallahi kuwa, sam sam baki dace da Faruq ba, ke din matar manya ce, amman fa karki fada masa cewar kina da aure domin na ce masa ke din bazawara ce”

“Ke ma dai da wata magana, ya za'ayi na fada, Allah dai ya sa inda zamu je ba public place ba ne, domin akwai wadanda bana son su gan ni”

“No guest house dinsa ne, muje dai kar mu bata lokaci”

“Amman kin san me? Idan na fita da kwaliyar nan haka ina kamshi mutanen unguwa za su fara saka mana ido”

“To ya zamu yi? Ke dai ina ruwanki da mutane ne wai?”

“Aa bari dai a saka hijab da nikab idan na je can sai na cire a motarki”

“Haka yayi yi sauri”

Ta juya ta koma dakinta da sauri ta dauko katon Hijab ta saka tare da niqab sannan fito ta rufe gidan.
Tun daga yanayin ginin unguwar da shuke shuken zaka san cewa unguwar manyan mutane ce, a gaban wani katon gate suka faka Ramlee tai horn Mai gadin ya leko tai magana da shi sannan ya bude mata ta shiga, a harabar gidan tai fakin ta ciro wayarta ta kira shi.

“Alhaji mun iso”

“To yayi Kyau Hajiya Ramlee a barta ta dan huta gani a hanya, garin sauri ma na kade wasu amman dai na gama komai zan iso yanzu”

“To yayi Alhaji sai ka iso”

Ta aje wayar sannan ta labartawa Rafi'a abun da ya faru da shi.

“Kuma ki sake jikinki ki kwashi arziki, domin yana son ki Wallahi na fada miki hotonki kawai ya gani amman duk yabi ya rufe balle kuma ce ya yi arba da ke”

“Inshallah ba zan baki kunya ba”

“Yayi kyau, haka nake son ji, yanzu mu shiga ciki na nuna miki falonsa sai n fito na bar ku ku sha shagalinku”

Ramlee ta fada tana murmushin jindadi. Sai Baturiya ta cire Hijab din da Niqab ta kai hannu ta bude motar wayarta tai kara.

“Allah yasa ba mijin nan naki ba ne”

Cewar Ramlee tana tabe baki, fasa fitar Baturiya ta yi ta ciro wayar daga jakarta ta duba.

“Shi ne kuwa, ban san mi zai ce min ba, ko kuma ya dawo gida ne oho”

“Karki dauka dan Allah zai wargaza mana shiri ne”

“Ai ba zan dauka ba”

Ya fada tana kallon wayar dake ta ringing har ta gaji ta tsinke, sai gashi ya sake kira sai dai wannan karon ta ji gabanta ya dan fadi.

“Kai wannan miji na ki da ci yake, gaskiya ki kashe wayarki kar ya zo yana damunki da kira ya lalata mana shiri”

“Wallahi kiran Fahat kawai nake jira, saboda yace zai kira ni anjima bana son na kashe wayar ya kira ya jita a kashe zai damu ne”

Ramlee ta mata wani kallo.

“Da alama dai shi ma dan hannu ne”

“Aa Wallahi shi ai son aure yake min da gaske, na nuna Masa ni Budurwa ce”

“Amman ke yar banza ce, ya zaki yi da Faruq?”

“Haba Ramlee kina min fatar zama da shi? Ai rabuwa zamu yi, kin ga idan ya sake ni ina zubar da cikin nan na cika idda zai na yi aurena”

“Kina ganin Faruq zai sake ki ne?”

“Dole na idan na bude masa shikashikan rashin mutunci ai dole ya sake ni”

“To dan fa ki yi yaya da shi? Ai kin san za a bincike ki musamman yayan manyan mutane basa aure zai sun zurfafa bincike”

“Ai idan na fita zan bar Sultan a gurin Faruq ne, ba da shi zan je ba, kuma shi Fahat din ai yace min a Lagos yake aiki, kin ga zamanmu a can zai kasance ba a nan ba, zan iya boye komai”

“Ki ce kema kin iya bala'i

Sai duk suka saka dariya, kiran Faruq ne ya sake shigowa wayar, wannan karon wani tsaki taja ta kashe wayar gaba daya.




TALBA POV.

Sai da yai sallah azahar sannan ya karaso gida, tun kamin yayi fakin idonsa suka sauka akan Leila dake zaune a daya daga cikin kujerun da suke balcony rike da wayarta sai cup din lemu a gaban kujerarta tana taunar cingan har wani kis kis take. Yayi kusan five minutes a motar sannan ya bude ya fito ya nufo inda take zaune ya zauna ba tare da yace da ita komai ba, hakan ya bata damar dauke kai daga gefen da yake ta maida wani gurin tana cigaba da taba wayarta.

“Can we talk?”

Ya fada ba tare da ya kalli inda take ba, sai ta juyo ta kalleshi.

“Ta fada maka ba ni ba ce ba kenan?”

Shi ma juyowa yai ya kalleta fuska ba yabo ba fallasa.

“Daddy ya damu dake ne i want us to talk”

“Da gaske?”

Sai ta mike tsaye ta dauki cup din lemun ta wuce ta bar masa gurin. Tana kokarin kai hannu ta danna door bell din kofar falon sai ga Kabir ya fito, ko kula shi bata yi ta shige, da kallo ya bita kamin ya juya ya kalli Talba dake kallon harabar gidan, har lokacin tunanin Aminatu yake. Karasa Kabir yai ya zauna a inda Leila ta tashi.

“Ya jikinta?”

“Da sauki...”

Talba ya amsa ba tare daya kalleshi ba.

“Ka yi magana da Leila ne?”

Ya girgiza masa kai.

“Wani lokacin baka sanin damuwar mutane idan baka kusantar su, you see yan gudun hijirar nan da kake gani a hanya wasu a fankon guri, suna da labaruka masu taba zuciya”

“Ita ma tana daya daga cikinsu ne?”

“Tana daya daga cikinsu ne?”

“Yeah they raped her, killed her Father, mother suka gona musu gida, suka kashe yayyunta and raped her mother in front of her, labarinta akwai tsoro da taba zuciya, yanzu haka she can't walk saboda wahalar data sha gurin mutanen nan, and bata da kowa kuma tana bukatar kulawa sosai”

Talba ya fada cikin yanayin dake nuna zuciyarsa ta tabu sosai da labarin Aminatu.

“You know a lokacin da kake raina ni ni'imar da Allah yai maka, wasu da yawa suna can suna neman kadan, a yadda na fahimta now yanzu farinciki take bukata, saboda ya cire rai daga shi har tana neman kashe kanta, and Ali and wannan likitan sun fada min abun nan ya taba ta”

Kabir ma saurarensa yake cike da tausayin Aminatu duk da kasancewar ba taba ganinta ba, sai dai ya san waye Talba duk abun da zai saka shi a damuwa ko tunani ba abu ne kadan ba.

“Yanzu a wane matsaya take”

“Tana samun kula a asibitin, amman babu mai kwana a inda yake kuma kasan da ace tana uwa ko wata yar'uwa a raye zata fi samun kulawa, tana jin tsoro sosai har magana take idan tana bachi, and likitan ya fada mim idan tana yawan damuwa zuciyarta zata iya bugawa, yarinya ce karama kamar Amal, bata san inda zata je ba”

“Haka ne mutane suna cikin hali, sai dai idan baka shiga cikinsu baka sani”

Talba ya mike tsaye yana saka hannunsa aljihu. Ya nufi bangarensa, Kabir ya bishi da kallo yana murmushi.

LEILA POV.

Tana shiga dakin ta dauki wayarta ta kira Madina ta fada mata abun da ya faru, a ciki har da kudinta na son ta fadawa Daddy cewar ta fasa auren Talba.

“Anya idan kika yi haka baki yi kuskure ba? A Maimakon ki ta wannan haukan ba kara ki nuna masa kina son yarinyar ba ko da a munafunce ne”

“Lallai Madina baki gama sanina ba, ke a tunaninki zan iya share miji ko saurayi da wata? Har sai na nuna ina son ta bayan duk abun da yai min, ni fa na san ba sonta yake ba kawai yana amfani da ita ne ya cusa min bakinciki?”

“Idan har haka ne, ke me zai hana ki yi amfani da abokinsa ki rama abun da yai miki?”

“Waye kenan?”

“Ali mana, ta hanyarsa ma zaki iya tabbatarwa idan Talba yana sonki da gaske”

“Kin kawo shawara, tabbas zan iya rama abun da yai min ta hanyar Ali”

“Yes amman ina fatar hakan ba zai janyo matsalar da zata hana a dauke ni aiki ba, kin san fa ina nan ina ta jira”

“Aiki ai dole a dauke ki, bari anjima ma zan yi ma Daddy magana, ki kwantar da hankali cikin kwana biyun nan za a dauke ki aiki”

“Alhamdulillah, na gode sosai yau zan yi kwana farinciki ko ba komai ai hakan zai kara kusantar da alaka ta da ku”

“Haba ai mun fi haka dake, zan kira ki anjima”

“Okay thank you”

Ta sauke wayar tana murmushi, har cikin ranta take jin cewar Madina ta sama mata mafita na bata shawarar ta yi soyayya da Ali, ta san idan tai haka zata Talba sosai kuma zai gane irin zafin da take ji ita ma.
20

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa


*Khadeeja Candy*

*Khadeeja Candy*


Ko kin san kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin sa kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya domin siye ko sari ku tuntu Ramla incense ta wannan number +234 703 839 2576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa


*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min! Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


Zaunawa yai saman gadon yana goge ruwan jikinsa. Sannan ya kai hannu ya dauki wayarsa dake ringing.

“Ali ka dame ni fa”

“Ai dole na dame ka Talba, ka bawa Leila hakuri?”

“Na yi maka kama da wanda zai yi wannan?”

“Seriously Talba baka kyauta ba, kuma ya kamata ka bata hakuri, be kamata alakarku ta lalace saboda wata bare can da baka san inda ta fito ba”

“Leila ta yi abun da yake bani mamaki ne, so dole na zargeta akan halin da yarinyar nan ta shiga, lastly karka sake min maganar bada hakuri”

“Really kana ganin ka kyauta kenan? And me yarinyar ta fada maka?”

Can sama sama Talba ya fada masa abun da Aminatu ta fada masa.

“Yanzu ina yarinyar take?”

Ali ya tambaya yana sauke ajiyar zuciya.

“King's and queen's hospital”

Cewar Talba sannan ya mike tsaye yana shafa fuskarsa.

“Labarinta be taba ka ba?”

“Kai ya taba ka kenan?”

“Yeah, duk wani mai imani ne dole ne labarin yarinyar nan ya taba shi”

“Kar tausayinta ya saka ka manta da yadda kake da Leila, tsakani da Allah yarinyar nan tana sonka kuma tana azabtuwa da irin abun da kake mata”

“We can talk later”

Yana fadar haka ya kashe wayar ya jefa saman gado, sannan ya shiga dan karamin dakin da aka tanada domin ajiyar tufafi ya saka riga da wando na suit blue sannan ya fito ya dawo gaban madubi yana duba kansa. Komawa yai ya dauki turare ya murza a hannunsa na fesawa kuma ya fesa a jikinsa. Sannan ya dauki abun da ya kamata ya dauka ya fice daga dakin yana kokari saka wayarsa aljihu.
Ya fito bangarensa ya nufi bangaren Momy sai dai turarensa ya riga shi isa bangaren Momy saboda karfin kamshinsa, yau kam a bude ya samu kofar falon Zulai nata aikin mopping tana ganinsa tai saurin risinawa ta gaishe shi, sai dai be ma kalleta ba balle har ya amsa mata. Motsin da yaji a kitchen ne yasa ya nufi kitchen din, sai dai be karasa ciki ba saboda ya hango Leila a tsaye kusa da Momy da alama yau kamar a tare suke hada abun karyawan.

“Momy ina kwana?”

Momy ta juyo ta kalleshi, sai ta amsa fuska ba yabo ba fallasa.

“Lafiya Kalau an tashi lafiya?”

“Alhamdulillah”

Ya amsa sannan ya juya da zimmar ficewa, sai Momy tai masa tayin abun kadyawan.

“Ba zaka tsaya ka karya ba?”

Kamar zai ce a a sai kuma ya juyo.

“Idan an gama a saka min a kula zan tafi da shi”

“Okay”

Momy ta amsa sannan ta dauki abu ta shiga zuba masa dukan abubuwan da suka hada, yana ganin haka ya fice daga kitchen din, ko da ya fito Zulai ta gama mopping din sai ta bude masa kofa da sauri, ya fice yana addu'ar fita daga gida, sannan ya nufi inda Motarsa take fake, tun kamin ya karasa ya danna remote din hannunsa motar tai kara ta bude kanta daga lock. Hannunsa ya mika ya bude motar ya shiga ya zauna yana warming dinta, yana kokarin yin reverse da Motar, Mairo da fito da gudunta rike da kwadon abinci ta nufo inda yake, after yayi reverse din ta bude gidan baya ta saka masa sannan ta rufe motar tana masa addu'ar Allah ya tsare.
Kamin ya isa gate ya daga wayarsa ya kira Daddy, domin ba al'adarsa ba ce ficewa ba tare da ya gaisa da Daddy ba, sai idan Daddy na bachi ko kuma baya garin, ko kuma wani ne, shi kadai ne ke saka shi fita ba tare da yayi ido biyu da Daddy ba. Har ya hau babban titi Daddy be dauki wayar ba, as usual idan ya kira sau daya ba a dauka ba zai sake kira ba.
Sai kawai ya aje wayar ya cigaba da tukinsa, a gogon hannunsa ya duba a daidai lokacin daya faka motarsa harabar asibitin, sannan ya bude motar ya fito ya bude baya ya dauki abinci ya nufi ciki, akwai jama'a sosai a asibitin ba kamar jiya da shekaran jiya ba da suke ranakun hutu, yau kam Monday mutane sai hada hada suke, kamar bako haka ya tura kofar dakin ya shiga. Zaune ya same ta tana ta kallon kofar kamar mai jiran shigowar wani, hawaye suna mata zuba, sai da ya maida kofar ya rufe sannan ya karasa kusa da ita ya aje abinci.

“Ya jikinki?”

Sai ta juyo ta kalleshi, ta kasa amsawa.

“Ya sunanki?”

Ya tambaya yana cigaba da kallonta.

Nan ma bata ce komai ba, sai ya matsa kusa da inda aka aje file dinta ya bude yana dubawa Ramlat Ibrahim ya ga an rubuta.

“Ramlat...?”

“Aminatu...”

Ta amsa tana kallon wani wajen tare da kai hannu ta share hawayenta.

“Mamana, ba ki gajiya da kuka?”

Sai ta sake kallonsa a karo na biyu tana murmushin da ya fi kuka ciwo.

“Baka san yadda nake ji ba, yanzu ba ni da mai damuwa da ni, babu wanda ya rasa kamar yadda na rasa komai a lokaci daya, yanzu bara zan koma a titi, ina zan kwana? Me zan ci ko na ci babu ruwan kowa, ni kadai na rage.... ”

Kamar fada take maganar tana kuka mai karfi, sai kuma ta saka hannayenta ta rike kanta tana lumshe ido. Kallonta kawai Talba yake har ta fara yunkura sauka saman gadon.

“Zauna karki sauka”

Dagowa tai ta kalleshi, sai ta zauna din kamar yadda ya bukata ta rumgume kanta tana hadiyar yawun bakinta da ya bushe. Dukawa yai ya fara bude abincin yana dorawa a saman gadon da take sannan ya duba fruits din daya kawo mata jiya, domin tun jiya da ya kawo mata fruit din ya fita be sake dawowa ba.

“Baki ci komai ba?”

Ya tambaya yana kallonta. Sai ta daga masa kai.

“Ina jin yunwa amman bana iya cin komai, kuma hannuna baya kaiwa”

Be sake ce mata Uffan ba, ya bude mata abinci.

“Zaki iya cin wannan?”

Ta kalli abinci sai ta girgiza masa kai, alamar aa domin komai na duniyar baya burgerta. Zai sake yin magana likitan daya karbeta ya shigo dakin rike da takardu da wata Nurse a bayansa.

“Yauwa, daman ina son magana da kai”

Likitan ya fada sannan ya mika masa hannu suka gaisa. Sai kuma ya shiga duba Aminatu.

“Kina jin wani ciwo ne?”

“Kirjina yana ciwo sosai ksmar zai cire, kuma idanuwana ma suna ciwo suna kai kayi”

“Ki daure ki rage tunani, da yawan kuka damuwace ke saka haka, ita kuma damuwa bata da magani kamar a gusar da abun da yake rai”

Ya fada yana rika hannunta ya saka mata abun hauna bp ya aunata, bayan ya gama ya kalli Talba dake tsaye ya ce

“Tsakani da Allah yarinyar nan na bukatar kulawa, akwai maganin daya kamata ace ana shafa mata a kafa kuma ana bata lokaci zuwa lokaci, and tana yawan kuka wanda hakan yana kara mata damuwa, kamata yayi ace akwai wani abu da zai dauke mata hankali, ka ga ko shiga bandaki ya kamata ace akwai mai rikata domin jiya ma a nan tai fisari
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment