Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ce kee zata kalleni amman bayan haka bata yin komai, na sha jera sunaye ina kiranta da su amman bata taba min wata alama da zan gane sunanta ba, kuma kafanta ya kumbura wanda hakan ke nuna ta yi tafiyar da ta wuce kima kuma ta taka abubuwa da yawa gaskiya yarinyar tana bukatar taimako”

“Ta ina ya kamata na taimaka? Irin mutanen kamata yai ace gobnati tana daukar nauyin maganinsu fa”

“Wallahi kuwa ni ma abun da nake fada kenan amman sai kaga an barsu kara zube ba a kula su. Yanzu dai tana bukatar a duba lafiyar duka jikinta, a kula da kafafuwanta, private part dinta dai yana samun sauki sai dai da zata samu wanda zai kula da ita da zata fi samun sauki”

Ali na kaiwa nan ya mike tsaye.

“Zo muje ka ganta”

“No ba sai na ganta ba, kasan akwai mutane sosai a gurin nan”

“Haba dai irin abubuwan nan suna karawa mutum tsoron Allah, Allah kadai ya san halin rayuwar data shiga, ni ba abun da ya fi bani tsoro kamar rashin maganar ta, kuma gashi har yau babu wanda ya taba zuwa nemanta, and bata kallon mutane idan zan shiga inda take har na yi abun da zan yi na gama ba zata kalleni ba sai idan na dauko allura, and wani lokacin sai kaga hawaye na sauko a idonta, idan aka aje mata abinci bata ci yadda ka bar shi haka zaka zo ka tararda shi, idan ka danka mata abu a hannu bata rikewa”

“Ya ake take rayuwa bata cin komai?”

“Ta hanyar allurar da maganin da muke saka mata a drip”

Talba ya lumshe ido ya bude.

“Mutanen nan suna ganin rayuwa, farincikin da suke so, kadan ne amman ya gagaresu, a kashe su, a kwashe dukiya a kune kuma wandanda aka raunata a bar su da daukar nauyin kansu, Allah kadai ya san abun da akai mata ko ta gani”

“Wallahi ai mu muna ganin abubuwa sosai”

Ali ya nufi kofa Talba ya bi bayansa sai suka fito tare suka jera zuwa gurin da ake aje marasa lafiya, suna tafe Ali na masa hirar wasu da aka kawo da yadda sukai ta fama da su, Talba dai be ce Uffan ba har suka shiga female ward din suka doshi gado na 36 da inda Aminatu take kwance. Ko da suka isa sun tarar an ja mata lalube gurin da take, an rufe ta ta ko'ina ta yadda bata ganin kowa kuma kowa baya ganinta. Ali ne ya fara daga labulen ya shiga sannan Talba ya shiga. Kwance suka same ta idonta a rufe hawaye na saukowa ta gefen idonta. A zatonsa babbar mace ce sai da ganinta yarinya mai kananan shekaru yasa jin tausayinta ya karu da kashi talatin cikin dari, domin ya san fyade na daga cikin abun da yake lalata rayuwar ya mace, kuma yana daga cikin abun da mace tafi tsana balle kuma wannan da take karamar yarinya. Ali ya saka hannu ya dauki safar dake gurin ya saka a hannu sannan ya taba kafarta sai ta bude idonta da suka yi ja da alama ta dade tana hawayen ta sauke su akan Talba dake kallonta fuskarsa cike da haiba da annuri. Shi ma kallonta yake ba yabo ba fallasa, daga can cikin zuciyarsa cike take da tausayinta sai dai jinkai da rayuwarsa daya daukarwa kansa ya saka ya kasa barin hakan ya bayyana a kyakkyawar fuskarsa.

“Da son samu ne, a ware mata daki daya ita kadai saboda halin da take ciki, so that ta samu kulawa ta musamman kuma tana bukatar ayi mata gwaje gwaje, tana ma bukatar jini”

Ali ya fada yana kama hannunta ya tabawa. Har lokacin Aminatu Talba take kallo ji take kamar ta taba ganinsa a wani gurin sai dai bata san ko'ina ba ne, ji take kamar ta bude baki tai magana sai dai bara da kuzarin yin haka, kamar yadda take jin jikinta be da kuzarin riketa balle har hannunta ya jimke wani abu, tabbas yanzu kam ta tabbatar da kalamanta sun kare, kamar yadda take jin komai na rayuwarta a yanzu ya zama tarihi, bata yarda ita ce dai wacan Aminatun dake rayuwa a karkara tare da iyayen da yan'uwa ita ce a nan ba.
Da ace zata iya bude zuciyarta ta sun yi arba da tarin bakinciki da duhu zuci, wanda idan suka karanta wata kila likitan zai tausaya mata ya daina bata taimakon da yake bata na drip da allurar so that ta samu ta huta ita ma tafi sahun yan'uwanta da iyeyenta. Har gobe tana jin karar bindigar da aka kashe mahaifinta da mahaifiyarta a cikin kanta, ta kasa manta yadda yan ta'addan suka rika yawo a jikinta a lokacin da suke kokarin keta rigar mutuncinta, idanuwanta sun ki su goge hoton fyaden da akai ma mahaifiyarta a gaban ido wai shin miya rage mata? Miyasa take a raye har yanzu?

Ali ya kalli Talba dake tsaye ya kalli Aminatu data kafe Talba da ido, a zahiri shi take kallo, a badini kuma rayuwarta bayan take hange a cikin idanuwan mutumen da take jin kamar ba a yau ta taba arba da shi ba. Har lokacin hawaye ba su daina zubar a idonta ba.

“Kallon mutane ba dabi'ar bace ko dai ta san ka ne?”

Ali ya tambaya, kallonsa kawai Talba yai ya dauke kai.

“Kin san shi ne?”

Bata dauke ido daga kallon Talba da take ba balle har ta kali Ali ta amsa masa. Ali ya kalli Talba dake kallonta shi ma har lokacin.

“Ka yi mata magana wata kila zata amsa”

“A canja mata daki idan kana ganin hakan ya dace, idan ka yi list din ko nawa za a ashe sai ka fada min”

Shine abun da Talba ya fada sannan ya sakar ma Aminatu murmushinsa mai tsada kadan wanda yafi kama da na yake ya juya ya fice. Yana fita sai ta lumshe idonta kamar mai bachi sak rayuwar da take a gidansu ita da iyayenta da yan'uwanta ya soma kawata idonta dake rufe. Juyawa Ali yai ya fice yana kokarin cire safar hannunsa.
14

Shin kin san Kamshi na daga cikin abun da yake daga darajarki? Kamshi yana saka a ga kimar mutum a girmamashi musamman ma na Ramla incense, tana da turaruka kala ka kama daga na jiki dana daki da na tufafi, irin su Halud
Sandal flakes
Sandal wood
Signature
Kajiji
Damboun kajiji
Halud ball
Wardrobe ball
Coconut sandal
exclusive gowe
Black humra
Body milk
Kulaccam
Misik humra. Ramla Incense ta shirya tsab domin aika muku da turarenku har garin da kuke, da kudinki kalila ki samu turare mai kyau mai dadin kamshi da sanyaya zuciya, domin siye ko sari ku tuntubi Ramla incense ta wannan number 07038392576 tana aikawa har wajen Nigeria. You can check her Instagram handle ramla_incense. https://www.instagram.com/invites/contact/?i=1fl5k3wnc4opb&utm_content=43xtopa


*Dan girman Zatin Allah karki karanta idan baki biya ba. Masu sharing Allah yai muku yadda kuke min. Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci. Pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith bank, then send the evidence via 08036126660*


BATURIYA POV.

Bayan ta gama zazzagawa Alhaji Sule rashin mutunci ta shiga tai wanka. Ta shirya cikin farin lace sai aikin gogawa fuskarta powder take, can kuma ta mike tsaye tana kallon kanta a madubi, sai ta ji ana kwankwasa gidanta, jiki na rawa ta aje soson hodar dake hannunta ta fice daga dakin da sauri taje ta bude gidan domin ta san da zuwan Ramlee.
Rumgume juna sukai ita da Ramlee kowa ne na murnar ganin wani kamar wadanda suka shekara basu saka junan a ido ba.

“No no ba dai lace din nan kika saka ba? Ai yanzu kuma kin wuce saka kananan kaya”

Ramlee ta fada tana yatsina fuska

“Ke mai tsada ne fa, yayata ta ba ni shi, mai kudi take aure fa”

“Baturiya kenan yanzu ai kin wuce wata ta kwance ta baki ki daura, sai dai ke ki kwance ki bawa wata ta saka, ga wata abaya nan na zo miki da ita kamin mu fara zuwa siyayen tufafi masu tsada”

Ta karashe tana mika mata jakar dake dauke da abayar, wani irin tsalle Rafi'a tai ta dire tana murna.

“Amman Wallahi kina da zuciya mai kyau, kamar kin san ina mararin abaya”

Ta karba da sauri ta nufi cikin dakinta sai Ramlee ta bi bayanta tana murmushi, a falo ta zauna har sai da Rafi'a ta canja tufafin jikinta daga lace zuwa sabuwar abaya, ita kanta ta yaba yadda bakar abayar tai mata kyau kasancewarta fara, cikin zumudi ta nufo falo.

“Allah ya miki sura Baturiya Wallahi kina da kyau”

Ramlee ta fara tana kallonta.

“Wallahi zaki sha kudi, manyan masu kudin nan suna son fararen mata amsu kananan shekaru”

“Da gaske?”

“Uhm har sai na rantse miki ma, a ciki ma zaki samu wanda zai ce miki aurenki yake so, ko ma be ce ba idan kin ga ya miki sai mu bada sunansa kawai a kama mana shi, dube ki gani fa Wallahi ke matar manya ce Baturiya”

Baturiya ta yi murmushi tana jin wani irin dadi, sannan ta koma ciki ta dauko. Jakarta da karamar wayarta da makulli ta fito.

“Ina Sultan”

“Tun dazun na tura shi makota”

“Aiko kin kyauta, domin yara akwai sa ido zai iya fadawa Babansa na zo”

Suka yi dariya sannan suka fito daga falon kamin su fita daga gidan gaba daya Baturiya ta kulle gidan. Sannan suka nufi bakin titi inda motar Ramlee take, front seat Baturiya ta shiga Ramlee kuma ta ja motar suka kama hanya, suna tafe suna hira har suka shigo cikin gari, gaban wani katon shagon siyar da wayoyi Ramlee ta faka motar, kusan a tare suka fito ita da Baturiya, tana kokarin rufe motar ta hango Alhaji Garba jikin mota yana waya.

“Ramlee bari na gaisa da mijin yayata ga shi can”

“Ba zai ce wani abu ba?”

“Zan ce ke na rako ai, ban sani ba ko zai ba ni wani abun yana da alheri ai”

“Shikenan bari na jira ki daga ciki”

Kai ta daga mata sannan ta nufi gurin da yake tsaye jikin motarsa yana waya, ganinta yasa yai hanzarin yanke wayar da yake ya kalleta yana murmushi.

“Baturiya ina kika fito?”

“Ai kai zan tambaya na sani ko wata budurwa ka rako”

Yayi dariya.

“Zaki bari ne? Ai kin tare kowa ya gida ya kowa ina mijinki?”

“Kowa lafiya kalau, ina Anty”

“Lafiya Kalau take, me kika zo yi nan?”

“Wallahi wayata ta bata kwanan baya shi ne na zo siyen karama”

“Oh haka fa, Yayarki ta fada min Allah maida alheri, ai da na san da zuwanki da na riko miki wani abu gashi bani da enough a mota”

“Uhm Alhajina kenan ai kai babba ne, kuna da kudi sai dai idan ba ayi niyar ba mu ba, tun da alherin zuwa zuwa ne”

Ya sake yin dariya yana kallonta.

“Haka yayarki ta fada miki?”

“Aa yayata bata fada min komai ba, haka dai na gani da idona”

Ya bude motarsa yana dariya.

“Baturiya sarkin rigima ashe dai mijin naki yana fama”

“Kana dai fama zaka ce, ko ka bawa wani ne?”

Yayi dariya mai sauti.

“Zankadediyar mata irinki zan kyautar na dai ara masa shan miya, yanzu dai bari na siye bakin nan naki dan karki je ki fadawa yayarki kin gan ni a gurin siyen waya”

Ya fada bayan ya zauna cikin motar, sannan ya ciro bandir din yan dari dari 10k ya mika mata.

“Gashi na rufe bakin nan kar yayarki ta ji”

Murmushi tai ta karba.

“Karka damu Alhajin Allah, ai ko mutum ka yanke agabana ka bani wadannan ka rufe bakina babu wanda zai ji”

“Da gaske? Ashe za a iya siye ki da kudi?”

“Ba wai za a iya ba, ana ma yi ne”

Ta fada tana wani irin kashe masa ido kamar wata tsohuwar karuwa. Binta da kallon da shi kadai ya san manufarsa yana murmushi har ta shiga cikin gurin. A bakin kofa ta samu Ramlee tana jiranta.

“Yayarki tana da miji kamar wannan kike zaune a talauci?”

“Uhmm yan uwa yanzu ai babu ruwansu da son zumunci idan sun samu daga su sai yayansu”

“Shiyasa nake son ki gina kanki ki yi naki arzikin”

“Wallahi kuwa, babu abun da yake burge ni kamar katon gida da katuwar mota da kayan sakawa da na ci masu kyau masu tsada, Wallahi ko hoto ake turowa a group zaki ga ko wace shegiya da katon falo, haka nake ta ganin friends dina a gida masu kyau da sutura mai tsada, ki duba ko yan'uwana kowa tana auren mai rufin asiri amman ni kullum abushe ko abunda zamu ci wani lokacin gagararmu yake”

“Karki damu kin warke yarinya ke dai ki goge kawai ki iya dadin baki da kwarkwasa da jan hankali”

Haka suka cigaba da nisawa cikin shagon suna ta hira, an tsara shago gwanin sha'awa camera a ko'ina ga gilashi da haske gulob kamar ba rana ba,.kana ganin gurin kasan na manyan mutane ne.
A tare suka jera da Ramlee suka nufi gurin da aka jera wayoyin techno. Ramlee ce ta fara dubawa sannan ita ma ta kai hannu zata dauki wata sai ta ji an riko hannun nata, saurin kallon gefenta tai da tsoro sai tai arba da mutumen daya rage mata hanya a wacan lokacin da ta sauka tasha daga Kano, murmushi ta sakar masa kamar yadda yake mata murmushin shi ma, sai ta janye hannunta.

“Sarki alkawari”

Ta watsa masa wani irin kallon irin na masoya.

“Daman na yi alkawari?”

“Ba ki yi ba amman dai ai ya kamata ki ce min na isa gida lafiya ko?”

Ta yi murmushi, shi ma murmushin yai ya gabatar mata da yarinyar dake gefensa.

“Ku gaisa da kanwata, ya kamata ku san juna tun yanzu ai”

“Sannu”

Baturiya ta fada. Sai ita ma yarinyar dake kama da saurayin ta maido mata.

“Yauwa sannu, sunana Salima”

“Ni kuma Rafi'a amman anfi kirana Baturiya”

“Yeah kin fi turawan kyau ai”

Cewar saurayin sai duk suka yi dariya har shi.

“Me kika zo yi nan?”

“Waya na zo siya kasan wayata ta bata”

“Oh haka ne, amman kin san na tashi koma gidan nan sai kuma wata zuciyar ta bani hakuri ashe rabon zan hadu dake ne a nan, gaba daya na kasa samun natsuwa tun da muka rabu Wallahi nake ta mamarin ganinki har Hajiya na bawa labarinki”

Ta yi murmushi.

“Gashi yanzu, ai mun hadu katin daka bani ya bata ne”

“Ayyah”

Ya fada sai kuma ya kalli Ramlee dake ta duba wayoyi.

“Ko zaki bani aron kawar nan taki mu zagaya gurin masu IPhone”

“Yeah ba matsala, zan jiraki a mota”

Ramlee ta fada tana murmushi, sai Baturiya ta daga mata kai.

“Okay”

Bayan Ramlee ta wuce ya bawa kanwarsa key din motar.

“Je ki jirani a moto”

“Okay sai anjima in-law”

Budurwar ta fada sai duk suka yi dariya, sannan ya nuna mata hanyar da zasu bi su bullo gurin da aka jera iPhone din.

“Fahat sunana duk dai baki tambaya ba”

Ta kalleshi ta yi murmushi, da kansa ya zaba mata iPhone mai kyau, sannan ya nufi wajen biyan kudi ya mika atm dinsa, kamar ance ta juyo, tana juyowa tai arba da Nura tsaye gurin biyan kudin, da alama wani ya rako, suna hada ido tai saurin dauke kai gabanta ya shiga faduwa da mugun karfi. Bayan ya biya ya rakata har gurin motar Ramlee ya sake ciro katinsa ya mika mata.

“Ki tausayawa zuciyar nan tawa ki kira wayata ko zata samu sukuni”

“Karka damu zan kiraka, na gode sosai”

“Nine da godiya yau zan yi kwanan farinciki”

Ya fada sannan ya rufe mata motar Ramlee yaja suka bar gurin.

“Ina kika san shi? Baturiya Allah ya miki farin jini”

Dariya tai kamin ta labarta mata yadda akai ta sanshi, sannan ta dora da na ganin da Nura tai mata abokin mijinta kuma amininsa.

“Ke kar ya dame ki, idan ma ya fada masa ki bururuce ki ce ki kam sam ba ke bace, idan ya dage ke din ce kice tare da yayanki kika je siyen waya”

“Kuma fa kin kawo shawara, idan ba haka ba kam zai iya fusata sosai domin dazun na ci mutun mai mana maganar kudin haya na san kuma za su fada masa”

“Saboda me? Ai ba haka ake ba, nawa ne kudin hayar?”

“80k”

“Just 80k? Yanzu zan baki 100k da mutumen ya baki sai ki nemi inda mai hayar yake ki bashi gaba daya, wayar da ban siya miki ba zan baki kudin daman na yi niyar kashe miki 50k akan wayar dan haka zan baki su a hannu, gobe kuma zan kawo miki kayan mata masu kyau ki fara shirya kanki kamin lokacin da saku gana da Alhajin”

“Har da wani shan kayan mata?”

“Eh mana, kuma idan kika fara sha karki yarda ki bar Faruq yaje kusa da ke”

“Ni daman bana shan kayan mata ai, mutum yana fama da talauci ko a sha kayan mata me zan samu? Shiyasa ba ruwana da shan su, kuma ba kullum nake barinsa yana damuna ba”

“To ki dai kiyaye, yanzu kina isa gida ki fara neman mai kudin hayar ki bashi hakuri ki bashi kudinsa, kin ga idan ya dawo zai rage jin zafin tun da kin biya kudin hayar”

“Haka zan yi Inshallah na gode sosai kawata”

“Allah dai ya bar mu tare”

“Ameen”

A inda ta faka motarta dazun ta sake tsayawa, ta ciro kudin ta bata sannan sukai sallama, Baturiya ta fita ita kuma ta juya ta hau titi.




FARUQ POV.

Kamin ya isa gida sai da ya kira abokinsa Nura ya fada masa yadda sukai da abun da ya samu kana yai masa godiya. Ya isa gida cikin farinciki, ba zai ce be taba rika 100k ba amman ba kasafai ba, rabon daya rika 10k tashi ta kanshi ma ya manta.
Yana isa ya zare dubu biyu ya bawa Asiya ya ta girka abinci, sannan ya shiga daki ya taba mahaifiyarsa dake zaune tana maida numfashi a hankali.

“Mama ya jikin na ki?”

“Alhamdulillah, Aisha tace ka zo dazun ina bachi”

Ta amsa tana kallon yanayinsa dake bayyana irin farinciki da yake ciki.

“Eh na zo na tararda jikin na ki ne sai a hankali...”

Ya dora mata da labarin yadda komai ya faru ciki har da abun da Malam Musa ya kira shi yana fada masa Rafi'a ta yi, kamar wanda aka cirewa ciwo sai Mama ta nemi ciwon ta rasa zuciyarta tai fal, daman ciwon nata hawan jini ne na tunanin auren Aisha da kuma yunwar da suke wuni da ita su kwana da ita, abu ga talaka bawan Allah kadan ya ishe shi.

“Amman Allah ya saka masa da alheri, Allah ya faranta rayuwarsa ya daummawar da farinciki a cikin zuciyarsa kamar yadda ya faranta ranmu”

“Ameen, ni kaina ina tafe a hanya ina ta masa addu'a, Wallahi na jidadi sosai, domin rashin lafiyar nan naki ya dame ni, yanzu ki tashi ki shirya mu tafi asibiti”

“Aa wace asibiti kuma Faruq? Ai ni yanzu na ji sauki, daman ciwon ai na rashin kudin ne”

Wata kalar dariya Faruq yai wanda ya manta rabon da yai irinta har ya manta.

“Haba Mama saboda ciwon ki fa naje karbo kudin nan, kuma har ga Allah ni asibitin nai niyar kaiki”

“Aa ai ciwo kuma ya warke, da aje a kashe kudin a banza ai kara a kara ayi hidima, Idan aka karbi kudin lefe aka rage wani abu cikin nan ai sai a dan kara, in yaso sai ka dauki rabi ka ba mai hayar ka bashi hakuri”

“Ai ba za su isa ba, 80k ne muke biya shekara”

“Eh ka bashi ko 50k ne dai ka bashi hakuri kamin Allah ya budo mana wata hanyar samu sai ka cika masa”

“To Allah ya sa ya yarda, wannan matar ta kira min ruwa, Wallahi na gaji da halin Rafi'a Mama kullum da kalar fitinar da take bullo min da ita, bata da wata magana sai ta na sake ta”

“Ka kara hakuri tana maka haka ne saboda tana ganin baka da kudin yin wani auren, da ace ta san kana da kudi da ba zata maka haka ba, koma na rayuwa dan hakuri ne wata rana zaka ga komai ya wuce kamar ba ayi ba”

“Allah ya kara min hakurin domin har ga Allah ta kai kulu, ba wai zan sake ta ba ne bana son shiga hakkinta ne”

“Yanzu dai tashi ka tafi gurin sana'arka in yaso gobe sai ka samu mai hayar na san zuwa lokacin ya huce sai ka ba shi hakuri ka bashi dubu hansin din, Allah ya warwareka yai maka albarka, zuwa da yamma zan tafi gidan Kanen mahaifinku na fada masa yayi ya aiko da kudin lefen sai a hada da dan abun da aka samu”

“Toh Allah ya taimaka ni zan tafi”

“Ka dai baro mata abinci ko?”

“Eh akwai Taliya da wake, da cefane, idan na koma anjima zan siya mana abinci ina son na cire 5k a ciki”

“To Allah ya taimaka yai maka albarka”

“Amin Mama Allah kara miki lafiya”

Ya fada yana mikewa tsaye sai ta bishi da kallo ina na uwa da da tana jin kaunarsa na karuwa a ranta, ta fi kowa sanin cewar idan Faruq yana da mafita da tuni ya share mata hawayenta.
Kudin ya ciro ya cire 50 na mai haya sannan ya cire 5k ya mika mata 43k da suka yi saura, sannan ya fito ya nufi gurin aikinsa.
A hanyarsa ta tafiya ya saye waina sannan ya karasa shagon daman yana da plate da spoon da dan copinsa a shagon bayan ya bude ya wanke plate din sannan ya zuba wainar ya ci, ya siyo ruwa ya sha, tukuna ya hau gyaran shagon kamar yadda ya saba.
Be tashi ba sai 7:30 daman haka yake tashi kamin ya isa gida 8 tayi sai ya tsaya yai sallah a massallacin unguwarsu sannan ya shiga gida. A duk lokacin da zai shiga gida da tunani da fargabar abun da Baturiya zata masa, amman a yau haushin shiga gidan ma yake ji, har be san ta inda zai fara mata ba idan ya shiga.
Kamar kullum sai da ya tsaya yai sallah, sannan ya biya gurin mai siyar da balangon unguwarsu ya siye na dubu daya, ya biya shago ya siye shimkafa da sauran kayan masarufi sannan ya nufi gidansa.
Yayi mamakin ganin kofar gidan a bude domin bata saba barin kofar a bude ba, rufewa take wai a cewarta masu kudi ma basa barin gida bude sai takawa, hakan yasa duk wanda ya zo sai ya kwankwasa mata sannan ta bude. Sai dai yau kofar a bude ya same ta, sai ya shiga rike da ledodin a hannu nan ma sai ya samu kofar falon a bude, be yi sallama ba ya shiga saboda ransa a bace yake. Sultan kadai ya samu a falon zaune yana shan bobo, Sultan na ganin mahaifinsa ya sauko daga saman kujerar da sauri ya nufe shi.

“Daddy sannu da zuwa”

Sai da ya aje ledodin hannunsa sannan ya dauki Sultan yana murmushi.

“Sultan ya keke?”

“Lafiya”

“Me kake sha?”

“Bobo Momy ta siya min Bobo”

Jimmm Faruq yai sannan ya sauke dansa ya bude masa ledar naman daya siyo ya aje masa a gabansa.

“Zauna ka ci”

“To”

Ya zauna da sauri ya fara ci yana ta murna.

“Momy ma ta siya min kifi dazun”

Faruq be sake ce masa komai ba ya nufi kofar dakin tana tabawa ya ji a rufe, sai ya juyo ya kalli dansa.

“Sultan ina mamanka?”

“Tana ciki”

Kwankwasa kofar ya fara yi.

“Rafi'a ki bude kofar nan”

Sai ta amsa masa daga can ciki.

“Wallahi ba zan bude ba, ai na san dokana zaka yi”

“Kin san abun da kika yi kenan?”

“Eh mana, haka kawai muna fama da talauci zai zo ya kara mana da wata damuwar kudin haya shiyasa na karbi number sa na zage shi ai”

“To kin jawa kanki ya bamu kwana daya mu tashi mu bar masa gidansa, Rafi'a mi yake damunki ne wai? Miyasa ke baki son zaman lafiya? Duk wani abu da zai tayar min da hankali shi kawai kike nema”

“Ai na bashi 100k yau, na biya shi kudinshi kuma ya bada takardar ya yarda mu zauna”

Natsuwa yake kokarin yi wai ko zai fahimci inda kalamanta suka dosa, ta bashi kudi haya?

“Rafi'a”

Ya kiranta a hankali, sai ta amsa daga jikin kofar da take, rike da sabuwar wayarta.

“Na'am”

“Maimaita abun da kika fada min”

“Na ce na bashi kudin hayar har na kara masa da 20k sama”

“Ina kika samu kudi?”

“Yaya ne ya ba ni Umma ta cika min sauran”

“Bude kofar nan mu yi magana”

“Ba fa zan bude ba, tufafin ka nan a falo na fitar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On BAKAR WASIKA
avatar
aisha-7-1

6 months ago

Reply

Nice novel

Please Login or Register in order to submit comment