Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dashi.

Kafafuwanta da wani irin nauyi ta karasa cikin dakin. Suna jin takun tafiyarta suka juyo. Ganinta yasa suka matsa daga jikin gadon.

Tana sauke idanuwanta kan nawaf zuciyarta tai wata irin dokawa da take ji har cikin kanta. Kallonshi take. Kanshi nade yake da bandage. Gefen fuskarshi ma haka.

Inhar baka sanshi ba ba zaka gane shi ba. Inda ba shida bandage din dinkine yakai hudu. Da duk takun da take da karin karfin bugun zuciyarta.

Gaba daya jikinshi na.urorine harda abin abinci ta hancinshi. Gani tai tafiyar daga inda take zuwa gadonshi ta mata wani irin tsaho.

Kaman so ake ta kare mishi kallo. Taga yanda ya koma kamin nan ta karasa inda yake. Hakan kuwa take.

Kafafuwanshi duka biyun a nade suke da irin abinda hannunta ke ciki. Bata taba sanin zaka iya jin tarwatsewar zuciyarka ba sai a wannan lokacin.

Bata taba sanin haka tashin hankali yake ba sai a yanzun nan. Bata taba gane rayuwa ba abakin komai take ba saida ta karasa bakin gadon da nawaf yake kwance.

Hannunta na rawa sosai tai kokarin kaishi kan fuskar nawaf. Saidai ta rasa inda zata ajiye shi.

Ko ina ciwuka ne. Kafafuwanta taji suna wata irin rawa. Ta dafa gadon dakyar tana zama. Bakinta ta bude saidai kalma ko daya ta kasa fitowa.

Banda wani irin ihu da take jinshi cikin zuciyarta da kanta amman sautin shi yaki fita.

Hannunta ta sauke kan kirjin shi. Kai take girgizawa. Fata take ta farka daga wannan mafarkin da takeyi. Su koma gida abinsu da nawaf dinta.

Koda kuwa markadata zai dingayi karewr duka inhar zata ga fuskarshi babu wannan abin.

Yanayin Nuriyya da nawaf din ya sake karya zuciyar duk wani wanda ke cikin dakin. Su kansu mazan daurewa kawai suke.

Can Allah ya taimaketa muryarta ta dan dawo.

"Nawaf......"

Ta fadi. Baiko motsa ba ballanta na tai tunanin yajita ko zai bude ido.

"Nawaf......!"

Ta sake kira wannan karin da karfi.

*

Ji yai kaman muryar nuriyya. So yake ya bude idanuwanshi amman sun masa wani irin nauyi. Yana ji da wata irin murya ta sake fadin.

"Nawaf ka tashi......!"

Kokarin bude idanuwanshi yake yi daga duhun dake riqe dasu. Nuriyya ce. So yake ya tashi ya bata hakuri. So yake ta yafe mishi. Yana jin yafiyarta ce kawai zata yaye wannan duhun.

Da wani irin karfin hali ya samu ya soma motsa idanuwanshi. Ji yake komai ya mishi nauyi. Kamun a hankali ya bude idanuwanshi. Ya dade sosai kamun ya fara ganin alin haske haske.

"Nawaf......"

Ta sake fadi. Baya son yanayin da yakeji cikin muryarta. Raunin da yakeji fiye dana kowanne lokaci ne. Sake kiran sunanshi tai.

Sai lokacin ya fara ganinta dishi dishi. Yanaji daga can gefe wani kaman yaya khamis na fadin.

"Call the doc"

Saidai baya ganinsu. Nuriyya dinma dishi dishi yake ganinta. Kanshi yakeji kaman ana doka mishi wasu irin karafa ciki. Ya rasa a ina ma yake jin ciwon a jikinshi.

Har cikin tsokarshi ciwo yake ji mai tsanani. A hankalo fuskar nuriyya ke washe mishi. Dakyar muryarshi can kasa yace.

"Nuri...."

****

Bude idanuwanta tayi ta sauke su kan fu.ad dake zaune yana rike da hannunta. Wani murmushi yai mata dayau ta kasa mayar mishi.

Kamun ta kalli gefenta. Sofi ce zaune. Sake maida kallonta tai kan fu.ad.

"M....."

Ta kira shi a hankali. Hannunta ya sake dumtsewa cikin nashi yana jin yanda zuciyarshi ke bukatar suna mabanbancin wanda take kiranshi dashi.

Sumbatar hannun yayi hadi da fadin.

"Princess. Sannu"

"Ku kaini wajen shi"

Wani numfashi fu.ad yaja saboda safiyya ta mishi bayanin komai tun dazun. Harta gama fada mishi baice komai ba.

Saboda baya son zuciyarshi ta fara tauna dukkan maganganun. Komai zai iya faruwa. Nana tafi bukatarshi. Komai da nashi lokacin.

Ba Nana kadai ke son ganin wannan bawan Allah ba. Har shima yana son ganinshi. Yana son mishi godiya akan karamcin dayai ma Nana.

Yana son mishi godiya duk da tayi kadan akan abinda shi yai mishi. Baida wani abin da zai iya bayarwa banda wannan.

"Zaki ganshi. Yanzun ki huta sosai. Kici abinci kisha magani sannan"

Kai ta girgiza mishi tana dakuna fuska.

"Yanzun nake son ganinshi"

Sauke numfashi fu.ad yai yana kallon sofi data kawo mishi dauki. Kauda kanta tayi gefe. Tasan halin Nana. Ba ta cika nacewa kan abu ba.

Saidai duk lokacin da tayi haka din. Lankwasata abune mai wahala. Kawai sai dai ai mata abinda take so shine kwanciyar hankalin kowa.

Hannunta ya sake dumtsewa cikin taushin murya yace.

"Baki yarda dani ba? Nace miki zamu je. Kici abinci kisha magani tukunna........"

Kwace hannunta Nana tayi. Ta kauda kai gefe idanuwanta na cikowa da hawaye. Ba zasu gane ba. Ta jima tana son sake ganin shi tai mishi godiya.

Ko sunanshi bata sani ba. Ranar ta dauka zasu fito su same shi a waje. Sanda suka fito baya nan. Tun ranar duk fitar da zata yi tana duba fuskarshi a fuskokin mutane da dama.

Dawowar fu.ad yasa ta sake son ganinshi. Saidai taba mishi addu.a. Tana mishi addu.ar samun wadatacciyar lafiya a rayuwarshi.

Dan a wajenta tana jin banda mumynta da babanta babu abinda yafi mata lafiya muhimmanci. Yanzun data ganshi.

Cikin jini. Tana so ta ga halin da yake ciki. Hawayen dake idanuwanta suka zubo.

"Ba zaku kaini inganshi ba sai na mutu ko shi ya mutu tukunna ba......"

Da sauri fu.ad yakai hannu ya rufe mata baki. Fuskarshi babu walwala ko kadan yace.

"Shhhhhhhh zamuje. Zamuje Nana ki daina wannan maganar. Ya girmi shekarunki"

Hannunshi ta kama dayaje bakinta ta sauke shi. Mayarwa yai yana goge mata hawayen dake fuskarta. Kamun ya mike.

Safiyya na kallonshi ya fice daga dakin sannan ta taso daga inda take ta zauna kan kujerar daya tashi.

"Kinsan ba....."

Da sauri Nana tace

"Mumy please. Ina son ganinshi. Kuma ina son magana da yan jaridar nan."

Da mamaki safiyya take kallonta. Ta dauka ta manta da maganar tunda fu.ad din ya dawo. Duk da bawai hakura sukai su da son magana da Nana din ba.

"I thought M ya dawo. Shikenan"

Girgiza kai Nana tayi.

"Ina son magana dasu har yanzun. You promise mumy"

Jan numfashi safiyya tayi ta fitar kamun tace.

"Zan kira su. Damun bar asibiti in shaa Allah"

Sai lokacin tai murmushi.

"I love you mumy"

Dariya safiyya tayi takai hannu taba dan jan hancin Nana din.

"Sarkin rigima. I love you more"

Girgiza kai tayi bata yarda ba. Zatai magana fu.ad ya turo dakin da sallama. Suka amsa mishi.

"Nagano dakin da yake. Saidai family kawai ake bari ganinshi"

Da sauri Nana tace.

"Kuje dani. Zasu barni"

Girgiza kai fu.ad yayi. Baya son sake ganin hawaye a fuskarta. Kai ya sake zurawa waje ya hango likitan da sukai magana dashi ya taho.

Hanya ya bashi ya shiga cikin dakin. Ya cire ma Nana karin ruwan dake jikinta yana barin abin a jiki dan in sun dawo a mayar mata.

Da idanuwa fu.ad yai mishi godiyar fahimtarshi da yayi. Tahowa yai inda Nana ke kokarin sakkowa daga kan gado yana son kamata.

Hannunshi ta dafa ta kalle shi tace.

"Zan iya fa"

Tana saukowa. Takalmanta ta saka. Ta dauki yar hijab dinta ta saka a kanta. Sai yaga tayi wani irin kyau kaman ya saceta.

Daukarta yaxo yi ta matsa baya. Da murmushi tace.

"Um um. Zan iya"

Girgiza mata kai fu.ad yai yana kawo hannuwa zai dauketa. Ta rike su duka biyun. Idanuwanta take yawatawa cikin fuskarshi kamin ta furta.

"Ina son yin komai da kaina yanzun da zan iya. Zakuyimun amman da dan saura"

Runtsa Idanuwanshi yai yana jin nauyin da zuciyarshi tai a kirjinshi. Yama kasa cewa komai sai hannunta kawai daya kama cikin nashi.

Kallon safiyya yake da wani irin yanayi da shi kanshi ya kasa fassarawa. Kamun yaja Nana a hankali suna takawa zuwa kofa.

Binsu safiyya tayi tana jin wani irin abu na daban. Ta kasa fassara kallon da fu.ad yai mata. Sai dai ta kwammace hararar data kan samu lokaci lokaci a wajenshi da wannan kallon mai cike da fassarori da yanayoyi kala kala.

*
Kaman yanda fu.ad din ya fada. Family ne kawai zasu iya ganin nawaf. Fu.ad nata fama amman sunqi saurarenshi.

Nana ta ja mishi hannu. Nuna mishi tai daya dagata. Dan basa hangota saboda counter din data boye su. Dagata yai.

Likitocin dake wajen ta kalla idanuwanta cike da hawaye.

"Please please ku barni inganshi. Bazan yi wani hayaniya ba. I promise.

Yamun taimako a rayuwata. Shi ya tayani gano babana. Ina so in ganshi please please"

Kallon Nana suke su dukansu. Daya daga cikin likitocin ya gane Nana. Murmushi yai. Koma bai ganeta ba bazai iya hanata ba.

Cayai su jira yaje yai magana da wani cikin family din nawaf din. Yakai mintina goma kamin ya dawo yace zasu iya wucewa.

Sosai sukai mishi godiya. Wannan karin fu.ad bai sauke Nana ba. Shibya dauketa har suka karasa dakin da aka fada musu.

****

Sam allurarar baccin da sukai ma nawaf taqi kama shi. Wani irin kuka nuriyya keyi mai taba zuciya. Tana kallon murmushin da nawaf keson mata cikin idanuwanshi.

"Ki yafemun Nuri. Ki yafemun duk abinda nai miki"

Hannunshi ta sake damtsewa gam. Bata son wannan kalaman da yake ta maimaita mata tun dazun.

"Ki fada kin yafemun inji da kunnuwana"

Dakyar cikin kuka tace

"Na yafe maka nawaf. Ka yafemun nima"

Dakyar yadan gyara kanshi da alama hakan ba karamin wahala yai mishi ba.

"Nagode nuriyya. Ina sonki. Zuciyata ke kadai take so. Kece ta farko a cikinta kuma ke zaki zama ta karshe.

Ina farhan?"

Tambayarshi ta mata wani iri. Dago ido tayi ta sauke su kan farhan dake gefe. Yaji tambayar da nawaf din yayi.

Dan haka yadan karasa. Sai lokacin family din nawaf suka gane wanene shi din. Dan bama tashi suke ba.

"Ka kula da ita. Ka sota fiye da yanda na sota. Karka bar hawaye ya zuba a idanuwanta kaman yanda nayi.

Karka daga hannunka akanta kaman yanda nai. Ka zama farin cikin ta tunda na kasa. Ka kula da Nuri farhan"

Duk wani haushin nawaf da yakeji ya nema ya rasa. Dan yanzun ya tabbatar da nawaf da babanshi mutanene ne mabanbanta.

Duk abinda ya faru daya masa fahimta ya fahimci nawaf na son nuriyya. Son da yake tunanin ko shi bazai iya mata ba.

Sai yanzun ya fahimci taimakon da nuriyya ke fadin nawaf na buqata. Muryarshi a dakushe yace

"Kai zaka kula da nuriyya. Kai zaka zama farin cikinta. Saboda duk muna tare dakai.

Zamu taimaka maka"

Baice komai ba. Saboda yanda yake jin a jikinshi sun gama taimaka mishi. Idanuwanshi yakai kan mamanshi da babanshi da suke tsaye sun zuba mishi idanuwa.

Kallon da yake musu yasa ya suka karasa inda yake da sauri. Farhan ya matsa musu ya na komawa gefe.

Cikin sanyin murya yace.

"Ku yafemun. Na saka ku bacin rai da yawa a rayuwata. Ku tayani roqon Allah ya yafemun......"

Kuka sosai mama takeyi. Yana jin kukansu har cikin zuciyarshi.

"Ina su yaya khamis"

Dukkansu suka karaso inda yake. Suma yafiyarsu ya nema. Ibrahim ne karshe. Shakuwarsu dabance ko a cikin yan uwanshi.

Kallonshi ibrahim yake da wani irin yanayi.

"Karka fara nawaf. Muna tare. Babu inda zaka je. Inka tafi dawa zan kula?"

Da karfin hali yai masa murmushi saboda ciwukan dake fuskarsh.

"Zaka kula mun da su mama. Zaka kulamun da duk wanda na damu dasu. Zaka kulamun da kanka.

Yaya nagaji sosai."

Dafa shi ibrahim yai. Ya mike yana fita daga dakin. Dai dai zuwan wani likita dake tambayarshi wasu abubuwa da bai fahimta ba. Yadai amsa shi da to ne kawai.

Yana nan tsaye ya hango wasu su biyu suna karasowa inda yake tare da wata yarinya kyakkyawa a sabe a kafadar namijin.

Karasowa sukai wajen shi sukai mishi sallama ya amsa musu. Fu.ad yace.

"Nan ne dakin da nawaf yake?"

Kallonsu yake dan baigane su ba sam. Zai iya rantsewa bai taba ganin su ba. Hakan fu.ad ya fahimta yace

"Muma bamu sanshi ba. Kaga wadda ta sanshi nan. Yamana karamcin da bazai mantu ba.

Shisa muke son ganinshi inba damuwa"

Yanda nana ke kokarin ya sauketa ne yasa shi sakkota a hankali. Karasawa tai ta kama hannun ibrahim.

"Dan Allah kabarni inganshi. Zan mishi godiya ne kawai"

Dan dafe kai ibrahim yayi. Inhar sunce nawaf ya musu karamci waye shi zai hana su ganshi. Da kanshi ya kama hannun Nana zuwa dakin.

Su fu.ad na biye dasu. Kallo daya safiyya tai mishi tai baya idanuwanta na kawo hawaye. Bata da juriya irin wannan dan haka ta dakata.

Koshi fu.ad daga gefe ya tsaya. Kallon family din nawaf yake. Yanda suke a hargitse yana jin zuciyarshi na cika da wani irin tsoro.

A hankali Nana take takawa har inda nawaf yake kwance da wata a gefenshi tana wani irin kuka. Su dukansu kallon nana suke.

Dai dai fuskarshi ta tsaya tana kallon shi.

"Ya jikinka?"

Ta tambaya. Sosai nawaf yake kallonta yana son gane inda ya taba ganinta. Ga zuciyarshi na wani irin zafi. Yana jin yanda yake kokawa da numfashin shi.

"Da sauqi"

Ya fadi a hankali.

"Naga babana."

Tace mishi. Sai lokacin ya tunata. Oh rayuwa kenan. Cike da taushin murya yace mata.

" Naji dadi. Ya jikinki"

Dan daga kafada tai alamar yana nan kamun tace.

"Zan maka godiya ne. Da banga babana ba badan kai ba. Ba haka naso in ganka ba.

Na kasa ganewa ni fa. Na rasa me yasa mutuwa ta zabeni. Kuma kaganka yanzun."

Murmushi nawaf yai mata kamun yace.

"Lokaci da dama mutuwa tana da rudani. Sai dai hutu ce ga mumini.

Ina son in huta. Ina son in samu nutsuwa"

Jinjina kai Nana tayi kaman ta gane me yake nufi. Fuad yadan dafa kanta. Ya kallo nawaf.

"Mungode sosai nawaf. Allah ya baka lafiya"

Sai yake jin wata nutsuwa ta daban. Ko ba komai sanadin shi wannan yar yarinyar ta gane babanta.

Da idanuwa ya amsa saboda ya gaji sosai. Sosai nana ta matsa kusa da kunnen shi yanda bamai iya ji tace.

"Kana jin tsoro?"

Shima da rada takai kunnenta yace mata.

"Sosai. Amman ganinki yasa na daina"

Wani murmushi tayi kamun ta sake ce mishi cikin kunnenshi.

"Nagode. Allah ya baka aljanna. Sai mu zama abokai acan"

Lumshe idanuwanshi yai yana jin kaunar Nana har ranshi. Kama hannunta fu.ad yayi. Tace.

"Zan dawo....."

Baice mata komai ba. Har sunkai kofa yace

"Ya sunanki?"

Juyowa tai da murmushin nan sannan tace

"Nana safiyya"

Kai yai kokarin daga mata wani irin tari ya sarqe shi. Da gudu Nana tai niyyar karasawa ganin yanda jini ke fitowa daga bakinshi fu.ad ya dauketa.

Kwantar da ita yai a kirjinshi tana wani irin ihun kuka ya fita da ita daga dakin da gudu.

Gaba daya family din nawaf suna kanshi. Sun rikice sosai kowa kwala mishi kira yake.

Nuriyya tana rike dashi da hannunta tana jijjigashi.

"Nawaf ina zaka tafi kabarni?"

Sosai take kuka. Shi kanshi farhan wasu hawaye yaji sun cika mishi idanuwa. Mama kuka take kaman zata shide.

Yaya khamis ya kasa koda motsawa daga inda yake. Babane yaga yanda numfashin nawaf ke sama ya soma karanto mishi kalmar shahada da karfi.

Aikam kaman nawaf ya na saurarenshi. Yana karanto mishi muryarshi na rawa. Nawaf din na maimaitawa daya bayan daya.

Dagaji harshen shi harya karye. Kuka suke sosai. Ibrahim na rike da hannunshi daya yana kallon yanda numfashin shi ke sarqewa.

Muryarshi bata fita sosai. Kamun komai ya tsaya.......!

Fita baba tai daga dakin. Yaya khamis ne ya karaso yasa hannu ya rufe mishi idanuwanshi yana zubda hawaye.

Kallonshi nuriyya take yi. Tana jinta kaman ba a duniya take ba. Ibrahim mikewa yai yana ja da baya. Ya kasa yarda nawaf yabarsu.

Ya kasa yarda da abinda yake gani. Mama na mikewa ta yanke jiki ta fadi. Da gudu sukai kanta. Nuriyya kuwa ta zuba ma nawaf idanuwa.

Tana kallon murmushin dake kan fuskarshi. Hannu tasa a hankali ta taba jikinshi. Sanyi taji yayi karara.

Girgiza kai take yi. Sake taba shi tayi kamin a hankali ta jijjigashi. Gani tai yaqi motsi. Gabaki daya yanayinshi ba iri daya bane da nata.

Mikewa tayi tana girgiza kai. Wata irin gigitacciyar qara ta saki tana faduwa kasa......!

*#TeamNawaf*
[7/9, 1:20 PM] πŸ…° "πŸ…° " D'πŸ…±β­•YπŸ”›πŸ”: *_POST BY GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100_ πŸ“šπŸ“š_*
[7/9, 1:20 PM] πŸ…° "πŸ…° " D'πŸ…±β­•YπŸ”›πŸ”: AKAN SO 37
*πŸ’˜πŸ’–AKAN SOπŸ’–πŸ’˜*

~Written by~ :Luβπα SufyΞ±Ο€

37

*PLEASE inajin dukkan comments dinku nakuma gode. Abu daya zance sa readers na AKAN SO. Gaba dayanshi zai zama da happy ending. Sai dai ina tafiya da reality as much as i can. So please amin hakuri in gama cikin kwanciyar hankali. ILYA*

*Naga addu.o.inku daga kan masu mun text da masu kirana a waya. Allah ya saka da alkhairi. Alhamdulillah na samu sauqi sosai. Hopefully zaku dinga jina lokaci lokaci. #AnaTare*

Kallon fu.ad take sai kai kawo yake da Nana akan kafadar shi yana ta bubbuga bayanta a hankali. Tunda suka dawo daga ganin nawaf yake lallashinta har tai bacci.

"Ka kwantar da......."

"Shhhhhhh"

Fu.ad ya katse ta yana daquna fuska. Shirun tayi ta zuba masa idanuwa kawai. Da alama baya ji da ganin kowa banda Nana a yanzun.

A hankali take jin wani abu a zuciyarta yana dokawa a hankali. 'Ina sonki sofi' kalamanshi suka fado mata.

Kowa ya turo kofar ya taimaka mata ba kadan ba. Murmushi ta dora kan fuskarta ganin Ansar ne. Shima murmushin ya mayar mata.

Fu.ad dake tsaye yana kallon su yadan runtsa idanuwanshi yana jin kaman ya shaqare Ansar din nan. Ya ringimo katon kanshi yazo.

Karasawa yai ya mikama fu.ad hannu. Ya karba yana kauda kai gefe. Murmushi ansar yayi. Fu.ad din nan na bashi dariya ba kadan ba.

"Ya jikin nana?"

"Da sauqi. Mungode"

Ya amsa dakyar. Karasawa yai yaja kujera ya zauna suna gaisawa da safiyya. Wani irin abu yaji ya tsaya mishi a wuya.

"Zan wuce safiyya. Idan Nana ta tashi ki kirani a waya mu gaisa"

Kasa kasa fu.ad yace.

"Kaman kasan bama bukatarka"

Harara safiyya ta watsa mishi. Ya dan bude mata idanuwa dake fassara 'Gaskiya na fada'. Murmushi Ansar yayi ya mike ya ajiye ledar dake hannunshi.

Mikewa safiyya tayi.

"Ina zaki je?"

Fu.ad ya bukata yana tsare ta da idanuwa. Wucewa tai tabi bayan ansar. Safiyya ta raina shi yanzun shine tunanin da yake yi.

Karasawa yai a hankali ya kwantar da Nana yana gyara mata kwanciya yaji an kwankwasa kofar.

"Yes....."

Ya furta batare daya juya ba. Sallama akai aka turo kofar. Duk dadewar dayai baiji muryarba bai hana shi ganeta ba.

Da sauri ya juya dan ya tabbatar da abinda kunnuwanshi suka ji. Aikam hamza ne. Shima tsaye yai rike da kofar yana kallon fu.ad din.

A hankali ya saki handle din kofar da yake rike dashi ya na shigowa cikin dakin sosai.

"Hamza....."

Fu.ad ya fadi cikin sigar gaisuwa. Da dan guntun murmushi hamza ya amsa da fadin.

"Moh...."

Sosai ya karaso cikin dakin. Sai lokacin yaga da mutum a bayan hamza. Daga kasan kafafuwanta ua fara yawatawa da idanuwanshi.

A hankali har yakai kan fuskarta inda ya tsayar dasu cak. Tsaye take tana wasa da hannayenta. Idanuwanta na yawo ko ina na dakin banda kan fu.ad.

Wani abu yaji zuciyarshi tayi. Ga bakinshi ya wani bushe. Dakyar ya hadiyi miyau ya furta.

"Hussaina. Little sis"

Hannuwanshi yasa ya goge fuskarshi da yake jin kaman zufa a jiki. Mikewa yai daga kan gadon ya karasa inda take tsaye.

"Hussaina........"

Bata kalle shi ba. Asalima rabashi tai ta wuce inda hamza yake tsaye ta tsaya kusa dashi sosai. Hannuwanta ta saki.

Takai daya ta kama na hamza ta dumtse gam. Idanuwanta na kasa. Kallonta sosai fu.ad yayi. Inda take tsaye. Sannan ya maida hankalinshi kan hannunta.

Hannun hussaina cikin na hamza a dumtse. Lokaci daya ya fahimci me hakan yake nufi. Sai sannan ya lura da yanayin hussaina.

Cikine a jikinta harya turo. Hussaina tayi aure. Lumshe idanuwanshi yai. Yakai hannu yana murza goshin shi da yake jin wani abu na yawatawa.

Safiyya ce ta turo dakin da sallama ta shigo. Tagansu tsaye cirko cirko. Kallon hussaina take. Sai lokacin ta gane ta.

"Hussaina?"

Dagowa tai ta sauke idanuwanta kan safiyya.

"Anty na"

Da sauri fu.ad ya kalleta. Baisan yanda yai kewar muryarta ba sai yanzun. Baisan kewarta dayai tayi girma haka ba sai yanzun daya ganta.

Wani abu yake ji a dukkan jikinshi. Gaisawa safiyya tai da hamza sannan suka gaisa da hussaina. Taja musu kujeru suka zauna.

"Ya jikinta?"

Hussaina ta bukata. Safiyya ta amsa ta da.

"Da sauqi. Bacci take"

Kai hussaina tadan daga mata hadi da dorawa da.

"Daman munzo dubata ne. Zamu dawo gobe in shaa Allah"

"Allah ya kaimu goben. Mungode sosai"

Da sauri hussaina ta katse ta da fadin.

"Saboda ita nazo. Badan kowa ba"

Kallonta safiyya tayi ta rasa me zatace. Mikewa tai hamza ma haka. Gani yai sun nufi kofa. Da sauri ya karasa inda suke.

"Hussaina.....!"

Bude kofar tayi ta fice. Hamza ma haka. Da sauri fu.ad yabi bayansu. Gudu hussaina take tana nufar hanyar da zata fiddata daga asibitin.

Tsayawa hamza yai yana tare fu.ad. Hannunshi dake kan kafadarshi fu.ad yabi da kallo. Yana jin wani irin daci a zuciyarshi.

"Me hakan ke nufi hamza?"

Da wani yanayi a muryarshi hamza yace.

"Please ka kyaleta kawai. Ba lafiya gareta ba sosai....."

Ture hannun hamza fu.ad yai yana mishi wani irin kallo.

"Ka sake bani dalilin binta kenan"

Dafe kai hamza yai kamun yace.

"Look. Ba wai ina so in hanaka bane. Kanwarka ce. Amman inada hurumin dazan damu da lafiyarta"

Kaman daga sama fu.ad yace.

"Kana sonta?"

Kallon wannan wacce irin tambaya ce hamza yaima fu.ad.

"Kawai ka amsa ni. Kana sonta?"

Wani dan murmushi hamza yai.

"Baka ga shaida a jikinta ba"

Duka fu.ad yakai mishi ya kauce yana dariya.

"That is disgusting hamza. Kanwata ce"

Dafa shi hamza yadanyi.

"Karka damu. Ina son hussaina. Ina sonta sosai wallahi. Please zata sauko. Right now space take bukata kabata"

Sauke murya fu.ad yai sosai.

"Badamuwa. Just...... Just take care of her"

Kai ya daga mishi. Yana kallo ya juya yakoma. Hanya ya nufa yana ficewa daga asibitin. Cikin mota ya samu hussaina a zaune ta hada kanta da jikin motar tana wani irin kuka.

Saida ya shiga motar ya kullo sannan ya matsa ya rikota. Hannunshi ta rike cikin nata ta na dora fuskarta akai. Kuka take sosai da sosai.

"Shhhhh baby please. Kukan ya isa...."

Cikin shesshekar kuka tace.

"Duk....duk shekarun da nake son mishi magana.... Yanzun ban kula shi ba..... I.....i miss him sosai...."

Hannunshi ya zame daga nata. Ya tallabi fuskarta. Cikin idanuwa ya kalleta.

"Shima yai kewarki."

Girgiza kai hussaina tayi.

"Daya neme mu. Saboda me bai neme mu ba duk lokacin nan?"

Bashida amsar tambayarta. Don haka yasa hannunshi yana goge mata fuskarta.

"Saikin haifo mana baby rigimamme ko"

Murmushi tayi. Yadan kissing gefen fuskarta.

"Ko kefa. Komai zaiyi dai dai kinjini ko? Bana son kukan nan"

Gyara zamanta tayi tana kara goge fuskarta.

"I love you"

"I love you more"

Ya fadi yana kunna motar.....

****

Kwance take jikin mamansu nawaf. Tun jiya bayan ankai nawaf makwancin shi ta nemi hawaye ta rasa.

Sai dai zuciyarta da take ji kaman anbi takanta da mota. Ga wani irin zafi da take ji tana mata. Bawai bata yarda da cewar nawaf ya rasu ba.

Tadai kasa yarda data rasa shi har abada. Ta kasa yarda da cewar ya tafi bata gama fada mishi duk irin son da take mishi ba.

Bata gama fada mishi duk yanda take godiya da kalar taimakon dayai mata ba. Tunda yasanta burin shi yaga ya tsameta daga rayuwar da take ciki.

Amman ita ta kasa janye shi daga tashi. Kirjinta tafasa kawai yake kaman an zuba mishi garwashi. Maganar mutane sama sama take jinta.

Gaba daya duniyar ta mata wani irin empty. Ji take ba tada kowa daya rage mata a cikinta. Duk da farhan da zuciyarta ke sane da zamanshi bai hanata jin bata da kowa ba.

Tana jin mazaunin nawaf daya bari a zuciyarta can wani gefe da take da yaqinin har tata mutuwar ta same ta babu abinda zai cike shi.

****

"Tun dazun inata maka magana baka ce komai ba?"

Ajiyar zuciya ya sauke.

"Banda abinda zan fada indai kan fu.ad ne saboda na jima da cire shi daga zuciyata ballantana ya dame ni"

Dafe kai momma tayi. Wani lokacin sai taga da gangan ake cewa fu.ad din na da taurin kai.

"Ni dai zanje in sake dubo yar yarinyar nan."

"A dawo lafiya. Allah ya bata lafiya"

A sanyaye ta amsa da.

"Amin thumma amin"

****

Baije ko ina ba sai hotel din daya sauka shima wanka yai ya sako kaya ya dawo. Safiyya taje ta dawo.

Yana zaune kusa da Nana da tunda ta farka bata ce mishi komai ba tayo shiru. Ya rasa me zai fara ce mata. Duk sai yake jin shi ya wani daburce.

"Ya rasu ko?"

Ta tambaya. Da sauri fu.ad ya riko hannunta yana girgiza mata kai.

"Kibar wannan maganar Nana. Mumynki taje ta dawo. Zata taho da abinda zamuci.

Ko kina son wani abin daban?"

Kai ta girgiza mishi tai shiru kawai. Tun jiya yaqi barin zuciyarshi tazo mishi da zancen nawaf saboda ba karamun tsorata shi hakan yake ba.

Da dare baiyi bacci ba sam. Ya rasa me ya hana shi bacci sai yanzun ya tuna result din test din da akai mishine zasu karba yau.

Zuciyarshi yaji wasu abubuwa na tsinkewa a ciki suna barin mazaunin su. Matsawa yai wajen fuskar Nana ya sumbaci goshinta.

Wani kasalallen murmushi ta sakar mishi.

"Mumy ta koya maka ko?"

Murmushin ya mayar mata. Yadan daga kafada alamar baima fahimci me take nufi ba.

"In mumy tana son jin ko jikina da fever bata son tambaya haka take yi fa. Bata

Please Login or Register in order to submit comment