Join Our WhatsApp Group

DUNIYA TA AMNA Complete Hausa Novel Document by DUNIYA TA AMNA


DUNIYA TA AMNA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 64096



DUNIYA TA AMNA

Reading Time: 5 Hours

Added On: 06, Oct 2023

Author: Asma Baffa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : 08033933642, +227 90 79 59 39

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 326.01 kb

File Type: txt

Views: 829+

Download: 771+

Last download: 1 day ago

Description/Story: : DUNIYA TA





BISMILLAH

INA MATUKAR GODIYA GA ALLAH DA YA BANI RAI DA LAFIYA DA KUMA IKON RUBUTA SABON NOVEL DIN NAN DUNIYATA.


MAKARANTA NOVELS DINA DA BIBIYATA INA MUKU GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI,ALLAH YASA WANNAN NOVEL YA FADAKAR YA KUMA NISHADANTAR,KAMAR YANDA MUKA FARA LAFIYA ALLAH YASA MU GAMA LAFIYA AMEEN.

KAMAR YANDA KUKA SANI NOVELS DINA NISHADI YAFI YAWA CIKI,INA KUMA GODIYA DA KUKE KARANTAWA HAR MUTUM YA SA KUDI YA SIYA WANNAN YAFI KOMAI DADI,INA GODIYA ALLAH YA BAR KAUNA.











1-5










FREE PAGE





LITTAFAN DANA RUBUTA

GASKIYA CE
MARAICIN RAHMA
MAAIKACIYAR GOMNATI
CIRANIN AMANA
DUK INDA TA FADI
KAMARSU CE DAYA
KASUWANCI NA
JIN DADI SABO
HADIN KAI
ME MAGANI
TUBABBIYA



NA KUDI DANA RUBUTA

RASHIN SA'A
TA GYARU
YAR KWANGILA
ADDUAR KAWA
GIDAN GWAURO/DAN NAZIA
DANGIN RABI
DUNIYA TA.......





GA MASU BUKATAR SHIGA GROUP DIN DUNIYATA DARI BIYU 200 NE


ACCOUNT NUMBER
0175487861 ASMAU GARBA MUHAMMAD, GTBANK.

MASU TURA KATIN MTN KO VTU GA NUMBER TA
08033933642

'YAN NIGER KU NEMI WANNAN NUMBER
+227 90 79 59 39











Official








By
AsmaBaffa










Page din farko naku ne Fans Dina duk wacce ke cikin groups Dina.














Zaune suke a wani katafaren Palo na Alfarma,Palo Wanda yaji furniture Dan gaske,duk Wanda ya Shiga wannan Palo bazai so Fitowa ba,wani uban kamshi da sanyi ne ke tashi,Family Guda su Shida rakacal sai ta bakwan Yar karamar yarinya tana Wasa a kasa,Kidan Bob merly ne ka tashi a wata katuwar plasma tv kamar ka dakko mutum,gaba Daya sunyi Shuru duk Basu cikin nishadi,Ahmad Dake narke cikin luntsumemeyar kujera shine yake kada Kai cikin maye da kwaya da gani kasan Kansa ba kalau ba,sai bin wakar yakeyi da bakinsa,gashi babu Wanda ya Isa yace ya kashe ko ya daina,baya Jin Maganar kowa,Mummy dattijuya itace ta nisa fuskarta dauke da damuwa Tace Haba Ahmad Kaine fa babban Danmu Amma ka duba yanda ka maida kanka Completely Useless har mun gaji da Dake Hanya tun daga Lagos muna zuwa Nan Kaduna wajenka akan magana Daya kaki ji,tunda hakane yau da Yamma zamu koma,Wani farinciki ne ya bayyana a kyakyawar Fuskarsa,ya Mike tsaye yace wow Mama the Mama,Allah yau zaku tafi?yawwa Haka nake so sabo da na samu freedom,yau kwananku biyu Kun dameni dama,Shut up Daddy ya Furta banzan yaro marar tarbiyya,ai Kai dama Daddy nasan baka so na,Zama ya sake Yi Yana bin wakar Bob merly,sai Chanel din Suka cire wakar aka Sako tallan Wani body lotion.

Wata Uwar Tsawa Ahmad ya saki tare da nuna Tv da yatsa cikin mayensa na giya da kwaya ya kalli dalleliyar Budurwar da aka Nuno tana tallan Body lotion a tv yace Kai...dalla ku matsa can Kar ku kawo Mana Harkar Daudu anan,mu ba Daudu Muka zo gani ba Ana Harkar arziki zaku zo Mana da Mata Yan Daudu,ke dalla ja can, Dan uwarki a Nan Nigeria muna da man shafawar mu Habiba yawwa,Muna da Habiba Muna shafawa Muna Kara Baki wuluk abin mu yafi Mana,Dariya ya Bawa duka Yan palon har Daddy ya kalle shi yace Ahmad Kai da kake fari Kal jinin Larabawa Kuma a gidan uban wa kake shafa wannan Man,sannan ce maka aka Yi Habiba karamin company ne? Mummy Tace Allah ya shirya min kai,Baki ya turo tare da gyara Ass down dinsa da yayi da wani Creazy jean.

Wata Yar kyakyawar jar mota ce Honda tayi parking a bakin wani Restaurant,Yar kyakyawar Budurwar ta fito Hannunta dauke da Handkerchief tana goge zufa, Hannayenta ta Shiga tafawa tana Waka Sannu da Zuwa.....Sannu....da zuwa kekashashe na,Oyoyo Dan Kedararre na.....Oyoyo Karmashashe na,Barka da dawowa Dan tsomalalle na,My Karmash I miss you,Wani saurayi ne matashi mugun siriri wuyansa kamar murkin laima,Kugunsa Kamar zai tsinke,Baki ne wuluk Kamar Iska zata dauke shi Haka ya fito daga jar motarsa Yana wani basarwa a dole babban yaro,Bakinsa ya Bude da Niyyar magana Yan hakoransa manya na gaba Guda hudu Suka yo waje,Yana kallon Budurwar yace naga Alama Baki da tarbiyya,Kamar Ni saurayinki Ina sonki kina so na Amma kina ci min Fuska,glass dinsa ya zare a Fuskarsa ya kalle ta sama da kasa yace Yar talakawa Dake matsiyaciya ki kalle Ni kina wani ce min Oyoyo Karmashashenki? Baki da Manner? An fada Miki badan so ba Zan iya tsayawa da Yar matsiyata irinki? Ki kalle Ni nafi karfinki ta ko Ina,Yar budurwar kyakyawar gaske fara Tace Kayi Hakuri Wasa nake maka wallahi badan naci fuskarka na fada ba,Tsawa ya daka Mata yace dalla ja can dama iyayenki Basu Miki tarbiyya ba,Baki da hankali dai,Ran Budurwar ya baci tace kaga Malam na maka tauna na maka hadiya baka gani ba,to naji bani da tarbiyyar sai kace Iyayenka suzo su Yi min,daga na maka Wasa Kai baka San wasan masoya ba,wannan ne wasan a gidan uban wa ya Zama Wasa? Nan take Budurwar ta bashi amsa a gidan Ubanka Kamalu,Baki Bude ya kalle ta yace Aamna a gidan wa kika ce? Wacce aka Kira da Aamna ta sake cewa a gidan Ubanka nace Kamalu,Kamalu ransa ya dugunzuma yace it's over between me and you,bani ba ke,Aamna Tace ae naji Nima bani ba Kai tsotsatsen banza,me zanci da Kai dama idan anyi auren ma Banda kashinka ya dinga suka na me zanyi,Dana kwanta a jikinka gwara na hau katifar fasasun kwalaba,Kuma da na aureka ka min kiss da bakinka me hakora Kamar kacar Keke gwara na tsotsi Kusa me tsatsa,Yace irin na Ubanki ne ai hakoran,naji ta furta tare da koma cikin Restaurant taci gaba da aikinta.

Wajen masu girkin taje ta faki idonsu ta saci yankan nama Uku ta watsa a Jakarta ta fito ta baya can ta cinye Naman sannan ta dawo ciki ta Iske Fried rice an Gama an kaiwa wani yaci ya bar Rabi kadan ma ya ci,Aamna da sauri tazo Wajensa Tace Alhaji ka Gama Zan gyara wajen 2pm yanzu resturant zai cika,kafin yayi magana ta sunkuce abincin ta dauke Masa lemon da ko budewa baiyi ba ta Sha kwana tayi ciki,Alhaji ya saki Baki Yana cewa ke ke ke ban Gama ba Amma Ina Aamna tuni Taki ma kula shi,tana zuwa Tace Alhaji ya koshi ta zauna ta lashe abincin ta Balle lemon ta shanye sannan ta fito fes da ita da mamakinta sai taga Alhajin Bai tafi ba,da sauri ta koma Wajensa Tace Alhaji wani abincin Za'a kawo maka ne? Alhaji ya kalleta yace ke Amma wacce iri ce bance na koshi ba kin dauke abinci lemon ma Dan wulakanci ko Bude shi banyi ba kin dauke Ina ta kiranka bakya ji? Aamna Tace eyya Allah sarki kayi Hakuri matsalar kunne gareni banji ba Kuma gashi na zuba komai cikin shara bare na dawo maka da shi,Harara ya balla Mata tare da zube wani kudin yace kawo min wani abincin,da murna ta dauka dama Bata koshi ba,taje ta hadowa Alhaji duk abinda ya bukata,wata white rice with salat ga kwai da kaza,ga lemo,Aamna tunda taga Haka take ta faman zaga wajen da mopper a Hannunta Wai a dole gyara takeyi,tana ta faman goge goge a saitin Alhaji,Alhaji yace ke kin dameni da goge goge ga customers can sunzo kije Mana Haba wannan wacce irin Maaikaciya aka dauka Haka idan bakya so sai na daina zuwa cin abinci a wajenku aikin banza,Aamna tayi murmushi tare da gyara pcap dinta Tace afwan Alhaji ta juya ta tafi Amma sai ta labe a bayan wani lungu daga ciki tana ta kallon Alhaji tana so yayi ya Gama ta samu rabonta,Siyama ce kawarta taje ta sallami wasu customers din Aamna tana labe tana zalama wajen Alhaji,Siyama tayi Dariya tare da kallon Aamna tana labe labe Tace Allah ya shirye ki,Alhaji kadan yaci ya bar komai ya tafi kafin ya Gama fita tuni Aamna ta kwashe komai tayi ciki,Nan ma ta zauna ta cinye ta koshi sannan Tace saura na dare kafin na tafi gida,dole na dinga kiba Ina yin kyau,Aiki a restaurant ai Dadi gare shi ko ba komai Zan cika tumbi na.


Dattijo ne fari me gemu sosai Wanda shi kanshi gemun ka kalla kasan Dattijon ya tsufa domin yayi fari,da gudu gudu sauri sauri ya shigo gidansa inda yake wani mugun Rubabben gida,Gida ne na Haya Kuma gidan Talauci,da gani ba sai an fada maka ba Dattijon Talauci ya Gama da shi,cikin Gida ya Fado Yana masifa tare da furta me zangani Aishatu?me zangani yau,wacce ya Kira da Aishatu ta kalle shi shekeke tare da balla Masa Harara Tace mene? Gashi can kina karar min da kudi,kina min asarar Duniya da Almubanzanranta,yanzu ki duba sabo da Allah tunda na taho Ina kallon kwalabati kumfar Omo tana ta bin ruwa tana ficewa Ful...ful,Yanzu a zamanin Nan kumfa ka gani a kwata kasan kudinka ake kashewa,kina ta kashe min kudi kina abinda kika ga dama,Ga jarabar karar da Ashana kiyi ta kyastata sai ta Kare,Takaici na yanda kike wanki ko wanke wanke sai asarar Omon bala'i,to wallahi da sake baza ta yuwu ba,kullum Ina fama a hanyar sakateriya wajen Dan aiki na Wanda masinja ne ni nayi retired Ina nemowa Ana wulakantawa bazai yuwu ba,Daga yau ko mangyada ne za a zuba a abinci to kowa cokali Daya Daya babu kari aikin banza,Wata buta yasa kafa tare da yin fatali da ita Yana zare Ido yace Ina Aamna sakarai da Sweety Zuhra?Aishatu banza tayi Masa ta ci gaba da aikinta,yace Aamna har yau ba labarin Mijin Aure?

Aishatu tayi Shuru,Dattijon yace na gaji da yahudanci wallahi da nasan Haka ne Aamna ko secondary baza tayi ba,Dan fa Kawai Ina tunawa Amana ce a wajen mu, Nima ban San ya akayi basirata ta toshe na biya Mata har tayi wani HND sabo da asara,ai karatun mace Bai da amfani,amfanin mace aure da girki tayi ta zazzago Haihuwa,yarinya ta Zama bayahudiya abinda taga Dama shi takeyi,Nima jarabata ce tasa Rana tsaka Ina Kauye tare daku cikin sutura na dawo damu Birni na Kama haya,da Muna Kauye da tuni hankalinmu kwance,da duk wannan karyar Bamu shige ta ba,Aishatu Tace ai sai Dana fada maka kaki ji Aamna tana secondary a Kauye Ss3 ka kwaso mu Muka dawo birni gashi yanzu ta waye Taki aure muna ta ciyar da ita a banza ,wallahi baza ta Sabu ba,gidana ya koma na yahudu bazai yuwu ba,ai Birni na dawo ne Kawai Dan na samu sana'a me kyau to gashi hakan Bata samu ba,Dan pension Nawa ma baya Isa Nawa yake Ina abin,kullum sai talauci ne ke karuwa,birni kwai masifa Ni tunda nazo banga wayewar ba,ban wani waye ba,Aishatu Tace yo shekarar mu Nawa a Birnin kwata kwata shekara hudu fa rak Ina wani wayewa Aamna da Zuhra ne Kawai Suka Dan waye Dake su Yara ne,Dattijon yace ke tafi can Aamna Ina ta waye ai gwara Zuhra,Amma Aamna kina gani magana ma Bata iya ba ta Kauye takeyi duk abinda yazo bakinta dankarawa mutum takeyi Dan tayi makaranta ne ma take Dan canjawa,ni dai na fada Miki a kiyaye asarar Omo yawwa ya furta tare da ficewa falau falau da rigarsa doguwa ta wani tsohon yadi dinkin wani falkeke komai ta Masa yawa

Kuka Aamna ta saki Wiwi tana Hawaye tare da nuna Budurwar da Hannu tana masifa tare da Furta In Allah yayarda Shedan sai ya sumbace ki,Shedan sai yayi kissing dinki,muguwa,Azzaluma, maciya Amana,Baza kiga dai dai a rayuwarki ba Saratu,Saratu anyi asarar Duniya,An Sarai asarar duniya,Shegiya wacce Shedan yayi Mata fitsari a Kai, Wacce ake Kira da Saratu murmushi ta saki tare da karkada key din motarta Tace nafi karfinki Kina talaka kucaka me Deeni zaiyi dake duk kudinsu,ke wawiya ce Baki da hankali da har kina me siyar da Abinci a Restaurant kike tunanin Dangidan Dan Majalisar jaha Deeni zai so ki,ai ko kansila Aamna bazai tayaki ba,ganinki kyakyawa Fara Wai zai sa samari su soki? Kinyi kuskure Aamna,ai yanzu samari sai masu kudi suke Nema gidan da Suka gaji arziki,ai yanzu sai kana da kudi ake rayuwa da kai,ke Dan Dakikiya ce tunaninki kyau Yana sawa a so mutum? Dan kina da kyau har Shishigi kike Yi to ki sani samari sai dai su yaudare ki Amma yanzu duk munin masu kudi Haka ake aure su,Talaka ma Bai son Auren talaka bare irin su Deeni masu kudi,Ina Baki shawara ki fita Harkar Deeni ba ajinki bane.

Aamna tana tsaye sanye da Jean skert Blue da rigarta T-shirt fara tas me Rubutu Red a Gaban Rigar An saka A&G Food Joint,ta Sanya pcap Red takalminta ma Red,ba karya Aamna karshe ce a kyau,haskenta me kyau ba fari Kal Kal ba Amma fara Ce dai ba Wanda ya Isa yace wankan tarwada ce,dole dai farar ce,Gashinta har gadon baya Baki wuluk,Ga Zararan gashin Ido tare da kwantaccen Gashinta dake goshinta,Girarta wuluk me yawa,Hancinta me kyau bai cika tsayi ba,Fuskarta ba doguwa ba baza Kuma ace Round face ba,Dan Bakinta gwanin Sha'awa Karami with pink lips,Gata doguwa Amma ba can ba,ga Uban Hips kamar ita tayi kanta komai nata me kyau,hakoranta kanana farare tas,Idonta dara dara, Mashaallah,Aamna baza ta wuce 24years ba,Haka kanwarta ma Zuhra kyakyawa ce Amma ita chocolate ce kamarsu Daya da Baba.
Murmushin takaici Aamna tayi Tace ai gaki Nan da Muni yayi Miki yawa Deeni zai kwasa ki cinye Deeni please ta juya tare da komawa Kan bakin aikinta wurin masu siyen abinci,ita kuwa Saratu Tsaki ta ja tare da Bude dalelleliyar motarta baka ta Shiga sannan ta fisgeta a Tamanin.

Sai 11pm ta tashi a Aiki ta saka After dress dinta me Dan kyau tare da rataya handbag dinta tayiwa abokan aikinta Sallama ta wuce gida,Napep ta Shiga zuwa gida,can cikin wata Unguwa ta masu rangwamen gata aka sauke ta a Kofar gidansu na Bulon siminti Amma ka rantse kango ne baiyi Kalar gida bane,da Sallama ta Shiga da kyar aka samu aka amsa mata,Mama Wato Aishatu ta Iske tana Daura Net a dakin babansu Tace Mama na dawo,Tsaki dattijuwar ta ja Tace to sai me,idan da sabo ta Riga da ta Saba,Baba ta kalla Yana daki Tace Sannu Baba,da kyar ya amsa,Kai Kawai ta girgiza ta wuce kitchen Nan ta Iske abincinta an zuba Mata Amma an barshi a Bude baza a iya rufe Mata ba,ta Saba Kawai ta dauka tare da Fitowa sai ga Daya matar gidan tunda dama gidan Haya ne,mutum Uku ne a ciki ko wacce mata da dakinta biyu da kitchen Amma toilet Guda Daya ce du,Gaisawa...


Read / Download DUNIYA TA AMNA

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album