Join Our WhatsApp Group

NAFEESAT RETURN PART 1 Complete Hausa Novel Document by NAFEESAT RETURN PART 1


NAFEESAT RETURN PART 1

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 87451



NAFEESAT RETURN PART 1

Reading Time: 7 Hours

Added On: 05, Nov 2023

Author: Nafisat Isma'il Lawal ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Paid

Category: Love Novels

File Size: 454.54 kb

File Type: txt

Views: 489+

Download: 335+

Last download: 3 hours ago

Description/Story: [29/08, 1:27 pm] OumƊahira نفيسة: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
*DOCTOR'S FAMILY*
🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
*NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱


*MALLAKAR:*
_NAFISAT ISMA'IL LAWAL_




*بسم الله الرحمن الرحيم*


*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

_Thanks be May God bless everyone, peace and blessings be upon our leader Prophet Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, may God bless you and grant me the ability to write this book, may God grant me the ability to write what will benefit the nation ameen._

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY.*_

*LITTAFAN MARUBUCIYAR*
_NAFEESAT._
_BARRISTER IBRAHIM KHALIL._
_LABARIN DEEBIZAH._
_MALAMA LADI._
_JARUMAI_
_LUBABATU (ƴar ƙwallon ƙafa)._

.

*EPISODE One*

Doctor '' Al'ameen Abubakar Khabeer Cindo '' and his wife '' Prof. Nafeesa (Baby) Isma'il Audu, '' as you know in the story of * NAFEESAT * They live in Kaduna, and they still live in the city, owned by their five children.

*1_ DOCTOR NOOR (LAWAL AL'AMEEN ~YARON UMMEE NAFEESA~)* Wanda a yanzu ake kiran sa Big Dady, matar sa ɗaya *Hajiya Asiya (Hajiya) ƴa ga Muhsina,* yaran su uku, Doctor Usman, sai Doctor Zainab ~yanzu haka tayi aure,~ sai kuma Yusra.

*2_ HAJIYA RABI'ATU AL'AMEEN (IKRAM) ~WANDA A YANZU TANA AURE A GARIN KATSINA~* tana zaune da iyalan ta acan.

*3_ DOCTOR ABUBAKAR AL'AMEEN ~WANDA YANZU AKE KIRAN SA DA ABBA~* matar sa ɗaya Doctor Fatima (Hajja Fatu) ~ƴa ga Abokin Doc. Al'ameen wato Haidar da ƙanwar sa Ihsan,~ yaran su Biyu, Doctor Al'ameen (Baffa), sai ƙanwar sa Shakira.

*4_ DOCTOR AL'AMEEN AL'AMEEN (ABBU)* Matan sa biyu, ~Bilkisu (Umma) ƴa ga Baseera,~ yaran ta uku Doctor Zulaiha ~tayi aure,~ sai Fadila da autan su Fadil. Sai matar sa ta biyu *A'ISHA (AUNTY AMARYA)* yarinyan ta ɗaya '''NAFEESAT''' suna kiran ta da Ɗahira.

*5_ HAJIYA LAILA AL'AMEEN* yanzu haka tana aure a Kano, ta auri babban Yaron *WALID.* Suna zaune da iyalan su can.

Waɗannan familyn yanzu haka suna zaune ne a gida ɗaya kowa da part ɗin shi, sai dai akwai Babban parlour'n da ya haɗa su, yanzu haka Doc. Al'ameen Wanda a yanzu suke kiran sa da *KAKA* ya kai shekaru 89years. Tuni ya ajiye aikin sa sakamakon yana fama da ciwon ƙafa wanda a halin yanzu yana zaune ne a wheel chair, matar sa Prof. Nafeesa (Baby) Shekaru uku kenan da Allah ya amshi abin sa.

Za kuyi mamaki idan nace muku duk ka familyn Doc. Al'ameen gaba ɗayan su *DOCTORS* ne, wannan shine burin sa kuma Allah ya cika masa.

Babban asibitin da ya gina ya ƙara haɓɓaka shi wanda a halin yanzu Five Block ne, kuma sosai asibitin me suna *(AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL)* tayi fice a ƙasar Nigeria, gaba ɗaya familyn suna aiki ne a Hospital ɗin.

Yanzu haka a halin yanzu an shirya yin babban Walima don taya Doc. Ɗahira(Nafeesa) Al'ameen Al'ameen, Doc. Shakira Abubakar Al'ameen, Doc. Yusra Noor Al'ameen, da Doc. Fadila Al'ameen Al'ameen. Murnan kammala karatun su na likitanci, wanda za su soma aiki ne a ranan da a kayi musu waliman tare da sabbin ma'aikata da za'a ɗiba a ranan.

*KU BIYO NI DON JIN LABARIN WAƊANNAN FAMILYN*

Zaune suke su Huɗu a Babban katafaren parlour'n gidan da ya'amsa sunan sa a haɗuwa da ƙayatarwa, da shigowan ka parlour'n Babban Hoton Prof. Nafeesa (Baby) zaka soma cin karo dashi, wanda tayi sa ne lokacin da ta zama Professor, tana sanye da baƙar abaya me tsananin kyawu da burgewa, wanda duk da kasancewar ta baƙa ba ƙaramin kyau yayi mata ba, sai tayane kanta da Milk Colour ɗin Veil, kyakykyawar fuskarta yalwace take da murmushin da ya ƙara fito da tsantsan kyawun ta tare da Dimpul ɗin ta, a tsaye take ta riƙe ƙugu da hannu biyu tare da ɗan ɗage kanta, da alamun sanda akayi hoton bata san ma za'a yi sa ba. kusa da hoton kuma wani tanƙamemen hoton ne da a cikin sa Al'ameen ne tare da ita Babyn, suna zaune manne da juna sun saka ankon shadda me ruwan powder, gefe da gefen su kuma Noor ne tare da Ikram jingine da jikin su, duk kan su dariya suke yi time ɗin da aka ɗauki hoton, sai gefe kuma sauran hotunan ƴan gidan ne kowa da iyalan sa, sannan sai aka ɗau guda ɗaya wanda su kayi gaba ɗaya familyn, shi wannan ba'a daɗe da yin sa ba, don gab da rasuwan Prof. Baby akayi sa, gaba ɗaya idan ka kalle su sosai suke kamanceceniya da juna, sai dai banbancin launi da ya raba su.

Doc. Al'ameen wato KAKA tare da yaran sa maza su uku zaune cikin parlour'n suna tattauna yanda za su gudanar da Waliman yaran su kamar yanda suka saba a duk sanda yaran gidan suka gama karatun su na likitanci.

"Kai takwara yaushe matarka zasu dawo ne? Kasan jibi ne walima, ya kamata su dawo don itama Matata (yana nufin Ɗahira kenan) ta sami damar shiryawa yanda Ya kamata". Kaka dake zaune saman wheel chair yake wannan maganan

ABBU yace, "insha Allahu Dady zasu dawo zan sake tuntuɓan su inji, sabida mahaifin A'isha (matar sa Aunty Amarya) jikin ta yayi tsanani ne shiyasaka suka jin kirta".

Kaka yace, "to shikenan Allah ya dawo da su lafiya".

Gaba ɗaya suka amsa da "ameeen".

Sannan ya kalli Big Dady yace, "Kai kuma da yaushe ne Usman yace "zai dawo?"

Big Dady yace, "Allah ya taimaki Dadyna! na yi masa magana amma yace "in ba ka haƙuri ba zai samu daman zuwa ba sabida aiki sun yi masa yawa".

Cikin nuna alamun fushi Kaka yace, "wai yaushe Usman yabzama me taurin kai ne? Ko don yana tunanin na ba shi dama ya zauna acan yayi aiki shine yake son ɓata min rai? To, ka gaggauta kiran sa ka faɗa masa umarni nake ba sa; dole ne ya zo wannan taron Waliman da za'a yi, ko me yake yi ya'ajiye sa ya halarci taron nan".

Gaba ɗayan su su kace "Allah ya huci zuciyar ka Baba".

"Insha Allahu zan sanar masa Dady kuma zai zo". Cewar Big Dady kenan

Gyaɗa kansa Kaka yayi kana yace, "za ku iya tafiya na sallame ku, Allah yayi muku Albarka".

Gaba ɗayan su suka amsa da "ameen" kana suka tashi suka fice.

Shi kuma Kaka janyo Remote yayi ya sauya tasha zuwa African t.v yana sauraron wa'azi

Da sallama Fadil ya shigo parlour'n, wanda ya kasance shine ƙaramin gidan don shekarun sa baza su wuce 14yrs ba. zama yayi kan kujeran da ke kusa da na Kaka ya saka hannu ya ja gemun Kakan da ya kasance fari fat, yana dariya yace, "Kakus kana hutawa ne?"

Kaka bige hannun sa yayi yana faɗin, "Ƙaniyar ka Fadil, kai ma ka koyi jan min gemun ne yanda Matata take min?"

Dariya ya tuntsire da shi yace, "to ai hakan ya fi dace wa da kai Kakus, don me baza ka aske gemun ba ka bar abu sai faman lilo yake yi, wlh watarana kana barci zan silalo in cire maka kowa ya huta".

Dariya shima Kakan yayi yace, "lallai ka raina ni da yawa amma ina da me maganin ka, ka jira ya dawo zan faɗa masa duk abinda kake min".

Zumbur Fadil ya miƙe yana waro ido waje yace, "afwan Kakus kaima ka san ba mu haka da kai, wlh yau ne kawai nace bari in ɗana Amma baran sake ba, Kar kasanar masa don Allah kaji Kaka na". Yaƙarike maganar nasa yana me marairaice fuska kamar zai yi kuka

"Shaƙiyin yaro ashe kana da tsoro har haka?"

Waro idanu Fadil ɗin ya sake yi yace, "iyyee Kaka taya bazan ji tsoro ba bayan kana son ka haɗa ni da Zakin gidan mu? Ni dai ka ga tafiya na don tunda ka'ambato shi bazan iya zama anan ba". Yana ƙarisa maganar ya ruga aguje yabi hanyar part ɗin su

Da dariya Kaka yabraka shi, kana ya girgiza kan sa aran sa yana cewa, "lallai Usman ka koya ma yaran gidan nan tsoron ka, ba ka a cikin gidan ma shekara da shekaru amma har yanzu tsoron ka be bar cikin ran su ba".

Ci gaba da kallon sa yayi, sai can kuma ya ɗago kansa yana kallon hoton matar sa Baby, Wanda take ita kaɗai ɗin, murmushi da hawaye ne a haɗe suka taho mishi tunawa da rayuwan su, kullum ranan duniya sai ya zub da hawaye a kan ta, coz Ko wacce rana sai ya kalli hoton ta sama da ashirin, kuma aduk sanda zai kalla ko yayi kuka ko yayi dariya sabida abinda zai tuna na game da rayuwan su a wannan lokacin, gaba ɗaya ɗakin sa idan ka shiga hotunan ta ne birjik, da sanda take tashen ta da sanda ta tsufa, har ta bakin gadon sa inda yake saka kansa akwai hoton ta da ya'ajiye a wajen, mutuwan ta ya bala'in girgiza sa wanda yayi kamar bazai rayu ba, sai daƙyar ya dawo hayyacin sa bayan dogon jinyan da yayi, har yanzu har gobe soyayyar ta tana nan daram a zuciyar sa, domin kamar ƙaddara ne da Allah ya saka masa na tsananin ƙaunarta, kullum fatan sa ace ga ranan da zai bi ta, shima ya koma ga mahaliccin sa kamar yanda ta tafi ta bar sa..

Dafa kafaɗun sa da akayi shi ya dawo dashi hayyacin sa, Yusra ce tsaye kansa tana kallon sa, idan da sabo yaci ace sun saba da ganin Kakan nasu cikin wannan halin, kuma sun san da cewa ba komi yake saka sa a halin nan ba illa tuna Kakar su.

"Kaka har yanzu dai ka ƙi ka dena tuna wannan tsohuwar matar taka, har yaushe ne zaka cire ta arai ne kayi rayuwan ka cikin kwanciyar hankali? Mu nan mun ishe ka rayuwa ba sai ka tuna ta ba, me ake yi da tsohon Zuma bayan ga sabbin zuma? Don Allah ka dena ɓata time ɗin ka a kan ta".

Hannu ya saka ya share hawayen yana murmushi yace, "Yusra kenan baza ki taɓa gane wa ba, amma kowa ya san da cewa tsohon zuma shi ne wanda ke magani, sannan ba'a iya manta shi ko wani hali mutum ya shiga, Ni Matata ta fiye min ku duk kan ku, idan da za'a bani zaɓi daku da ita in zaɓa, ita zan zaɓa in bar ku".

Taɓe baki Yusra tayi tace, "to don baka zaɓe mu ba sai me Kaka? Our parents will vote for us because they love us."

Kaka yace, "to naji ban ce kiyi min rashin kunya ba, said me to my room".

"Da can Ni na ɗauko ka?"

Hararan ta yayi yace, "I have noticed that Yusra is jealous of my wife, but you will die. I will never love you. She is the only one who betrays me. kuma wlh idan baki gungura Ni kin mayar dani ɗaki na ba da Yayan ki zan haɗa ki, ke ce farko wacce zan kai ƙara wajen sa".

Turo baki tayi ciki-ciki tace, "ka daɗe baka kai ɗin ba, in yaso sai ya kashe Ni kar ya bar Ni da rai".

"What are you saying?" Kaka said looking at her

"Me kuwa kaji na ce?" Tafaɗa tana huro hanci kafin ta soma tura sa

Murmushi Kaka yayi yace, "na san maganin ku dani kuke zan cen".

Tana gungura sa cikin ɗakin sa ta fito tayi nasu part ɗin cike da haushin Kakan.
[29/08, 1:28 pm] OumƊahira نفيسة: 💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎
             *DOCTOR'S FAMILY*
                         🩺
💎💎💎💎💎💎💎💎💎💎

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
  *NAFEESAT RETURN*
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱


*MALLAKAR:*
                 _NAFISAT ISMA'IL LAWAL_




*بسم الله الرحمن الرحيم*



*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

*SADAUKARWA*
_Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. *GOMA'S FAMILY*_

*NATSUWA A SALLAH*
      _Sallah babbar matsala ce. Ganawa ce tsakanin Bawa da mahaliccin sa, Ubangiji maɗaukakin sarki. Saboda haka ana buƙatar cikakkiyar natsuwa, a tattara hankali wuri ɗaya domin wannan ganawa ta musamman._
     _A cikin ayoyi biyun farko na suratul Mu'uminun ana faɗa mana cewa:_
     _"Lalle ne, muminai sun sami babban rabo, wanɗanda suke a cikin sallar su masu tawali'u ne."_
    _Watau, Muminai wanɗanda idan sun tsaya yin Sallah sai gaɓoɓin su da zukatan su su natsu, babu wani abu mai shagaltar da su daga ambaton zatin Allah maɗaukakin sarki, to, irin su suke rabban ta. Natsuwa cikin sallah da ƙasƙan da kai ga Allah su ne alamun imani na gaskiya da Tauhidi tsantsa, don kuwa ko yaushe bawa yayi kusa da Ubangijin sa sai ya haɗa jin tsoron sa, musamman ma dai a sallah inda yake ganawa da shi, yake tunawa da girman sa._

.

    *EPISODE Three*

     A hankali ta sanya hannun ta ta soma jan gemun sa

Hakan yasaka ya buɗe idanuwan sa ya sauke a kan ta, murmushi yayi yana kallon ta yace, "Ni dama nasan babu wanda zai min haka sai ke, When did you come back?"

Murmusawa tayi tana janye hannun ta tace, "yanzu babu daɗewa".

Tashi zaune yayi yana faɗin "To ya me jikin da fatan ya samu sauƙi?"

Sai da ta dawo kusa dashi kana tace, "Alhmadulillah Kakus suna gaishe ku kowa da kowa".

"Mun gode muna amsawa".

"My Kakus miss you so much".

Murmushi Kaka yayi yana ɗaura hannun sa a kan ta yace, "nima haka Matata, You have left me alone I miss you, kin bar ni da waɗannan yaran mara su kunya masu ido a tsakar ka ko hiran basu taya ni".

Dariyan ta me kyau ta saki tana jingina kanta jikin Kakan tace, "Kakana kenan! don't worry, I'll be back. hira har sai ka gaji daji, akwai labarin ma da na samo maka".

"Well I hear you tell me".

Ƙofar da aka turo ne ya sanya Ɗahira rufe bakin ta without saying a word. Big Dady ne tare da Abbu suka shigo da sallama, amsa musu su kayi yayinda Ɗahira ta tashi da sauri ta nufi Mahaifin nata ta rungume shi tana faɗin

"Abbu na".

Murmushi yayi yana shafo kanta yace, "to ya kin dawo ko zaki fara?"

Dariya tayi tace, "I'm really missing you, Abbu."

Sai kuma ta sake shi, Then she hugging Big Daddy and said, "Daddy, I'm the only one."

Shafo kanta yayi shima yana smiled and said, "my daughter when did you come back?"

"Now Dady".

"To ya me jikin yaji sauƙi dai ko?"

Gyaɗa masa kai tayi tana faɗin "Alhmadulillah".

Big Dady yace, "madalla haka ake so".

Sannan ya juya yana kallon Kaka yace, "Dad, we're here to talk about new products da za'a shigo dasu."

Kaka yace, "to shikenan".

Abbu da ya samu wuri ya zauna yace, "Mamana bamu wuri za muyi magana".

Big Dady yace, "a'a barta kawai ta zauna".

Murmushi Ɗahira tayi tana kallon Big Dad tace, "bari dai inje in dawo Dady, because I have some things to do".

"Well shikenan Daughter".

Daga nan fita tayi ta rufo musu ƙofa, She did not go back to the General Parlor. Sai tabi ta wani Corridor da zai sada ta da Part ɗin su, tana cikin tafiya ta hangi Baffa ya taho shima ɗin, yayi shigan nan nasa na ɗamewa irin shigan wizaye, kansa babu hula sai kwantaccen gashin kansa da ya sha askin zamani, sosai yayi masa kyau ya sake fito da kyawun sa ainun, hannun sa Sigari ne yake sha, shima yana hango ta ya matse Sigarin a hannun sa ya kashe kana ya tura shi...


Read / Download NAFEESAT RETURN PART 1

START READING

OR

DOWNLOAD TXT NOW
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album