Join Our WhatsApp Group

HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN Complete Hausa Novel Document by HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN


HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 11088



HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

Reading Time: 0 Hours

Added On: 10, Oct 2023

Author: Unknown

Ebook Compiler : Shuraihu Usman

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Tales

File Size: 55.87 kb

File Type: txt

Views: 596+

Download: 120+

Last download: 19 hours ago

Description/Story: This Document is compiled by
Shuraihu Usman - 08140419490
YEAR of compilation - 2023;
Published to Taskarnovels.com.ng

01. HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN
Allah shi ne Sarki mafi daukaka daga dukkan sarakuna. Shi ne mafi tsarki daga dukkan abubuwa. Tsira da aminci su tabbata ga Manzonsa kuma Annabinsa, Muhammadu dan Amina (SAW).
A wani shudadden zamani, a wani gari na cikin kasar Farisa, an yi wadan su mazaje guda biyu yan uwan juna. Babban sunansa Kasim karamin kuwa sunansa Ali Baba. Bayan rasuwar mahaifinsu, aka raba musu gadon yar dukiyar da ya bari, kowa ya kwashi rabonsa.
Kasim ya auri yar wani babban attajiri na garin, shi kuwa Ali Baba ya auri wata yarinya wacce iyayenta sun kasance talakawa ne. Ba a dade ba, sai surukin Kasim ya mutu, yarsa ta gaji dukkan dukiyarsa, domin ita kadai ce yar da ke gare shi. Ita kuma ta damka dukiyar nan a hannun mijinta Kasim. Nan take Kasim ya zama babban attajirin da babu kamar sa a duk fadin garin.
Shi kuwa Ali Baba sai ya kasance dan abin da ya gada na dukiya daga mahaifinsu ya kare. Ya zama talaka wanda bai mallaki komai ba sai jakai guda uku. Sai ya rika zuwa daji da jakansa yana saran itace yana lafto wa jakan nan yana kawowa cikin gari. Idan ya sayar, ya siyo abincin da za su ci, shi da matarsa.
Ana nan haka kullum, wata rana Ali Baba ya shiga daji domin yin sana'arsa kamar yadda ya saba. Bayan ya gama dora wa jakansa itace, yana haramar ya kora su ya tafi, sai ya hango 'kura ta toshe sararin samaniya daga nesa, ta tinkaro inda ya ke. Ya ga cewa idan ya ci gaba da tafiya mahayan nan za su cim masa, sai ya kora jakansa cikin rami, shi kuwa ya sami wata babbar itaciya mai duhuwa, wacce zai iya ganin abin da ya ke kasa ba tare da wanda ke kasa ya gan shi ba, ya haye.
Bai jima da hawa saman itaciyar nan ba, sai ya hango mutane akan dawaki a sukwane sun nufo inda ya ke. Suna zuwa wurin, sai duk suka ja suka tsaya. Kowane daga cikinsu ya sauka daga kan dokinsa, ya daure shi. Ali Baba ya dube su da kyau, ya ga cewa dukkansu samari ne majiya karfi, kowane yana rataye da takobi, yana dauke da kaya a kan dokinsa. Ya kirga su, ya ga cewa su arba'in ne cif.
Ashe mutanen nan barayi ne, masu tare fatake suna yi musu fashi, yanzu ma sun zo ne wurin da suke boye kayan da suke satowa. Ali Baba ya ga daya daga cikinsu, wanda yana zaton shi ne babbansu, ya tafi gindin wani dutse da ciyawa ta lullube shi, wanda idan ba yanzu ba Ali Baba bai taba lura da akwai dutse wurin ba. Ya tsaya gaban dutsen ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Dutse ya tsaga gida biyu, sai ga kofa ta bayyana. Barayin nan suka yi ta duruwa ciki da kayan da suka sato, bayan kowa ya shige, sai babban ya bi daga baya. Yana shigewa, sai dutsen ya koma ya rufe, tamkar babu dutse a wurin.
Ali Baba yana kan bishiya, yana kallon dukkan abin da ke faruwa. Bayan barayin nan sun shige cikin dutse, sai yayi kamar ya sauko ya kama doki daya ya hau, ya kora jakansa ya tsere, sai kuma ya tuna idan ya sauko kuma aka yi rashin sa'a da barayin nan suna fitowa daga dutsen nan, lalle za su kama shi. Saboda haka sai ya canza shawara, ya ci gaba da zama a kan bishiyar.
Can zuwa wani lokaci sai ya ga kofar dutsen nan ta bude, shugaban barayin ya fara fitowa ya tsaya a gaban kofar yana kidaya barayin nan a lokacin da suke fitowa, har ya kidaya talatin da tara, gami da shi arba'in ke nan. Da suka gama fitowa, sai Ali Baba ya ji ya ce, "Garam, rufe dutsen Simsim." dutse ya koma ya rufe. Suka hau dawakinsu suka juya ta hanyar da suka fito.
Da Ali Baba ya ga kurarsu ta bace, ya sauko daga kan itaciya, ya nufi inda ya boye jakansa da sauri domin ya kora su zuwa gida, sai wata zuciya ta ce masa, "Ka gwada fadin kalmomin nan ka ga ko dutsen nan zai bude." Ya tafi gaban dutsen ya tsaya dai dai inda ya ga shugaban barayin nan ya tsaya, ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Yana fadar haka kuwa sai kofa ta bude.
Ali Baba ya kutsa kai cikin dutsen nan. Yana shiga sai dutse ya koma ya rufe. Da farko yayi zaton zai ga duhu dindim a ciki, amma sai ya ga haske kamar an kunna fitilu. Ya duba haka, sai ya ga dukiya tsibi-tsibi. Tsibin zinariya daban, tsibin azurfa daban, na tagulla daban, gefe kuma ga kudi nan tsaba cunkus. Ali Baba yayi mamakin yadda wadan nan barayi suka tara dukiya mai yawa haka. Ya ce a ransa, lalle sun gaji dutsen nan ne tun daga kaka da kakanni, domin yawan su ba su isa su tara wannan dukiya ba koda kuwa sun yi shekara dari suna tara ta.
Ya tattaro wasu buhuhuwan zinariya, wadan da ya san jakansa za su iya dauka. Ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Dutse ya bude ya fito da buhuhuwan waje, sannan ya ce, "Garam, rufe dutsen Simsim." Dutse ya koma ya rufe. Ya jawo jakansa ya dora musu dukiyar nan sannan ya dora musu itace daga sama ya rufe yadda mutane ba za su gane ba. Ya kora su da sauri ya nufi gida yana murna.
Da ya isa gida, ya kora jakunan ciki ya kira matarasa suka sauke kayan. Koda ya zazzage, sai wurin ya haske, matar ta ga zinariya tana daukar ido. Ya shaida mata dukkan abin da ya faru. Ta yi godiya ga Allah, ta ce, "Dare daya Allah kan yi bature, hakika duk fadin garin nan yanzu babu wanda ya kai mu arziki. Bari na kidaya na gani"
Ali Baba ya yi dariya ya ce, "Mene ne na batan lokacinki wajen kidaya wannan zinariya? Sai ki yi kwanki ba ki gama gidaya ta ba. Abin da na ke so da ke shi ne, bakinki kanen kafarki, kada ki kuskura wani ya ji wannan labari. Zan je na haka rami mu binne wannan dukiya da Allah ya ba mu."
Matar ta ce, "Duk da haka dai ina so na san adadin wannan zinariya. Kafin ka gama haka rami bari na je nan makwabtanmu, gidan yayanka Kasim na aro karamin mudunsu na awon hatsi domin na ga ko mudu nawa wannan zinariya za ta yi."
Ya ce ba laifi amma ta tabbatar ba ta fadawa kowa abin da za ta auna da mudun ba. Ta fito ta shiga gidan Kasim, ta taras da matarsa. Bayan sun gaisa ta ce ta zo ne aron mudunsu na awon hatsi. Matar Kasim ta tambaye ta babba ko karami? Ta ce karamin ma zai yi. Ta shiga cikin daki domin ta dauko ma ta, ta ce a ranta, me wadan nan matsiyatan za su yi da mudu? Ina kuma suka sami hatsi mai yawa haka da har sai sun auna shi da mudu? Kuma wane irin hatsi ne wannan? Sai ta sami karo kadan ta manna shi a cikin kusurwar mudun wanda ta tabbata karon zai like kwaya daya ta hatsin da za a auna, ta haka za ta iya gano kalar hatsin da suka auna idan an maido mata da mudun. Ta kawo wa matar Ali Baba.
Bayan ta dawo gida, sai ta fara auna zinariyar nan mudu-mudu har ta gama kaf. Ta je ta sahida wa mijinta da yake hakar rami ko mudu nawa ta auna. Ta ce za ta je ta mayar musu da mudunsu. Ashe ba ta lura ba, kwayar zinariya daya ta manne da karon nan a can kasan mudun. Da matar Kasim ta karbi mudu, bayan matar Ali Baba ta tafi, sai ta duba cikin mudun. Wani irin mamaki ya rufe ta lokacin da ta ga kwayar zinariya a cikin mudun.
Nan take hassada ta daki kirjinta ta ce, ashe Ali Baba har yana da zinariyar da ta fi karfin a kidaya ta da hannu sai dai awo da mudu. Ina ya sami wannan dukiya? Ko ya fara sata ne? Bari mijina ya dawo in fada masa halin da kanensa yake ciki.
*** *** ***
ZA MU CI GABA JIBI INSHA ALLAHU02. HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

Lokacin da Kasim ya dawo daga kasuwa tun bai huta ba, matarsa ta tare shi ta ce, "Maigida, na san da cewa ka dauki kanka a matsayin wanda ya fi kowa arziki a duk fadin garin nan, to amma abin da ba ka sani ba shi ne, yanzu akwai wanda ya dame ka ya shanye game da arziki cikin wannan gari namu. Domin yana da tarin zinariyar da ta fi karfin a kidaya ta da hannu sai dai a auna ta da mudu."

Kasim ya ce, "Wane ne wannan attajiri haka, amma dai bai dade da zuwa garin nan ba ko?"

Matar ta ce, "Ba kowa ba ne face dan uwanka Ali Baba." Ta kwashe dukkan labarin yadda matar Ali Baba ta zo aron mudu a wurinta, da kuma dabarar da ta yi har ta gano abin da aka auna da mudun.

Kasim ya kasance ba ya kula da taimakon dan uwansa Ali Baba duk da tarin dukiyarsa, ba ya ko yarda ya matso kusa gare shi, wai kada ya shafa masa talauci. Da ya ji wannan labari daga matarsa, sai ya cika da mamaki tare kuma da hassadar jin cewa wai har akwai wanda ya fi shi arziki a garinsu. Ya ce a cikin ransa, "Yanzu dare ya yi, amma gobe tunda safe zan je gidan dan uwana na ji inda ya sami wannan dukiya da rana tsaka. Lalle idan ya fara sata ne, zan tsegunta wa Sarki a daure shi." Ya kwanta amma ya kasa yin barci, yana ta kahon dandi har gari ya waye.

Da gari ya waye, tunda sassafe Kasim ya sallama wa Ali Baba. Bayan ya fito, ko gaisawa ba su yi ba, sai Kasim ya ce, "Ali Baba ka yi wa mutane badda sau, suna ganin ka a matsayin talaka wanda bai mallaki komai ba sai jakai guda uku da kake zuwa daji kana yiwo itacen siyarwa. Amma abin mamaki, jiya bayan na dawo daga shagona, matata ta ba ni wannan kwayar zinariyar ta ce mini a cikin mudun da ta ara muku ta makale. Wannan ya tabbatar mata da cewa ba hatsi kuka auna da mudun ba. Wannan ne dalilin da ya sa yanzu na yo maka sammako domin na ji inda ka sami wannan dukiya, idan kuwa ka ki fada mini zan je na shaida wa Sarki cewa kana daya daga cikin barayin nan da suka addabi mutanen wannan gari da kewayensa da sata, yanzu haka ma zinariya na nan kime a gidanka da kuka sato. Kuma na tabbata idan aka bincike gidanka kaf, za a gan ta."

Da Ali Baba ya ji wannan zance na dan uwansa, sai ya tabbatar da cewa matarsa ta fallasa musu sirrinsu ba tare da ta sani ba, don haka babu wani boye-boye illa ya fada wa dan uwansa gaskiyar abin da ya faru.

Ali Baba ya kwashe labrin abinda ya faru duka ya fada wa Kasim. Ya yi masa kwatancen dajin nan da kuma dai dai wurin da dutsen da barayin nan suke tara dukiyarsu ya ke. Ya kuma fada masa abin da ake cewa dutsen ya bude da kuma abin da ake cewa ya rufe.

Kasim na gama jin wannan labari, bai zame ko'ina ba sai kasuwa. Ya siyo jakai guda goma, kowane da mangalarsa, ya kawo gida ya daure.

Tun da asuba ya daura wa jakuna mangaloli, ya nufi dajin nan da Ali Baba ya yi masa kwatance. Can zuwa rana tsaka ya isa, ya bi kwatancen da aka yi masa har ya gano wurin da dutsen ya ke. Ya daure dabbobinsa a kusa da dutsen.

Ya tsaya gindin dutse ya ce, "Fayau, bude dutsen Simsim." Rufe bakinsa ke da wuya, sai ya ga kofa ta bude daga jikin dutsen. Mamaki ya rufe shi, nan da nan ya kwanto mangaloli daga jakunansa ya kutsa kai cikin dutsen, yana shiga dutsen ya rufe.

Kasim ya ga ashe dutsen wani katon daki ne mai cin dakuna sama da uku. Ya ga tarin dukiyar da ko a tunani bai taba zaton akwai irinta ba a fadin duniya. Komai bangarensa dabam, zinariya da azurfa da tagulla da tsabar kudi, ga su nan bila haddin. Ba tare da bata lokaci ba, ya fara cika mangalolinsa da ita yana tunanin abubuwan da zai yi idan ya kwashe ta duka ya kai gida.

Da ya gama cika mangalolinsa, ya ga kamar ma bai debi komai ba, domin babu alamun dukiyar nan ta ragu. Ya kiyasta cewa koda zai kwashe dukiyan nan duka, to sai ya yi wata uku ko fiye yana zuwa kullum yana dibar ta. Ya zo inda kofar dutsen ta ke ya ce, "Fayau, bude dutsen Cimcim." dutse ya ki budewa. Ya kara cewa, "Fayau, bude dutsen Jimjim." Dutse bai ko motsa ba.

Kasim yayi ta kiran kalmomi kamar su, Timtim, Kimkim, Zimzim, amma Allah da ikonsa har ya gaji ya kasa tuna kalmar "Simsim." Kamar ma da dai, bai taba jin kalmar ba. Daga nan sai murna ta koma ciki, domin ya tabbata idan barayin nan suka dawo suka same shi a ciki, lalle kashinsa ya bushe.

Sai duk dukiyar da ke cikin dutsen ta fita daga ransa, ya fara safa da marwa yana kokarin tuna kalmar da ake fada dutsen ya bude. Yayi duk iyakar kokarinsa amma ya kasa tuna kalmar. Da ya gaji sai ya sami wuri ya zauna yana tunanin makomarsa idan barayin nan suka same shi a cikin ma'ajiyarsu.

Bai san tsawon lokacin da ya kwashe a cikin dutsen ba. Can sai ya ji karar kofatan dawaki suna nufo wurin da dutsen ya ke. Tun yana jiyo su daga nesa, har suka zo daf da gindin dutsen. Daga nan sai ya ji duk sun sauka daga kan dawakansu. Ya duba cikin dutsen nan ko zai ga wani makami da zai kare kansa da shi, bai samu ba. Ya duba ko akwai wani wuri da zai iya boyewa, ya ga babu. Ya yanke shawarar ya tsaya daf da bakin kofa, idan dutsen ya bude sai ya yi wuf ya yi waje da gudu ya kama dokinsu daya ya sukwane shi, idan Allah ya taimake shi zai iya tserewa. Don haka sai ya tsaya daf da wurin da kofar za ta bude cikin shiri.

Su kuwa barayin nan da suka zo gindin dutse sai suka ga jakai guda goma a daure, suka duba ko'ina ba su ga mai su ba. Sai jikinsu ya ba su, domin ba su taba sa ran wani dan Adam zai iya zuwa cikin wannan daji ba, kuma har...


Read / Download HIKAYAR ALI BABA DA BARAYI ARBA'IN

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album