Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

islamiyya Jalila ba taje ba, kuma Ummi batace ta shirya taje ba, ta kyaleta idonta duk ya kumbura saboda kuka
"Allah sarki baby na banajin dadin ganinki a haka amma kedin ce Zuma seda wuta, gara in horaki" Ummi tayi maganar a zuciyarta
Da yamma likis su Jalila sukaji tsayuwar mota a kofar Gida, Jalila tana tsakar Gida ta zurawa Ummi ido kaman bata Santa ba, Ummi tanaa shan fura,

Cikin izza sukaji sallama
Ummi ce ta amsa sallamar tare da jiran shigowar Wanda yayi sallama
Jalila tana zaune bata amsa sallamar ba balle ta motsa daga inda take,
"Sannu da zuwa shigo"
Ummi tayi maganar tana mikewa tsaye bata gane matar ba tayi zaton irin customers dinta ne
"Ba zamane ya kawoni ba"
"To lafiya meyafaru?"
Ummi ta tambaya
"Nasan baki sanni ba nice Hajiya Safiyya Mrs. Captain Rasheed "
Da sauri Jalila ta daga kai tayi arba da Hanan da mamanta
Maman Hanan ce ta janyo hannun Hanan
"Kalli duba ta'addancin da y"arki tayi kina tunanin kunci bulus ne?"
Gaban ummine ya fadi da taga Hanan

Share please
More comments more typing............
Ina alfahari da masoyana da masu yi min addua ina godiya โคโคโค
Masu bukatar shiga group dina akwai link din group din Asama amma akwai dokoki

๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_
(2020)

_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 26

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

๐ŸŒนhttps://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa

-MY FIRST NOVEL-

Wani mugun kama Ummi taga Hanan tanayi da Jalila, ciwon goshin Hanan ta kalla
"Eyya kiyi hakuri ai munje makaranta akan case din, mun bada hakuri, babanta yace komai ya wuce kiyi hakuri Dan Allah"
"Keda kinsan da bada hakurin kika haifi Yar da bata da tarbiyya, kika haifi yarinyar Datafi karfinki ni na dauka ma Yar wata hamshakin ce Ashe ba Yar uban kowa bace face Mara galihu?"
"Duk me ya kawo wannan maganar, haba ke kuwa Jalila tana da tarbiyya rashin ji ne kawai na yara, kuma batun gata kowa gatansa Allah,"
Wani abune yakawo wa Jalila iya wuya motsa baki tayi da niyyar rashin mutunci cikin tsiwa sukayi ido hudu da Ummi seta hadiye maganarta tayi shiru
"Da wallahi niyyata ubanta zansa akoyawa hankali in yaso gobe yabawa yarsa tarbiyya ya banbance mata matsayin yayan gata da marasa galihu"
"Kar a kuma sakomin uba, a barshi ya kwanta cikin aminci a kabarinsa, ni nayi laifi ba shiba"
Jalila tayi maganar tana jujjuya idanu
"U see mummy wannan yarinyar bazata yi nadama ba memakon tabaki hakuri rashin kunya zatayi miki, in bakiyi Sa a bama zaginki zatayi, kawai kisa a dauketa a je a horata"
Hanan tayi maganar tana kallon Jalila
Da yarabanci Ummi tayiwa Jalila magana, Jalila ta yamutsa fuska ta Dan kara hade rai
"Naji yata ba Yar uban kowa bace bamu da gata se Allah mu bamu su arziki bane, amma kiyi hakuri batun a dauki Jalila a horata be taso ba, bazata karaba"
"Tsiyar talaka kenan ko ince matsiyaci, ya dakko abunda yafi karfinsa, karshe yazo yana karya murya,"
Ta maida idonta kan Jalila
"Kekuma kinci Sa a da ubanki zan Sa akama, wannan uwataki ce ma tabani tausayi, ba dan haka ba da sena Sa an sauya miki halittu, kibari kitaka wani matsayi kisamu me tsaya miki in kinyi rashin mutunci, a yanzu dabaki da galihun nan wahala zaki sha Mara tarbiyya kawai"
"Nice ma ke saboda rashin tarbiyya kuma kar......
Jalila ce tafara magana ummi ta dakatar da ita
Ummi ta kalli mummy Hanan sannan tace,
" nace kiyi hakuri ko, se magana kike akan gata se dai ko nan gaba amma a yanzu dai banajin kinsamu gatan dana samu a rayuwata, sannan yata ba Mara galihu bace ba, da gatan ta, daliline yasa kiga ganmu a haka, amma bazan gazaba Allah yabaki hakuri"
Tsaki mum Hanan tayi taja Hanan suka fita, ga magana fal abakin Jalila amma Ummi ta hanata magana,
Wata kwallar bakin ciki ce ta taru a idon Jalila, meyasa Ummi ta hanata magana daki ta wuce ta kyale Ummi a tsakar Gida

Jawwad Yana ta duba ta inda Jalal ze taho ya hangoshi yana nufo inda motarsu take da ledoji a hannunsa da sauri Jawwad ya karaso
"Ina ka tsaya daga siyen abu"
"Au fitowa kayi nemana, da nasani kulleka nayi a cikin mortar"
"Bar wannan maganar ban mukullin mota ni zanyi driving dinmu"
"Me yasa?"
Jalal ya tambayi Jawwad da mamaki, be bashi amsaba yasa hannu ya karbi key din daga hannun Jalal, suka shiga suka tada mota
Jalal ne ya kalli Jawwad
"Nifa bangane wannan abun da kakeyiba, ina kuma zamuyi , ba gida zamu tafi ba?"
"No wani guri zaka rakani"
"Ina kenan?"
"Just watch" inda sukayi zasu hadu da Hannah ya kaisu, ya kulle Jalal a motar ya fita da wayar Jalal kaman yadda shima yayi masa dazu lambar Hanna ya kira
"Kina daiยฒ ina gamu munzo restaurant din"
"Nabar nan gurin ina bayan layinku rukunin sababbin gidajen nan"
"Haba Hannah amma ba haka mukayi da farko ba"
"Na canza ra ayine ina daf da zuwa gidansu Jalal in bakuyi Sauri ba" katse kiran yayi ya koma motar da sauri ya kunna ya ja motar ya bar gurin
"Nikam naksa gane ma'anar abunda kakeyi Jawwad wai meye haka?"
"Zaka gane ma'anar abunda nake yanzun nan"
Inda Hanna tayiwa Jawwad kwantace nan Jawwad ya kaisu ya kirata yace gasu sunzo, sannan yacewa Jalal ya fito daga motar, ba musu ya fito daga motar yana kallon Jawwad, daga cikin tata motar Hannah ta fito tana wani taku cike da iyayi da isa wata shedaniyar rigace a jikinta straight found ce amma yadin robaยฒ ya kwanta a jikinta yakamata tsam se Dan kwali data daure kanta dashi ta fito da Wig's dinta ya bazu a gadon bayanta,
Da mamaki Jalal ya kalli Jawwad cike da tuhuma da sauri Hannah ta karaso domin rungume Jalal amma yayi saurin matsawa baya
"Meye haka wannan wane irin shirmene baki da hankali niza ki hugging? Meye ma anar hakan daka kawoni nan gurin Jawwad?
Yai maganar a fusace yana kallon Jawwad, Jawwad bece masa komaiba
" ba laifinsa bane, ni nace yakawomin kai ko in maka ba daiยฒ ba kuma Dan na rungumeka ai ba laifi bane, Jalal why are you avoiding me? do you thinks am Jocking danace ina sonka, se wulakanci kake min haba Jalal kalleni sama da kasa banyi kama da irin matar daza a wulakanta ba meye aibuna"
Kallon Jawwad yayi
"You see, meye amfanin hakan dakayi, ka dakkoni ka kawoni gurin wannan mahaukaciyar yarinyar, kalleta kalli jikinta, dan ta rainamin hankali kuma tace tana sona, koda nake shan giya nasan abunda ya dace dani"
Jalal se fada yakeyiwa Jawwad duk yadda Jawwad yaso ya kwantar da hankalinsa yayi masa bayani yaki yadda se fada yakeyi, murmushi Hannah tayi sannan tace
"Masoyina naji kana kasan abunda ya dace da kai, ai babu wani abu me kyau da yadace da kai babyna, nidin dai nina dace da kai, kai duba da yanayin taka rayuuwar, da kuma tawa suna kamanceceniya babancin kadanne kawai"
Kurawa Jawwad ido Jalal yayi"kagani ko ka kyauta" shine abunda Jalal yafada Yakama hanyar tafiya, da sauri Jawwad ya bishi "Dan uwa Dan Allah ka saurareni"
"Nika rabu dani babu abinda zaka gayamin, wallahi in kayi wasa sena Sa an batarmin da yarinyar nan, Dan me zaka dinga cusamin ita dolene sena dinga shiga sabgar matan, I hate her"
Ya juya yayi tafiyarsa yabar Jawwad a nan gurin a tsaye Hannah kuwa dariyar farin ciki tayi saboda tayi nasara, so take dama ta Dan janye Jawwad daga jikin Jalal don tasamu damar gudanar da abinda tayi niyya, tayi nasara tunda Jalal har yayi fushi haka
Jawwad ne ya dawo inda yabar Hannah cikin damuwa ya dubeta
"Haba Hannah baki kyautamin ba kalli yadda yayi fushi, ba haka mukayi dake ba, anya son gaskiya kike masa?"
"Kwarai kuwa son gaskiya nake masa, kayi kokari nagode daka yi dalilin dayasa naganshi at least dukda yaji haushi amma ka faranta min"
"Dan Allah ina rokonki, karki je gidansu Jalal a hakan ma fama ake akan ya canza halayensa, in kika kuma sanadin lalacewarsa biki kyauta ba, Hannah ke mace ce baza kiso ace Jalal danki ne ko yayankine a haka ba"
Yadda Jawwad yai maganar abun tausayi har Hannah taji yana nema ya kashe mata gwiwa Dan haka da sauri tace
"Thank you, ni na tafi semun kuma haduwa"
Ta juya tai shige motarta, bashi dazabin da ya wuce shima ya tafi, Dan haka ya hau motar da sukazo ya tafi

Bayan sallar magariba Jalila durkushe agaban Ummi tana kuka"Ummi Dan Allah kiyi hakuri, najanyo anzo har Gida anci zarafinki nasan laifinane amma insha Allah bazan kuma ba kiyi hakuri Dan Allah "
Hannu Ummi tasaka tana gogewa Jalila hawaye"ya wuce baby amma ki canza halinki ki rike maraicinki ki dena dakko mana magana"
"Ummi na dena insha Allah"" yawwa baby nima ba a son rains name fushi dake ba" rungume Ummi Jalila tayi"nagode Ummina Allah yabaki tsawon rai me amfani"
"Ameen, Allah ya shiryamin me yabaki miji nagari" shiru Jalila tayi tareda kuma gyara kwanciyarta a jikin Ummi
"Ummi amma kinfasa maidani kano ko?
" tafiyarki kano tana nan"
"Ummi meyasa?"
"Haka mahaifinki yace kafin ya rasu" dagowa tayi ta kalli Ummi
"To amma ai yanzu baban nawa baya nan,"
"Zaki kumako ai bazaki canza halinki ba dagani ni"
Mikewa tayi daga jikin Ummi taje ta samu guri ta zauna tana tunani

Duk yadda Jawwad yaso ya shawo kan Jalal ya nuna masa dalilin dayasa ya kaishi gurin Hannah amma Jalal yaki saurarensa
Haka Jawwad ya hakura ya kyaleshi ya tafi gida, yaje yayi salla sannan ya shiga cikin Gida bangaren Abba, ya tarar dashi yana kallon labarai
"Sannu da zuwa Abba ya kabarosu ya hanya"
"Lafiya kalau Jawwad, ai tun dazu na dawo naita zuba ido in ganka, amma banganka ba"
"Mun Dan fitane da Jalal, Abba ya akayi da case din, munyi ways da wani Dan ajinmu yacemin ai ita yarinyar kanwarasa CE"
"Eh kam mun hadu yace ya sanka, ajinku data, Ai Allah ya temakemu abun yazo da sauri,"
Abba ya labartawa Jawwad abunda ya faru
Jinjina kai Jawwad yayi"amma Abba Jalila takirani a waya tana kuka, tace kunce nan zata dawo, zama tare damu"
Murmushi Abba yayi
"Hakane amma Dan mu tsorata ta ne mun yanke seta kammala wannan ajin da take, sannan zata dawo nan, kasan wasiyyar kanina kenan, gara ta dawo nan maybe sekaga ta nutsu"
"Hakane, to Abba ita ummin fa haka zata cigaba da zama ita ka dai"
"A a Jawwad itama zata koma gurin iyayenta ne, intaje insun karbeta se akai Jalila taga dangin mahaifiyarta, ina ganin in Jalila ta dawo nan bata ganin idon umminta zata dena fitina"
"Hakan yayi kyau Abba Allah yasa mudace,"
"Ameen Jawwad"
Haka suka cigaba da tadi daga baya Jawwad ya fito ya koma gurin Jalal amma da yaje baya nan ya kirashi a waya amma baya dagawa,
Girgiza kai Jawwad, yayi yasan ba makawa Jalal ya tafi mashaya
Aikuwa hasashen Jawwad yazama gaskiya domin kuwa don kuwa bayan abunda yafaru tsakaninsa da Hannah da Jawwad, Jalal yakoma Gida yaji ransa yakiyi masa dadi, ransa yagama baci Dan haka ya fita ya tafi mashaya
Aikuwa Jeje ya takewa Jalal cikinsa da giya yayi mankas ya fita hayyacinsa sannan ya kalli Jalal
"Mutumina wai me yabata maka raine haka naganka some how"
Cike da maye Jalal yafara magana yana tangadi
"Wata usless creature ce take son takurawa rayuwa ta, ga Jawwad shima ya bata min rai mtseww, wai meyasa mata suke da matsala kasan mene ma"?
Murmushi Jeje yayi
"sekafada nawan"
"Kasan wannan kanwar tawa ko? Ilham itama fa hadamin zafi tayi da safe so nayi in tattakata amma Jawwad ya hanani kaga itama wannan banzar da take takuramin wallahi so nake inyi maganinta"
Seda Jeje yakuma banka masa giya sannan yace
"To meye a ciki man Hannah ta kai macen daza a sota she's so beautiful fa" Jeje ya dakko waya yana nuna masa hotunan Hannah da wasu irin kaya a jikinta me bayyana surarta
Ture hannunsa Jaalal yayi yana tsaki
"Kai jeje ni bana sonta bana son shirme aikin banza kaima batamin rai zakayi meye hakane kakeyi"
Jalal Ya mike yana tangadi yana shirin tafiya
Jeje a ransa yace lallai gayen nan akwai taurin kai a bugen ma yana da lissafi amma muje zuwa zaka gane kuskuren ka
A zahiri kuma mikewa Jeje yayi ya riko Jalal in bahakaba ze iya faduwa, Dan baze iya tuki ba Dan sosai yake tangadi

Ilham ce take ta kaiwa tana kawowa a dakinta tana tunanin me yakamata tayine, dan tayi Alkawarin fitinar Jalal tako ina bazata bari yafara soyayya da wata banza ba, ba itaba Dan hakan daiยฒ yake da rushewar shirinmu ana samun kuskure komai ze lalace, dabara ce ta fado mata
Dan haka gaban mudubi taje ta zauna, ta fara shafa mayuka a jikinta, tareda fara tsara simple make up a fuskarta, dogon wando tasaka skin tied se wata karamar Riga body hook, ta dakko wannan turaren ta shafe jikinta da shi, parking din gashinta tayi ta Dan Dora mayafi akanta ta nufi hanyar fita
Jeje ne yakawo Jalal gida a buge part dinsa ya kaishi ya kwantar da shi
Jawwad da yake kofar gida yaga wucewar motar Jalal koba a gaya masa ba yasan Jeje ne yakawo Jalal, kuma ba makawa a buge yake, girgiza kai Jawwad yayi cikin bacin rai yakoma cikin gida
Bayan jeje ya kwantar da Jalal ne yazo fitowa daga part din Jalal sukayi clashing da Ilham
"Wow so cute, common beb u look so beautiful"
Jeje yai maganar yana mata wani shedanin kallo
"Kai kashiga hankalinka, ka kiyayeni, bani hanya"
"Meyasa kikeso in baki hanya me zakije kiyi masa? Gaskiya na kyasa ya za ayine?"
Wani mugun kallo Ilham tayi masa
"Eh kaman ba gidan ubanka bane nan, meye na tambayata me zanyi masa kai me kayi masa, ka kiyayeni ka fita hanyata, niba Sa arka bace sakarai kawai"
Ta hankade Jeje ta wuce ajiyar zuciya Jeje yayi "gaskiya yarinyar nan ta hadu I have to do something"
Yasa kai ya fice, Ilham har cikin bedroom din Jalal ta shiga ta ganshi kwance yayi daiยฒ akan gado yana bacci. Murmushi Ilham tayi ta shiga cikin dakin ta samu gefen Jalal ta zauna hannu tasa ta Dan shafa sajensa zuwa cikin sumarsa
Dan jijjigashi take
"Yaya Jalal wake up please"

Share please
More comments more typing................



๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_
(2020)

_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 27

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

๐ŸŒนhttps://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa


-MY FIRST NOVEL-

A hankali ya bude idonsa da sukayi jawur, saboda buguwa ya mayar ya lumshe sannan ya fara magana a cikin mayae
"Ni wannan yarinyar bana sonta, narasa meyasa Jawwad yayi min hakane, nace masa bana so amma shi......se wani"
Sekuma yayi shiru, Ajiyar zuciya Ilham tayi tace"munafukan banza daga Jawwad har kanwar tasa, zasu gane kurensu
Matsawa takuma yi ta kwanta a jikinsa sannan ta Dan dago ta kalleshi
"Meyasa baka sonta"
"Mtseww nifa bana son tambaya, bana sonta kawai bata da hankali," ya Dan girgiza kai ya yamusta fuska warin turaren nan yaji da yabaya so
"Itakuma Ilham meyasa baka sonta?"
Dan bude ido yayi ya mayar ya lumshe"wannan fa kanwata ce, meyasa zanyi wani soyayya da ita, kanwata ce kawai"
Shigewa jikinsa ta kumayi sosai
"But I love you, karkayi soyayya da wata bayan ni, Ilham ce kawai take sonka, sauran duk bamasu kaunarka bane, Ilham tana sonka kaima kasota kaman yadda take sonka"
Dukda yana cikin maye setaga yayi murmushi"ka yadda zakaso Ilham"
"Bacci nakeji ki kyaleni da wannan mafarkin"
"Mafarki kake?"
Ya gyda mata kai "ya kusa faruwa a zahiri"
Tai maganar tana shafa gashin kirjinsa ya mutsa fuska yayi ya rike mata hannu"kidena bana so"
"Meyasa bakaso?"
Shiru yayi be ce mata komai ba
"Shikenan tunda bacci zakayi bari in tafi,"
Durkusowa tayi da nufin tayi kissing dinsa se ya juyad da kansa alamun baya so, kallonsa tayi
"Why?"
"Ki tashi ki bani guri nace miki bacci zanyi"
Gabanta ne ya fadi dataji yayai normal magana ba tare da maye ba, kallonsa tayi taga ya bude idonsa fes akanta, sekuma ya mayar ya lumshe yacigaba da bacci Ajiyar zuciya tayi tare da fading"Allah ya temakeni na dauka giyar tasakeshi ne"
Kissing dinshi tayi akan lips dinsa sannan ta mike ta fita ta nufi cikin Gida, me gadi ya hango fitowarta daga part din Jalal
"Kai me yarinyar nan take a bangaren yaron nan a wannan tsohon daren,
Allah ya kyauta bayan shan giya kuma yafara biyeยฒ mata, abun kunya kuma da kanwarsa Allah ya shirya"

Da safe Jalila tanata shirin makaranta, wata makwabciyarsu bata wuce sa ar Jalila ba ta shigo tacewa Ummi Dan Allah ta sammata abunda ta girka ita tayi girkin takasa ci dayake tsohon ciki ne da ita
"Allah sarki hawwa'u Allah yaraba lafiya bari azuba miki
Jalila zubomata abinci"
Jalila kam zuwa yanzu Hawwa haushi take bata gani take tsabar kwadayine da iskanci komai bazata iya Ciba sena gurin ummi, Ummi kuma bata taba hanata ba ko kyararta
Jalila tana zumbura baki taje ta zubomata dataga ummi bata kallonta ta dungurar mata da kwanon da kayan tea
"Gashi nan kwadayayyiya seki hada Sa kanki niba Yar aikinki bace"
"Eh naji kwadayaiyiyyar ce ke in naki yazo maga yadda zakiyi"
"Bawani nan komai kidorawa ciki, dayana da baki se yace karya kike masa"
Dariya Hawwa tayi ta hada abincinta ta fara ci suna hira da ummi tana gama ci ta kama aman abincin nan dataci seda ta amayar tsaf
"Kai kekam kin banu sekace akanki aka fara ciki ga rakin tsiya ni bari in bar gidan nan tun kafin nima kisani aman"
Jalila tai maganar tareda daukar jakar makarantarta tayi waje
Girgiza kai ummi tayi indai Jalila ce bazata canza ba

Wajen karfe Tara sannan Jalal ya tashi daga nannauyan baccin da yayi kansa yana ciwo, jiyayi yana warin turaren Ilham tsaki yaja yafara tunanin abunda yafaru wannan wane irin shaยณ mafarki yayi kuma ma da Ilham (shi a zatonsa abunda yafaru mafarkine)
Mikewa yayi yaje yai wanka ya fito yayi sallar asuba karfe Tara na safe

Jalila tana kokarin shiga makaranta taji ana tayimata horn bata waiga ba ta koma gefe akakuma tahowa inda take a fusace tajiyo tana masifa
"Wai meye hakane anyi Horn na canza hanya ankuma biyoni if you like bi ta kaina komawaye"
Bude motar yayi ya fito tana dariya Allah yabaki hakuri Yar baba,
Yayan Hanan ne Abdallah yakawo Hanan makaranta murmushi Jalila tayi
"Au ai bansan kai bane ina kwana"
"Lafiya kalau ya mamanki"
"Tana lafiya"
Juyawa yayi ya kalli motar yace"ke Hanan fito mana kin wani Zauna a cikin mota"
Sannan ya dawo da kallonsa kan Jalila "Yar baba kaman kuwa kinsan daddy yace agaisheki har yabada sako abaki"
Hanan ya kalla wadda se wani cika take tana batsewa
"Hanan bani sakon nan"
A wulakance ta bude Jakarta ta miko masa wata Leda
Ya karba yabawa Jalila
"Kai amma nagode sosai Yaya Abdallah ka cewa baba Yar baba ta gode, Allah yasaka masa da Alkhairi yabashi abunda yake nema duniya da lahira, Allah yabashi ladan kyautatawa marainiya"
Ba Karamun burge Abdallah tayi ba,"zangaya masa insha Allah"
Tsaki Hanan tayi ta wuce abunta cikin school, Jalila ma cikin makaranta ta shige, duk zafin kan Hanan bata kuma kallon seat din Jalila ba balle takuma sha awar zama a gurin,
Zama Jalila tayi ta dakko abunda akabata chocolates ne kalaยฒ a ciki murmushi tayi gaskiya mutumin nan yana da kirki
Bayan anfita break Jalila taje seat din Hanan ta zauna a kusa da ita kawata ya kike
Wani mugun kallo Hanan tayi mata ta dauke kai, bude chocolate dinta tayi tafara sha sannan ta kalli Hanan kawas
"Bismillah"
"Abun ya fito daga gidanmu sannan kice insha ke dai da kike kwadayaiyiyya seki sha dama Dan talaka akwai iya shishshigi,"
Murmushi Jalila tayi sannan tace "duba ajin nan akwai yayan Wanda sukafi mahaifinki dukiya, amma abun be baki mamaki ba ina Yar talaka amma nake makarantar yayan attajirai kaman Hanan rasheed, ashema Baku wani Tara ba tunda har Yar matsiyata kamar Jalila Aliyu take a irin makarantar Ku"
Mike kafa Jalila tayi ta Dora a saman bencin
"In ana batun gata Hanan, be kamata kisaka baki ba, Dan baki da gatan da Jalila take dashi"
Jalila se gayamata bakaken maganganu take tana shan chocolate dinta, Hanan tana fargabar ramawa saboda gani take Jalila bata Risina ba zata iya maimaita mata abunda tai mata amma duk da haka ta dake tana ramawa

Jawwad ne yakuma dawowa gurin Jalal amma Jalal yayi masa banza yaki kulashi, haka ya hakura ya tafi ya kyaleshi

Bayan an tashi daga makaranta Jalila ta dawo Gida amma ummi bata nan wani bakin ciki Jalila taji ta tsani ta dawo Gida taga ummi bata nan
Waya ta dakko ta kira ummi
"Ummi ina kika tafi ne?"
"Kinganmu a asibiti Hawwa muka kawo ta haihu Dan ba rai yanzuma Karin jini ake mata"
Zaro ido Jalila tayi
"Wace hawwan dazu fa da safe tazo"
"Bayan tafiyarki tafara nakuda"
"To meyasa akayimata aure yanzu se wahala takesha?"
"Aa seki bari in danginta sunzo ki tambayesu"
"Allah yabaki hakuri itakuma Allah yabata lafiya amma Dan Allah ki dawo Gida"
"Bazan dawo ba din a can zan zauna"
Ummi ta kashe wayar

Seda Jalal ya shafe sati baya kula Jawwad, sekuma daga baya Dan kansa ya sakko, suka shirya
yayinda kullum se Jalal yaje mashaya, Hannah tasamu damar cigaba da cusa kanta, a gefe daya itama Ilham tanata nata kokarin, sunsaka Jalal a gaba, Jalal dai se kara shirircewa yake

Alhamdilillah Neman maganar Jalila daga Islamiyya har boko yayi sauki, ta fara nutsuwa, yayinda mahaifin Hanan keta kyautatawa Jalila, amma Jalila ta takurawa Hanan, kullum tana manne da ita, Hanan ta zageta ta gaya mata bakaken maganganu amma Jalila batajin haushi takance mata"Hanan mahaifinki yana da karamci, yana kyautata min, komai zakiyi min bazanji haushi ba, shiya hadamu kawance kuma ni na karba"
Hanan mulkinta take zubawa a cikin makarantar daga malamai har dalibai shakkata sukeyi,amma banda queen J

Watarana anayiwa wata Yar ajinsu Jalila birthday a aji, kunsan yayan masu kudi aka dinga jijjiga champaign suna sakinta a sama, suka dauki turare suka dinga fesawa a ajin sun ware kida suna cashewa
Hanan ce ta nufo ajin ta shiga tana shiga wannan kamshin turaren da akasaka ta shaka nan take ta fadi kasa dama tanada asthma, da sauri Jalila taje kanta tana jijjiga ta
Yan ajin tsayawa sukayi suna kallon Hanan data ke ta fama da numfashi,
Jalila ta dinga jijjigata "Hanan meyafaru, ki tashi"
Jalila taga hakan bazeyiba tasa ta dago Hanan ta rungumeta zata fita da ita amma jikinta yariga ya saki yan ajin suna kallo ba Wanda yabi takan Hanan saboda rashin mutuncinta balle ayi tunanin me temakamata
Jalila ce kawai taketa kiciยฒ da hanan, ana haka Sega siyama
"Jalila meyasameta?"
"Nima bansaniba amma kaman asthma ne,"
Jalila da siyama ne suka kama Hanan suka kaita school clinic akaimata abunda yakamata amma babu wani cigaba duk ta fita hayyacinta
Aka kira gidansu hanan aka sanar dasu, sukace akaita wani asibiti private anan likitan dayake duba hanan yake,
a motar makaranta aka saka hanan Jalila tana rungume da ita

Please Login or Register in order to submit comment