Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ransa
Abba yayi murmushi
"Jalila kayan Jalal aina Jawwad ne, Dan haka tasuce su biyun" Jalila ta kalli Jawwad
"Yaya congratulations Allah yasa rai da lafiya akayiwa"
"Ameen baby mungode"
"Abba to mu se yaushe za a saimana?"
Nana tai maganar a shagwabe
"Ku tambayi yayanku, shize saimuku, gata mamanku can Ku dinga hawa ko Jawwad yabaku tsohuwar tasa, in kunshiga university seku dinga Ja"
"Abba ta Yaya Jawwad dinfa duk ta tsufa wallahi,"
"Yana jinki dai, in kun gama Ku nabaku naku tsarabar a cikin Gida"
Daga nan Abba yai cikingida yana dariya, Maama tabi bayansa
Jalila ta kalli Jawwad
"Yaya muje a danamu a motar, dama zamuje duba exams"
"To ku taho muje daga nanma muje shan ice cream"
"Amma Yaya yaushe zaka fara koyamana mota,?"
Nana ta tambaya
"Ku tambayi Jalal seya koyamuku rigimanmun Abba kawai"
"Tabdijan, waye ze koyamana tukin, ba tukin jirgin sama mukeso akoyamana bafa tukin mota Yaya Jawwad, wannan ai tukin jirgin sama yakewa mota"
Jalila tai maganar tana hararar Jalal, yana kallonta ta cikin mudubin motar
"Ba ruwana ke dashi"
Jawwad yafada yana dariya, cikin Gida suka nufa suka dakko hijjabai, da wayoyinsu suka fito
Tunda Jalila taga, Jalal a mazaunin direba taga shi ze tuki jikinta yayi sanyi, Dan tana ganin yanda yake Jan nasa motar

Share please
More comments more typing...........................
Love u all my fans comments dinku na kayatar dani dakuma Sani nishadi
Love you allโคโคโคโค
SANARWA!!!
wasu suna tambayata ko nayi joining wata kungiyane na online writers
Gaskiya ni banyi joining kowace kungiya ba, kamar yadda kuke gani wannan shine Novel dina na farko, kuma basirata ce nake amfani gurin nishadantar daku tareda aikawa da wasu sakonni, babu wata ko wani marubuci dayake bani gudunmuwa
Dafatan masu tambaya kun gamsu
Game gyara, comments, tambaya ko korafi, akwai lamabata danake sakawa a farkon kowane page a tuntubeni ta wannan lambar nagode
Taku har kullum Yar babanta(daddy's girl)
๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[8/31, 8:30 AM] Safiyya: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_
(2020)

_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 35

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

๐ŸŒนhttps://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys โคโคโคโคโค

-MY FIRST NOVEL-

Nana ta bude motar ta shiga, motar tayi kyau matuka, Jawwad ya kalli Jalila
"baby shigo mana"
Jikinta a sanyaye ta bude motar ta shiga, Jalal yai musu banza yacigaba da danna wayarsa
Jawwad ya kalleshi "muje ko"
"Ina zuwa" yacigaba da aikin wayarsa sun shafe kusan minti goma shabiyar a zaune sannan yayiwa motar key, aikuwa kamar yadda Jalila take fargaba a guje ya fafari motar nan kaman zasu tashi sama, Jalila se rarraba ido take tana karanta adduo'i dabanยฒ a zuciyarta, tabbas Jalila ta yadda sun hau motar Dan giya, yadda yake gudu dasu sekace a Action movies kaman ba mutane ya dakko ba haka yake ratsa manyan motoci yana overtaking
"Wayyo Allah Nikam nashiga uku gaskiya a tsaya in sauka wallahi, na hakura da duba Jarrabawar, ni kadai Ummi ta Haifa baza a kasheni a wannan gangancin ba"
Jalila tayi maganar da karfi
"Yi hakuri baby, Jalal Dan Allah sassauta gudun nan Jalila a tsorace take, guri yasamu yaja wani arnen parking
" ta sauka ta fita in bazata iya zama ba"
"Wallahi bazan sauka ba sedai kai ka sauka ai ba......." Bata gama ba Jalal ya juyo yana kallonta tai saurin yin shiru
Jawwad yace
"Baby kiyi hakuri babu abinda ze faru lafiya zamuje insha Allah"
"Ni gaskiya tsoro nakeji"
Nana ta kalli Jalila tana dariya
"Runtse idonki ki kwanta akan cinyata zaki denajin tsoron"
Ba musu ta kwanta akan cinyar Nana ta runtse ido Jalal ya Dan kalleta, ya maida kai ya cigaba da bawa sabuwar motar Jawwad wuta
Jalal Ya samu cafe a hanya yayi parking
Suka fito daga motar gaban Jalila se faduwa yake tana fargabar me zata gani a result dinta, Jalal yana zaune a cikin mota be fito ba
Jawwad yai musu Jagora suka nufi shiga cafe Jalila ta tsaya a kofar shiga
"Ya dai muje mana"
Nana tai maganar tana janyo hannun Jalila
Jalila tayi ajiyar zuciya
"Nana karbi exam card dina ni bazan shigaba abinda kuka duba seku gayamin"
Ta karasa maganar kaman zatayi kuka
"Haba Jalila in kika karaya nikuma ince me, karki damu taho mushiga"
"Nana Allah bazan shigaba, ina nan sekun fito"
Haka Nana ta hakura ta kyale Jalila, tabi bayan Jawwad yayinda Jalila ta tsaya a kofar gurin, kallon da mutane kewa Jalila ne yafara bata haushi Dan ita bata San kallo
Jikin motarsu ta koma taje ta jingina ta tsaya, Jalal ya bude kofar motar ya kashingida a jikin kujerar mota
Jalal ne yake waya tana iya jiyo abinda yake cewa dukda a hankali yake maganar
"Hannah meyasa kike takuramin a rayuwata, kin uzzuramin wallahi,
Ke ko zuciya baki da ita, haba Dan Allah nifa bazan iya wannan shirmen nakiba, kozanyi aure Hannah kinsan bazan iya auren mace kamarki ba"
Jalila ta Dan waiga ta kalleshi,
Taja tsaki
"Mtseeew shirme, sekace wani mutumin kirki, suna zubarwa da Kansu mutunci a gurin wannan Dan giyar, wahalallu dagasu har shi, kowace wannan Hannah oho" ta cigaba da mita daga inda take
Wayarsa yacigaba da yi Dan besan tanayi ba
Jawwad ne da Nana suka fito daga cafen, fuskarsu babu annuri suka nufo inda Jalila take
Hankalinta ne yai mummunar tashi ganin yanayin fuskarsu, suka karaso bakin motar
"Na fadi ko yaya, banciba, na fadi Jarrabawar ko?"
Mikomata paper yayi sannan yace
"Congratulations my dear u got it, am proud of you"
Yai maganar yana murmushi tareda Jan hancin Jalila, bude result din tayi
Aยน bakwai tasamu B guda biyu
Rungumeta Nana tayi
"Ina tayaki murna Babyn Abba"
Jalila ta kalleta "Nana me kika samu"
"Nine credits ne"
Murna suka cigaba dayi
"Is OK murnar ta isa haka, kushiga muje, aje shan ice cream, proud of you all, Allah yayiwa karatunku albarka"
"Ameen suka fada a tare"
Suka bude motar suka shiga, Jawwad ya dubi Jalal yace
"Jalal kaga results din su Nana, Alhamdilillah, result yayi kyau, mussaman na Jalila"
Dan kallon papers din hannun Jawwad yayi yana kokarin kunna motar
"Mmm yayi kyau Allah yasa ba satar amsa tayiba"
Kutmelesi Jalila taso gayamasa bakar magana Dan dai Jawwad yana gurinne, Jawwad ya kalleshi
"Wuce nan bros, duk cikinsu ba wadda take satar amsa"
"How sure are you?"
Jalal ya tambayeshi
"Obviously na yadda da kannena, ranar graduation dinsu Jalila awards din da aka bata sun isa su tabbatar daba ta satar amsa"
"Hmmmm" shine abinda Jalal yace ya fizgi motar a guje yabar gurin
Jalila kuwa se kunkuni take tana magana a ranta, ita kuwa Nana se hira take mata, tana kuma jinjinawa Jalila dangane da result dinta, itakuwa Jalila Kalmar satar amsa ta bakanta mata rai sosai
"Ashe dai ba iya Neman maganar aka iyaba kan yana kawo wuta, shiyasa kike burgeni mutuniyata, baki da wasa"
Nana ta fada tana Jan hancin Jalila
Jalila ta rirrike Nana, saboda gani take a kowane lokaci motar nan zata kife saboda tukin da Jalal yake
A wani joint sukayi parking Jawwad yayi musu rakiya sukaje suka sai abinda sukeso, sannan suka fito suka nufo hanyar gida
Suna cikin tafiya Jawwad yace
"Baby, Nana dai mass com takeso, kekuma fa?"
"Yaya ni nursing nakeso,"
"Wow, u can do it, Allah ya temaka"
Wayar Jalila tafara ringing bakuwar lamaba ce, kamar karta daga, sekuma ta daga tare da yin sallama
"Wa alaikum salam, Jalila Ashe kinkoma kano babu labari?"
Jalila ba ta dau muryava Dan haka tace "wake magana"
"Kai Yar baba, kardai kice baki ganeniba"
"Subhanallah, Yaya Abdallah yi hakuri kasan banida lambarka se yanzu nagane, barka da yamma"
"Yawwa Jalila, yakike?"
"Lafiya kalau ya daddy"
"Yana lafiya, Ashe kinkoma kano, nazo Gida attending birthday Hanan, take gayamin"
"Aikam dai Yaya Abdallah ina kano,"
"Kice zamu dinga haduwa kinsan a bayero nake karatu, na dinga kawomiki ziyara"
"To shikenan Yaya nagode sosai"
"Insha Allah weekends din nan zamuzo, da daddy da Hanan"
"Dagaske Yaya"
"Dagaske nake"
Zuwa yanzu Kishine yake cin Jawwad jin yadda Jalila ta saki jiki tana waya, da wani namiji, Jalal ya Dan kalleshi yaga yadda ya wani hade rai, Dan murmushin gefen baki Jalal yayi yacigaba da tukinsa
Jalila suka gama waya da Abdallah ta kalli Nana
"Nana da weekends insha Allah usainata zasuzo, zasu kawomin ziyara"
"Wa kenan?"
"Hanan mana"
"Dan Allah dagaske"
"Wallahi Nana"
Jawwad ya Dan gyara zama
"Baby da wa kike waya?"
"Yaya Abdallah ne"
"A ina yake?"
"Abokin nan nakafa, Dan gidan captain Rasheed"
"Hmm nagane"
Daga nan be kuma cewa komai ba harsukaje gida, lokacin ana kiran sallar magariba,
Suna zuwa gida suka tarar Maama tana salla Abba kuma ya tafi masallaci, Dan haka suka tafi dakinsu, halimace ta biyosu a baya, tana fadin
"Jalila ya akayi,? Ya jarrabawar kuwa?" Jalila ta tsaya tana murmushi, Nana kam bata tsayaba ta wuce dakinsu
"Leemart jarrabawa Alhamdilillah, kinga results dinmu" Jalila ta mikamata result din
Karba halima tayi ta duba
"Masha Allah, Jarrabawa tayi kyau kam, Allah ya sanya alkhairi, Yasa a ci gajiyar karatu"
"Ameen my leemart, bari inje zanyi salla"
"To shikenan"
Bayan sunyi sallar magariba suka tarar da Abba a part dinsa Maama ma tana part din, suka bashi result din yayi murna sosai yai musu addu a, da fatan alkhairi
Sannan ya dauki kayan da yakawo musu tsaraba yabasu, na Jalila harda brown din Teddy da kayan sawa na alfarma, sukayi masa godiya
Nana se tsokanar Jalila take wai ta ci sunanta baby ta girma amma tana wasan teddy
Maama ta tabe baki
"Nima haka Nagani, yarinya da girmanta amma kana sai mata teddy, wannan ai sangarta ce"
Murmushi Abba yayi
"A ganinkine sangarta, ni a gurin kyautatawane"
Da Jalila taji haka ta mike ta bar part din gaba daya ta koma dakinsu
Suturar da Abba yabasu manyan suturune masu tsada matuka
Bude trolley dinta tayi ta debo wasu kaya masu kyau kala hudu, ta Dora turare body spray da roll on, ta bude kayan dasuka siyo, dazu dasuka fita ta dakko ice cream roba daya ta hada ta fito, sukayi clashing da Nana ta kalli kayan hannunta
"Wannan kuma fa? Me zakiyi dashi"
" Halima zan bawa"
"Saboda me"?
"Nima Allah yabani wasu, ba tare da yayi shawara daniba"
"Kudi fa ake biyanta meyasa zaki dauki kayanki masu kyau kibata"
"To meye a ciki Nana, naci jarrabawa Alhamdilillah Abba yamin kyautuka, yakamata mu farantawa wasu muma"
Dan tabe baki Nana tayi ta wuce daki yayinda Jalila ta nufi dakin halima

Ilham tarasa abinda yake mata dadi yan kwanakin nan takasa gane inda Jalila tasa gaba shin da gaske Jalila tana son Jalal, kokuwa, amma in tana sonshi ya za ayi tagaya masa wannaan miyagun maganganun,
Amma kuma ya akayi Jalila take gaya masa maganganu son ranta amma be dau wani mataki akanta ba, Wanda ta tabbatar ita bata Isa tayi masa haka ba,
Kenan shima yana son Jalila, tunda take gaya masa maganar data ga dama amma ya kyaleta
"Kan uba karyane wallahi ina wani shirmen hakan ze faru"
Tai maganar a fili
"Ko mami zan kira in gaya mata abinda yake faruwa, yanzu ina gaya mata ni zatayiwa fada tace laifinane, kuma baze yiwu in gayawa Nana ba tunda Yar uwattace za a iya hada kai da ita a cuceni, yanzuma watakila bakinsu daya"
Tayi nannauyar ajiyar zuciya to ni yazanyine?
Ko gidan malamin nan zanje da kaina innemi yaseera ta rakani(kawar Ilham ce) hakama za ayi inje inji ya za ayi aimin maganin wannan tantiriyar
Da wannan shawarar da zuciyarta ta bata ta samu nutsuwa

Halima ta kalli Jalila
"Jalila inani inasaka wannan kayan masu tsada"
"Leemart to meye a ciki, ba wani kaya masu tsada, sedai in abun hannuna ne bazaki karba ba"
"A a Jalila ba haka bane,"
"To in ba hakabane kawai ki karba"
"Nagode Jalila, Allah ya faranta miki kaman yadda kikayimin"
"Ameen leemart"
Jalila ta koma daki ta kira Ummi a waya tagaya mata abinda tasamu a result dinta Ummi tayi murna sosai, sannan tace
"Jalila ya yanayin zamanki a kano? Naji muryarki cikin farin ciki ina fatan komai lafiya?"
"Komaiafiya Ummi, bakiga Mayan da Abba ya siyo mana ba,"
"Masha Allah, haka nakeson ji, yacigaba da hakuri da rayuwa Jalila,"
"To Ummi insha Allah, Ummi da weekends insha Allah Hanan zasu kawomin ziyara"
"Dagaske baby"
"Dagaske Ummi, dazu Yaya Abdallah ya gayamin"
"Allah sarki gaskiya suna kaunarki Jalila, Nima next week insha Allah zanzo, daga nan zan wuce garinmu"
Haka nan se Jalila tayi jikinta yaysanyi
"Ummi tafiyar tana nan Ashe zakiyi,?
"eh tana nan zanyi insha Allah"
"To Allah ya kaimu, next week din"
"Ameen ki gaida mutan gidan"
"Zasuji insha Allah"
Nana ta Dan kalli Jalila
"Yanaga jikinki yayi sanyi"
"Nana banason tafiyar nan da Ummi zatayi"
"Haba Jalila, Ummi yakamata tayi tafiyar nan yana da kyau taje taga danginta"
"Hakane Nana"
"Yawwa to kidena tayarda hankalinki, kiyimata addu a kawai"
"To Nana"
"Yawwa babyn Ummi"
Daren ranar Ilham batayi baccin kirkiba se tufka da warwara kawai tekeyi, kamar ta janyo safiya tayi domin taje gurin malamin nan
Washe gari da safe wajen karfe goma Ilham ta shirya tacewa mummy zataje gidansu
Ummi tace seta dawo, tana fita ta tafi gidan su yaseera, suka gaisa da Maman yaseera sannan ta wuce dakin yaseera, ta tarar yaseera ta shirya ita take jira ko zama Ilham batayiba suka fita ita da yaseera sukayi gidan malamin nan

Share please
More comments more typing................................


๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[8/31, 8:30 AM] Safiyya: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_
(2020)

_ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 36

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

๐ŸŒนhttps://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys โคโคโคโคโค

-MY FIRST NOVEL-
Ilham ce da yaseera gurfane a gaban malamin nan, malamin ya kalli ilham sannan yace
"Ya kikazo keka dai yau ina babartaki?" Ilham ta Dan gyara zama
"Malam akwai matsalane fa"
"Matsalar me?"
"Malam, nifa na fara gajiya da wannan wahalar danakeyi akan Jalal, ina ta nawa kokari amma, wata Matsala na kokarin kunno kai, duk wannan wahalar danake yana kokarin fara soyayya da wata yarinya daban, hankalina duk a tashe yake"
Malamin ya numfasa ya kalli Ilham sannan yace
"Anya kuwa dagaske kike yafara soyayya, a aikin damukayi akansa bana tunanin ze iya fara soyayya cikin sauki, har se burinku yacika,"
"Malam nifa tsoro nake, kar inje shirin ya rushe gaba daya"
"Hakane in dai ba wancan sharadin ne ya afkuba, to aikin damukayi masa yana tareda shi har yanzu, koda kuwa yayi soyayya da wata, sedai in wancan sharadi ya karya"
"Wallahi ji nake kamar kawai in aiwatar da me gaba dayan tunda har yanzu yaki yadda ya soni, balle ya aureni"
"Wannan kuma ya rage naki sekije kicigaba da kokari, ko be sokiba daya aureki shikenan aiki ze kammala"
Yaseera ta kalli malamin
"To yanzu malam babu yadda za ayi da wannan shedaniyar yarinyar, tunda akwai yiwuwar ya iya fara soyayya"
"Wannan kuma Ku zakuyi wannan aikin ni nayi muku kokarin da yakamata sekije ki bada himma, zanyi bincike akanta, muga abinda za ayi akanta"
"To shikenan malam zanje in cigaba da kokarin"
"Yayi kyau, abinda ake ciki zan sanarda ke"
Suka mike suka fito yaseera ta kalli Ilham
"Wai Ni kuwa Ilham wace wannan yarinyar"
"Hmm wallahi kanwar abokinsa ce wata Mara mutunci da ita, yaseera yarinyar nan bata da mutunci Sam, idan banyi wasa ba fa zata bata min aiki, kinga rashin mutuncin da take masa amma ko kallonta ba yayi balle ya dau mataki, kuma da nice na gayamasa abinda take masa da tuni ya hukuntani"
"Kince sonshi take, kuma kince tana masa rashin mutunci, anya kuwa son nashi takeyi"
"Nima abinda nake ta tantama kenan, amma nafi tunanin borin kunya suke a gabana amma sonshi take, kinga a yadda nagansu kuwa ranar a gidansu, wallahi bantaba tunanin haka kishi yake ba se ranar"
"Wai ma inane gidansu"?
"A gidansu Nana take fa cousin dinsu ce"
"Muje gidan inga wace ce, inga iya rashin mutuncin nata se mu San ta inda zamu bullo mata"
"To shikenan mu karasa, ki ganta,"
Hannah ce kwance akan gadonta tana zancen zuci, "mace kamarni ace Jalal yake wulakantawa, ga yadda maza kemin layi amma akan wannan Dan tahalikin, nake wahala har wani cewa yake ko ze aure baze aureniba, na tabbatar ranar Dana kirashi wannan kanwar tasa ce ta daga har take zagina, zanyiwa Jeje aikinsa sannan itama kanwartasa senayi maganinta, nita zaga saboda tana son Jalal, zata ga tsiya, indai Hannah ce ta taro daidanta"

Nana ta fito ta tarar da Jalila a kwance akan kujera tana danna waya
"Jalila zan Dan fita, zanje bayan layi ne Maama ta aikeni"
"To sekin dawo"
Fitar Nana ba dadewa aka turo kofar palourn ba ko sallama, mutane taji tsaye akanta
"Dan Allah ina Nana"?
Shiru tayi ba tako daga kai ba, balle ta ga suwaye
" magana fa nake miki"
Ba ta dago kanta ba tabada amsa
"Taje akoya mata sallama, inzaka shiga guri"
Yaseera ta kalli Ilham, sannan tace
"Yi hakuri Dan Allah, salam alaikum"
"Wa alaikum salam warahmatullah"
Jalila ta amsa sannan ta tashi zaune
Ta dubesu ta danyi murmushi
"Sannunku da zuwa bismillah ga guri Ku zauna"
Ilham se wanj hura hanci take
Jalila ta Dan kalli Ilham sannan ta maida idonta kan yaseera
"Nana ta Dan fitane ba nisa tayiba yanzu zata dawo insha Allah"
Yaseera ta danyi murmushi,
"To mungode"
Suka samu guri suka zauna
Jalila tace
"Ilham ya kike,? Ya Gida"
Ilham tai mata wani irin kallon up and down
"Da nazo nayi miki maganane? Kokuma ke a dole sekinshiga harkata"
"Ko in shiga harkarki ko kar inshiga harkarki babu abinda zaki kareni dashi ko ki rageni dashi, tunda ba abunda nake nema a gurinki nayi hakanne kawai Dan sauke hakkin addinina, ke Yar uwatace musulma, kuma makociya, muna da hakki akan juna shinake kokarin saukewa kawai, bawai wani abuba"
Tabdijan yaseera a zuciyata tace "lallai wannan yarinyar yar duniya ce tana da baki, gashi komai nata abin birgewa yanayin yadda take magana kawai ya isa ya dau hankalin mutum, ga iyayi kuma dajin maganarta kaga shgwababbiya gashi ta iya juya ido in tana magana" yaseera kallon Jalila kawai take
"Bakuwa bari in kawo miki abin tabawa kafin Nanan ta dawo, naga Ilham se wani cika take tana batsewa bansan menayi mataba"
Jalila ta mike tana tafiya a gayance ta nufi fridge
Lallai dole Jalila ta tafi da imanin duk Wanda yai tarayya da ita dukda Ilham tace mata bata da mutunci amma tana ganin hakan duk cikin iya takunta ne
Lemo Jalila ta kawo musu da ruwa sannan ta kira Nana a waya, ta gayamata tayi baki, Nana tace mata takusa karasowa tana daf da Gida
Yaseera ta kalli Jalila
"Nagode Yar uwa"
"Bakomai yiwa Kaine bakin Nana ai baki nane"
Ilham bata kuma cewa komaiba, tunda Jalila takuma gaya mata magana, sema haushin yaseera daya kamata ganin yadda ta zage suna hira da Jalila kamar sun saba
Ana haka Nana ta dawo,
"Yawwa ga Nana nan ta dawo"
Nana ta kalli inda su Ilham ke zaune
"Yaseera dama talaka na ganinki gaskiya akwaiki da zumunci"
"Yanzunma unguwa mukaje nacewa Ilham mu biyo mu gaisa kwana biyu bamu haduba"
Nana tace "hmm kin kyauta ya Gida ya kwana biyu?"
"Lafiya kalau"
Jawwad ne yayi sallama a palourn suka gaisa dasu Ilham
Sannan ya kalli Jalila
"Baby yunwa fa mukeji kuma munji ki shiru, Jalal ze sha magani beci abinci ba"
Kallon Jawwad tayi ta danyi murmushi
"Aini yau banyi girkiba, in kuma kunajin yunwa to kuzo kuyimin wankeยฒ wani yayi gyaran kayan miya" murmushi Jawwad yayi ya nufi hanyar kitchen Jalila ta mike tabi bayansa, Ilhaam kam Dan bude baki tayi
"Hmm Yaya Jawwad manyan"
Nana ta fada tana Dan murmushi
Ita dai yaseera ta jinjina yadda Jalila take gudanar da
al amuranta cikin nutsuwa, lallai indai da Jalila, Jalal yake
Shirin fara soyayya to se Ilham tayi dagaske, don Jalila bazata sha wahala gurin sace zuciyar duk Wanda taso ba
Jawwad ne yake bubbude kwanuka a kitchen
"What are you looking for?"
Yaji muryar Jalila a bayansa, juyowa yayi ya kalleta
"yunwa fa mukeji baby" yai maganar yana kwaikwayon JALILA
"Yi shiru karkayi kuka jeka zan kawo"
"Inyi kuka sekace wani baby, Babyce me kukan allura, kuma nasan in tanajin yunwa ma setayi kuka"
Dariya sukayi gaba daya
Wanda hakan yayi daiยฒ da fitowar Maama tana kallonsu ta window kitchen, kwafa maama tayi ta nufi parlour
Su yaseerana suka gaida maama ta amsa musu sannan tace ma Nana taje tacewa Halima tana kiranta, tajuta ta koma dakinta
Su yaseera suka mike sukace zasu tafi, dama ba ziyarar Allah da annabine ya kawosu ba Dan ILHAM ta nunawa yaseera Jalilane, suna shirin tafiya
Jalila suka fito ita da Jawwad, suna dariya, Ilham ta kallesu taja uban tsaki
Jalila ta kallesu "har zaki tafi, yaseera, mungode ki gaida Gida, Ilham ki gaida mummy"
Ilham bata kula Jalila ba itama Jalila bata damuba Dan tasan ILHAM ba amsawa zatayiba, tai waje da kayan abincinsu Jawwad
Nana ta kalli Ilham
"Haba Ilham, Jalila tana miki magana amma kin wani shareta"
"Kinsan bana son rainin hankali, kuma kinsan halintane dan haka ni bana shiga sabgar mutum inaga hankali be isheshiba"
"Kut lallai Ilham amma kinsan da a gabantane dase ta gaya miki wadda tafi takin zafi"
"To yanzu tunda bata nan seki rama mata"
Ilham ta fada tana Harar Nana
"Rufamin asiri, ina ni ina iya shigarwa Jalila fada ai sedai inyi kallo"
"Ya fiye miki"
Haka Nana tarakasu ILHAM had bakin gate suna tafe suna fada,

Jalila tabi bayan JAWWAD da kwanukan abinci zuwa part dinsa, oga Jalal yana zaune yana kallo sekace dakinsa, Jalila ta ajiye kayan abincin tareda fadin "wash" JAWWAD ya Dan kalleta "kai baby har kin gaji"
"Niba gajiya nayiba"
"Hmm dagaske?"
"Eh mana"
"OK tunda bakgajiba serve us"
Seda ta kalli Jallal ta Dan hade rai
Ta dau plate tayi serving Jawwad, ta kalli JAWWAD "sekuma me?
"Baby Jalal fa, serve him too"
Yamutsa fuska tayi
"Ni na gaji"
"No Jalila, kefa kikace Baki gaji ba, hakan ba halinki bane"
Kafin tayi magana Jalal ya taso daga inda yake cike da gadara, yasa hannu ya dauke plate din gaban Jawwad da Jalila tayi serving din Jawwad, ya dau spoon ya samu guri ya zauna, ya fara cin Abincinsa

Bayan sun fitane yaseera ta kalli Ilham
"Tab wai yanzu kina nufin wannan itace budurwar JALAL din"
"Hmm gata nan kin dai ganta ko?
" ai ko ta hadu"
"Kamarya ta hadu, kinsan dai na fita kyau ko?"
"Ke dalla wayake ta wani kyau Ilham, duk kyanki akwai qualities din da in kika rasa, to kyan yazama shirme, banda abinki ma dame kika fita, hasken fatarne kawai amma wallahi kyakykyawa CE"
"Au yaseera hakama zakice dame ta fini?"
"Kallifa mu matama kalli da yadda take mana magana INA ga in agaban namijine, gashi ta iya iyayi da siyasa, kincemin fada kuke, amma dukda munzo tare kalli yadda ta mutuntani, gata Yar gayu"
Ilham ta hade rai sosai sannan tace
"Ni duk ban iya wannan abubuwan ba kenan?"
"Bahaka bane ba, amma kin San meyake cutarki"
Ilham ta girgiza kai
"Rashin hakuri, saurin fushi, ga garaje, gaki da sakaci, kinga in bakiyi dagaskeba akwai matsala kina ganin yanda take wani juya ido in tana magana"
"To yazanyi yaseera,?"
"Waima tukuna naji yayan Nana yana batun akai musu abinci shida Jalal, Abincin ma ita take kai musu"
"To inaga ita take kaimusun mana" Ilham tai maganar cike da damuwa
"Cab wato ita take kaimusu abinci, lallai ILHAM da sauranki, gaskiya akwai tendency na JALAL yafara soyayya, kuma abinda kike gudun yafaru"
Ilham ji tayi kaman ta Dora hannu a ka ta fashe da kuka
"Yaseera ya zanyi, nikam indai nabari shirin mami ya rushe batareda ta dau fansar nan ba nayi asara
Wallahi yaseera se yanzu nagane son gaske nakewa Jalal, wallahi zan iya komai akansa"
"Kina wannan sakalancin zaki iya komai akansa? Malama ki dage Dan wallahi wannan yarinyar da bariki zatayi zata Tara abun duniya,
Yanzu ki saurareni, batun kice kin gaji be taso ba, duk masifar

Please Login or Register in order to submit comment