Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Jawwad ya damu sosai
Karfe sha biyun rana ummi ta iso gidan, Jalila kaman ta shige cikin ummi dan farin ciki, tayi murna matuka, Abba yana gidan saboda zuwanta, Maama dai ba yabo ba fallasa ta tarbeta saboda idon Abba, Jawwad ya shigo domin gaida ummi, se lokacin yaga Jalila, ta dan fada idonta yayi zuru2 tana manne a jikin ummi, tausayinsune yakama shi, suka gaisa da ummi, daga nan ya shantake akayi ta hira, ya tashi ze fita ya waigo ya kalli Jalila yace
"Jalila, dan Allah kawomin coffee"
Abba yace
"Yayana kafiye takura, tana zaune tana jin dumin ummin zaka sakata aiki, murmushi Jawwad yayi yana dan sosa keya, Maama kam wani mugun harara tayi masa, suna hada ido da Maama ya sunkuyar da kansa kasa, ummi kuma tace
" Ai ba wani takura dan yasata aiki, ai kanwarsa ce, tashi ki kaimasa"
Jalila ba dan tasoba ta mike taje ta hado masa, ta fita domin kai masa, Maama a ranta tace "lallai Yaron nan, wato beji maganar da mukayi masa ba kenan?, aikuwa sena saba masa"
Jalila tana kaimasa, ta ajiye ta juyo zata fice Jawwad ya kira sunanta
"Jalila" cak ta tsaya amma taki yadda ta kalleshi,
Tasowa yayi yazo gabanta ya tsaya, suna iya jin numfashin juna, muryarsa a sanyaye yace, "Baby menayi miki na cancanci wannan hukuncin? Kin kauracewa ganina, tsawon kwana biyu, kinki daga wayata, kinsani cikin damuwa, Baby why?"
Dan dagowa tayi ta kalleshi, idonta sun ciko taf da hawaye, ta sunkuyar da kai, kallonta yayi ya kuma sassauta muryarsa
"Ohhh no Baby, nagane, Jalila you are not suffering alone, i also feels what you feel, Baby dan Allah kiyi hakuri akan abunda akayi miki, kar hakan yasa ki kuma, kauracemin kwana biyun nan na shiga damuwa, sannan kidena zubar da hawayen nan, banaso, kuma in Ummi, taganki cikin damuwa bazata ji dadi ba"
Gaba daya jiknta yayi sanyi, duk yabata tausayi, ta gyada masa kai alamun ta gamsu da maganarsa
"Kindena kukan?"
Ta gyada masa kai, ya ciro handkechief a aljihunsa yabata, ta goge hawayen da yake idonta, ta mika masa, sannan ta fito, ta koma cikin gida,
Ta tarar ummi tana cin abinci, spoon ta dauka tazo ta zauna, suna ci da Ummi,
Zuciyar Ummi fal tausayin Jalila, akwai abunda yake damunta, amma taki fada mata,
Nana ta fito taga Jalila da ummi suna cin abinci tare, ta kalli Jalila
"Wato dan ummi tazo shine, yau bazaki ci abinci dani ba?"
Dan murmushi Jalila tayi, wanda iyakacinsa lebenta
"Ni na isa, Nana"
"gashi nan makuwa nagani"
Ummi ta kallesu tana murmushi
"kema dakko spoon dinki, kizo muci"
Haka kuwa akayi, suka zauna suna cin abincin tare
Ummi tagayawa Abba, kwana daya zatayi, ta wuce,
Maama ta shige daki ta kira Naana, ta hanata fiyowa, karshe ma ta aiketa tabar gidan, ta bar Ummi se Jalila da Halima, dakinsu Jalila taja Ummi, ta dinga mata magiya ta tafi da ita, amma Ummi tace mata baze yiwuba, Yanayin yadda taga Maama ta karbeta, tasan akwai matsala amma Jalila tace komai lafiya kalau suke zaune
Haka Jalila sukai ta hira da Ummi wanda hakan ya rage mata bacin ran da take ciki ,
Rabin hirarsu da Ummi, Nasiha ce take mata akan hakuri da karbar kaddara a duk lokacin datazo mata,
Da dare yayi ma Maama cewa tayi Nana ta kwana a dakinta, tabar musu can, dan bazata kwana a gurinsuba bata san me za a koyamata ba.
Washegari tunda safe Ummi tafara shirin tafiya, tun wayewar garin Jalila take kuka, ko karyawa takiyi, karfe goma na safe, Ummi tagama shirinta tsaf ta fito, Jalila janye da trolley din Ummi tana share hawaye, Nana kuma ta dakko karamin jakar Ummu, hakan yayi dai2 da fitowar Abba wanda shi zeje yasa Ummj a motar garinsu, Abba yace a kirawo Maama suyi sallama da Ummi, Maama ba dan tasoba ta fito, sedan kar Abba yayi mata fada,
Abba ya kalli Jalila yace "Baby muje, asaka kayan a mota" Jalila tayi gaba ita da Nana, ya bisu a baya, suna zuwa harabar Gidan, suka tarar da Jawwad ya kunna motar ya bude kofofin, suna zuwa yaje ya karbi trolley din hannun Jalila yana kokarin bude boot
Ummi ta kalli Maama da take tayi mata kallon banza, ta danyi murmushi sannan tace
"Zainab har yanzu ina ganin kiyayyata a idonki, bansan dalilin hakan ba, amma ina rokonki ga Jalila nan amana, kar kiyayyata ta shafeta, ki dubi Allah ki dubi maraicinta, in kikaci amana Allah yana kallonki, badan wasiyyar mahaifinta ba Zainab, babu abunda zesa in bar yata a gidanki, tunda nasan ba kya kaunarta, keda danginki, da da ita zan tafi, ko ina ne" Maama ta katseta ta hanyar cewa
"kinga saurara, amanar yarki a hannun dan uwan mijinki take baniba, dan ba muhada dangin komai dake ba, ni ban hada jini da arna ba balle abani amanarsu in karba"
Murmushi Ummi tayi me ciwo sannan tace"shikenan Zainab ki fadi abunda kikeso, kema kin haifa, bazan fasa fada ba Jalila amana ce, zan iya yafe duk abunda zakiyi min amma banda cin amanar gudan jinin Aliyu, wato Jalila " Ummi na zuwa nan a zancenta tayi waje tana share hawaye, tareda tausayin tilon Babyn ta.
Harabar gidan ta fito, suka koma gefe, da Abba suna magana, Jalal ne ya shigo gidan, ya hangi Ummi yana ganinta ya karaso da sauri yana murmushi, yace
" Ummi saukar yaushe"?
"Abdul Jalal haka ka girma, Jalal ka yadani, ka manta dani"
Ya dan girgiza kai
"ummi wane ni in manta dake ni na isa, yanzu kikazo ne?"
"A a tafiya zanyi, tun jiya nazo"
Kallon Jawwad yayi, sannan ya kalli Ummi
"Ummi Jawwad be gayamin ba danazo mun gais, yaushe rabon da naganki"
Abba yace "Lallai Jawwad baka kyauta ba tunda baka gaya masa ba"
Jawwad yace "Abba ba laifina bane jiya throughout ban ganshiba, ban san inda ya tafiba"
"amma lambar wayata ma baka ganta ba itama ta tafi yawon"
Jawwad yayi dariya
"Allah yabaka hakuri"
Jalila mamaki takeyi yadda ya ke girmama Umminta haka, yasan Ummi kenan, amma ranan datayi mata zancen waye JALAL tace mata bata saniba
Ummi tace "Abdul Jalal ina Mummynka?"
"tana nan Ummi, yanzu nan ta fita", daddy kuma baya gari,"
Ummi tace Allah sarki, dan Allah a gaishesu
" zasuji Insha Allah Jmmi"
Jalal ya kalli Abba yace "Abba ka bari, semu rakata"
Abba yace masa "ai ba kano zata koma ba, tasha zasu kaita, zataje garinsu"
"Ba komai Abba, bari mu kaita"
"to shikenan yarona, karbi mukullin"
Jalal yasa hannu ya karba,
Seda Jalila ta zare ido, ko dai Abba besan irin tukin da Jalal yake ba, yabashi mukullin motarsa
Abba suka gama maganar dazasuyi da Ummi, Jalila da Nana suka shiga bayan motar, sannan Ummi ta shiga,
Jawwad kuma ya zauna a gaban mota, sekuma Jalal da zeyi tuki
Suna tafe Jalila tana kuka, Nana, da Jawwad suna rarrashinta yayinda Ummi ta maida hankalinta kan JALAL sunata hirarsu, bawai dan batajin kukan Jalila ba sedai kar garin rarrashinta itama tayi kukan,
Ummi tace "Jalal ya karatu fa?"
Yace"Ummi kicigaba da yimin addu'a, very soon zakiji labari me dadi"
"to Allah ya tabbatar da alkhairi, yabaku mataye nagari kuyi aure"
Dariya Jalal yayi "Aure kuma Ummi"
"Eh mana Jalal, aure ai shine cikat mutum"
"ko ba hakaba Jawwad"
"hakane Ummi"
Jalal yai murmushi, tareda dan girgiza kai,
Haka suka cigaba da tafiya, har suka je tasha, Jalal hira suke da Ummi, aka samawa Ummi mota, suka saimata ticket, Rirriketa Jalila tayi tana kuka,
"Ummi dan Allah kidawo da wuri, karki tafi ki zauna Ummi"
Ummi ta dan goge kwalla tana dan dukan bayan Jalila, alamun rarrashi, sannan ta kalli su Jawwad
"ga sister dinku nan, asaka ido akanta, kuyi hakuri da halayenta, dan Allah,"
Nana tai saurin cewa "Ummi karki damu, Jalila bata da wani damuwa, lafiya kalau muke zaune"
Jawwad ma yace "ummi karki damu shagwaba nsme kawai takeji, shiyasa take kuka, amma ba wani damuwa," murmushi Ummi tayi sannan ta dago Jalila tace
"Baby na is ok, bazan dadeba zan dawo insha Allah, zamu dinga waya, Baby kiyi hakuri da rayuwa, sannan kizama me hakuri da kaddararki, kizama me yafiya da kauda kai, akan al amuran rayuwa, banda tsokana da neman magana duk abunda yasameki kiyi tawwakali ga Allah kinji baby"
Gyada mata kai Jalila tayi
"Yawwa Allah yayi muku albarka, ya hada kanku gaba daya"
Jawwad yace "Insha Allah Ummi" Ummi ta kalli Jalal "Abdul Jalal ni zan tafi, Allah ya jishemu alkhairi, in ka koma makaranta, a ko bikin yazo kar a manta dani"
Dariya yayi yace "Hajiya ummi, kidena batun auren nan fa, zan karbi lambarki gurin Jawwad mudinga gaisawa"
"to shikenan ku koma haka nagode sosai,"
Ta dan rungume Jalila tai kissing dinta a goshi
"kidena kuka, addu a zakiyimin"
Daga haka Ummi ta shige motar
Jikin Jalila a sanyaye, suka koma motarsu suka dau hanyar gida,
Jawwad se bawa Jalila baki, yake kan tayi hakuri amma kaman yana zigata, ta kwanta akan cinyar Nana, se kuka take,
Kukan Jalila ne yacikawa Jalal kunne, ya samu guri, yayi parking, sannan cikin tsawa yace "dallah Malama ki rufewa mutane baki, se wani lallabaki ake kina cigaba da kukan, Wani abunne yasamu, Ummin dazaki dinga yiwa mutane kuka haka, in baki rufemin bakiba sena makeki wallahi"
Yadda yayi maganar seda hantar cikin Jalila ta kada, saboda cikin tsawa yayi maganar, Jawwad yace wa Jalal "dan Allah kayi hakuri ka kyaleta
" Bazan kyaleta dinba Wallahi ta cigaba damin kuka seta sauka, bana son shirme"
Nana tace "Yaya Jalal dan Allah kayi hakuri, tadena, Jalila dan Allah kiyi shiru"
Banza Jalila tayi musu, amma ta rage sautin kukan, da kyar Jawwad ya lallabashi, yaja motar suka tafi,
Bayan sun koma gida Jalila kaman wata marainiya, abun duniya duk ya dameta.
Halima ta lura da damuwar da Jalila take ciki, dan haka Halima taita rarrashinta
"sayyada Jalila dan Allah ki saki ranki, gidan ba dadi in bakya walwala, Ummi zata dawo fa"
Jalila ta danyi yake
"leemart baki san yanake Jiba, wallahi zuciyata ba dadi"
"Nasani Jalila, amma kiyi hakuri, damuwa ba shine mafita ba"
"hakane nagode"
"yawwa kisaki ranki"
Jalila taita kiran Ummi tana tambayarta ko ta karasa, Ummi tace mata in taje zata kirata,
Hakanan Jalila taji hankalinta yaki kwanciya, bayan la'asar ta kuma kiran wayar Ummi amma taki shiga, da farko tayi tunanin ko network ne amma wasa2 har karfe tara na dare wayar Ummi a kashe, hankalinta ya tashi matuka,
Nana tace "dan Allah Jalila ki nutsu ki kwantar da hankalinki, maybe bata da cajine"
"Nana cewa kike in kwantar da hankalina, ta yaya? Dazu fa muka gama waya amma ace yanzu wayar bata shiga"
"To kika sani ko network ne, kinsan hanyar, akwai dazuka, dan haka ba lallai asamu Network ba" da haka hankalin Jalila ya dan kwanta,
Amma har gurin karfe sha biyun dare, Jalila takasa hakuri trying lambar Ummi ta kumayi, amma still switch off
Jifa Jalila tayi da wayar ta fashe da kuka


Share please
More Comments More typing...............................


Aimin afuwa rashin samun posting da wuri, ina busy ne sosai
Amma ina godiya da addu"oinku

🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
[9/13, 10:22 PM] +234 816 830 7871: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 44
PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Ina me neman afuwarku masoyana, kwana biyu banyi typing ba wayata ta dan samu matsalane
Sannan ina kuma neman afuwarku bazan samu dinga yi muku posting kullum ba saboda zan koma lectures online, Nagode da kulawa

_My first novel_

Sosai Jalila take kuka, tareda surutai,
"Haba Ummi dan Allah ki daga wayata mana, hankalina ya tashi"
Sam bacci ya gagari Jalila, tayi trying lambar Ummi bata san adadi ba amma a kashe, Nana kam tuni tayi bacci, yadda Jalila taga rana haka taga dare, bacci ko barawo be dauketa ba, ta kagu gari ya waye,
Da asuba Nana tashi tayi taga Jalila akan dadduma, ta sunkuyar da kai, bata san Jalila batayi bacci ba ta dauka dai ta tashi da wurine, Kamar kullum Nana tayi sallar asuba ta koma baccinta, mikewa Jalila tayi ta fita daga dakinsu idonta ya kumbura, yayi jawur, ga rashin bacci ga kuma kuka da tasha, kai tsaye kofar part din Abba ta nufa, a hankali tafara knocking, tayi ya kai sau hudu, sannan taga an bude, Maama ce ta bude, ta kalleta a wulakance
"Ke! Meye haka zakizo kinamana knocking da safiyar nan"
Jiki a sanyaye Jalila tace "Kiyi hakuri gurin Abba nazo"
"ikon Allah yaushe kika zama matar gidan nan dazakizo gurinsa da sassafe haka"
"A a Maama dama wayar Ummi ne tun jiya da yamma ya dena shiga shine...
" Shine Me? Fitowa zeyi ya tafi nemo miki ita, Allah ka dai yasan gidan uban data tafi, dalla matsa kibani guri"
Maama ta maida kofa ta rufe, silalewa Jalila tayi a gurin, tacigaba da kuka kuka
"Kingani ko Ummi dakin tafi dani da koma mene ze faru ina tareda ke"
Se karfe tara na safe Abba ya fito, yaga Jalila a kofar part dinsa a zaune, tana kuka, "Subhanallah Jalila me yasameki haka,?"
Kuka takuma fashewa dashi
"Abba, Ummi tun jiya da yamma, lambarta ta dena shiga,"
Tabbas dan shima ya kirata amma taki shiga, cikin sigar lallashi yace
"Kiyi hakuri kinji diyata, yanzu kije kiyi breakfast, zan cigaba da trying lambarta, in be shiga ba zanje tashar motar da kaina inji me ake ciki"
Gyada masa kai tayi ta mike ta koma palour ta zauna tayi shiru, se hawaye dayake bin fuskarta
Wasa2 har azahar babu labarin lambar Ummi, taki shiga, Jalila fa tafara fita hayyacinta, babu cin, Abinci takasa nutsuwa, Jawwad da Abba suka tafi har tashar da akasaka Ummi a mota, amma aka tabbatar musu da cewa motar taje har garin sun juyo, sedai sunyi tsaye2 sun sauke fasinjojii, amma lafiya sukaje suka dawo,
Se dare su Abba suka dawo, amma ba wani labarin samun Ummi, Wunin ranar babu batun nutsuwa a tareda Jalila, kuka kam idon harya kafe, babu hawaye se ajiyar zuciya kawai da take yi, Maama ko kallon Jalila ba tayi ba balle wani magana me dadi ta fito daga bakinta, Nana da Halima ne kawai suke rarrashinta,
Su Abba suna dawowa Jalila ta mike, tana tambayarsu, ya akayi? "
Abba yakama hannunta ya zaunar da ita, sannan yace
" ki kwantar da hankalinki, kinji, munje tashar motar, sunce mana motocinsu sunje lafiya, sun sauke fasinjojin su lafiya sun dawo, dan haka muna da tabbacin Ummi ta sauka lafiya, watakila wayarta ce tasamu matsala amma sunje lafiya, zuwa gobe Insha Allah nida Jawwad zamu kuma komawa, in takama mu bibiya har can garin nasu zamuje, amma muna fatan komai lafiya " hankalin Jalila ya dan kwanta kadan,
Abba ya mike, ya koma part dinsa, Jawwad yasa halima ta zubo Abinci ta hado da tea, ya zauna yasaka Jalila a gaba, ya takura mata, amma ta tsakuri kadan tace ta koshi, karbar Abincin yayi, ya dan hade rai, sannan yafara bata a baki, karba take tana ya tsuna fuska, "Yanaga kina bata raine, kiyi hakuri kici Abincin mana" ta yamutsa fuska, muryarta kasa2 tace
"kaina fa ciwo yake"
"to yi hakuri, ci Abincin, se in kawomiki magani" ta gyada kai
Yana cikin bata Abincin ne, Maama ta fito, wani mugun kallo tai musu
"Kai Jawwad meye haka, ban isa in gaya maka kaji bako?, meye nawani zama kana bata Abinci, tashi kabar nan malam, tashi kafita sha3 kawai, jiki a sanyaye ya mike yana waiwayen Jalila, yayinda ita kuma ta sunkuyar da kai, Maama ta kalli Jalila sannan tace" Mayya kawai, Mara zuciya" dagowa Jalila tayi ta kalli Maama, ta mike ta bar mata palourn, takoma dakinsu,
Jawwad ya koma dakinsa abun duniya ya dameshi, yayi wanka yayi sallar isha'i ya dawo ya zauna a palour, yayi shiru yana tunani,
Jalal ne ya shigo, yazo ya tarar da shi a palour ya samu guri, ya zauna ya kalleshi
"Ina kashigane nazo baka nan, ina ka tafine?"
Ajiyar zuciya Jawwad yayi sannan yace
"Akwai matsalane Jalal"
"matsalar mene?"
"jiya bayan mun kai Ummi tashar mota, tun bayan la asar har yanzu danake maka magana ankasa samunta a waya, lambobinta basa shiga, har tashar motar mukaje nida Abba, amma sun tabbatar mana motocinsu sun isa lafiya sun dawo,"
"To ya akayi haka tafaru?"
Jawwad yace "nima ban saniba Jalal, gashi Jalila ta daga hankalinta fiye da yadda kake tunani, ko abinci taki ci, yanzu na tursasata ina bata, Maama ta koreni, kuma hada gayamata munanan magana, Jalal narasa me zanyi, a halin Yanzu Jalila na bukatar me kwantar mata da hankali, ta damu kwarai"
Ajiyar zuciya Jalal yayi sannan yace
"to yanzu wani mataki aka dauka amma da mamaki ace wayarta bata shiga kuma by now, dai nasan ta isa, kwara state, kuma nasan bazata kasa kiran wayaba"
"Koni jiyan da azahar munyi waya da ita, Gobe in Allah ya kaimu zamu koma tashar, in takama mutafi can garin nasu se muje, ina tausayin Jalila,"
"Allah yasa komai lafiya"
Jawwad yace "Ameen" Jalal ya dafa kafadar Jawwad
"Ka kwantar da hankalinka, karkasa damuwa a ranka, komai zezo da sauki, bana son ka damu"
Dan murmushi Jawwad yayi sannan yace "to naji"
Daga haka Jalal ya tashi ya tafi gida, yunwa duk ta ishi Jalal dan ba wani Abincin kirki a cikinsa, saboda Jawwad baya nan, gashi baya son shiga cikin gidansu, dan yasan inya shiga kafin ya fito se an bata masa rai, har ya kwanta, ya tashi ya nufi cikin gida bakowa a palourn, dan haka ya wuce kitchen zuwa yayi yaita bude2, ji yayi kaman da mutum a tsaye a bayansa yana waigowa yaga Ilham a tsaye, da wata yar riga a jikinta, iya gwiwarta, dauke kansa yayi, yacigaba da abunda yake, a hankali ta tako ta karaso cikin kitchen din, ta dan kalleshi
"My star, me kake nema ne?"
Be amsamata ba balle ya kalleta,
"Ko kanajin yunwa ne?" shiru yayi mata, ya nufi fridge, bayansa ta kuma bi
"haba star, ka kalleni mana, ka amsamin"
A fusace ya juyo
"Ohhh God, haba wai meye hakane? Kinyimin magana nayi miki shiru, base ki kyaleniba, kalleki kalli Jikinki, ya dace kizo inda nake a haka, get out from my side"
Ita a tunaninta shekaranjiya da ya shigar mata fada ko yafara sakkowane, amma yanzu setaga abun bahakaba, shi har yawani san abunda ya dace, ko be daceba, bayan giya yake sha, ga sauran lefuka, amma ta maze ta matso inda yake
"Yaya Jalal kenan, nasan yunwa kakeji, kawo in dafa maka wani abun kaci"
"No need" shine abunda yace mata kawai, kuma matsawa tayi daf dashi, yana juyowa suka hade, zuciyarsa ta buga da karfi,
Ta dan tsura masa ido,
"Meyasa kullum baka da burin daya wuce azabtar da zuciyata ne, kasan ko yadda nakeji? Please Yaya na, love me too"
Shiru yayi mata yasa hannunsa biyu, ya tureta gefe, yakama hanyar waje, sauri takumayi tasha gabansa, tana kallonsa, Ajiyar zuciya yayi sannan yace
"bana son yi miki wulakanci, u are pushing me to the wall, meye haka ne? Meyasa bakida kamun kai Ilham, a hakan kikeso in aureki,? Kalli yadda kikemin ba kya tunanin haramcin hakan, kina tunanin ko na aureki zan yadda dake"
Ta dan nisa
"Yaya Jalal kome nayi kaine sila, meye laifina dan Nace inasonka, da soyayyarka na budi ido why Yaya Jalal? Msyasa baka sona"
Hade rai yakuma yi "Ana so dolene? Tun farko nagaya miki, niba na
ra ayinki, kije kisamu wani, ni bani da niyyar aure yanzu, ki hakura mana, nagaya miki gaskiya bazan aureki ba, "
"Yaya Jalal agaban idona kake gayamin bazaka aureniba, to bari ingaya maka, kayiwa duk wadda zaka aura Albishir din, ta tari bala'in dabata san karshensa ba, wallahi kowa ka aura, sena hana muku farinciki baka isa ka auri wata baniba indai ina raye a doron kasa, kuma ko bana raye fatalwata seta hanaku sukuni,"
Murmushi yayi kawai yai waje, ya fasa daukar abunda yayi niyya, a ransa yace" lallai yarinyar nan bata da hankali"
Ilham takoma dakin tana jujjuya maganganun Jalal "Wallahi karya kakeyi Jalal, kozan tafi tsirara se nacikawa Mamina burinta, zakaga tsiya, senayiwa Jalila abunda se ta mutu da bakinciki, dan na lura itake kara, batamin aiki, da raina wallahi bazakayi aure ba da wata mace inba niba, if not inyi abinda zan karya asirin kowa ya huta, haka Ilham taita surutai marasa kan gado,
Shikam Jalal, Ya fita harabar gidan ya tsaya, yana nazari, ya Kalli agogon hannunsa daga baya ya dau motarsa ya fita, Club ya tafi abunsa yaje aka cashe aka sha giya, yai manksa abunsa, yana tangadi se kawoshi gida akayi.
Dare yaraba, Jalila se nafila takeyi, tana addu a Allah ya bayyana mata Umminta yasa tana lafiya, se gefin asuba bacci yasaceta akan daddumar datayi salla, a cikin baccinnata maimakon tayi mafarkin Ummi tunda itace a ranta, setayi mugun mafarkin data saba yi akan Jalal, a firgice ta farka, tana ambatar sunan Allah gaban ta na faduwa, Nana ta taso tazo inda take, ta dafata "Jalila lafiya kuwa?" rirrike Nana tayi ta fashe da kuka
"is ok dear, yi hakuri, Insha Allah komai zezo da sauki, a yau za a ga Ummi Insha Allah" gyadawa Nana kai kawai tayi, seda ta dan samu, nutsuwa sannan ta mike tayo alwala tazo ta tayar da sallar asuba,
Da sassafe karfe shida Jalal ya tashi yai wanka yai salla, ya dau motarsa ya fita ba tareda wani yasan inda ze tafiba, dan ko Jawwad be gaya masaba.

Karfe takwas na safe Abba da Jawwad suka hadu a palour zasu kuma fita, Maama ta Kalli Abba
"wai Dan Allah yanzu fita zaku kumayi, ko karya bakuyiba, nasan wallahi wani gurin tai tafiyarta amma duk ka daga hankalinka"
Abba ya kalleta
"kina tunanin, zata iya tafiya wani gurin batareda sanin yarta ba, bari in tunamiki abunda kika manta, Maryam da Jalila amanar dan uwana Aliyu ce dasu Inna, idan naci wannan amanar Allah baze barniba, dolena innemo abunda yasamu Maryam dan na tabbatar, da taje lafiya, da komai lafiya nasan, komae ake ciki, zata gayamin"
"kai kake ganin hakan amma a gurin su aikata irin wannan ai ba wani abun damuwa bane, ai abun kunyane ta koma garinsu da yarinya bayan basu san tayi aureba, kodayake su ina suka san wata kunya"
"Ya isheki haka Zainab, Wallahi zan bata miki rai fiye da yadda kike tunani, akan cin zarafin matar Dan uwana, babu bawan da ya isa ya kuskurewa kaddararsa,"
Jawwad ganin sa' insa na neman barkewa tsakanin iyayennasa, se ya kewaye ya tafi dakinsu Nana, ya tarar da Jalila ta dora kanta akan cinyar Nana, tana zubda hawaye, yayinda Nana take bata hakuri, karasowa yayi ya tsuguna
"Baby baki dena kukan bako? Dagowa tayi ta kalleshi, sannan ta sunkuyar da kai, kiyi hakuri yanzuma fita zamu kumayi da Abba Insha Allah zamu gano inda take, ki dena kukan nan kinji, ze iya kawo miki matsala"
Ta dan Jinjina masa kai, ya Kalli Nana yace "Nana dan Allah ki tabbatar taci Abinci"
"to Yaya Insha Allah" daga haka ya mike yafita cike da tausayin Jalila,
Yana fitowa palour yaga ba kowa dan haka ya fita harabar gidan ya tarar da Abba a zaune a cikin motar yana Jiransa, Jawwad ya shiga motar ya kunna suka fita,
Har la'asar babu wani kyakykyawan labari, dasu Jawwad suka samu game da Ummi, kuma har yanzu wayarta bata shiga, haka suka gaji suka dawo gida, koda Jalila taga sun dawo, da sauri ta tashi, ta fita domin sanin me ake ciki, Abba yasa aka kiramasa Jalila, Jalila tazo, ta durkusa a gabansa
Koda taji Abba yafara dayi mata nasiha ta karaya ta kuma fashewa da kuka
"Shikenan na rasa Ummina, Ummi dama haka zakiyimin, kikayimin wayo kika tafi kika barni, yanzu ba Abee ba Ummi"
Jawwad yace "haba Jalila duk bagamuba, kuma Ummi fa

Please Login or Register in order to submit comment