Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

me yake damunkine naga baki da walwala tun jiya?"
Rasa mezatace tayi kawai setace masa
"Yaya Jawwad, meyasa abokinka bashida kirki? Jiya munje gidansu da daddare Mummy tanata kuka saboda shi Yaya ka dinga yi masa nasiha, ni a ganina tarayarka dashi bata da amfani"
Dan kurawa Jalila ido yayi na wasu sakanni, ya dan sunkuyar da kai sannan ya kuma kallon ta
"Jalila" ya kira sunanta
"Na am Yaya Jawwad" ya mike tsaye sannan yace mata
"Biyoni"
Ba musu ta bi bayansa, har palournsa sannan ya nuna mata guri ta zauna
"Jalila rabuwata da Jalal ba mafita baneba, ina tareda shima kalli halin da yake ciki, inaga inna rabu dashi, babu wasu abokan arziki a rayuwarsa kowa yayiwa dansa kashedi akan mu amala dashi, babu wasu mutanen kirki da yake rayuwa dasu, ko ransa ya baci sune mutanen da suke tarairayarsa, kowa yana kyamarsa shiyasa abune mawuyaci ya rabu da shayeยฒ indai mutanen kirki sukayi karanci a rayuwarsa"
"To Yaya meyasa bazaka masa fada ba ya canza rayuwarsa haka yaga kowa yana yi, babban abun damuwar yadda yake treating mahaifiyarsa, Sam be dace ba" Jawwad yayi ajiyar zuciya
"Abunda yake tsakanin Jalal da mahaifiyarsa sirrine na rayuwarsa, amma dai a da mutumin arziki ne, bahaka yake ba, wani azzalumin aboki ya hadu dashi waishi Jeje shine silar lalacewar Jalal nayi iya kokarina ya rabu dashi, amma yaki, akwai wani mummunan kuduri da Jeje yake dashi akan Jalal Wanda ni kaina ban saniba, yanzu ga wata shedaniyar yarinya data shigo rayuwarsa, wadda nake kyautata zaton bakinsu daya da Jejen wai ita Hannah"
Dan dagowa JALILA tai ta kalleshi "Hannah kuma?"
"Eh Hannah, ta shigo rayuwar Jalal, iatama, Jalal kaman Wanda akayiwa asiri, gashi cutar dashi suke amma baze iya rabuwa dasuba, duk lokacin da nayi yinkurin yi masa nasiha, idan yayi kaman ze dauka seya birkicemin ya dingamin tsawa jijiyoyin kansa su kumbura, wani lokacin seya suma, shiyasa na barwa Allah komai nake masa addu a"
Shiru Jalila tayi wato Jawwad yasan Jalal yana wannan abun
Jawwad yabata labarin nan a dukunkune bata wani gane komaiba amma waye Jeje she needs to know him
Jawwad ya kuma dubanta
"Yana daga abunda yasa bazan iya rabuwa da Jalal ba halaccin mahaifinsa Jalila bayan Abba da Abee, daddyn Jalal yana cikin mutanene daba zan mantaba,Jalal ya kaunaceni tun ina dan talaka na, Jalilalokacin ina zuwa gidansu Jala, y'an fashi suka shigo gidan da daddare, tashin hankalin daddyn Jalal karsu yimin wani abu da sukaga haka se sukai kokarin harbina, Jalal ya taremin harbi, aka sameshi a memakona, Jalal seda yayi jinya a kasar waje, badan ya tureni ba ya tsaya.dani zasu samu "
Zare ido Jalila ta yi, ya gyada mata kai
"Da gaske Baby, idan nafara gaya miki halaccin da yayi min dayawa, dan haka idan na gujeshi nayi butulci, naci amanar kauna da soyayya da yayi min, kitayani yi masa addu a komai ze zama daiยฒ insha Allah"
Nannauyar Ajiyar zuciya Jalila tayi "zan dinga yi masa addu a insha Allah"
"Yawwa baby in kakayi haka kingama min komai"
Daga nan JALILA ta tashi ta koma cikin Gida
Tunani ya hadu yayi mata yawa, Yaya Jawwad be bayyana mata komai sosai ba, yagayamata abubuwan a takaice kuma a dukunkune, ko wazata tambaya
Yana da kyau tasan waye Jejen nan, amma to kuma meya kawo Hannah cikin lamarin nan akwai kanshin bakinsu daya da Jeje kenan
"Kai JALILA karki bari kwakwalwarki tayi bindiga mana kin takurawa kanki akan wannan shaยณ dabe masa ciwon Kansa ba mutumin da giyarsa tafiye masa komai inyi rayuwata mana, haka Jalila ta cigaba da takura kanta, seta dena wannan tunanin son sanin waye Jalal"

Maama kuma tunda ta fita zuciyarta ke tafasa kan wannan kusanci da shakuwa dake tsakanin Jawwad da Jalila, saboda gani take abun nasu na shirin komawa soyayya, idan kuwa tana Raye bazata taba bari hakan tafaru ba, dama gidan wata abokiyar kasuwancinta zataje dan haka tana zuwa a gurguje tai abunda zatayi ta fito ta tafi gidan yayarta mairo
Tana zuwa kuwa tayi Sa a tana Gida dan gantalalliya ce ta innaniha dillaliyace yau tana nan anjima tana can
Ga ta da 'yan mata manya irinsu Sa ada da Naja da sauran mannensu amma har shabiyun rana ko wankeยฒ ba suyiba
Daki suka shige da Maama da Yaya mairo, suka gaisa sannan
Yaya mairo ta kalleta "lafiya dai Zainab naganki haka?"
"Inafa lafiya game da wannan yarinyar ne"
"Wace yarinyar?"
"Jalila mana"
Yaya mairo tayi mutmushi
"Kice Jalila ta gurin arniya, ai jiya Naja data dawo tabani labarin komai, yarinya ta samu sakewar yin abunda taga dama,wai ta dawo gidanki da zama, narasa wace irin macece ke Zainab, ya akayi kika bari ta dawo miki Gida harta samu wannan yancin? Ashe kinshirya ganin ya'yanki sun fara binta coci"
Maama tai ajiyar zuciya
"Ni duk ba wannan ba Yaya, yaron nan fa Jawwad alamu sun fara nunamin kamar Santa yakeyi"
Zare Ido Yaya mairo tayi "ita wa din?"
"Haba Yaya mairo ya zaki dinga tambayata kaman baki San akan Wanda nake maganaba"
Yaya mairo ta jinjina kai
"Tirkashi, se yau na tabbatar da Zainab baki da wayo kina me hakan ke shirin faruwa garin Yaya?"
"Kedai bari duk yadda na kesa musu ido amma alamu sun fara nunamin hakan"
"To yanzu wani mataki kika dauka?"
"To Yaya mairo da na dauki wani mataki ai da banzo nanba"
"Gaskiyane, yanzu abunda ze faru zanzo gidan naku, zan zo in samesu, nasan abunda zanyi"
"To shikenan har na danji sanyi, wallahi"
"Karki damu kibar komai a hannuna"
Da haka sukayi sallama Maama ta koma Gida

Jeje ne ya kalli Hannah,
"Hanna akwai bukatar kara himma akan Jalal, idan mukace zamu cigaba da bin komai a hankali muna lallabashi to aikin nan base yiwuba"
"Nima nayi tunanin hakan amma me kake gani za ayi?"
"Birthday Jalal saura wata daya, a wannan lokacin nakeson mu kaddamar da komai, ko ya rayu yayi abunda mukeso, ko kuma...................

Ilham tana kwance ta lumshe ido, da alama tana son yin baccine, wayarta ta fara ringing, yamutsa fuska tayi takai hannu da niyyar yin rejecting kiran taga sunan malam Wada a jikin screen din, da sauri ta tashi zaune taje tasawa kofar dakinta key ta dawo ta daga kiran
Suka gaisa, sannan yace
" dama batun Yarinyar nan da kikayi min magana akanta ranan ne"
"Nagane Jalila kenan"
"Yawwa ita nayi bincike akanta amma akwai Matsala............


Share please
More comments more typing..........................


๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน
๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 42
PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Ina me neman afuwarku masoyana, kwana biyu banyi typing ba wayata ta dan samu matsalane
Sannan ina kuma neman afuwarku bazan samu dinga yi muku posting kullum ba saboda zan koma lectures online, Nagode da kulawa

_My first novel_

Sassauta murya Ilham tayi sannan tace
"Malam matsala kaman yaya?
" eh nayi bincike akan yarinyar nan, amma abune mawuyaci asiri yayi tasiri akanta, zanyi kokari inga aikin dazanyi akanta amma kema sekin dage danaki kokarin domin samun nasarar kawar da ita gefe"
Ajiyr zuciya Ilham tayi,
"to shikenan malam nagode"
Sukayi sallama Ilham ta yi shiru nawani lokaci sannan tai kwafa
"indai makircine Jalila tasamu daidanta, nasan abunda zanyi"

Hanan tacigaba da kiran Jalila tana takuramata akan Jawwad, in Jalila taki dagawa tabita what's app, duk Yadda Jalila taso ta dinga kokarin danne kishinta amma takasa, itakuma hanan kaman Jalila tana zigata, ta dage ita Jawwad takeso.
Wajen karfe shadaya na safen yau yaya mairo tazo gidansu Jawwad, tunda matar nan tazo gaban Jalila yake faduwa, dan tasan yau ranar cimata mutuncine, tunda yaya mairo bata kaunarta,
Aikuwa tunda tazo take bakaken maganganu, ita dai Jalila ta makale a daki taki fitowa
Jawwad sun gama breakfast dinsu, suna hira da Jalal, Nana ta kira Jawwad a waya
"yaya kana ina? Nazo part dinka baka nan?
"Nana ya akayine? Muna tareda Jalal"
"Yaya Jawwad, yaya mairoce take nemanka fa"
Gabansa ne yafadi
"Nana nikuma, me yafaru? Wani abun nayimata?
"wallahi bansaniba, se faman fada take niban san akan me take fadan ba, tace lallai kazo"
Ajiyar zuciya yayi
"to gani nan, ina zuwa"
Ya sauke wayar a hankali, Jalal ya kalleshi
"ya akayine?"
"wai yaya mairoce tazo tana nemana bansan me nayi mata ba, banason fadan nan nata"
Tsaki Jalal yayi
"ni wallahi kana bani mamaki, to dolene sekaje ai ba dole bane,"
"haba Jalal itama kamar uwa take a gurina fa, ya za ayi takirani naki zuwa"
"to haifarka tayi, sekayi tayi, tashi muje, akwai abunda zanyi a dakinka"
Jawwad ya Mike suka fito, suka tafi gidansu Jawwad, Jalal yayi part din Jawwad shikuma Jawwad yai cikin gida, Jawwad yana zuwa ya tarar da Yaya mairo, A palour Maama na kusa da ita, ya shiga cikin palour ya tsaya daga bakin kofa, ya durkusa yana gaida yaya mairo
"shigo mana kawani tsaya daga bakin kofa, kaman mara gaskiya, dama ba gaskiyarce da kaiba"
Karasawa yayi gabanta ya zauna ya da n risinar da kansa, sannan yace
"Nana tace kina nemana"
"eh ai naganka, takanas nazo gidan nan domin in maka Jan munne, Mahaifiyarka taje har gida ta sameni akan taga take2nka na shigewa wannan yarinya, yar gidan arniyar nan, to bari kaji kaf zuriarmu babu arna dan haka bazamu hada zuria dasuba jan kunne nake maka, karka kuskura kasawa zuciyarka zamu bari ka aureta, bamu shirya ganinka tsakanin massalaci da coci ba"
Dagowa yayi ya kalli yaya mairo
"haba Yaya, Jalila fa ba arniya bace kuma koba komai itama kanwata ce, kuma batada wani aibu"
Maama ce ta kalleshi
"au Jawwad abun har ya Kai ana maka magana kana mayarwa"
Yaya mairo ta kalleta
"ai shiyasa nace kinyi sake zainab,"
Jalila kam ga gaji da zaman daki ga shi ko karyawa batayiba, cikinta yafara kullewa ga sauran aikin gida, dazatayi, dan haka ta mike ta fito
Aikam karaf miyagun maganganun Yaya mairo suka fara dira a kunnuwanta
"muna da ya'n mata a dangi ga su Naja nan da kannenta ka duba a ciki, kasamu matar aure amma ka kiyayi kanka da fara soyayya da wannan yarinyar arniyar ragowar titi, suda basu san abun kunyaba, Allah ka dai yasan mazan da take bi, ni muslincin nasu ma ban yadda dashiba"
Gani sukayi ya kurawa kofar corridor ido suna juyawa, sukaga Jalila a bakin kofar tana hawaye
Yaya mairo ta tabe baki
"to almira da kika tsaya kina mana kuka ai ba karya nayiba"
Maama tace "to tama ce karya kike mana, aikowa yasani, nidai fatana a kyalemin yarona, ato bana son wannan shishshigin da ake masa"
Jawwad yace "haba Maama harda ke?"
Maama a tsawace tace "dalla rufemin baki,"
Yaya mairo ta juyo ta gyara zama sosai ta fuskanci Jalila
"ke ki bude kunnenki da kyau kijimu, gida dai gashi nan kinzo kin zauna, amma Jawwad karki sakawa ranki zamu bari ya aureki dan Zainab tace kusancinku da kuma zakewar dakike yayiwa kashedi nake miki yanzu, kisani 'yar dangi' yar cikakkun musulmai zamu aura masa, yar asali yar dangin uwa da uba ba wadda take da raunin nasaba ba, ba wanda yasan uwarki daga ina tazo ya akayi suka....
Juyawa Jalila tayi cikin kuka ta koma dakinsu, bazata iya jure wannan maganganunba, dan inta cigaba da tsayuwa za a iya samun matsala, Jawwad yabi Jalila da kallo, yana jin kukan Jalila har cikin ransa ya dawo da kallonsa kan Yaya mairo
"haba Yaya mairo, be kamata kisata gaba kina cin zarafinta ba, babu wanda Allah yayi shawara dashi lokacin da ya shiryamana kaddararmu, meye laifin Jalila anan"
Maama ce tace "wallahi ka kuma magana sena mareka, mu zaka gayawa abjnda ya dace muyi, kaika haifemu? Koka fimu sanin abunda ya dace da kai"
Yaya mairo tace
"kyaleshi ya dakeni, se insan kaji haushi"
Halima tana daga dakinta amma tana jin duk abunda akeyi, ranta ya baci matuka, bataji dadin abunda akayiwa Jalilan ba, cin mutuncin yayi yawa,
Ita kam Jalila tana zuwa dakinsu da kuka ta shiga, Nana tasan Yaya mairo ce tayi mata wani abun, dan girgiza kai Nana tayi ta Mike ta fito palour
Itama tazo ta tarar yaya Jawwad ya sunkuyar da kai yayi shiru Yaya mairo tanata surfa masa fada hadi da cin mutuncin Jalila da mahaifiyarta, ita kanta daba ita akayiwa ba seda taji ba dadi, dakinsu ta koma ta tarar da Jalila tana kuka hada sheshseheka zama tayi tana rarrashinta, amma Jalila taki yin shiru
Seda yaya mairo tayi me isarta Maama tana tayata, Jawwad ko kai bekuma dagoawa ba balle yace zece wani abu seda sukagama sannan yace "Allah yabaku hakuri za a kiyaye Insha Allah" daga nan ya tashi ya fita
Yaya mairo ta dawo da kallonta kan Maama sannan tace "to kema bazama zakiyi ba ki mike tsaye ki tsaya akan yaranki ki tabbattar kin rabasu, ba ruwanku da ita in tagaji ta tattara ta koma inda ta fito, baze yiwuba ankawo miki arniya an ajiye tana mjamala da yayanki ba"
Jiki a sanyaye Jawwad ya shiga dakinsa, yasamu guri ya zauna, ya kashingida a jikin kujera ya lumshe ido, Jalal dayasaka systems agabansa yana dannawa ya dan dago kai ya kalleshi ya maida kansa kan abunda yakeyi, Jalal gani yayi Jawwad bashi da niyyar yin magana, Jalal ya dan gyaran murya
"Me yafarune, me kayi mata?"
Seda Jawwad yaja wasu seconds sannan ya dago ya zauna sosai ya kalli Jalal
"Jalal narasa me Baby tayiwa Yaya mairo ta tsaneta haka ba"
Dan tabe baki Jalal yayi "Maybe Rashin kunya take mata"
"No Jalal, Jalila ba abunda tayi mata ta tsaneta, yanzu ma kiran datakemjn wai Maama taje ta sameta akan wai Jalila tana zakemin, wai kar insa ran zasu bari in aureta, babban abunda ya Kuma bata min rai, kiran Jalila da suke da arniya, me raunin nasaba, kuma Jalila taji, amma matar nan takiyin shiru tacigaba da cin zarafinta, ina jin kukan Jalila a cikin zuciyata"
Dan kurawa Jawwad ido yayi sannan yace
"Wannan matar bata da hankaline? Kokuma bataje Islamiyya ba, ita Jaleeelan shashashar inace ta tsaya, aka dinga zagin mahaifiyarta, Uwa tafi Uwane?"
Jalal yai maganar a hasale
"No Jawwad, nasan Jalila kara take mana amma tabbas da a wajene, bazata yaddaba, ni nasan hakan"
"Ba wata kara Jawwad kadinga gayawa yayar mahaifiyarka gaskiya, dan tana zaune a gidanku bekamata a dinga cin zarafinta ba, koni nan"
Ya nuna kirjinsa,
"koni bazan bari wani banza a gari yazagarmin uwaba, dukda abjnda ke tsakanina da mahaifiyata ba, me yasa za a dinga dawo da abunda ya riga ya wuce?"
"Haba Jalal ya kakeso inyine nayi kokarin nusar da ita amma itada Maama sun rufeni da fada"
"Mmm ba yadda zakayi, amma Jawwad mahaifiyar Jalila, Mutum ce, ba abar yarwa bace agurinmu, be kamata a ci zarafinta a gabanmu ba"
"Nasani Jalal, amma ka fahimceni, ba yadda na iya ne, nasani kowaye akayiwa haka baze Ji dadiba, Ina iyajin pain din da Jalila takeji amma ba yadda na iya, da nayi tunanin ko Abba zan gayawa, amma hakan ba mafita bane, ze kuma haddasa fitinane kawai"
"to wai ma tukuna zuwa kayi kace musu kana sonta"
Kallon Jalal yayi
"Jalal koban fada ba shakuwar dake tsakanina da Jalila, bata y'an uwanta bace kawai, Jalal ni son Jalila nakeyi dagaske aurenta nakesonyi"
Wani dogon tsaki Jalal yayi
"Wannan yarinyar mara kunya ita zaka aura, lallai kaci kai,"
"kaman ya naci kai? Meye aibunta?
"Babu kam, bayanma bata da kunya ka aurarwa Ummi yarta, wannan matar tazo tana zagin mata mahaifiya, ni danta wannan yarinyar komeyema akmata ban damu ba, amma cin zarafin Mace kaman Ummi be kamata ba, bekamata a cigaba da wulakanta taba saboda kanason yarta ba" Jawwad ya dan gyara zama sannan yace
"Jalal ina fatan komai ze daidaita insha Allah, amma ina son Jalila, so bana wasa ba"
"to shikenan Allah ya kyauta"
Cikin gida kuwa Jalila tayi kuka, har ta gaji, Nana taibata hakuri, se ajiyar zuciya Jalila take, Nana ta tashi ta tafi palour domin dakkowa Jalila ruwa, tana zuwa itama Yaya mairo tafara saukemata nata fadan, itakuwa Nana ta hade rai tana kunkuni
Jalila tana Cikin kukanne ummi ta kirata a waya, ta dinga kallon screen din har wayar ta katse, kuma kira ummi tayi amma wannan karon se ta Kai hannu ta daga
Ta tattaro nutsuwarta, suka gaisa da ummi
"lafiya kuwa naji muryarki kaman kina kuka"
"lafiya kalau Ummi banajin dadiine"
"meyasame ki?"
"Ummi ciwon marane fa kawai"
"Hmm Allah ya sawwake" tafada ba dan ta yaddaba"
Kaman an tsikari Jalila tace
"ummi yaushe zakije garin naku dan Allah ummi kije ki dawo, in dawo gurinki"
"akwai matsala kenan?"
"ummi ta tambayeta
" ba wani matsala ni dai kawai sonake kije ki dawo, bazan iya rayuwa ba kya kusadaniba, sannan na kagu inga yan uwanki ummk, "
Jikin Ummi yayi sanyi tasan akwai matsala ne take kokarin boye mata,
" Baby wayace miki idannaje dawowa zanyi? Bazan kuma dawowa ba nima a cikin ahalina zan zauna"
"haba ummi karkiyimin haka mana, wallahi ko ina kika tafi sena biyoki, bazan iya rayuwa babu ke a kusa daniba"
Ta karashe maganar tareda fashewa da Kuka, dama kukan take ta boyene dan kar ummi tagane
"is ok my dear, ina nan zuwa jibi Insha Allah, a satin nan zanje gida Nima kidena kukan haka"
Ummi taita rarrashinta, sukayi sallama
Wunin ranar Jalila a daki tayishi tana kuka, gashi ko abinci bataciba, Nana tayi juyin duniya akan Jalila taci abinci amma taki ci, haka take ma a bangaren Jawwad shi yayi breakfast amma bayan nan beci komai,
Jalal ya kalleshi
"kai nifa yunwa nakeji, kaje kace ta kawo mana abinci"
Jawwad ya kalleshi
"wakenan?"
"kafini sani ai, ni yunwa nakeji"
"haba Jalal nagaya maka halin da take ciki, ya za ayi ta wani dafa abinci"?
"Ina ruwana da halin da take ciki? Halin da cikina yake ciki ne ya dameni,"
Jawwad ya kalleshi
"toni na damu da halin da take ciki, ina ji a jikina har yanzu kuka take"
"Ko? Da gaske ka damu,? Aini ban saniba, tunda banga kana kukan ba kaima, sharokhan sarkin soyayya, kagani ka tashi kasamomin abinci"
Wani mugun kallo Jawwad yayi masa, ya tashi yashige bedroom ya bar Jalal a palour
Jalal yai murmushi ya girgiza kai
Bayan la'asar Maama ta kira Nana tasata a gaba suka fita, tareda Yaya mairo, sannan ta aiki Halima, akabar Jalila a gida,
Jawwad yaji karar motar Maama ya leka ta window palournsa yaga fitar Maama da Nana da Yaya mairo, Jalal ya uzzurawa Jawwad se ya tashi ya rakashi cin abinci, dan baze bari yjnwa tayi masa illa ba Badan Jawwad yanasoba ya tashi suka fita,
Fitarsu Nana, hakan yabawa Jalila damar yin kukanta yannda take so
Tabbas da watace ta gaya mata abunda aka gayamata yau a cikin gidan nan to da setayiwa Yaya mairo rashin mutuncin da harta mutu baza akuma yimata makamancinsa ba
Amma kash koba komai yakamata tayi al kunya ko dansu Jawwad, ga nasihar umminta data dingayi mata akan tayi hakuri dazaman da zatayi da mutane, gajiya tayi da zaman cikin gidan, zuciyarta na ayyana mata abubuwa, tasan tunda aka fara haka, lallai Maama zata dau shawarar cigaba da cuzgunamata, kuma yau da gobe se Allah dan wataran zata iya marin mace akan taba mata uwa.
Tashi tayi ta fito harabar gidan, zuciyarta na saka mata abubuwa dayawa
Ilham ce ta shigo gidan, ta hangi Jalila tsaye a wajen kofar shiga cikin gidan, ta nade hannuwa tayi shiru alamun tana tunanin wani abune,
Zuwa tayi zata wuce amma Jalila na tsaye a bakin kofar bata fito ba bata shigeba,
Seda su Jalal suka je karshen layi, sannan ya tuna yabar wayarsa, yace Jawwad yayi parking ya jirashi yaje ya dakko baxe dade ba, Jawwad yayi parking, Jalal ya sakko ya tafi.

Ilham ta karasa inda Jalila ke tsaye
"Zan wuce" Ilham ta fada tana kallon Jalila
"basa nan masu gidan, ki koma inda kika fito" Jalila ta fada a takaice
"ke bana son shirme, ba gurinki nazo ba ai"
"Nasan ba gurina kikazoba, bazaki shiga bane kawai tunda ba kya ganewa nace miki ba sa nan"
A tsawace Ilham tace
"Ke dakata Malama, karki gayamin magana mana, da kikemin wannan gadarar, aiba gidan ubanki bane, dan nasan ubanki ko taku daya bashi dashi a gidan nan" aikuwa Jalila tayi niyyar sauke fushinta akan Ilham, takuma kallon Ilham
"Ke daga inda kike gidan naki ubanne ai, saboda tsabar arzkin ubannaki shiyasa naga yabarki kina ragaita tsakanin gidan yan uwa, saboda kwadayi"
"Hmm Aida tuni gidan ubanane, wasu dalilai suka hana faruwar hakan, amma wataran dukiyar da kike magana zatazama mallakina"
Kallonta Jalila tayi baki bude
"A matsayinki nawa, dukiyar uban wani zata zama taki kwadayayyiya, aje ai takama da dukiyar uba, bata uban waniba, malama kijuya inda kika fito,
" Karki gayamin maganar banza malama, kodamene ubana yafi ubanki, tunda nasan kowa kika tambaya ze gaya miki inada Uba, amma ke wayasan naki uban
Wani wawan Mari Jalila ta saukewa Ilham batare data bari Ilham tagama maganar ba
" Karki kuma dukanmin kanwa, inkika kuma sena rama mata"Muryar Jalal ce, suka waiga gaba daya

Share please
More Comments More Typing.............................

Love u all my Fans
Ina me baku hakuri bazan cigaba da posting kullum ba, saboda zankoma online lectures, amma zan cigaba da kokarin cigaba dayi muku posting nagode sosai




๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ๐Ÿ–Š๏ธ
[9/13, 10:27 PM] +234 816 830 7871: ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน
๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 43
PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Ina me neman afuwarku masoyana, kwana biyu banyi typing ba wayata ta dan samu matsalane
Sannan ina kuma neman afuwarku bazan samu dinga yi muku posting kullum ba saboda zan koma lectures online, Nagode da kulawa

_My first novel_

Jalala ya karaso inda suke, ya kalli Jalila, "kina kuma marinta kema sena mareki, mara kunyar kawai, Ilham sa'arki ce?"
Wani banzan kallo Jalila tayi masa
"Ilham din banza Ilham din wofi, wallahi ta kuma zagina sena kuma wankamata mari dama Jakace kaima kasaba jibgarta, sha3 Karya banza
Mamakine ya cika Ilham wai ita yake tarewa fada, kallon Jalila tayi
" Kece babbar karya baniba"
Jalila tace "kinga karnuka nan" ta nuna Ilham da Jalal,
Ilham tace "Nida yaya Jalal dinne karnuka"
Tsaki Jalila tayi, ta shige ciki, ta hankado kofa, Ilham ta kalli Jalal
Zatayi magana kawai yai tafiyarsa, yabar gurin dama dan ya kuma kunna Jalila yayi, ba nufinsa ya shigarwa Ilham ba, suka batta a tsaye baki bude
"to me suke nufi da hakan?"
Babu me bata amasa dan haka ta juya ta koma gida, se bayan sallar isha'i sannan su Nana suka dawo, Nana tai tabawa Jalila hakuri akan sun tafi sun barta ita kadak, Jalila ta nuna mata bata damu ba, tun ranar da Yaya mairo tazo tayi wannan cin mutuncin Jalila bata kuma bari sun hadu da Jawwad ba, ya damu sosai ko wayarta inya kira bata dagawa, ko palourn ma ta dena fitowa se dai ta zauna a daki,

Yau ta tashi da murnar ummi zatazo, amma haryanzu ba saki jikinta ba abunda su Yaya mairo sukayi mata yana taba mata zuciya, sannan idan ta tuna ummi tafiya zatayi ta barta a gidan, setaji ba dadi,
Nana da halima ne sukayi wa Jalila kara sukayi girki domin tarbar ummin Jalila, amma ita kam ko san fitowa batayi, seda Abba yasa aka kirata ya tambayeta ko akwai matsala kwana biyu baya ganin gilmawarta, amma tace masa ba komai, Jawwad ma yayi sintiri a cikin gidan amma baya samun ganin ta, gashi yana tsoron yaje dakinsu Jalilan, saboda Maama, in yakira Nana yace tabata wayar se taki karba,

Please Login or Register in order to submit comment