Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nibana son zaman Asibiti "

"To maama yanzu zan iso insha Allah, nace ya kuwa Jalilan ta farka ne"
"Ban saniba in kazo kaganewa idonka kaita wani rawar kai akan yarinyar nan ka kiyayeni wallahi"

Ta kashe wayarta
Shidai a iya tunaninsa beyi wani abu dabe daceba amma meyasa maama ta dau zafi haka yayi ta zancen zuci har Jalal yagama shiryawa suka tafi

Sun isa asibitin dukda Jalal ya Dan bata musu lokaci
room din da aka kai Jalila suka nufa
Jawwad ne ya bude kofan tare da sallama
Maama ce ta amsa dayi musu sannu da zuwa,
yawwa tunda kunzo bari mu je Gida dama ruwa zasu karasa mata da allurai kawai su sallameta,
Ninazata tun dazu zakazo Abbanku yazo ya dubata yanzu ya tafi.

shikam gogan kujera ya janyo ya zauna abinsai be kula kowa ba

Alhamdilillah jikin Jalila yayi kyau sun sameta tana rama sallolin dabatayiba

"In ta idar Jawwad ka kira nurse din suzo su karasa mata abinda zasuyi mata seku taho Gida" Maama tafada tana shirin tafiya
Sukagama abinda zasuyi maama da Nana suka tafi Gida.

"Yaya ina kwana"
Jalila ta gaisheshi

"Lafiya qalau ya jikinnaki?"
Jawwad yafada cike da kulawa
da sauki Yaya
"Waime yafaru dakene? Ya akai haka tafaru"?

seda ta kalli inda Jalal yake suka hada ido, tai sauri ta dauke kanta
Ta maida kallonta ga Jawwad

"Kwarewa nayi" tafada a takaice
"Kwarewa kawai numfashi ya dauke ko kinada asthma ne?"

"A'a Yaya banida asthma"

Duk abun nan Jalal danne² wayarsa kawai yake, ba Wanda ya kula a cikinsu
"To tunda kin idar bari inje inkira nurse suzo su miki alluran dafatan kinci abincin?"

"Eh naci abinci, amma ban idar da sallah ba zanyi walhane"

"Kai sisyna bakida lafiya fa ai Allah yaga zuciyarki"
Jawwad ya danyi maganar a shagwabe

Jalal ji yayi kaman ya shake Jawwad yaga yanata wani lallabata hada yiwa mace shagwaba saboda shirme

(Niko nace a ganinka ba)

Itama a shagwaben tafada maganar

"Nifa zan iya Yayana kasan sallah haske ce me girrma kuma tana hana mutum aikata wasu laifukan,
Yayana abune mawuyaci kaga Wanda ya tsaida sallah yana aikata wasu miyagun laifuka da baya kunyar yinsu agaban mutane,
Koda ze aikata yana kunyar mutane suganshi
Kaga inka tsaida salloli biyar seka kara da nafila bakasan abinda Allah ze duba a ayyukanka ba yai maka rahama"
"Nice one sisyna proud of you
Allah yasa iliminki ya amfaneki ya amfani al Umma"
Jawwad tafada yana murmushi
"Proud of u too bros"

Jalal yasan da biyu tayi wannan maganar amma yai kaman besan me sukeba

Seda ta idar da sallah takoma kan gadon sannan
Jawwad ya kalli Jalal
"yace brother zomuje induba nurse din suzo susa mata ayi ai sallamemu"

"Jeka dawo ina nan" abinda Jalal yace kenan
"OK to bari inje"

Gaban Jalila ne yafadi ta kalli Jalal idonsa yana kan wayarsa ba ita yake kallo ba
To in yayi min wani abun fa

Jawwad nafita Jalal ya kalleta
"
Kina tsoron in kumayi miki wani abun ne?"ya mike daga inda yake yadawo kujerar gaban gadonta

"Meyasa baki gaya musu gaskiya cewa taba kika shaba,
rashin sabone kawai, in bahakaba daga shan sigari seki suma kikusa shekawa lahira?"
yafada yana murmushin mugunta

Banza taymasa taki kallon sa
"Yanzu sauranki giya da kwayoyi tunda ina sha kema sekin sha,
Kwanan nan kema zaki fara zuwa mashaya"
Yafada yana hade rai

"Allah ya kiyaye ya tsareni, dazama irinka bazan taba zama irinka ba Mara tarbiyya...
" ohoh wait ashefa Ke kin tsaida sallolinki biyar a rana hada nafila nikuma banayi shiyasa Ke ba irirna bace,"
Nima bani na saiwa kaina ba amma zanyi meyuwuwa inga kinzama Irina tunda jiya kinfara ki rubuta ki aje sauraanki giya da kwayoyi zaki zamaa abar kwatance kaman ABDULJALAL sha³ jahila, I hate u"

"God forbid, over my death body kwatance in dai bana Alkhairiba indai irinnaka ne Allah ya kiyaye kuma niba Jahila bace wallahi"

Hannu yasaka a aljihunsa ya dakko taba da lighter
"naga kaman ta jiya bata isheki ba sokike in kara miki wata"

girgiza kai tashigayi tana zare ido

"Mara kunyar karya kawai"

Yafada tare da maidasu aljihunsa

Ya mike ze koma kujerar da ya taso kawai yaji muryarta tana fading

"Kuma wallahi Allah ya isa abinda kamin jiya kodayake bakasan ma'anarta ba kona maka bazaka damu ba amma ban yafe wallahi azzalumi kawai me kama da yan daba"

Ohh God yarinyar nan ba zata canza ba,

Dawowa yayi inda take har gaban gadonta yasa yatsunsa biyu a side din kumatunta ya matsa da karfi

Wani uban ihu tasaka saboda zafi jitayi kaman ze Huda mata kumatu da yatsunsa nan da nan hawaye ya shigo zubowa daga idonta wani nabin wani sedayaga fuskarta tayi jawur hawaye na ambaliya a fuskarta

Sannan ya cikata Yakoma inda yake zaune da farko yana danna waya
Jawwad ne yayi sallama tare da nurse
Kallonta Jawwad yayi
"lafiya kuwa sisy kukan me kikeyi?"

Seda ta kalli inda Jalal yake amma ba ita yake kallo ba
"Ni Kaduna zankoma gurin Ummi'"
Tai maganar tanakuma fashewa da kuka

Se da Jalal yayi murmushi mugunta

"Haba Jalila dama hayanzu kina wannan rikicin naki kiyi hakuri in muka koma Gida mayi wannan maganar"
Kai kawai ta gyada masa

Nurse din takarasa mata abinda yakamata aka sallemesu.

Har suka Shiga mota suka kama hanyar Gida kuka takeyi shikuma
Jawwad se aikin rarrashi yake

Shikam Jalal Jawwad yafi bashi haushi se wani lallabata yake

Itakuwa ita kadai tasan zugin da fuskarta takeyi ga kirjinta hayanzu ba dadi saboda wahalar yin numfashi da tayi
(Nikam nace in rashin kunya abinyine gobe maki kara)

Maama da Nana suka iso Gida Nana wanka tayi ta kwanta saboda batasamu tayi bacci sosai ba Daren jiya
Maama kam datayi wanka seta shiga kitchen da niyyar Dora sanwar rana
Sallama taji a parlour Dan haka ta aje abinda take ta domin ganin me sallamar
Wata matace mekama da maama sekuma wata budurwa da batafi sa'ar su Nana ba

"Yaya mairo sannu da zuwa yanzu kuke Tafe da ranar nan"

Wadda takira da Yaya mairo tace

"eh mune ai munzo tunsafe bakowa a gidan narasa INA kuka tafi da safe haka gashi ni ba waya a hannuna tasamu matsala,
Kukuma makota kowa gate a rufe sekace marasa gaskiya"

"Wallahi kinga Jalila ce tazo mana hutu se kuma ta yanke jiki tafadi jiya,
A Asibiti muka kwana sedazu muka dawo, mun baro za a sallamata Jawwad ze taho da ita"

Wani mugun kallo Yaya mairo tayi mata

Sun iso gida lafiya sukayi parking
Jalila fuska duk hawaye amma se cewa tayi "Yaya JAWWAD an kira azahar ka tsaya a masallaci kai salla
Kasan sallar jam'i tafi lada akan sallar mutum daya kodayake garama Wanda yakeyi shika dai wanima bayayi"
Jawwad ne ya kalleta da mamaki da nufin yayi magana

Ta bude kofa tafice da Sauri

Shiko Jalal yasan dashi take sarai haka halinta yake bazata canza ba amma seyayi kaman beji me tace ba shi dariya ma taso bashi ganin fuskarta duk hawaye amma Neman magana take

Ta nufi cikin gida abinta har yanzu jikinta babu kwari sosai, tana shiga ta nufi dakin maama domin ta Sanar da ita ta dawo an sallameta
takama handle din kofar da nufin ta shiga
amma maganganun datajine
Suka Sa ta daskare a tsaye zuciyarta ta fara bugawa da karfi

"Gaskiya zainabu baki da hankali yanzu har asibiti kikaje jiyyarta kika barota da danki, dangin arna ababen kyama kika bari tana mu'amala da yayanki hartazo miki Gida Hutu koda take musulma ai daga tsatson arna tafito!!!"""

Tirkashi wasa farin girki

Please share

More comments more typing......



🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 5
PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

I want comments not stickers😢😢😢😢
Comments dinku shine kwarin gwiwata

_My first novel_

Haka ta tsaya daga inda take ta dinga caccaka masa maganganu son ranta maganganu masu ciwo ciki harda Kalmar dayafi tsana Mara tarbiyya sabida tasan baze iya cinmata ba

"Inda zuciya kadena shaye shaye kazama mutumin kirki kacigaba da abota da yayana in ba zuciya kuma kacigaba da zuwa kana like masa cingam ko kuma ince
Salansa sarkin hayaki ""

Ta juya takoma cikin Gida abinta kaman batayi komai ba
Maama ta tarar a palour tana tsifa

"Maama kawo in tayaki naga tsifar dayawa "
"To karbi kibiyar"

Hmm yarinyar nan akwai shiga rai ba ruwanta dukda tasan abinda ke tsakanina da mahaifiyarta amma ko a fuskarta ban taba ganiba,
inma dai salon wani makircinne duk zan iya daku d'a na ne dai ba a isa a hada min zuri a da wadda take da raunin nasaba ba, tayi wannan zancen a zuciyarta.

Shikam tsayawa yai cak kaman an dasa shi, yama rasa wani mataki ze dauka, fasa zuwa gurin Jawwad yayi ya koma gida ya shige dakinsa, ya dinga tuttulawa cikinsa giya seda yayi mankas sannan ya zube a gurin yana bacci.

"Nana gaskiya abinda Yar uwarki tamin ya mugun bata min rai, ya dace tafadamin haka agabana taci zarafin Dan uwana, wallahi taci albarkacinki dasena shukamata rashin mutunci wallahi"

Itakuma tsayawa zatayi tana kallonki ba bakisan wannan uwarkice a fitsara ba kina ganinta haka shi kansa uban gayyar ina tsoron randa ze danketa (Jalal)Nana tayi maganar a zuciyarta a fili kuma Se cewa tayi

"Nasani Ilham bata kyauta ba amma zanmata magana haka halinta yake bata boye abu a ranta komene ne zata fada a gabanka amma kiyi hakuri insha Allah hakan baze kuma faruwa ba"

"Kinga ni tafiya zanyi bansamu biyan bukatana sema karamin takaici da kukayi"

"Naface kiyi hakuri Dan Allah ki gaida mommy"

Banza tayi mata tai tafiyarta
a palour taga Jalila nayiwa Maama tsifa harara ta wurgawa Jalila amma me ita seta maida mata da murmushi

"Kigaida Gida sister Ilham agaida mummy da yayanmu" tafada dauke da murmushi a fuskarta

Maama CE

"Ilham kicewa mummynku in ankawo lesunan tamin magana zan turosu su zaba"

"To zangaya mata"

shine abinda ta iya fada saboda Jalila takawota iya wuya.

Tana zuwa Gida dakinta ta wuce ta nemi guri ta kwanta maganganu Jalila suka shiga dawo mata

{"Sedai in akwai wani sirri da kike
boyewa Wanda bakowa yasani ba"!!}

To ya akayi tasani, taga a iya tunaninta babu Wanda ta taba wannan zancen dashi balle ya gayawa Jalila
To ya akayi tagane akwai wani abu a ranta haka taita tunane²
Har bacci yayi awon gaba da ita

Se banyan isha'i sannan giyar da yasaha tasake shi ya farka daga nannauyan baccin da yayi, ji.yayi kansa yayi mugun nauyi kaman ba a jikinsa yake ba haka ya tashi yana rarraba hanya ya shiga toilet yayo wanka tare da alwala

Ya fito palour ya shimfida sallaya yayi azhar yayi la'asar ya dauke sallayar

(Nikam nace magariba da ishan fa?)

Cikin gida ya shiga ya tarar mummy na waya, ya kai minti biyar yana jira amma wayar taki karewa har ya kosa yagaji da zama yafara tsaki

"To Dan sarkin Mara kunya tsakin me kake" mummy tafada bayan ta kammala wayar

"Tun dazu na shigo kina kallo amma kin tsaya kina surutu a waya kin barni ina zaman jiranki kuma kinsam gurinki Nazo"

"Wayar da nake ne surutun JALAL?"
Tafada tana kallonsa

"Munyi waya da megidan nan dazu yace in gaya miki yana dawowa jibi"
yafada a takaice batare daya bata amsan tambayrta ba, inba hakaba yanzu zata fara masa fada Takara masa wani takaicin, kuma shi a rayuwarsa ya tasani fada.

Ilham datake kitchen taga shigowarsa Dan haka ta aje abinda takeyi ta dakko juice da cup ta dorosu a tray ta fito palour tana yauki ta nufi India Jalal yake

Cikin iyayi tafara magana

"Yayana ga juice na kawo maka"

Bece komai ba sema Kafeta da yayi da ido ko kiftawa ba yayi
Nan ta sha jinin jikinta saboda kallon da yakemata

"Mtsewwwww" yaja wani dogon tsaki ya mike ze bar palourn

"Haba Jalal meyasa kake hakane? Ilham fa kanwarkace koba komai ai yakamata ka karba kasha" mummy tayi maganar adan hasale

Ko takansu be biba seda yaje bakin kofa ya tsaya batare da ya waiwayo ba

"Yace in gayamiki jirgin karfe hudu ze biyo" (yana nufin mahaifinsa)
Yayi gaba abinsa

"Na shiga uku mummy meyasa Yaya Jalal yakemin haka kwata² bana gabansa mommy kiyi wani abu Dan Allah wallahi ina son Yayana amma ni meyasa baya sona"
Ilham takarasa maganar cikin sheshsheka kuka

Rungumota mommy tayi tana rarrashi
"kiyi hakuri Ilham ina iya kokarina ni kaina fama nake Jalal kinagani ina mahaifiyarshi amma ban isheshi komai ba
Amma in dai ina raye Jalal bashi da wata matar inba keba insha Allah"

Aikuwa daga ranar da burina yacika kingama yawo mummy dan sekinyi kuka da hawayenki Dan ba lefi bane in anmaka abinda kayi tafada a ranta amma a zahiri kuma secewa tayi

"Allah yasa mummy kitemaka min burina yacika in mallakeshi Dan Allah wallahi in ba shiba bazan iya auren kowaba"

"Karki damu Ilham keda Jalal duk abu dayane a gurina insha Allah zanyi duk meyiwuwa inga kin auri Jalal"
"Nagode sosai mommyna inkikamin haka kingamamin komai"

Wai ni Jalal yarinyar nan take cewa innayi zuciya indena kula yayanta saboda muna da banbancin tarbiyya
Zanyi maganinta ai rana dubu ta barawo daya tak itace tame kaya zan kamata a hannu
Haka yayi ta wannan zancen zucin

Bayan kwana daya
Gidansu Jalal suka tashi da aikace² saboda shirin dawowar magidan,
sedai aikin yayiwa mummyn da Ilham yawa saboda me aikinta ta tafi kauyensu za ai bikin yayarta ga Ilham da shegen son jiki.

Dan haka mummy ta Yanke shawarar kiran maama a waya tace Dan Allah tabata Aron su Jalila su tayata aikin dan yayi musu yawa,
kimanin wata hudu kenan rabon mahaifin Jalal da Nigeria Dan haka dole ayi shiri na mussaman domin tarbarsa.

A waya ta kira maama ta sanarda ita Dan Allah inba abinda su Jalila suke ta turo su tayata aiki ayyukan dayawa

Itakuma tace zata turomatasu

Dakinsu mama taje ta sanar dasu sakon mummyn Jalal

Nanace tace

"To maama zamuje insha Allah"

Itakuwa Jalila cikinta ne yayi wata kara me sauti kuuuuuuuu!!!

"Na shiga uku ni Jalila !!?

" me yafaru ne Jalila?" Nana ta fada tana kallon Jalila

"Au tambayata ma kikeyi yanzu in Jalal ya ganni fa? Yanzu ni yazanyi"

"Tab yanzu meye abunyi ainamanta da kinmasa rashin M,
shiyasa nace miki ba ruwanki dashi Jalila yanzu ga irinta nan"

(Nikuwa nace hmm danma bakomai kikasani ba jiyama tamasa rashin kunya" Jalila sarkin rawar kai da shishshigi)

"Kinga ni ba wannan ba ko ince kawai bani da lafiya? Se in zamana base naje ba"

"Kai Jalila wannan ba shawara bace yanzu fa Maama ta shigo ta ganki ras dake sannan kice baki da lafiya wannan ba shawara bace Sam"

"To ya zanyi? Inkuma muka hadu fa ?"
"Bazaku haduba insha Allah kitsaya a waje in leka in baya nan seki shigo"

"To amma nikam ina jin tsoro Nana"

"Ba abinda ze faru insha Allah, kwantar da hankalinki taso mu tafi"

A kofar Gida Jalila ta tsaya tana waige² itakuma Nana ta shiga domin dubawa in Jalal yana nan minti uku Sega Nana ta fito ta kalli JALILA ta girgizamata kai

"Shigo baya nan"
"Kin tabbata"?

"eh na tabbata banganshi a ciki ba,
Hmm waike dama kinsan kina jin tsoro amma kika tsokano shi"

"Ke ni matsa in wuce tun kafin ya dawo ya ganni anan" Jalila tafada a gaggauce

Tare suka shiga cikin gidan Jalila tana ta faman rarraba ido

A palour suka ci karo da Ilham rike kwanuka zata shiga kitchen, bata kula suba tai shigewarta batace musu komaiba ta shige kitchen ta ajiye kwanukan sannan ta fito sewani shan kanshi take tana hura hanci

"Waike Ilham har yanzu abinda yafaru be wuceba a gurinki kike ta wani kallonmu kina hade rai
Indai Jalila CE ita tamanta ma kunyi kiyi hakuri Dan Allah"

Jalila kuwa a ranta cewa tayi
Tab lallai aiki yaganki indai nice bana gani inyi shiru

"Hmm bakomai ya wuce kuzo mukarasa mummyn tana ciki"

Suka bita gaba daya wani part suka nufa Wanda tunda Jalila tazo a rufe take ganinsa tana kyautata zaton shine part din mahaifin Jalal

Shigarsu yayi dai² da fitowar mummyn dauke da labulaye a hannunta, Nana daga inda suke ta Dan rusuna ta gaisheta ita Kuwa Jalila seda ta durkusa har kaasa, sannan ta gaisheta, fuskarta a sake ta amsamusu

Har cikin ranta taji inama Jalal din tane haka yake girmamata

Karasawa Jalila tayi gurin mummy ta karbi kayan hannunta
"mummy kawo ina za akaisu?"

"Dama wasu za a canza wannan zan badasu wanki biyoni seki karbo wasu a canza tace to"

Juyowar nan dazatayi taganshi zaune akan kujera, alamu ya dade a gurin itace bata lura dashi ba

Nana kuwa tun shigowarsu taganshi a zaune amma ta lura JALILA ba ta Ganshi ba,

Be dago ya kalleta ba seda mummy tayi gaba tabiyo bayanta, sannan yayi mata kallon zamu gauraya dake

Itakuwa kallon up and down tayi masa hada murguda baki tayi sauri tabi bayan mummy

Akajima Jalila ta dawo da labulaye a hannunta suka fara gyaran part din yana zaune beje ko ina ba

" mummy tace Nana da Ilham suzo su siyo abinda babu saboda girki tunda taga Jalila tafisu rashin son jiki"

"Mummy indai Jalilace intaga dama batajin aiki "
"Ainima naga alama Nana"

ILHAM da Nana suka tafi cefane yai saura Jalal, Mummy, se Jalila

Mummy ce take kokarin Jan wata durowa na litattafai amma takasa,
Jalila tazo ta tayata amma suka kasa,
Takaici ya ishi Jalila ganin ga JALAL a zaune amma yakasa temakawa tsaki taja

"Mtsewww mummy wannan Dan naki bashi da amfani Sam wallahi yana kallo muna fama amma ko a jikinsa"
"India JALAL ne kadan kika gani bari in dakko bagco a rage litattafan mugani ko zamu iya janye durowan"

Ita Jalila a hankali tayi maganar batai zaton yajiba,
Sedai kawai gani tai yana kallonta

Mummy na Barin dakin,
ya tashi ya tako har gabanta yana muzurai yana mata wani irin kallo, yana zuwa gabanta yatsaya yadan kura mata ido

Nan da nan jikinta ya dau rawa

"Mara tarbiyya, Mara amfani, mutumin banza, mekama da yan daba, Dan shaye² Niko?" Yanuna kansa da yatsansa

"To bari ingaya miki wani abu ba tsoronki nakeji ba Dana kkyaleki ban kakkaryaki ba,

bana son in batawa Dan uwana rai sedai kawai zan maidake Irina ne, shize tabbatar miki bani da tarbiyya kinga in mukazama mu biyu semunfi dadin kwatance
Sha³ Jahila kawai dakikiya na tsani ganin ko fuskarki"

Ya juya da nufin yafita yabar dakin

" duk jahilcina nasan girman iyayenaa kuma inazuwa makarantar islamiyya,
a islamiyyarmu ma nasan akwai ukuba game sabawa iyaye tundaga duniya, dukda Jahilcina bana zuwa mashaya ina girmama manyana, kaga sekanemi waye jahili"

Yana jinta kalamanta suna dukan zuciyarsa amma ya fice ya kyaleta da sannu ze maganinta.

Haka sukayita aiki har yamma tayi suka shirya girke² suka gyara ko ina Wanda yakasance Jalila ce karfin aikin

"Karfe hudu da rabi dai² Jawwad da Jalal sukaje airport suka dakko Alhaji Habib Kamal,
mahaifin Jalal ya karaso gidansa cike da farincikin ganin tilon dansa cikin koshin lafiya, dukda yawan korafin da mahaifiyar D`an nasa kanyi masa game da miyagun halayen yaron nasu.

Gaba daya sukashiga cikin gidan kowa se fara a yakeyi ana mass sannu dazuwa
Daka ganinshi kasan mahaifin Jalal ne saboda tsabar kamar dasukeyi,


kaman yadda yake dabi'ar Jalila, har kasa ta durkusa ta gaisheshi,
Da sakin fuska ya amsa mata tareda cewa
" wannan fa?"

"Ai Yar wajen marigayi ce kanin babansu Jawwad" mummy tabashi amsa

"Allah sarki, Ashe takwarar Jalalce ta girma haka, tubarkallah
gata nutsatsiya
Allah yaraya ma naku gaba daya"

Suka amsa da "Ameen" gaba daya

Banda Jalal dayake ta cin magani a ransa yace "wai wannance nutsatsiya munafuka Mara kunya yarinya"

Watsewa suka farayi a hankali domin Barin daddy ya huta

Ilham ta tafi dakinta tashiga wanka saboda tagaji,
Jawwad yakoma Gida

Shikuma Jalal yatafi part dinsa

Jalila da Nana Suma suka nufi hanyar Gida har sun fito Jalila ta tuna wayarta tana gidansu Jalal inda ta kwaso labulaye daga Shanta

"Au Nana wayata rakani in dakko please"
"Gaskiya nagaji bazan koma b"

"Dan Allah ki rakani, inkuma Jalal yakamani fa?"

"A gabanki fa Yakoma part dinsa baya cikin gidan inajiranki anan jeki dakko"

"To bari inje"
Tashiga ba kowa a palourn Dan haka da sauri tashiga ta dakko wayar,

tana zuwa corridor din daze sadata da waje taganshi a tsaye yabawa inda take baya yana waya na Shiga uku inya kamani na shiga uku, wata dabara ta fado mata

Ta tako da gudu zata wuce tabayansa caraf ya riketa

"Haba karamar Mara kunya kinzaci bansan da shigarki bane yau babu me kwatarki zanga karyar rashin kunya",

" meye haka dalla malam cikani"
Tafada tana kiciniyar kwace kanta

"Ooh har kin manta da maganar mune
Zan maidake Irina ne kawai in samu abokiyar shaye²"

"Dalla ka cikani ni ba Yar iska bace "

"Nima ba Dan iska bane kawai Mara tarbiyane, kema kuma hka nakeso kizama,
yanzu sigari kawai zaki sha kema kizama salansa kaman ni kullum bakinki cikin hayaki"

Wani mugun kallo tayi masa

"Allah ya kiyaye in zama irinka kai halinka har wani abun sone mara...........

Bata karasaba yasaka sigarinsa a baki ya zuka hayakin a bakinsa

Ya rikota yasa hannunsa daya ya toshe mata hanci, yasa bakinsa a nata ya dure mata hayakin nan tas a bakinta,

aikuwa take numfashinta ya sarke,
Yakuma zuka ya dura mata sau uku

Sannan yasaketa ta zube tana wani irin tari tana Jan numfashi da kyar, idanun ta sukayi jawur, numfashinta yana sama yana kasa kaman me asthma

Share please

More comments more typing............




🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 7

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680

Is a free book

I want comments not stickers😢😢😢😢
Comments dinku shine kwarin gwiwata

_My first novel_

Aimin afuwa
Today's page isNot Edited




"To wai Yaya mairo me kikeso inyine yaje ya taho da ita yace anan zatayi Hutu to korarta kikeso inyi ko kuma yazanyi
Kinsan halin Abban su Jawwad yanason Dan uwansa akan yarinyar nan beki yamin wulakanci ba"
Maama tayi maganar cike da damuwa

"Seki hade mata fuska yadda nan gaba in ance tazo miki Gida bazata zo ba akan me azo akoyawa yaranki dabi'un arna kinsan ba kunyace dasu ba har kibarta da danki su kwana daki daya da yarinyarki"

Jikin Jalila a sanyaye ta saki handle din kofar ta koma da baya idanunta na zubda hawaye bazata iya cigaba da jin wannan miyagun maganganun da cin fuskar ba

Wai itace dangin arna ababen kyama to shikenan su arna ba mutane bane

Kaman wadda kwai ya fashewa a ciki haka taja kafarta ta nufi dakinsu ta shiga ta tarar Nana da wata budurwa wadda batafi sa'arsu ba (wadda sukazo da yaya mairo)
sallama tayi a hankali

Nana na ganinta ta mike ta rungumeta
"Oyo yo Jalilana sannu ya jikin"

Murmushin dole Jalila tayiwa Nana Wanda iyakarsa bakinta "
da sauki Nana nasaku wahala sannuku Nagode"

" shhhh meye kuma wahala anan bana son irin wannan zancen gaskiya babu haka a tsakaninmu"

"To na dena Ashe bakuwa kikayi"?
" baki ganeta ba Sa'ada cefa Yar gidan Anty mero"

"Eyya banganeta bane sannunki"
Jalila tafada
Sa'ada ta Dan dubeta a yatsine "yawwa sannu"

"Nana bari in Dan watsa ruwa"

"To a fito lafiya kiyi a hankali inda wani abu daba zaki iya ba kimin magana " Nana tafada cike da kulawa

"Karki damu zan iya komai da kaina"

Towel ta dauka ta shiga toilet dayake toilet din a cikin daki yake

Tana shiga bandakin Sa'ada ta gyara zama cike da gulma

"Ke Nana yanzu Dan Allah wannan danginsu arna ne?kuma kike zaune tare da ita ko kyamarta ba kyayi?"
A fusace Nana ta kalleta
"Mene haka Sa ada ina ruwanki?
Waima tukuna ubanwa yagaya miki haka karki karamin irin wannan maganar bana so" Nana tai maganar a fusace

"Daga fadan gaskiya se ki kama min jaraba, ai dai kinsan mamanmu bazatayi karya ba ke Yar uwata ce bazanso kishiga wani hali ba ni warin arna ma naji tanayi"

"Ke

Please Login or Register in order to submit comment