Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

musulmi kuma bahaushe

Kwanci tashi Aliyu ya kammala service dinsa
Dayazo da maganar auren marry Gida malam yace be yadda ba, ga yayan musulmi nan a garin nan dan haka ya hakura da maganar yarinyar nan.

Marry kuwa taita rashin lafiya saboda Aliyu ya tafi ga kuma anki yadda da ya aureta, mamanta ta dena kulata sarki yayi fushi da ita duk da soyayar da yake mata, ita kuma ta kafe tace ita se Aliyu
Shima nan haka Aliyu yake ta fama da malam amma yaki yadda, inna mairo CE kawai ta goyi bayansa amma malam ya kafe yace be yadda ba sedai ya auri musulma

Da wannan rikicin seda aka shafe shekara biyu ana fafa tawa da wannan rikicin

Marry taje ta samu maman ta tace itafa gaskiya zata tafi kano gurin Aliyu shi takeso bazata iya zama a garin nan ba
A gigice Maman ta taje tasamu sarki ta gaya masa, juyin duniya marry ta kafe tace itafa gaskiya tunda bazasu yadda ba tafiya zatayi,
Dan haka sarki yace to ya sallameta basu ba ita har abada karta kara dawowa, marry tace ta yadda,
Tana kuka mamanta na kuka haka ta hada kayanta ta nufo kano.........

Bayan la'asar marry ta sauka a kano layin Aliyu ta shiga kira bugu biyu ya dauka

"Aliyu kana ina ne?"
ta tambayeshi

"Ina gida"
Yabata amsa
"Kazo ka tafi dani Dan Allah"
"Ahh wai kina ina ne?"
"Aliyu kazo ka daukeni ina kano fa yanzu na karaso"

Zaro ido yayi
"Are u serious?"
"Dagaske nake"
A kidime ya tashi ze fita sukayi karo da Usman
"Dan uwa ina zaka, naganka a kidime haka"

"Dan uwa marry ce ta biyoni kano"
"What are u serious"
" yanzu mukayi waya da ita ta fadamin"
"Muje tare"
Usman ya fada yana Jan hannunsa suka fice

Kaman yadda ta fadamasa a tasha sukaje suka sameta rungume da akwatinta
Haka suka Dakkota suka taho gida

Suna zuwa Zainab ta karewa marry kallo

"Wannan fa daga ina"?
Tafada a yatsine saboda ta ganta tare da Usman ga kuma uban akwati

" bakuwace"
Shine kawai abinda Usman yace mata suka wuce bangaren inna mairo
Lokacin ana ta kiraye² sallar magariba dan haka suka kaita dakin inna mairo suka tafi masallaci
Bayan inna ta idar da salla ne tare da lazimi
Ta kalli marry tace mata
"Sannu da zuwa"
"Yawwa mama ina wuni"
Tafada da hausa amma a hausan tata zaka fuskanci ba cikkakiyar ba haushiya ce ba

"Lafiya kalau, amma banganeki ba "
Dan sunkuyar da kai tayi
"Tare muke da Aliyu"

Nan inna mairo ta gane wace ce

Tabata Abinci da ruwa tabata guri ta huta

Se bayan sallar isha'i sannan su Aliyu suka dawo gidan a dakin inna mairo suka hadu suna jiran zuwan malam Imam suji me ze yanke,

Zainab se sintiri take so take taji wace wannan bakuwar dasuka zo da Usman da Aliyu harda su trolley ita dai bata san taba

Akajima se ga malam imam ya dawo yazo ya samesu a zaune jungun² a dakin inna mairo

"Ya akayine na ganku a zaune kunyi shiru, bakuwa mukayine"

Inna mairo ce ta shiga korawa mamalam imam bayani

Ransa ne yayi matukar baci da jin inda jawabin NATA ya dosa, ya tashi ya bar gidan gaba daya
Seda yayi kwana biyu baya shiga harkarsu

Zainab kam ta uzzurawa Usman setaji wace ce yarinyar nan amma yaki gaya mata

A kwana na uku
Aliyu ne yasamu malam a tsakar gida yaje gabansa ya durkusa

"Baba na dama akwai lokacin da zezo kayi fushi dani haka kadena kulani Aliyun ka nefa dan autanka
Kasan bantaba dakko maka magana ba meyasa bazaka yadda da niba"

"Ya raina baze baci ba, seda na jamaka kunne akan yarinyar nan, amma saboda baka jin maganata kaje ka ja jubota ka kawomin ita gida haba Aliyu yaushe kafara dena jin maganata"?
Marry tanajin abinda ya faru a hankali ta tako ta karaso gaban malam imam ta zube

"Baba ba laifin Aliyu bane ni na kawo kaina dan girman Allah karka koreni, kafison in koma inda na baro kan addinina na baya?
Baba kaifa malamine kuma ubane dan Allah baba musulunta zanyi, ka auramin Aliyu idan na bar nan bazan koma gida ba wani gurin zanyi in ka koreni bansan inda zani ba,"
Duk wannan maganar da take cikin kuka takeyi
Aliyu ma gaban malam ya durkusa ya rike hannunsa

"dan Allah baba na ka amsa mana ka yadda in auri maryam dan Allah baba inba ita na aura ba wallahi bazan iya auren wata mace ba"
Usman ma gaban malam yaje

" baban mu tun tasowarmu kake sonmu kake kula damu, kake son abinda mukeso, baba ka amince da bukatar dan uwana,
Baba ka girmama son da maryam da Dan uwana kema junansu Wanda yasa ta baro daular da take ciki ta taho gurin mu, inka yadda da auren nan kaman kayi jihadi ne"

Inna mairo ma cewa take

"Malam a duba lamarin nan d'a na kowa ne mukanmu misaline munzo garin nan. Bamu da kowa"

Ajiyar zuciya yayi ya nisa sannan yace........



Share please


More comments more typing.................



Mss~dyjeer naga rago godiya nake😂
Anty Jamila a soye tabani ta hutaddani suya
Afshan
Rahmatoulaye
Salma
Afshan
Fatima zahrahs (tsofaffi)
And the remaining members
Ina alfahari daku ❤❤❤❤❤




🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_
(2020)

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 10

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
What's https: //chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Is a free book

Ina yinku AbdulJalal novel fans irin💯💯💯 da duk sauran masoya wannan novel ina jin dadin comments dinku love u all ❤❤❤

I want comments not stickers or just thanks😢😢😢😢
Your comments give me courage

Haka suka cigaba da tafiya sunayi suna hira jefi² har suka shiga garin Kaduna
Karfe 4 dai² suka iso kofar gidan su Jalila, suna parking Jalila ta fito bata tsaya bi takan JAWWAD ba balle trolley dinta, ta sakko ta ruga da gudu cikin Gida,
Ummi tana tsakar gida ta idar da salla Jalila ta shigo da gudu ta fada jikinta tana murna
"I really miss you ummina"

"To karyani ki huta sarkin fitina ga yanda kika shigo da gudu kaman an koroki,"

"Bikiyi missing dina ba ko ni duk na damu saboda rashinki a kusa dani amma daga zuwana kin faramin fada"
Ana haka JAWWAD ya shigo da trolley din Jalila,

"Au shi kikabari da dakon kayannaki? Kekam se a hankali"
Ummi tafada tana ture Jalila daga Jikinta

"Ba komai Ummi naga ta kagu ta ganki ne yasa ta manta da trolley"
Yafada yana murmushi

Murmushi Ummi tayi
Har kasa ya tsuguna ya gaida Ummi ya zauna
Ta amsa fuskata cike da fara'a haka ya zauna sukayi ta hira da ummi,
Ummi tana kaunar Jalal kodan yadda yake son diyarta dakuma yadda mahaifinsa yake tsaye akan lamuransu ita da yarta
Bayan haka kuma JAWWAD yarone me matukar biyayya da hakuri

Sallar la'asar yayi, be wani dade ba yace tafiya zeyi,
"Jawwad tun yanzu"
"Ummi bana son tafiyar dare ne"
"Hakane kam bata da dadi"

To Dan jirani ina zuwa daki ta shiga ta dakko wani turare me kyau tabawa JAWWAD yayi godiya sosai

Yayiwa Jalila alama da ido ta tashi tarakoshi waje
"Sisyna zanyi missing dinki zuwan nan naki yayi min dadi gashi kin dawo kin barmu"

"Allah sarki yayana nima banji dadin rabuwa daku ba "

"Sisyna kiyi karatu kinji nasan ke mutuniyar kirki ce, banda kula kawayen dabasu zuwa makaranta
Banda tsokana da shagwaba"
Ya karasa maganar da sigar tsokana

"Insha Allah yayana"
"Good very good sister, insha Allah very soon zan dawo mukoma"
Dan turo baki tayi batace komai ba

Mortar ya bude ya dakko wani jaka yabawa Jalila
"Thank u very much my brother"
"Shhhhh don't mentioned dear"

"Wish u safe trip brother thank u very much ka gaida min da Nana ta"
"Zan gayamata and karki manta dayiwa yayanki addu a"

"Addu a mekakeso in maka"?
"No bani ba Jalila yayanki Jalal"

"Yaya kaikam narasa wanan kaunar da kakewa Jalal"

"Hmm sisy na kenan zakiji komai insha Allah in kinkuma zuwa kano zakiji dalili"
Yabude mota ya shige yatada mota yana daga mata hannu
Seda ya bace ma ganin Jalila sannan ta koma cikin Gida

"Ummina gayamin me yafaru bayan tafiyata ?"
"Ke dai bari Babyna gidan ba dadi daba kya nan, kawayenki na islamiyya se sintiri suke min, nayi missing dinki sosai daughter na"
Ummi tafada tana shafo fuskan Jalila

Jalila ta riko hannun ummi
"Allah sarki ummina haka kike sona dama?"

"Hmm Jalilana a duniyar nan a yanzu wanake dashi bayan ke kin ko son soyayyar dake tsakani da da uwa, da baki tambayi haka nakesonki ba"

To amma ya akai tsakanin Jalal da mummyn Sa basa jituwa shi bayajin wannan soyayyar ta mahaifiyarsa a ransa, Jalila tai maganar a zuciyarta

Da daddare bayan Ummi da Jalila sunci Abinci
Ta je ta dakko trolley din ta, ta dakko kyautukan da ta zo dasu ta nunawa Ummi sannan ta dakko Wanda ,Jawwad yabata

Katuwar teddy ne Ja da kuma manyan kwalin chocolate kusan guda biyar
"Allah sarki yayana Allah ya karemin Yaya Jawwad har yanzu be manta abinda nake so ba "
Ummi kallonta ta tayi tai murmushi
"Hmm Jalila kenan, Jawwad ya biyewa shirmenki hada siyamiki teddy da girmanki"

"To ni ummi har wani girma nayi
Yawwa Ummina tambayarki zanyi"

"Allah yasa nasani"
" Naga nabaki abunda akabani a gidansu Jalal baki tambayeni waye Jalal ba ko kinsanshi ne?"

"Eh nasan yaron koba makotan su Jawwad ba"?

" Ummi shine, amma kinsan yazama dan shaye² bashi da tarbiyya Sam bakiga yadda yakewa mamansa ba ya akayi kika sanshi?"

"Allah sarki Jalal da ba haka yake ba daga baya yazama haka abokin Jawwad ne tun suna yara kanana
Daga baya yakoma haka saboda wani abokinsa ko wayake oho?
Amma naji ance hada laifin mahaifiyarsa amma bansan ya akayi ba nikam"
"To Ummi ya akayi mahaifiyarsa tabari yazama haka"

"Ke rabu dani nima ban saniba sarkin tambaya meyasa baki tambayesu a can ba ni rabu dani bacci nakeji"
"To shikenan Ummi "

Har sun kwanta bayan wasu mintuna da kwanciyarsu,
Jalila ta nisa
"Ummina"
"Na'am Jalilana"

"Yaushe zaki kaini garinku inga yan uwanki?"
"Jalila meyasa kikayi min wannan maganar, so kike ki hanani bacci ko rigimar zakimin daga dawowarki ko baby, bana so yi baccin ki kawai nasan kingaji"
"Ummi bazan iya bacci ba sekin Sa ranar dazaki kaini garinku ni wallahi ko wasu irine ina so inje in gansu Dan Allah Ummi koba Sa sanmu ni inasonsu a haka Ummi kitemaka"
Jilila ta karashe magNar tare da rike hannun Ummi tana hawaye"

Fizge hannunta Ummi tayi
"Nemi gurin kwanciya kafin in wanka miki mari"
Ummi ta daka mata tsawa haka Jalila ta kwanta ta juya wa Ummi baya tana kuka
Har cikin zuciyarta Ummi takejin kukan Jalila tareda tausayinta.

Tayi rigingine tana tuna abubuwa da dama dasuka shude

*********
Aliyu Imam Habib shine cikakken sunan mahaifin Jalila su biyune kawai a gurin iyayensu shida yayansa Usman Imam Habib (babansu Jawwad)
Mahaifansu sun haifi yara dayawa sun rasu su biyune suka rage asalin iyayensu Fulanin Adamawa ne ne akayi wata rigima yan fashi suka je rigar fulanin aka karkashe wasu, yawan hare² da ake kaiwa fulanin ya tilasta wasu suka watsu a Sassan Nigeria an kashe musu yan uwa da dama malam imam da shi da me dakinsa mairo sukayo hijira zuwa kano.
an kashe musu yan uwa dayawa, wasu daga cikin yan uwan Nasu kuma basu San inda suke ba abinda suka tsira dashi bashi da wani yawa, duk da kasan cewar su masu arziki a rugarsu amma haka suka siyar da abinda ya rage musu suka taho kano (ta dabo jalla babbar Hausa kodame kazo an fika)

Zuwansu kano a lokacin duniya tana kwance , a lokacin in akayi baki masarautar kano zamanin sarki Ado bayero ke bawa baki masauki Dan haka masarautar kano su sukabawa su malam imam masauki, inda akabasu katon Gida a unguwar mandawari
Gidansa ya kasance kusa da gidan wani alaramma malam shehu, malam shehu yanada Tarin almajirai dan haka zuwan malam imam kano basu San kowa ba wannan makocinasu shiya zama kamar Dan uwansu
Shi ya kai Imam kasuwa ya hadashi da wani almajiransa ya koya masa san'ar takalma a kofar wambai
Sannan in ya dawo sukan zauna da malam shehu ya koyamasa karatun addini
Imam yasamu Ilimi me tarin yawa a gurin malam shehu wanda ya kaishi ga zama mahadddacin qurani, sannan yana samun alheri a kasuwancinsa yA tsaya akan gaskiyarsa dai² gwargwado,
yana samun rufin asiri a sana'arsa
Haka bangaren matan malam uwar gidansa ta dauki mairo kaman Yar data Haifa yayinda amaryarsa takasance masifaffiya Dan bata shiga shirgin mairo tunda taga uwargidamta ta dauketa kaman ya, uwargidan malam shehu ta iya saka Dan haka ta dinga koyamata sakar kayan sanyi

A zamansu a kano mairo ta haifi yaronta na farko ya rasu a ranar da ta haifeshi yarasu bayan wani Dan lokaci ta Haifi na biyu
Suka masa sunan Usman wato sunan malam shehu, yatashi da ilimin addini da soyayyar iyayensa gashi malam shehu ya daukeshi kaman jikansa yana matukar kaunarsa da ya isa sakawa a makaranta akakai usman makarantar boko
Seda mairo ta kuma haifan yara biyu suna mutuwa sannan ta haifi Yaronta namiji akasamasa Aliyu
Addu'a Imam yayi tayi Allah ya bar masa Aliyu Usman ya samu Dan uwa,
Usman ya tashi da matukar kaunar Dan uwansa kullum yana tare dashi har Goya masa shi mairo takeyi,
Ba 'a Dade ba
Ta kuma haifar mace itama ta rasu daga nan bata sake haihuwa ba,
Haka suka rungumi yaransu suna kula dasu malam imam be sakasu a harkar kasuwanci ba se dai ya tsaya musu akan Neman Ilimin su, na islama Dana zamani,

A kwana a tashi malam shehu Allah yayi masa rasuwa, sun shiga matukar damuwa da tashin hankali haka akayi zaman makoki kowa ya watse.
Rayuwa tacigaba a haka malam imam be taba tunanin sunemi wani daga danginsu ba, yana ta kula da yaransa , yakuma siyan gidajen kusa dasu ya hade a cikin gidansu.

Usaman da Aliyu suka girma da matukar kaunar junansu, gasu masu matukar biyayya duk da kasancewar su maza amma daga kan shara gyaran gado wanke² bawanda basu iyabaan Usman yafi Aliyu hakuri, shi
Aliyu akwai kafiya da taurin kai sannan yana da zafi, halin babansu ya dakko, gashi shine karami amma in ya dau zafi sedai Usman ya kyaleshi amma duk da wannan halin nasa kaf kayan gidan nan shi yake wankewa ya goge sannan yana matukar son yayannasa amma wataran in kaga yasa Usman a gaba yana masa fada seka dauka shine babba
(Ashe JALILA ba a banza ta dakko ba)

shidai malam imam kullum zancensa be wuce
" Ku rike junanku Ku rike zumunci, kunga bayan imu IMU bamu da wasu dangi duk sun watse wasu sun mutu Ku rike junanku Ku nemi ilimi ko bayan ba raina karku yada zumunci"

Kwanci tashi asarar rai Usman yagama makarantar secondary ya shiga Jami'a yake karantar engineering,
Bayan ya kammalla jami'a ne aiki be samuba ya dawo Gida ya zauna yake dan bin babansa kasuwa, ana haka ya hadu da wata yarinya Zainab da farko dai suna mutuncine kawai kafin daga baya abin yakoma soyayya,
Lokacin daa malam Imam yasamu labarin Usman yana zuwa tadi gurin yarinyar ya kirashi yayi masa nasiha yace tun wuri in yasan ba aurenta zeyi ba ya dena zuwa gurinta

Shidama Aliyu be tsaya iya karatu ba yana taba kasuwanci
In yafita abinda yasamo se yabawa Dan uwansa yace yafara Tara kayan aure tunda ya fuskanci yana matukar son zainab,
Duk randa Aliyu beje makaranta ba haka zewuni Neman kudi ba abunda zeci a ciki haka ze dauka ya bashi,
Sannan dayake mutane dayawa sun San Aliyu saboda yana da baki ba kaman Usman ba salihi ne kaman mairo, Aliyu ya dinga shiga yana fita domin yaga danuwansa yasamu aiki amma abu yafaskara kai kace shine yake nemawa kansa aikin
Shekarar da Aliyu yasamu admission, babansu ya dauki kudin
Registration ya bashi amma daya tashi se ya hada kudin da Wanda ya dinga Tarawa ya tafi yaje kasuwa Yakama shago aka zuba takalma ya dankawa Dan uwansa yace gashi nan ya dinga juyawa yasamu yayi aure
Dafarko Usman kin amincewa yayi seda yaga Aliyu yadena kulashi, yadena cin abinci tare dashi yayi fushi sosai sannan ya yadda ya karba

Malam imam yace aikuwa badi se dai kanemi naka kudin kashiga makaranta, we da Aliyu yabata shekara biyu be fara makaranta ba saboda yaga kasuwancin da ya kafawa yayansa ya bunkasa

Duk wannan abun baya hana in Usman yayi masa laifi ya zauna ya kare masa masifa, amma beta ba yimasa gori ba.
Shekara ta zagayo Aliyu sannan ya Shiga Jami'a
Usman ya cigaba da kula da shago yasamu Sana'a yafara core ransa saga batun samun aiki

Ahaka har Allah yasa Usman ya auri Zainab aka ware masa bangarensa a cikin gidan yasata a ciki, tana zaune da mairo lafiya saboda ita Sam bata da hayaniya Dan haka Zainab bama Shiga harkarta take ba balle kyautatawa ko akasin haka ya Shiga tsakaninsu.
Allah ya Albarkaci kasuwancin usman, aciki ya dinga tallafawa karatun Aliyu dakuma iyayensu da girma ya cinmmusu,

A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah, matar Usman ta haihu ta haifi da namiji, aka sakamasa sunan Aliyu suke cemasa Jawwad, Zainab taji haushi ga mahaifinta memakon ayi mata kara a saka sunanshi se a wani saka sunan Aliyu
Aliyu yayi murna da haihuwar JAWWAD dakuma karar da dan uwansa yayi masa kullum yana tare da Jawwad, yaronma yana matukar kaunar Aliyu Jawwad, soyayyar da Aliyu yakema Usman Yakoma kan Jawwad,
Jawwad yana da shekaru biyar cif, Aka tura Aliyu bautar kasa kwara state yaji babu dadi sakamakon rabuwar dazeyi da gida gakuma dansa JAWWAD dayake matukar kauna

Haka Aliyu yayi shirin tafiya yayi sallama da mutan gida iyayensa sun masa nasiha sosai akan ya kula da Kansa da addininsa, Usman beji dadi ba ya Shiga damuwa sosai, saboda shi lokacin da yayi NASA bautar kasar a kano yayi beyi nisa da Gida ba.

Haka Aliyu ya shirya ya tafi kwara, wani babban kamfani aka turashi kamfanin yakasance mallakin masarautar garin Wanda ya kasance na construction ne na gine² dakuma tituna

Aliyu yaga mutane daban² wanda suke da banbancin addini da al'adu da zaman takewa na rayuwa

Aliyu ya hadu da wani bayerabe a kamfanin me suna Abiola Wanda ya kasance kuma hadimi ne a cikin masarautar garin dukda banbancin addininsu amma tasu tazo daya shiyake zagawa da shi gurare a cikin garin

In Baku manta ba kusan halin Aliyu da shige²
Dan haka yace yana so abiyola ya Shiga dashi gidan sarautar yaga yanda take, haka akayi ya dauke shi ya Shiga da shi cikin masarautar ya dinga nuna masa abubuwa, haka ya dinga kallonsu wasu iri saboda yanayin saraautarsu yayi daban da masarautar kano

Wasu abubuwan sun kayatar dashi wasu kuma sun bashi haushi haka abiola ya dinga bashi labarin
masarautar da abubuwan data kunsa ciki kuwa hada labarin shalelen masarautar wadda akan a batamata rai gara abatawa sarkin saboda tsananin kaunar da sarkin yake mata

Sarki yana matukar kaunar yarinya nan, shikam Aliyu duk surutun nan da abiola yake besan me yake cewa ba saboda ya shagala da kallon abubuwan kayatarwa da suke a masarautar,
Wani part suka karaso kai bakace a Nigeria ne ba ya hadu karshen haduwa an kawata shi da abubuwan zamani da kawatuwa
"Nan kuma inane?"
"Ai nan shine bangaren yarinyar danake gaya maka jikar sarki ce, bangaren shalelen gidan ne"

"Ehenn mushiga inga mene a ciki mana"
Zaro ido abiola yayi "sokake in kwana a kurkuku baza ja min wahala ba iyakacin mu nan"

"To meye a ciki gani fa kawai zanyi"
"Dan Allah kabari ka zo mutafi kaga akwai masu tsaronta Dan haka kazo mu tafi"
Da kyar abiola ya shawo kan Aliyu ya yadda suka tafi.
Abiola ne durkushe a gabanta, ta hakimce tana cin kayan marmari
Tayiwa hadimanta umarnin sutafi subata guri
Sannan ta mike zaune sosai
"Abiola"
Takira sunan shi
Ya Dan kalleta ya maida kansa kasa

"Waye wannan Wanda kuka shigo da shi dazu?"
Gabansa ne yayi mummunar faduwa ya tsorata, nan da nan gumi ya rufe shi ya kama in'ina
"Abiola bafa abu me wahala na tambayeka ba kawai na tambayeka waye shine
Ina kallonku dazu ta saman bene kuna jayayya waye shi? Daga ina yake? Mekuma ya zo yi nan"?

Da kyar abiola ya hadiye wani yawu ya daidaita nutsuwarsa Ya dan suka da Kansa yace
" your royal Highness Dan bautar kasane an turoshi kamfani domin yayi aiki sunanshi Aliyu daga kano state yazo nan"
A kidime ta kalleshi kana nufin musulmine
"Eh bahaushe ne kuma musulmi"
Gigicewa ta danyi tare da bashi umarnin ya tafi seta nemeshi
Nan ta Shiga sintiri a gurin
Da karfi tai shouting
"Impossible!!!!!!"
Wanda ya janyo hankalin masu yi mata hidima ,kafin su an kara........

Wata sabuwa



Share please
More comments more typing...............

Love u all Abdul jalal novel fans
🌹🌹🌹








🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

_ABDUL JALAL_
(2020)

_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

PAGE- 12

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa'azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what's app akan wannan lambar

07063065680
What's https: //chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Is a free book

Ina yinku AbdulJalal novel fans irin💯💯💯 da duk sauran masoya wannan novel ina jin dadin comments dinku love u all ❤❤❤

I want comments not stickers or just thanks😢😢😢😢
Your comments give me courage

Takabbalallahu minna wa minkum eid el Mubarak alaina wa alaikum
Allah ya karbi ibadunmu yasamu a Wanda yYafewa a wannan kwanaki goma na dhul hajj

-my first Novel-

Numfasawa yayi ganin yadda yaran gaba daya suke durkushe a gabansa ga maryam da take ta kuka

Ko ba komai Aliyu yaron kirki ne tun tasowarsa ba taba dakko masa magana ba dukda fadansa da shige shigensa baya dakko magana
Kuma ya duba misalin da inna mairo tai masa Suma yadda sukazo basu San kowa ba malam shehu ya daukesu kaman yayansa Dan haka ya numfasa

"To shikenan na amince Allah ya tabbatar mana da Alkhairi yayi muku albarka gaba daya"
Marry ta dago da sauri

"Baba dagaske ka yadda in auri Aliyu"

Ya gyada mata kai
Da gudu marry ta tafi gurin Inna mairo ta rungume ta

"Mama bani da bakin godiya mama kiyimin godiaya gurin baba, kun gama min komai a rayuwa da kuka karbeni nagode sosai.

" ba komai maryam nima nayi diya dama bani da ya mace"
Inna mairo tayi maganar tana sharewa marry hawaye

Aliyu da Dan uwansa haka suka dinga yiwa mahaifinsu godiya tare da adduo'i
Usman yaji dadin yadda baba ya amince ko ba komai shima Dan uwansa ya samu farin ciki

Bayan malam imam ya koma daki ya kira Aliyu yayi masa nasiha ya ja kunnensa game da rike amana da yi masa gargadin zama jakada nagari na addinin musulinci da kuma kabilar hausawa
Haka marry ta karbi musulinci ta koma maryam Amma aliyu yake kiranta da noorat saboda sunan mahaifiyarsa ne
Abubuwa sunzo mata da sauki saboda tasan addinnin musulinci se Dan abinda ba a rasa ba.
Itakuwa Maman Jawwad tunda taga abunda yafaru gashi kuma mutanen gidan sun karbi maryam.ta fara jin haushi, yadda inna mairo take kula da maryam kamar yarta amma ita dasukayi kusan shekara shida da ita bata wani shiga sabgarta,
Dan haka ta shiga yayatawa a anguwa kanin mijinta Aliyu ze auri kirista dukda tasan ta musulinta, hakanan se yan unguwa su shigo dan aga matar da Aliyu ze aura.

Duk surutun da ake a gari Aliyu da yan gidansu suka toshe kunnensu, dama ba a tunkarar Aliyu da maganar Dan ansan masifaffe ne
Sedai ayiwa Usman ko magulmata in sun shigo suyiwa inna mairo
Aka ware musu bangarensu a cikin gidan, dukda kasancewar maryam kabila kuma wadda tayi girma a gidan sarauta amma tana da matukar biyayya da girmama manya ba ruwanta da hayaniya, mamansu

Please Login or Register in order to submit comment