Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yawon iskancinta can ai kin sani, Momee da kyar tace Ina zamana lfy na lalata halina,na dauki mutanen banza na cusasu a jikina,gashi yanzu ko arzikin dubiya ban samu ba,Maman su Hafcy ma Wai itace ta kasa ko leko Ni sabo da yanzu bamu da kudi,Niima tace sai yanzu nake Nadama Momee Dana ki aurar Ahleef,ga kyau,ga Kudi,ga kyan Hali,karshe naje naso Mubaraq Wanda shine ya lalata min rayuwata Niima ta fashe da kuka tare da durkushewa a kasa tana na cuci kaina,kema Momee duk ke kika jawo mana.

Momee dake saman Bed ta zuro hannu ta zubawa Niima rankwashi tare da cewa ke dai kika cuci kanki marar mutunci ,Latifa ce ta shugo ta dawo daga yawonta ta iske su Niima da Momee kowannensu Yana Hawaye cike da Nadama,Itama tsugunawa tayi a wajen ta fara kalar nata kukan tace Momee kece du kika jawo Mana,Momee tace Dan ubanki wacce tarbiya ce ban baku ba? Ai sai daga baya shedan ya rudeni na canja hali akan son duniya,yanzu sai mu fara istigifari ko Allah ya taimakemu,su Momee yau sunyi Nadama,sunji karatun Duniya Dole uwar naki,Nan take suka fara istigifari suna tuba,Baji ba gani,Niima tace sai mu nemi Ahleef ya yafe Mana,Latifa tace shegiya bariki gashi da kaina naji wahala na tuba,Allah dai ya karbi tubanmu,Shukura ma munyi Mata kazafi,Momee kinyi silar lalacewar dubban alumma shi yasa Allah ya Rama musu akan yaranki,nayi shaye shaye da duniyanci Ina karamata,ga Niima itama an Rama akanta tayi ciki,da Baki sa an lalata yaran wasu ba wlh da muma Allah bazai Bari mu lalace ba,ga kudin gado duk ya Kare yanzu ko kin warke bamu San ya zamu Kare da talauci ba, naje Neman Ahleef wajen Farhan yace ai Ahleef yayi kudin da yafi na da,Kuma ya dauki Matarsa sun koma London,Haka Su Umma Saudatu basa kasar,nayi nayi ya bani number din Ahleef wlh yaki bani..yanzu Kuma talauci ne kawai zamu karba a jikinmu matukar Ahleef Bai zo ba, Niima da sauri tace wlh rannan a tv Naga Ana nuna shi tare da Shukura Kinga yanda suka dawo kuwa kamar turawa nayiwa kaina nayi asara,duk nice na dinga zuga Umma har na cusa Mata kiyayyar Ahleef,gashi mun kwace dukiyar da take halak dinsa har mukace ya daina zuwa gidanmu,gashi Allah yayoshi ba talaka ba ya sake yin new Money.

Momee tace to a Ina ya samu kudin da zai juya? Latifa tace hanyar Allah ko Kuma Farhan ne,Niima tace Allah ya nuna Mana Ahleef na bashi hakuri sannan Kuma na Masa tayin kaina ko zai aureni,wlh sai yanzu naji sonsa Yana ratsani,Dan Allah Momee idan ya dawo ki nemi Alfarma ko zai aureni Bayan na haihu ya Kara ta biyu Dani,kin San Yana jin kunyarki Kuma Yana sonki,baya manta alkhairi idan kin Sa Baki da wuri zai aureni.
Momee tace Allah yasa zanfi kowa farin ciki.
Latifa tace Ni Kuma Farhan nake so Momee,Momee tayi Dan Murmushi tace Allah nuna Mana zan nema muku Alfarma.

Latifa da Niima su sukaci gaba da kula da Momee da Dan ragowar kudin da ya rage musu,har aka samu akayiwa Momee aiki aka cire Mata Koda daya data lalace sannan ta samu sauki sosai sun Dade a asibiti har ta warke sannan aka sallamesu ammafa kudinsu sun Kare karaf sabo da Mubaraq ya Gama kwashe komai ya bar kasar abinsa ba a San inda yake ba.

Mama dasu Hafcy ma kansu Mubaraq ya gujesu Basu San inda yake ba,duk murnar da suke zasu Shana da kudi a banza domin ya gujesu,Alhj Adamu Bai San komai ba sai aikin neman Mubaraq yake, Mama Sai kuka kullum danta ya bace, Su Hafcy kuwa sai tsinewa Mubaraq sukeyi yayi kudi ya gujesu sun taimaka Masa Amma karshe abinda ya musu kenan, Momee bayan ta warke report ta kaiwa Yan sanda Mubaraq ya gudu da kudinsu,su kansu Yan sanda ganin ba wata sheda kwakwara sannan Momee Basu da kudi sai suka share Zancen kawai suka sallamesu bayan Dan karamin bincike da sukayi.

A kwana a tashi yau abincin da su Momee zasu ci gagararsu yakeyi sun tsiyace sai katon gida ba ko sisi a ciki, Momee tace Dole mu saida wannan gida mu koma cikin talakawa mu siyi karami ko zamu samu na cin abincin,Momee suka daga tallan gida ba Wanda ya Taya,sai Momee ce da kanta taje wajen Farhan kan ya taimakesu ya samo musu Mai siyan gidan,Nan take Farhan ya bugawa Hamshakin me kudi waya ya siyi gidan su Momee suka siyi karami can unguwar talakawa suka zauna,sauran kudin kuma suka siyi kayan abinci etc.

London

Ahleef suna Bedroom dinsu ko hutawa basuyi ba ya cirewa Shukura kayanta tare da nasa suka Shiga wanka, damunta yayi da tabe tabe tare da tsotsar inda yaga dama, ganin ya fara susucewa cike da Shagwaba tace pls ka Bari sai dare Mana kamar zata narke Haka tayi maganar, wani nataccen kallon so yake aika Mata, a hankali ta rungumeshi tana me bashi hakuri sai dare can,kafada ya makale shi bai yarda ba sam,Dole ta hakura taba da amanna suka farantawa juna rai sannan sukayi wanka suka fito da kanta ta shirya sannan ta shirya Ahleef dinta tana Gama taje Masa gashi tace to oya karbo Mana abinci yunwa nake ji, fita yayi Yana tsokanarta Wai ciki gareta tunda yanzu tafi cin abinci.

15mns ya dawo dauke da ledoji Niki Niki,da sauri Shukura tace sannu da zuwa ta karbi kayan tana wani farin ciki kamar yau ta sanshi, abinci ya siyo musu da Kuma kayan sawa hadaddun gaske,Shukura sai Murna takeyi tace Allah ya Kara budi, Ameen yace Yana kashe Mata Ido daya, Hero gaskiya Ni ka daina min irin kallon Nan nafa San me kake nufi, ta furta cikin tsantsar shagwaba, da sangarta tana cuno Masa Dan bakinta,wani birgeshi takeyi idan tana Shagwabarta har cikin jininsa yake Jin wani yarrr..

Murmushi ya saki me kayatarwa kana ya jawota jikinsa ta Fado saman cinyarsa zuwa kirjinsa Fuskarta ta dago tana kallonsa sannan tana Wasa da yatsunsa, Harshensa taji cikin bakinta a nutse Yana tsotsa kamar alawa baya gajiya da Shukuransa,ga Tsafta tana kula da jikinta sosai ko ina kamshi zaka ji,itama a ranta tana mamakin Tsafta da gayu irin na Ahleef kullum neat ko wacce gaba ta jikinsa kamshi take lungu da sako, ci gaba yayi da Shafarta ba tare da Bata lokaci ba Shukura ta rude jikinta Yana rawa daukan ta yayi zuwa saman bed Wasa ya canja salo sai da suka Raya sunna abinsu,Bayan sun samu nutsuwar,Ahleef ya kankameta a jikinsa kamar za a kwace Masa ita ya furta kullum Honey sweet kike karawa, you are too sweet har ban San me zan ce ba, Fuskarta ta fara goga Masa a tasa cikin kunnensa tace Kaine kake bani abinci da yawa Ina cinyewa yanzu zaka kaga na haihu ai ance idan mutum Yana ci Yana koshi ba yunwa a gidan mijinta to yanzu zan ta sullubo yara.

Dariya ta kama Ahleef sosai Yana ta yi Yana Kara kankame Shukuransa yace ai ban sani ba dama haka abin yake? Da sauri Shukura ta ae kwarai to Alhaji gidanka ba yunwa ni Naga na Dade ma kamata yayi ace na haihu tuni,Ahleef ya Kara kyalkyalewa da dariya, fushi tayi ta turo Baki Wai sai dariya kake min na daina kulaka ma sakar min jiki tunda Haka kake,sorry Bae na daina kin kusa Haihuwa saura kadan ai mace kike so ko Namiji? tab me zanyi da Namiji nafi son mace Yar yarinya ta na dinga Mata lalle da kitso,idan ta girma na dinga aikenta,tana min girki da aikin gida, na daka Mata tsawa nace je ki gyara room din Dad Hero Dina,Ahleef Yana dariya kasa kasa yace to Yar taki Zaki cewa Hero dinkin a gabanta ba kunya,Kai nifa ba ruwa na da wata kunya Baturiya ce ni,gidan turawa ne mu ba ruwanmu ko? Ahleef yace gaskiya gidan Yan gayu ma kuwa,Shukura tace da su Momee Basu raba mu ba ai da tuni na haihu,Amma na koma kauye yunwa zata karasani Taya zan haihu da wuri kuwa, Me gari da Matarsa sun Gama azabtar Dani, Wai Ni yake so in baka lbr ya dinga kallona idonsa kamar na aljanu, Ahleef Nan take ya Bata rai, kishinsa ya motsa yace kyale maganar karki jawo nasa a kamo min Me gari na kaishi prison.

Murmushi tayi tare da furta calm down Hero,abinci ya jawo suka ci tare abinsu Yana Bata a Baki da kansa tana ta bashi dariya da hirar kuruciyar ta, Bayan sun Gama, shiri sukayi sun dau wanka kamar baza a mutu ba suka fita yawon zaga gari abinsu gwanin Sha'awa da birgewa.








Ayi min hakuri Fans wannan Novel din bana bada page da wuri wasu Abubuwa ne suka rikeni in busy ne sosai,Dan Allah kuyi min hakuri da afwa da kyar nake samun time na typing.







AsmaBaffa
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO







71-75






Official







By
AsmaBaffa











Ahleef Yan London sun kwashe 2wks a garin suna zuba amarci kafin suka tafi Russia sun kwashe 1wk sannan suka wuce Saudi nan suka Iske Baba da Umma Sunyi Ibada sosai,sai kyau da haske da suka Kara tare da Yar kiba kowa ya gansu yasan suna Jin dadi,Shukura tana ta siyayya Ahleef Yana kashe Mata kudi sai abinda take so, Bayan sun Gama aikin hajji Su Umma suka dage zuwa Nigeria,Ahleef kuwa Shukura ya dauka suka wuce Dubai abinsu, Baba da Umma suna hutawa suka tafi Niger a jirgi wurin dangin Baba sada zumunci,can ma Sunyi Mamakin ganin Baba,domin tunaninsu baya Raye sai gashi ya kawo Musu ziyara tare da kyautuka na alheri, sunji dadi sannan Ya Basu labari dansa Ahleef, satinsu biyu sannan suka dawo Abuja cike da murnar ganin Yan Uwa.

Bayan 3weaks Su Shukura jirginsu ya sauka a Nigeria,Murna take faman yi zata ga su Umma, escort din Ahleef ne suka dauko su daga Airport zuwa gida, Umma da Baba ma murna suke sosai da dawowar yaran nasu,Shukura jikin Umma ta lafe sun Dade suna Hira har Ahleef tare da cin abincin Umma me Dan Karan dadi sannan suka wuce hadadden part dinsu cike da kaunar juna.

Niima ciki ya Kara girma sai fama take da laulayi, Momee kullum sai ta zubar da hawaye musamman yanzu da suke cikin talauci kudi ya Kare karaf,abincin da suka siya ma sun cinye Babu sai kadan,kudin cefane Babu shi kullum shinkafa fara da Mai suke ci abinda ya rage musu kenan, tuni suka daina girki da Gas sai itace ko coal,kamar kullum yau sun tashi sisi babu ko na Koko Basu samu ba sai taliya suka dafa suka ci da Mai,duk sun rame Sunyi Baki lalacewar tayi yawa ma,Babu Wanda yake taimaka musu,tunaninsu don sun tuba ga Allah shike Nan baza a jarab cesu ba sai gashi sunga ba Haka bane, wahalar tayi musu yawa yau Momee da kanta ta shirya tace Niima ku kula da gidan Bari naje wajen Farhan ko zan samu tallafi,Latifa tace Allah yasa a Dace Amma da na biki ko zanga Farhan naji sanyi, Momee tace to zo mu tafi,a gurguje ta gyara Fuskarta tare da yafa mayafi tabi Momee suka Shiga Napep suka nufi gidan Su Farhan.

Suna Shiga lokacin Farhan ya fito yaci wanka zai fita,Yayi mamakin ganin Momee da kanta,ya kallesu duk yaga sun lalace sun fita daga hayyacinsu da gani suna cikin wahala.
da sauri ya Isa wajen Momee tare da gaishe ta kamar yanda ya Saba, ta amsa fuska cike da annuri sannan ta fara karanto Masa matsalarsu ta Kara bashi hakuri sannan tace Dan Allah ka hadani da Ahleef ko ba komai zamu roki gafararsa tare da Matarsa.

Farhan ya tabbatar su Momee Sunyi Nadama,Latifa tana gefe ta wani rakube a bango kamar munafuka sai kallon Farhan take ba ko kyafta ido, Farhan Yana kallonta ya lura da abinda take suna hada Ido ya zabga Mata Harara tare da Jan tsuka kadan ya turo Dan lips dinsa gaba kamar yanda Mata sukeyi,Latifa tana gani sai ko ta bangale da dariya tana yaye Baki, fuska ya Kara tamkewa.

Farhan Yana kokarin bawa Momee Number din Ahleef sai ga Ahleef tare da escort dinsa sun shigo da motoci gidan,Momee Baki ta bude ganin motocin da Bata taba gani ba masu shegen kyau da tsada,Latifa kuwa ta ma manta a Ina take kamar Yar kauye Haka tabi motocin da kallo.

Da sauri suka budewa Ahleef mota ya fito cikin Shiga ta alfarma,tuni kamshi ya cika gidan,Yana fitowa ya Mika hannu tare da fito da Shukuransa cikin rantsatsiyar Shiga kamar zasu je gidan shugaban kasa,sun wani Kara ja da kyau,Momee da kyar ta ganesu,Haka Latifa ma Baki bude take kallonsu,Ahleef kuwa Bai kula dasu ba tunaninsa Yan maula ne.

Momee da sauri tace Dana Ahleef, Latifa tace ya Ahleef da karfi, Jin Muryar da ya sani da sauri ya juyo kallo daya ya ganesu, kafin yayi wani taku Momee tazo ta durkusa tana bashi hakuri harda kuka, Latifa ma Haka, Nan Momee ta fara bashi labarin duk halin da suke ciki da abinda Mubaraq ya musu etc.
Ahleef yace ba komai Momee Ni baku min komai ba Allah yafe Mana Baki daya,Shukura tana gefen Ahleef ta kankameshi Haka ta gaida Momee a ladabce, Momee ta kalleta da Faraa sannan tace ki yafe Mana Shukura mun zalunce ku,Shukura ta kalli Ahleef sannan tace Ni dama na yafe muku tuni ban rikeku a Raina ba,Ahleef yace kije Gida Momee zanzo anjima,Latifa tayi sauri ta bashi address din gidan da suke sannan suka tafi gida gwanin tausayi,har Sunyi Nisa Shukura tace kasa a kaisu gida a motarka,Nan ya bada Umarni driver dinsa daya yaja mota ya dauki su Momee ya maidasu gida,sai murna suke tare da bawa Niima labari itama sai dadi take ji zai aureta kwana Nan.

Shukura wurin Maman Farhan ta wuce,Ahleef Kuma ya tsaya tare da abokinsa suna tattauna magana kan su Momee, Farhan ya bashi labarin halin da suke ciki, Kuma gidan Dana maka waya ka siya shine nasu Momee, Ahleef ya tausaya musu kuma yasha mamakin karewar dukiya me tarin yawa Haka.haka Hukuncin Allah yake ko nawa ka Tara a duniya sai Allah yaso zasu zauna,komai kudin mutum idan Allah yaso ka talauce Dole su Kare Babu abinda ya gagari Allah har kaji mutane suna ai wane shi da talauci har abada,sai idan Allah baiga dama ba.

Wurin magrib Shukura tana wajen Maman Farhan tare sukayi girki suna hira,Mama tana Kara koya Mata dabarun rike me gida da yanda zata gyara kanta sosai,wasu Tsumin ta bawa Shukura iri iri da yanda zata dinga amfani dasu,har sukayi Sallar Isha Ahleef Bai dawo ba sun fita tare da Farhan.
Faskekiyar wayarta Shukura ta dauka tare da Kiran Ahleef, bugu daya ya dauka can kitchen ta shige sabo da tana kunyar Maman Farhan, kashe murya tayi tare da narkewa a hankali tana Shagwaba tace My Hero na gaji kazo mu tafi gida pls, wani yarrr yaji jikinsa ya amsa sabo da yanda tayi maganar,cike da so yace sorry Honey I wll be on my way soon, minti nawa zan baka? 10mnt Zaki ganni ok? Kai ta daga kamar Yana ganinta sannan tace to Allah kawo min Kai lfy sannan ta kashe wayar,har tazo bakin kofa zata bar kitchen din,Ahleef ya kirata back,ta daga taji me zai ce, tana dagawa yace na manta ban fada Miki ba? Tace mene fa? Albishirinki? Tace goro Fari Kar,tana jira taji sai yace I LOVE U SO MUCH, wani sanyi da sonsa ya Kara ratsata tayi Murmushi cike da farin ciki tace Love u much more, u are my World and u make me complete, sannan ya kashe wayar,sai ta sake kiransa again yayi picking tace missed u missed ur everything,Ur hand fit in mine just wanna sleep on ur chest sweety, Honey Zaki sa na kasa driving kina kashe min jiki, dariya sukayi gaba daya,Farhan Yana gefe Yana jinsa lokacin Kuma Niima da Dan cikinta tirtsitsi tana motar zasu kaita gidansu, su Momee tuni Ahleef ya musu kyautar gidansu back dama shi ya siye gidan.

Niima kamar tayi kuka taga yanda Ahleef suke ta diga love da Shukura baya kallon ko wacce mace sai Shukura, a ranta taji tsanar Shukura marar adadi ta kamata,Latifa da Umma su tuni Driver ya maidasu gidansu tare da kayansu.

Bayan sun ajiye Niima a kofar gidan suka juya sai gidan su Farhan,Maman Farhan tana mamakin Shukura yanda ta kasa zaune ta kasa tsaye ita mijinta ta Matsu ta gani kusa da ita, Dan yanzu Shukura tafi sabawa da Ahleef ko yini cikakke Bata iyawa ba tare da ta ganshi ba.

Tana Jin karar motar ta yafa gyalenta, sai gasu sun shigo,Maman Farhan tace Kun dawo kenan, wannan duk ta kasa sakewa baka Nan,Murmushi Ahleef yayi Yana kallon Shukura ta kasan Ido, a fili yace Haka takeyi ai da a Office nake ma da tuni taje, Farhan yace ki daina yarda Mama munafuki ne shima shine Dan anace Baya iya yini sai yasa an daukota, dariya Mama tayi tace to Dan sa Ido,Shukura tayi luf Wai kunya takeji,kallonta Ahleef yayi tare da cewa tashi mu wuce Madam,ta kwashi kayanta da Mama ta Bata sukayi musu sallama sannan suka fita,Shukura tace Ina escorts? Na sallamesu Ni zanyi Driving idan Kuma kina bukatarsu ranki ya Dade sai a kirasu sai abinda kike so, hararar Wasa ta watsa Masa suna nishadi suka wuce gida.

Suna Isa gida Umma tace Kun Dade yau,Ahleef da Shukura suka nemi wuri suka zauna a Palon Umma, Baba ma Yana nan, Ahleef ya kwashe komai da ya sani game dasu Momee ya sanar dasu sannan yace Umma yanzu Niima tana Nan da cikinta, gidan ma Allah yasa Ni na siya yanzu na bar musu shi kyauta,sannan kudin da Abba ya bani Wanda suke Usa an hanasu to nayi waya dasu nace a Basu na bar musu kyauta tunda Allah yasa sun iya business tun farko suja jari su juya kudin suna Samun na cin abinci,Sannan Niima Na Sa za a Bata aikin Gomnati su dinga yi tunda Ina da hanya Kinga ya Isa su rike kansu, Sai Latifa a nema Mata University taci gaba.

Albarka su Baba da Umma suka dinga sawa Ahleef yayi kokari da wani ne manta alkhairi zaiyi yaki tallafa musu, Ba komai Umma ai ko ba komai Momee uwata ce,ta rikeni Amana da Abba ko sabo da wannan ai bazan watsar dasu ba,har abada Ina ganin mutuncinta,dama Niima da Latifa sune suka Bata komai to Suma ga inda ta Kare musu. Allah ya kyauta yanzu idan Niima ta haihu sai Kuma tayi aure idan taga zatayi cewar Umma, Ahleef yace ai Momee tace aurarsu zatayi Baki daya Bayan ta haihu tayi istibrai, Farhan ma ya samu matar da zai aura Fatima kawar Shukura ce schl dinsu daya,Amma Wai wajen babansu yaje Kai Masa sako anan ya ganta,manya har sun Shiga zancen,Shukura ta kwalla ihun murna tace Fatima tawa dai Dana sani? Ahleef yace ae itace,yau Munje wajenta kawai naga Ashe itace ma, Umma tace Alhmdllh, Baba ma Haka yace Kinga kawa da kawa ga aboki da aboki,dariya sukayi Baki daya,Shukura sai murna take.

Umma tace Amma zaka dinga zuwa wajen Momee din taka kana gaisheta kamar da,Ae Mana, tace zata zo Wai har gida ta baku hakuri ma, sannan Niima zata zo Wai tayi sati daya anan gidan sabo da karfafa Zumunci,Umma tace Wlh mu ba komai mun yafe tuni ai.

Nan take Shukura ta hade fuska tunowa da tayi ai Tsohuwar budurwar Ahleef ce zai iya komawa yaso Abarsa,Kuma ance indai son farko ne ba a mantawa ko mutum ya tsufa soyayya zata iya tashi.

Kishi ya kama Shukura ta kasa Control a fusace ta mike ta nufi part dinsu,mamaki ya kama Umma da Ahleef,Baba Murmushin manya yayi yaje gano tuni,yace jeka Ahleef matar taka fa tayi fushi,Ahleef yace to me akayi Mata,Umma tace jeka wlh ka lallasar min yarinya ta.

Hankalin Ahleef ya tashi Shukura tayi fushi Bai San me akayi Mata ba,da sauri yabi bayanta,tun kafin ta Isa part dinsu ta fara rusa kuka, bedroom dinta ta shige tare da Sa key ta zauna dabar a kasa irin zaman Yan bori tana ta kukanta,Ahleef ya karaso da sauri ya Murda Handle Amma kofa Gam Gam,yace ki bude me ya faru,ko Baki da lfy Dan Allah ki bude Honey duk ya tashi hankalinsa.
Taki yin magana Kuma Bata bude ba kukanta take rerawa, magiya da rokonta ya Shiga yi idan baza ki bude ba to ki fada min me yake faruwa? tana shesheka tace Bayan kishiya kace zaka yi min, Ahleef Baki bude yace Ni din? Yaushe nace Haka? Yana mamaki tace ae ai Naga take takenka kuma wlh Allah indai kace Haka Ni Kuma sai ka sake Ni,Haka kawai za a kawo min jaraba gida a Jaja min cuta,Dariya ma abin ya bawa Ahleef Bai gane kan Zancen ba, yace Wai meke damun kanki ne? Ae kace Haka Mana ka zageni kaji dadi ai Dole kace min Haka tunda kaga wacce ta fini Kuma wlh baza ka dauko cuta a jikinta ka shafa min ba.

Salati Ahleef yaja shi bai San kan zancenta ba,tace idan shegiyar Nan tazo part dina wlh Allah da Kai da ita sai na yanka ku, Ahleef sai yanzu ya gane Niima take nufi ya Shiga sheka dariya yace to bude dai ki fito muyi zancen, da kyar ya roketa ta bude tare da fitowa, yasha mamaki ganin Fuskarta kamar an watsa mata yaji tayi jajir ga Hawaye ta ko Ina duk ac din dake gidan ta hada zufa.

Hannunta ya ruko ke yanzu Akan wata Niima kika Bata fuskarki Haka? Hawaye ya Kara shararo Mata tace gashi Nan yanda kake fadar sunan ma da dadi kake tsarawa kace NIIMA Mana Amma sai kayi iyayi kasa kalkala,Ahleef ya danne dariyarsa ya kumbura murya da Bakinsa yace to NI'IMA tace ai dai baka birgeni ba Tunda sai Dana fada kayi,yace muje nayi Miki wanka jiba yanda kike zufa Akan kishin banza,ai kinfi karfin kiyi kishi da Niima kucaka,Dariya Shukura tayi tana share Hawaye Wai taji dadi yace Mata kucaka.

Ya zura Mata Ido ya hango yanda take murna,Murmushi yayi tare da daura ta a cinyarsa yace to me zanci da wata Niima me katon goshi Bayan ga Shukura Balarabiya,Shukura ta Kara wani shigewa jikinsa tana Jin dadi Yana ta kushe Niima itace a sama, yace Shugabar Matana na aljanna Hurul ein,a aljanna ma sai abinda kika ce, Shukura tayi dariya tace Idan na Shiga Aljanna shuuma zan zama,Ahleef ya fara dariya,tace kasurgumar Yar giya zan Zama a aljanna kullum Nasha nayi tatul, Dariya Shidai Ahleef kawai yake na labarin Shukura sai da ya gaji sannan ya dauketa sukayi wanka suka kwanta suna hirarsu ta masoya bacci ya kwashesu me dadi.

Bayan sati biyu su Momee komai ya Dan fara gyaruwa suna Dan Jin dadi komai ya fara zamar musu Normal Ahleef ya gama musu komai Kuma Yana zuwa akan lokaci, yaune Kuma Niima ta hada kayanta ta nufi unguwar su Ahleef, da kyar masu gadi suka barta ta Shiga sai da ta Kira Ahleef a waya sannan ta samu aka bude Mata kofa, wani maaikaci ne ya rakata part din
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On JIN DADI SABO
avatar
mahamane-noura

11 months ago

Reply

Asalama alaikum, dan Allah yane ake sauke littafin akan waya

Please Login or Register in order to submit comment