Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya


Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[6/9, 11:00 AM] Teemarh: _...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers_
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️

*BY FATIMA* _{Real~Teemarh}_

_1~2_
*Thanks to Almighty Allah for giving me the ability and chance to start the book SHARIK HAYATI {My life partner}, Special greetings to the whole members of ZAMANI WRITERS ASS. Ina maku fatan alkhairi da kuma gamawa lafiya, My Ilham, Fatima (Baby), My Zee Auwab and Luvly KK can't luv u less sisters. Members of my groups are not excluded too, ina sanku sosai wallah 🥰 Finally my fans, Ina maku gaisuwa irinta addini aduk inda kuke, billah nima ina yinku over and over ❣️*

A firgice ta mike tana kallan agogan dake manne a bangon dakin, ta zare manyan
idanuwanta waje ta ce"What!!! Past 8". Quickly ta janye duvet din dake jikinta ta shige bathroom hankalinta a tashe, bayan 6 minutes ta fito daure da towel ta nufi gaban mirror, comb ta dauka ta fara combing gashinta, nan da nan ta gama ta dauka ribbon tayi packing smooth hair dinta waje daya, daga nan ta fara robbing body lotion shap-shap. Cikin few minutes ta gama ta nufi press dinta ta dauko doguwar riga baki ta saka kafin ta dauko veil dinsa ta yafa ta jawo side bag dinta dake jikin bag hanger sannan ta fice a dakin, daidai shoe rack ta tsaya ta dauka flat shoe sannan ta kama hanyar stairs cikin sauri ta fara saukowa. Ba kowa a falon sai TV dake kunne sai karan standing fan, hakan yasa ta wuce kitchen da gudu tana fadin "Ummi! Ummi!" Kafin ta karasa shiga kitchen din Ummi ta fito rike da warmer, kana kallanta kaga mahaifiyar yarinyar saboda tsantsar kama da suke. Ummi ta mata wani irin kallo ta ce"Are u ok? What's the essence of running" ta ce" Ummi ina da appointment a clinic yau fa" ta karashe maganar in a hurry, Ummi ta dalla mata harara ta ce"Wa kika gayawa to?", a hankali ta dan gyara veil dinta ta ce"I'm sorry Ummi, jiya da doctor hisham ya kirani kin riga kin rife kofa, and i didn't woke up early today". Ummi ta ajiye warmer din hannunta akan dinning ta ce"Kije Mustapha ya kaiki, i think i don't have to go,". Silently ta ce "To saina dawo" daga haka ta fice a kitchen din ta nufi kofar fita.
Babban gidane na gani na fada, yana dauke da shuke shuken flowers all over, part guda biyu ne daya na kallan daya sai kuma BQ daga gefe sannan parking lot a tsakiyan apartments din wanda ke dauke da motoci 6. Da sauri ta karasa jikin motar tana kallan Mustapha ta ce"Na makara fa Musty, kuma cewa yayi he's leaving the country today" ta karashe maganar tana shiga back seat, Mustapha ya rife kofar ya zagayo cikin hanzari ya shiga driver seat ya kunna motar yana fadin "Yanzu zamu isa Hajiya Karama, aini inasan shiga asibitin nan kodan ina ganin turawa, ance nasu nema asibitin ko?". Murmushi tayi me kyau ta ce"Sure, amma ai mutanenmu na nan suna aiki a caan" Mustapha ya washe baki ya ce"wa yake ta bakar fata Hajiya karama, ai turawan sunfi dadin gani, kaii Allah yayi halitta, farare kal kal dasu kamar ka bigesu jini ya fito, nifa ban ta6a ganin turawa ido da ido ba a garin kano sai a asibitin nan" ta ce"To menene abin san gani a jikin bature Mustapha, sai wani zuzutawa kake" cikin sauri ya ce"Ai wallahi Hajiya karama bature abin a ganshi ne, aini dana zauna kallan bakar mace gara a kaini gaban tsohuwar baturiya naita kallanta ina maimaitawa", dariya sosai tayi kafin ta ce"Wato dai Mustapha bakasan ganinmu kenan, kace baturiya zaka nemo" zaro ido yayi ya ce"Na isa ince banasan ganinki, ai wallahi dana fara ganinki na zata bakyajin hausa sai larabci" dariya ta fashe dashi tana girgiza kai, duk drivers din da suke yi a gidansu tafi san Mustapha saboda idan yana mata hira yana sata nishadi, ko bata da lafiya inya shigo gaisheta sai yasan yadda yayi ya sata murmushi. Yana parking ta fito a motar tana kallansa ta ce"To zan shiga Mustapha, ga turawa nan aita kallansu, idan na fito ka fadamin wacce ka za6a" bata jira amsarsa ba ta wuce ciki saboda sauri da take.Kamar me counting steps ta shiga clinic din very gentle, office din dake gefenta by d left ta nufa ta fara knocking a hankali, ta ciki aka bata izinin shiga sannan ta bude kofar a hankali ta shiga, Doctor hisham kawai take kalla tana murmushi ta karasa ciki ta ce"Morning Dr" ya mayar mata da murmushi ya ce"Morning Fatima, how are u?" A hankali ta ce "I'm fine Dr, i though u are leaving now". Dr hisham ya kalli wristwatch din hannunsa ya ce"I have 1 hour left, have a seat" ya karashe magana yana nuna mata kan sofa, juyawa tayi a hankali zata zauna ta ce"But Dr pls i don't want injection this time around i need just dru... " shiru tayi tana kallan Mutumin dake zaune kan sofa yana danna waya, saam bata kula da mutum a wajen ba, and his face look very familia, ta dan hade gira in a very low voice ta ce"Morning" ba tare daya dago ba ya ce"Same" daga haka yaci gaba da danna wayarsa, ta juyo tana kallan Dr dake rubutu ta ce"Can i have them now?" Ya ce"Yes wait a minutes, how is Abba?" Ta zauna kan hannun kujeran ta ce"He's fine". Very gentle mutumin gefenta ya tashi ya ya karasa wajen Dr Hisham ya mika masa hannu ya ce"Dr I'm going, thanks for all" Dr yayi murmushi ya ce"Alright friend Allah ya sauwake" zame hannunsa yayi cikin na Dr ya mayar cikin pocket dinsa ya ce"Ameen" daga haka ya nufi kofar fita a office din. Doctor Hisham ya mika mata takardar daya rubuta mata magunguna ya ce"Gashi, idan kika siya a pharmacy zasu miki explaining just like they used to" ta kar6a takardan ta ce"Thank u, and when are u coming back from cairo?" Ya ce"I'm spending just 5 days, idan akwai matsala u can meet Dr Aryan zai maki komai" ta ce "To nagode", daga haka ta fita a office din ta wuce pharmacy.
Still mutumin nan yana tsaye a wajen, ta samu gefensa ta tsaya tana kallan fuskarsa daya hadeta ko walwala babu unlike ranar daya taimaketa. Kallan magungunan da aka masa packaging kawai take, sak irin nata wanda take sha, kenan shima irin ciwanta gareshi? Abinda ta fada cikin ranta kenan. Mika nata takardar tayi bayan an sallameshi ya bar wajen, cikin few minutes itama aka mata packaging nata ta biya kudin sannan ta bar pharmacy din cikin gaggawa saboda bataso mutumin ya mata nisa. Tana shan kwana ta ganshi a zaune ya limshe idanuwansa kamar me bacci, ta karasa a hankali ta tsaya a kansa ta ce"Assalamu alaikum" ya bude manyan idanuwansa cikin cool and sweet voice ya ce"Wa'alaikum salaam" ta danyi murmushi dan batai tinanin zai amsa ta ba, wasa ta farayi da ring din hannunta ta sunkuyar da kanta kasa sannan ta ce"Thank u once again for helping me the other time, lokacin dana farka Salma tace min ka tafi, sai yau Allah ya hadamu, thank u so much" kallanta kawai yake yana sauraronta since she started talking, ya sauke kansa kasa ya ce"Ba komai, ki dinga kula" ta ce "Insha Allah" daga haka ta juya zata tafi ya ce"Your name" ba tare data juyo ba ta ce "Fatima Rafi'ah" ya mike tsaye yana kallanta ya ce"I'm Yusuf Muhammad" sai a lokacin ta juyo ta ce"Nice to meet u, thanks much" daga haka taci gaba da tafiya tanajin ta sauke wani babban nauyi na masa godiya da tayi.Ta bayanta taji ya ce "Rafi'ah" ta tsaya caak sai kuma ta juyo tana kallansa, da alama binta yake a baya, ya karaso wajenta yana folding hannayensa ya ce"Can u pls pretend as my girlfriend?"
Zaro ido tayi tana kallansa ta ce"What!" Ya gyada mata kai looking into her eyes ya ce"Yes, pls do help" cikin sarkakkiyar murya ta bude hannayenta tana kallansa ta ce"But why?" Hannayensa duka ya saka a pocket dinsa ya ce"I will explain ltr, just go back and have a seat there". Kallansa kawai Rafi'ah take with some expression, bayan 2 minutes ta dauke idanta a kansa, dai dai nan phone dinsa ta fara ringing, ya zaro wayar a aljihu ya dauka yana kallan Rafi'ah da kanta ke kasa ya ce"Hello Aunt... Ehh na daukota", from the other side Aunt dinsa ta ce"Zata bimu gida kenan kaga sai mu gaisa da kyau" kansa ya dan shafa ya ce"No no, i told u she can't follow us, just wanted her to great you and then she will live" ajiyar zuciya ta sauke kafin ta ce"Ohk to ku karaso mu gaisa" ya ce"Alright Aunt".
Kallan Rafi'ah yayi ya sauke phone dinsa a kunnensa ya ce"Let's go" ta dago tana kallansa sai kuma ta girgiza kai ta ce"Noo, i can't pretend, how will i even start? Driver na jirana kuma" ya ce "Just few minu..." Kafin ya karasa magana ta juya ta fara tafiya, binta ya dingayi da kallo yana tinanin what's the next thing to do, gashi ya fadawa Aunt dinsa sun iso asibitin. ta danyi tafiya me nisa kafin ta juyo ta kalleshi taga ya koma yana tafiya a hankali, duk sai taji bata kyauta ba, gashi ranar da ciwanta ya tashi he's the first daya taimaka mata a wajen ba tare daya santa ba, why won't her help him too? A hankali kuma ta ce"But i can't pretend, ta ina ma zan fara?" shiru tayi tana tinani, bayan few minutes ta nufeshi da niyyar ta yarda zata taimake sa shima, a inda ta sameshi dazu a nan wajen ta sameshi yana zaune just like before ya kama kansa, cikin sanyin murya ta ce"Na amince" ya dago yana kallanta ya ce"Are u sure?" Ta gyada masa kai, tashi yayi ya nufi wajen parking ta bishi a baya, sai buya take kar Mustapha dake caan gefe ya hangota, front seat Yusuf ya bude mata ya ce"Bismillah" ta shiga ta zauna sannan ya rife ya zagaya mazaunin driver ya sawa motar key suka bar harabar wajen.
Wata hanya yabi a cikin asibitin inda ya bullo dasu wani sashe daban an rubuta pediatrics clinic & ward, parking yayi ya juyo yana kallanta ya ce"Office dinta yana ciki, zamu shiga" ita dai sai kallansa take cike da mamaki, to menene dalilinsa na karyar budurwa, lokaci daya kuma zuciyarta ya tsinke, tofa kar watarana suzo da Umminta matar ta ganta ta nuna ta santa, wata zuciyar kuma tace bafa komai kije kawai. "Rafi'ah" jin ya kira sunanta yasa ta dawo daga tinanin da take, fitowa tayi shima ya fito sannan yayi gaba ta bishi a baya, tinda take zuwa asibitin bata ta6a shiga wajen ba, yayi kyau sosai, ga doctors turawa da bakake sunata zirya cikin clinic din, suna dai dai office dinta idansa ya sauka akan magungunanta dake hannunta, yasa hannu y kar6a ta tsaya kallansa ya ce"Idan mun fito zan baki" daga haka ya cusa ledan cikin aljihunsa ya murda handle din yana kallanta ya ce"Come in". Da sallama ya shiga tana biye dashi a baya, ya danyi murmushi yana kallan Aunt din tasa ya ce"Yau dai na cika alkawari ko?" Fara'a sosai matar take tana kallan Rafi'ah da kanta ke kasa ta ce"Masha Allah, u made it brother, wallahi na zata zakamin just like the other time" tasowa matar tayi daga mazauninta ta rungume Rafi'ah da zuciyarta ke bugawa, ta kama hannunta tana murmushi ta ce"Sannu da zuwa Kanwata pls have a seat" ta zauna tana kallan matar da take ta farin cikin, kallo daya zaka mata ka gane she is so happy at that time. Yusuf ya kalli Rafi'ah dake zaune kan kujerar office din ya ce"Sweetheart meet our first born, she's Anty Khadija by name" murmushin karfin hali tayi ta ce"Ina yini Anty" Anty Khadija ta kamo hannunta ta ce"Lafiya kalau kanwata, fatan kuna lafiya, yasu Mamanki?" Cike da nutsuwa ta ce"Suna nan lafiya kalau". Daga haka Anty Khadija ta mike ta bude fridge din dake office din ta dauko mata drink da glass cup ta ajiye mata a gabanta ta ce"I hope watarana zakije har gida ki gaisheni" murmushi Rafi'ah tayi ta langwa6ar da kanta kawai, Yusuf dake danna wayarsa ya dago yana kallan Aunt din nasa, sai dai baice komai ba, Anty Khadija ta kamo hannunta ta ce "Ur name sister" silenty ta ce"I'm Fatima but ana kirana Rafi'ah" Murmushi me kyau Anty Khadija ta sakar mata kafin ta ce"Wonderful, u are bearing our Mum's name" kara saukar da kanta tayi tana ta wasa da ring din hannunta, Anty Khadija ta mike ta ce"Bari na kira a kawo maki abinci" Yusuf ya dago da sauri ya ce"A'a Aunty yanzu zata tafi fa" harara Anty ta maka masa ta ce"Bafa Yusuf nace za'a kawowa ba" ya mike yana kallan Rafi'ah ya ce "Let's go" Anty Khadija ta bude baki tana kallansa ta ce"Are u ok Yusuf, ko ruwa ka barta tasha mana" har zaiyi magana wayar Rafi'ah ya fara ringing, ta kurawa screen din ido tana kallo ganin sunan Umminta yayi appearing, nan da nan kirjinta ya hau bugawa da karfi, karfa ta kira Doctor yace mata ya sallameta tin dazu.
"Who's that Fatima?" Muryar Anty Khadija da taji ne yasa ta mike tana kallanta ta ce"Is my Mum, i think i have to go Aunt, thanks for d care and i appreciate" Anty Khadija ta sauke ajiyar zuciya ta ce"Ohk, Allah ya tsare, ki gaida mutanen gida" daga haka ta kalli Yusuf dake shafa tulin gashin kansa ta ce"Burinka ya cika" ya danyi murmushi ya ce"Watarana zata zo maki gida Aunt" daga haka ya nufi kofa Rafi'ah ta bishi a baya tana kara yiwa Aunty Khadija sallama, binsu tayi a baya ta rakasu har mota sannan ta dawo ciki daga nan yaja suka bar wajen. Suna komawa inda ya dauketa tayi saurin bude kofar zata nufi nasu motar ya riko hannunta ya ce"Your drugs"...
[6/9, 11:00 AM] Teemarh: *_...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_


*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers_
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️

*BY FATIMA* _{Real~Teemarh}_

_3~4_

A hankali ta juyo ta kar6a ledan drugs din ta ce "Thank you" daga haka ta juya ta nufi inda motarsu yake. Mustapha na ganinta ya tashi da sauri ya bude mata back seat yana ta murmushi ya ce "Kinsan turawa nawa na gani sun wuce daga fitar ki?" Rafi'ah ta danyi murmushi ta ce "To idan munje gida zan gayawa Ummi sai kuyi magana" ya sakar mata murmushi yana shafa keyarsa ya ce "Haba haba ai maganar bai kai aje gun Hajiya ba, ni ina ni ina wadannan turawan" Dariya ta danyi taci gaba da danna wayarta shi kuma yaja motar suka fita a clinic din. Suna isa gida Mustapha yayi parking ya fito ya bude mata door ya ce "A huta gajiya" ta ce "Nagode" daga haka ta nufi entrance din gidan, a hankali ta murda handle din kofar ta shiga, sai da zuciyarta ya buga ganin kallan da Ummi ta mata, ta saurin sunkuyar da kanta ta ce "Kiyi hkr, i just saw ur missed call now" Ummi ta dauke idanta a kanta ta maida kan TV ta ce "Take ur breakfast now, after all kizo" akan sofa ta ajiye ledan drugs dinta sannan ta nufi kan dinning ta dauka plate da serving spoon sannan ta bude warmer. Few minutes ta gama cakalar abincin data diba sannan ta dauka glass cup ta bude dispenser ta diba ruwa kafin ta koma parlor ta zauna, ledan drugs dinta ta jawo ta balla wanda take sha as usual sannan ta mike zata bar parlor. "Rafi'ah" sunanta da Ummi ta kira ne yasa ta tsaya, ta juyo da sauri ta ce "Ohh Ummi na manta kince idan na gama" daga haka ta koma gefen mahaifiyartata ta zauna, Ummi ta sauke ajiyar zuciya ta ce "Yanzun nan na gaya maki abu har kin manta Rafi'ah? Me yake daminki ne two days? Or are u sick this days?" Girgiza mata kai kawai tayi, Ummi ta ce "To Allah ya shiryeki, can u remind how many days baki kira Anty Halima kin gaisheta ba?" Turo baki ta danyi kafin ta ce "Ummi ce maki tayi bana kiranta?" Ummi ta mata dakuwa ta ce "Ko karya ta miki? I don't know what's wrong with u this days, gaba daya kinyi turning upside down" Rafi'ah ta sunkuyar da kanta ta ce "Wallahi is her fault Ummi, haka kawai sai tai ta min wata magana da bana so" Ummi ta dalla mata harara ta ce "Do as u wish, ko yayyankaki take banga dalilin rashin kiranta ba, duk duniya ina da wacce ta fita ne, 'yar uwata daya tak a duniya kiyi kusan sati baki kira kinji lafiyarta ba, idan baki kirata ba who will u call?" Shiru tayi ta dinga jujjuya ring din hannunta bata ce komai ba, Ummi ta mike ta ce "Abbanku ma yace baki kira kin gaishe shi ba" Murmushi tayi jin an anbaci Abbanta ta ce "Ai Ummi na fita very early today, da bazan manta ba" Ummi ta ta6e baki ta tattara plate din kan dinning ta wuce kitchen.
Phone dinta dake kan TV stand ta dauka tayi dialing number Abbanta, bugu biyu ya dauka hade da sallama bayan ta amsa ya ce "Good morning Mummy nah" ta dan langwa6ar da kanta ta ce "Morning Abba, how is work?" Ya ce "All fine Mamana, u missed school today why?" cike da shagwaba ta ce "Abba naje clinic yau fa kuma ni kadai na" Abba ya sauke ajiyar zuciya ya ce "This is not safe at all, ya za'ai ta barki ki fita ke kadai?" Shiru kawai Rafi'ah tayi tana jujjuya ring din hannunta, Abba ya ce "How many days baki kira Hajiya kun gaisa ba? She called me day before yesterday and yesterday too still complaining, meya hanaki kiranta ki gaisheta? cewa tayi ma ni nake hanaki zumunci da ita" ta turo baki ta ce "Abba dazu fa Ummi ma saida tamin fada, kuma kona kira Mummy sai tai tamin maganar aure as small as i am" Murmushi Abba yayi kafin ya ce "And that not the reason da zaisa kiyi sati daya baki kirata ba Mamana, remember she the only one of your mother's sister" a hankali ta ce "To" Abba ya ce "Not just To alone, idan baki kirata ba wallahi Abba zai manta da Mamansa yayi mata fada" ta danyi murmushi ta ce "Insha Allah Abba, when are u coming back Abba, muna ta missing dinka nida Abdul" cike da rarrashi Abba ya ce "Worry not Mamana, zan dawo ending week din nan insha Allah" ta ce "Allah ya kawo ka lafiya Abba" ya ce " Ameen, try and be taking ur drugs kinji ko" ta ce "Yanzu ma nasha Abba" ya ce "Good, we will talk ltr in the evening i have a lot to cover" ta ce "Allah ya tsare" ya ce"Ameen Mamana" daga haka yayi hanging call din. Kwanciya tayi akan sofa kafin ta bude lock din wayarta ta kira number Mummy, yana fara ringing ta dauka, Rafi'ah tayi kasa da murya ta ce "Assalamu alaikum" ba tare da Mummy ta amsa sallamarta ba ta ce "Ai dama ubanki kadai zaice ki kirani kiyi" Rafi'ah da mood dinta ya canza ta ta6e baki ta ce "Bafa ki amsa sallamar ba Mummy kuma ba Abba yace na kira..." kafin ta rufe bakinta Mummy ta ce "Keep that ur small mouth shut, inba iskanci irin naki ba kwana nawa baki kirani ba? Ko danni ba Zainab bace?" Rafi'ah ta bubbuga kafarta a kasa ta ce "To kiyi hakuri, ni wallahi zancen auren da kikeminne banaso shiyasa bana san kiranki" Mummy taja dogon tsaki ta ce "Aida dangin ubanki ne da yanzu kin ishesu da kira, kowa da dangin uwarsa yake fara alfahari amma banda ke saboda wauta ta miki yawa, inba hauka ba me suke muku wanda kuke jin dadin sa?" A hankali Rafi'ah ta ce "To kiyi hakuri, i know i hurt but that's not my intention, how will i not call u Mummy, bayan kinyi 1 month bakya kasar, wallahi ina missing dinki sosai" Ajiyar zuciya Mummy

Please Login or Register in order to submit comment