Join Our WhatsApp Group

ABDUL JEY Complete Hausa Novel Document by ABDUL JEY


ABDUL JEY

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 47824



ABDUL JEY

Reading Time: 3 Hours

Added On: 28, Jan 2024

Author: Hajara Mamy Natty Girl ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : FANTASTIC STAR WRITERS (FSW)

Author Phone : ‪+234 806 061 7117

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 262.3 kb

File Type: txt

Views: 441+

Download: 455+

Last download: 23 hours ago

Description/Story: [2/9, 5:00 PM] ‪+234 806 061 7117‬: 💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊
*ABDUL JEY 1*
🕊💫💫🕊💫💫
🕊💫💫🕊💫
*🕊💫💫🕊Hajara*
*🕊💫💫Mami*
*🕊💫Natty*
*💫girl*

```INDICATED TO RUNKA```

*The story is for you only miss Salsabila lawan*

~FANTASTIC STAR WRITERS (FSW)~

```Bismillahir Ramanirrahim
Da sunan Allah Mai rahama mai jin kai Allah Ya ban ikon kammala wannan littafi sannan yasa in isar Da sakon Da nake San isarwa Ameen,```

*Wannan littafin badan in zagi wani ko wata zanyiba, actually key point Na wannan littafin nawa ya faru ne Da gaske iya key point din Amman labarin ni Na tsara inasan ko fahimceni Da kyau sannan Allah yasa mu gyara ameen,.*


Kallansu doctor din Yayi tare da cire glass din fuskarshi, kallan saurayin dake kusa Da tsohun Yayi me Yasa kukai Haka? Kamata Yayi ace tun lokacin Da kuka San yana Da wannan ciwon kuka kawoshi asibin Amman saida abun yai worst sannnan zaku kawoshi, kallan shi j man Yayi doctor ban gane inda zancen ya dusa bafa kamun bayani sosai mana, OK kana nufin kace mun baka San mahaifin naka yana Da HIV ba bane Dan har ta fara shirin shiga aid, da sauri j man ya mike Yana jijjga HIV how comes babana lafiyar qlau kallan tsohun Yayi baba kamai bayani kace Mai lafiyar qlau mana, tsohuwar dake kusa Da dayan bangaren kuwa shiru tai ta kasa Magana hawaye kawai take, kusa Da matar ya koma mama KO dama kinsan baba yana HIV Ne Amman Ni kuma banma dade dayin test ba me yasa banda shi, tsohan ganin yaronshi nasan zaucewa yasa Ya riko hannunshi GA wani uban tari Da yake, yi shiru Abduljabar zan maka bayani in munje Gida Amman kafin nan ka Fara kaini gun da nake aiki ina San zanyi magana Da ogan mu ya karasa yana tari, jijjaga kai doctor yai kafin ya dakko takarda ya mika Mai wannan kudin magungun gunan Da zai dunga amfani da sune duk Da kun makara Amman a jarraba,dubu ashirinne guda daya gasunan guda ukune, sosai kirjin j man ya buga dubu sittin ina zai gansu ,.

Karba Yayi kafin ya taimkawa baban nashi suka mike sannan Maman tashima ta mike tana rike Da kirjinta Dan heart dinta cixonta take daurewa kawai take, da guntun kudin hannunshi suka shiga texi sannnam suka nufi wannan company Da naga ansa diamond design company, sauka sukai dukda zafin Da Baba ke ji bai hanashi daurewa ba yai gaba j man ya tayashi, saida suka hau sama sakai tafiya sosai Dan company din babbane sosai, tsayawa sukai kafin baba Ya kalli j man ka jirani anan ina zuwa baba ba zaka iya tafiya bafa, Dan Allah abduljabar ka jirani anan, badan yasoba ya tsaya sannan shi kuma ya shiga,.
Da sallama ya shiga security din suna ganinshi suka Bari ya shiga tunda sun riga Da Sun San yana zuwa dama, saida ya tsaya na ciki suka fito sannan Ya shiga da sallama alhaji na dabo dake tsaya ya juyo ganin Wanda ke sallama yasa Ya hade rai Amman hakan baisa baba shiga, ina wuni alhaji? Kaga Umar ka fadi abun dake tafe dakai wai banace mudaina wannan harkarba na baka kudin ka bana San damufa, alhaji ba Haka bane, to yayane? Dama alhaji yau naje asibiti ake fada mun wai ina Da....... Tun kafin ya karasa ya karfe kana Da HIV dama baka San zaka samuba ai nima ina Da itta ina shan magani kardai kace mun kai baka sha kace karshen kane yazo? A dan razane baba Ya kalleshi dama kana dashi agunka na dauka kenan? Ah to saime kuma koda zaka kai kara bamai yadda dakai Bari kaji in fada maka, kallan agogan hannunshi yai kaga yanzu Ma Gida zanje, Da sauri baba yasha gabanshi Amman ka cuceni kuma insha Allah sai kaga sakaiya koda kuwa akan yarkace, aikuwa yana karasawa alhaji ya daukeshi Da mari karka kara hada wani abun Da yata wlh kurwarta tafi karfinka, banza kawai ,murmushin takaici Baba yai ba laifinka bane laifinane Da kuma laifin zuciyata Amman kaje duniyace ta isheka riga Da wando, han kadashi yai har saida ya bige sannan yai gaba yana fita yaci karo Da j man dake jiran banashi ya fito Da sauri ya shiga yadda yaga baban nashi hankalin ya Tashi, Baba meke faruwa wai? Karka damu Abdul dole yau in sanar dakai koma maye Dan nasan yau dinnan karshenane yaxo, plz Baba kadaina fadan Haka ,ya taimaka masa suka fita, a wajen Da sukabar mama nan suka sameta sannan suka kara hawa texi suka wuce,.

Sakkowa take daga stair tana taunar cigum ga key Na car a hannunta, sakkowa tai dinning, bako sallama ta zauna kafin ta kalli momy dinta Mormon momy? Maman bace mata komaiba lokacun wajen 12:00 Amman sai lokacin hasinat Ta Tashi, tabe baki tai ganin Maman bata ce mata komaiba tana bude cooler idonta ya sauka kan shinkafa Da miya, Da sauri ta Mike tare da furta Hafsa, wacca aka kira Da Hafsa ta fito Da gudu gani aunty, kafin ta rufe baki, hasinat Ta dauki wannan shinkafar ta juye mata sannan Ta dauki miyan ta juye mata, a hatgitse momy ta Mike da niyar bata mari Amman taji an rike hannun, juyawar Da zatai taga Ashe alhaji na dabo ne, dama tasan saishi, kallanshi tai Amman alhaji kana ganin abun datai, to saime naga kudin Dan itta nake tarawa, tsaki momy taja Allah Ya kawo karshen wannan kudin kowama ya huta ta fada ranta a bace,.

By hajara Mami natty girl
[2/9, 5:00 PM] ‪+234 806 061 7117‬: 💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊
*ABDUL JEY 2*
🕊💫💫🕊💫💫
🕊💫💫🕊💫
*🕊💫💫🕊Hajara*
*🕊💫💫Mami*
*🕊💫Natty*
*💫girl*

```INDICATED TO RUNKA```

*The story is for you only miss Salsabila lawan*

~FANTASTIC STAR WRITERS (FSW)~

Zaro ido alhaji yai aikuwa ta Allah ba takiba, kallan hasinat yai daughter mu tafi kinji, Da kallo momy ta bisu har suka wuce kafin ta maida kallan ta ga Hafsa Wadda duk ta jike Da miya, kiyi hakuri Hafsa Allah zai saka miki, murmushin yake tai babu komai ai ittama zata dena wata rana tana fadan hakan tai gaba dan gyara jikin ta inda take jin zafi, momy tai daki,.
Daddy fita zanyi zanje gidan su walida, OK to nawa kike Da bukata? Ahh daddy kamar dubu hamshin Ma Yayi ,bai miki kadanba, Ya isa just na Yau kawai, murmushi yai ya dakko wayarshi yai mata transfer din kudin, godiya tamai sannan Ta fita wajen motar taje ta shiga ta kama hanya,.

Haka su j man suka karasa gidan duk jikinsu babu dadi,har daki j man ya kai baban nashi mamanshi na zaune kusa Da shi itta dai gatanan Ne,.

Riko hannun j man Baban yai zauna gaka ga mamanka in baku labarin abun Da ya faru,.

Can watanni Da suka wuce abduljabar kana wannan karshen fitar ka daga university dinnan wannnan kudin Da ake nema ba kowane ya ban suba illah alhaji na dabo abun Da yasa naki in sanar dakai ranar saboda bansan wacce karya zan makaba lokacin farkon fitana, Na hadu dashi Da yaga ina Cikin damuwa ya tambayeni na sanar dashi bukatata Da nan yace zai ban Amman da sharadi nace ina jinshi nina dauka a wannnan lokacin sharadin Da zaiban zaice karna Dade ban kaimai kudinshiba Ashe ba wannan bane dan cemun yai wai sai na amince dashi lokacin daya fadan hakan ban gane inda zancen ya dusa ba saida yamun dallah nan dai hankalina ya tashi dan ban kowa alhaji yana aikata abu Irin wannan ba wai na miji ya dinga neman na miji abun ya daga hankali nan dai na tur Da zancen shi namai wa,azi Amman ya nuna bai daukaba karshema cewa yai yaban lokaci inje inyi tunani,haka naii yawun neman kudin ban sanuba Abdul kaima gashi aikinnan kake a garage Amman kamar bayi kakeba, Abdul na rasa ya zanyi gashi lokaci kara matsowa yake hakan yasa na yanke hukunci kawai in amince Da zancen shi, Abdul Haka naje nace Mai Na amince, Ya fada mun inda zamu hadu, rufe Mai baki j man Yayi shikenan ka amince akan wani banza kudi ka amince akan karatuna Wanda gashi na gama ba aikinyi karshema sai garage din dana kare a ciki me Yasa baba me yasa kai Haka,baban Ma kuka yake Abdul abun yaban mamaki bansan ana daukan cuta Irin wannan ta wannan hanyarba lallai kuwa Allah ne ya nuna mun ishara Abdul Abdul gashi duk kudin Da nake samowa agun alhaji basu Da wani albarka tunda gashi har yanzu dai a yadda nake hakan nake, banga ribar wannan abunba Abdul, kuka kawai j man keyi baba ba wannan ko kasan abun Da Allah yace a duk lokacin Da ake aikata irin wannan abun sama Da kasa hadewa suke sannan inda zakasa kwai a kasan gadon zai iya soyuwa KO dafuwa baba me yasa ka mantaa hakan me yasa, Amman Baba ka fada wa alhajin, nan ya sanar Mai yadda sukai, sosai ranshi ya baci, baba karar shi zan shigar, aa Abdul ka bari koka shigar wlh bazakai riba ba koma Maye ai nina jawowa kaina, jijja kai Abdul yai shikenan indai court ba zata dauki mun matakiba ni zan dauka Da kaina kudin Da suka jawo ka fada wannam abun ba zasu tafi a banza ba, rike hannunshi baba yai nace kabari KO Abdul me yasa bakajin magana ne? Kallan inda Maman take joy man yai kallanta yai kamar bata motsi hakan yasa Ya karasa inda take, Ya tabata aikuwa ta tafi luuui zata fadi yai saurin rikota, bata nunfashi abun daya furta kenan baba mamafa ta mutu, mama ya hau jijjagata Amman bata motsi Da sauri baban Ya mike dukda jikin bayamai dadi ya karasa gunta, halima yake kiran sunanta Amman shiru, kuka ya fashe dashi har yasa Ya Fara tari harda aman jini yi yake sosai, ajjiye Maman yai ya rike Baban ya isah haka baba ka daina kuka ganin har lokacin aman bai tsayaba ya Mike Bari inje in siyo maka magungunan kafin nan zan turo a dauki Maman,. H
Da sauri ya fice yaje makota ya sanar musu abun dake faruwa sannan Ya kama hanya aljuhunshi ba komai hakan yasa Ya yanke hukunci zuwa gidan yayan babanshi, haka ya nufi gidan dukda bayajin zai Sami abun Da yaje nema

By hajara Mami natty girl
[2/9, 5:00 PM] ‪+234 806 061 7117‬: 💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊
*ABDUL JEY 3*
🕊💫💫🕊💫💫
🕊💫💫🕊💫
*🕊💫💫🕊Hajara*
*🕊💫💫Mami*
*🕊💫Natty*
*💫girl*

```INDICATED TO RUNKA```

*The story is for you only miss Salsabila lawan*

~FANTASTIC STAR WRITERS (FSW)~


A hankali ya tura gate din gidan tare da sallama,, mai gadi dake zaune ya amsa yana kallan shi fuska dauke Da murmushi Amman yana ganin yadda j man din ya shigo ya tabbatar baya Cikin jin dadi gaida baba yai kafin yai ciki, saudat dake tsaye a kusa Da motan saurayinta suna hira Tana ganinshi ta hade rai, kallan saurayin nata tayi wannnan dan maulan yazo wlh yana Da matsala wai ace saurayi dashi yabar zuciyar shi ta mutu har Haka saidai mutun yaje maula kuma wai a hakan yace yana sona ni wlh yama gama dani, kallan ta j man Yayi Amman baya mood din ittama Da tasan dash take Yi ,.

Da sallama ya shiga parlour din matar dake parlour din ta amsa ganin shine yasa Ta hade rai kamar ba ittaba, yaron dake dining table ne a zaune ya kalleshi Yaya Abdul sannu Da zuwa? Yauwa Sameer ya fada tare da gaida matar Tana amsawa ta Mike tabar gun, sameer ne ya dakko ruwa a fridge Ya kaimai, rikoo hannunshi yai samer jeka cewa daddy nazo, OK Ya fada tare da yin sama ya dan dade kafinnan suka sakko tare shida sameer din,.

Kasa Abdul yai yana gaidashi ya amsa ba laifi, ina jinka Abdul lafiya na ganka a wannan ranar haka? Nan j man ya fada mai abuun dake tafe dashi, jijjaga kai yayi yanzu shidin baida lafiya Amman tunda bai fada mun na naimi kudi Da wuriba sai yanzu gaskiya Abdul yanzu banda kudi Amman GA shawara Mai zai Hana kaje jeji ka Dan Ya go Mai wasu ganyen ai suma suna maagani, sosai ran Abdul ya baci yasan Yayan baban nashi yana dashi bashinne dai Da bazai yiba yake Mai zancen banza,mikewa Abdul yai baice komai ba ya Kama hanyar fita,aa maye haka Abdul ina maka mmagana ka Kama hanyaar fucewa? Juyawa yai bana bukatar shawarar ka kawu ka rike abarka kawai ka fito kaace mun bazan baka kudinba Abdul shikenan fa Amman kaa tsaya kaana batan lokaci kaje Da kudinka kowa yana Da tasa ranar ai Yana kaiwa nan ya fice inda yabar kawu Nata zuba masifa wai yamai rashin kkkunya, a hannya suka hadu da raudat tai saurin matsawa dan tasan kadnne daga aikinshi in bai dauketa Da mariba, hakan yasa Ta bashi hanya,.

Haka ya fice bashi Da mufuta yanzu ina zaiyi Maye abun yi shine kawai abun Da yake tunani wanda har yai nisa baisan inda yake wullah kafarshi ba har yahau titima bai saniba, sai jin kitttttt Yayi alamar an taka burki Da kar dinnan, Cikin fushi hasinat Ta fito ranta inyai dubu toopah ya baci, hakan yasa Tana fitowa ta daukeshi Da mari Wanda yasa Ya dawo daga tunanin shi yamai Da kallan shi gareta zuciyar shi tafasa take wai wannan yarinyar cezata mareshi, daga hannun yai Da niyar ramawa yaji an rike hannun, mutunmin daya rike hannun ya kalllshi bai kamata bawan Allah ka Rabu da itta koba komai macece sannan kaika shiga gabanta dukda ittama bai kamata tai mariba, kallan mutumun yai kafin ya tina conditions din daya bar iyayen shi hakan yasa bai tsaya tamkawa ba yai gaba inda yabar hasinat Da masifa sai zagi take Tana gunda Mai masifa mutun yana tafiya hankali a sama dama nabi takanka inga uban daya tsaya maka a wannan duniyar gaba daya dan iska kawai banza Mara hankali, haka ta shige motan,.
Yana tafiya ya yanke Shawarar zuwa gun ogan Baban nashi dukda yace Mai yaje Amman yamai rashin mutunci Amman zai gwada shidin Da Haka yahau taxi ya wuce gidan alhaji Mai bado,
a kofar gidan aka saukeshi ya shiga ciki abunshi ya sami Mai gadi kan cewa yamai sallama damai gidan Haka kuwa akai,

By hajara Mami natty girl
[2/9, 5:00 PM] ‪+234 806 061 7117‬: 💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊🕊
💫🕊🕊💫🕊
*ABDUL JEY 4*
🕊💫💫🕊💫💫
🕊💫💫🕊💫
*🕊💫💫🕊Hajara*
*🕊💫💫Mami*
*🕊💫Natty*
*💫girl*

```INDICATED TO RUNKA```

*The story is for you only miss Salsabila lawan*

~FANTASTIC STAR WRITERS (FSW)~


Sanda mai gadi ya shiga ya sanarwa alhajin yace ace ya shigo,bayan mai gadin ya sanarwa...


Read / Download ABDUL JEY

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album