Join Our WhatsApp Group

BARIKI AUREN SOJA Complete Hausa Novel Document by BARIKI AUREN SOJA


BARIKI AUREN SOJA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 107810



BARIKI AUREN SOJA

Reading Time: 8 Hours

Added On: 29, Jul 2023

Author: Fenerh ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Horror novels

File Size: 598.38 kb

File Type: txt

Views: 2830+

Download: 2382+

Last download: 5 days ago

Description/Story: (¯`*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿`°¤,¸.•*´¯)



тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09

🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻
_*BARIKI*_
👨‍✈ _Auren soja_👨‍✈
🌻🌻🌻🌻🌻🌻🌻


_written by fenerh_
Maman Ammar



*Dedicated to*
Fiddousi mainasara


*Allahamdulilahi Ala kulli halem ina godiya ga Allah mai kowa mai komai da ya bani ikon dawowa a cikin sabon labari na wato BARIKI Auren soja duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah madaukakin sarki wanda ya bani ikon rubuta wannan labari Alkhairin dake cikin shi Allah yasa Alumma su Amfana dashi kuskuren dake ciki Allah ka gafarta min Ameen*


*KADUNA*

N.D.A BARRACK convoy ne na sojoji a Jere na hilux sai wata jeep katuwa guda daya a tsakiyar su,


Katon gate d'in suka shiga na w'anda gaba daya sojojin dake wurin suka kame Alamar girmama wa ga wanda ke cikin jeep din mai ruwan kalar sojoji,



Jiniya kawai ke tashi Alamar koma waye a ciki babba ne a Aikin, jerin manyan gidajen suka nufa w'anda daga gani na manyan sojoji ne dake cikin barikin wanda sune farkon shigowa,


Gidan da yafi kowanne girma suka tsayar da motocin, kuratan sojojin suka fito dauke da bindigogin su tareda kamewa domin jiran Fitowar ogan nasu,



Gaban motar aka bude gefen mai zaman banza wani soja ya fito rike da brief case da kuma manyan wayoyi har ma da jakar laptop duka a hannun shi,



Shi ya bude kofar bayan tare da sarawa da hannun shi daya Alamar girma mawa, w'anda ni a zatona shine ogan saidai ganin wanda yasako kafar shi a waje ai tuni na yi saurin boyewa bayan manyan itacen fulawoyin dake harabar gidan,


Wani kyakkyawa kuma kakkarfan matashi ne fari tas dashi ya fito daga bayan motar sanye cikin kakin green na soja,


Wanda da Alama da wuya ya kai shekara Arba'in a duniya, ga kakin ya mugun fitoda kwarjinin shi har ma da kara bayyanar da kyanshi a zahiri,



Cikin takun shi mai cike da kasaita da kuzari irin nasu na sojoji jarumai, ya fara takawa domin shiga cikin gidan nashi,


Nayi matukar jin mamakin ganin wannan karamin matashin ana bashi girma duk inda ya wuce,


General Muhammad Abdullah kenan G.O.C I DIV Nigerian Army Kaduna

Mutum mai matukar kwarjini da cikar haiba kana ganin shi kasan yana gina jikin shi ta hanyar training da kuma Abinci mai lafiya,


Yakai namiji ta ko ina domin samun kyakkyawan namiji sosai wanda ko wacce mace zataso ta mallaki irin shi,



Kofar gidan nashi ma sojoji ne masu tsaron lafiyar shi, ciki suka shiga shida PA dinshi wanda daga gani Akwai y'ar da mai karfi a tsakanin su da kuma Aminci,



Juyowa yayi cike da bada umarni ya kalle shi "Ahmed take care of them am going to take a bath and rest u can go to your house and rest too,


" tank you sir ya fada tareda mikamai kayan shi ya juya domin isa nashi gidan,


Motar ogan nasu ya bude ya Ciro bandir din kudi ya mika wa sojojin da suka rako ogan,


Sunyi matukar farin ciki shiyasa suke matukar kaunar megidan nasu domin Akwai kyauta kusan kullum sai ya basu kudi su raba,


Kafin su wuce,
Shima PA din da aka kira da Ahmed ya wuce gidan shi wanda yake gaba kadan da gidan ogan nashi wanda kana gani kasan boys quarters ne duk da suma ba laifi sun tsaru Amma ba kamar gidajen manyan ba,


Wata kyakkyawar mace ce ta fito da gudu tareda dan karamin yaronta ta tareshi da murna fal fuskar ta,


Da sauri ya riketa da hannu daya shima fuskar shi cike da fara a dajin dad'in ganin farin ciki a fuskar Matar tashi,



"Madam dina ya Akayi kike irin wannan gudu haka kin manta da Ajiya ta ne kikeso kimun Asara?


Kankame shi tayi gam tareda fara hawaye w'anda kana gani kasan na farin ciki ne. Da kuma jin dadi,


Dagowa tayi tareda Jan hannun shi suka shiga cikin falon su tana cewa " Dadyn Auwal ka tayani murna yau munyi waya da baba harda Mama yau da kanshi zai kawomin Yasmin Ahmed baba ya daina fushi dani,

Ta karasa tana fashe wa da kuka, kan kujerun dake falon ya jata tareda rungume su gam ita da yaron shi yana mai lallashin ta daga gani kasan Akwai wata akasa da har yakesa shi jin tausayin Matar tashi,



"Am sory Maryam nasan nine sanadin komai Amma ki daina damun kanki bazan taba juya miki bayaba kuma gashi kinga su baba sun hakura har zai kawo mana uwar rigima da kanshi,


To kija mata kunne karta zo tana leka min gidan oga don nasan tasa mai ido, ya furta cike da dariya domin kawar mata da damuwar ta,



Dariya tasa itama tareda goge fuskar ta " ai Yasmin Akwai tsiwa ita wai y'anda mata ke shiga da fitane yasa ta tsane shi kuma ko ganin shi bata taba yiba Amma ta mugun sashi gaba da Zagi,


"Hmm pray for him ni kaina ina son oga yayi Aure ko zai rage kwaso mata gidan shi, duk da nasan wasu suke kawo Kansu Amma inaso Allah ya bashi ikon daina wa,


Ameen tace tareda zamewa ta fara kwance mai boot din kafar shi ya rungume yaron shi dakyau a kirjin shi,


" mama tace kar inyaye Auwal inbari har inhaihu tunda bai kaiba, "haka nafada miki tun farko ai kika kiji yanzu tunda mama ta fada zakiji ai,



Dariya tayi tareda mikewa rikeda takalmin domin fita dasu susha iska, bin bayan ta yayi da kallo yana maijin son Matar tashi har cikin b'argon shi,



Muhammad na shiga falon shi yaci karo da takalmin mace, ya kwalawa kukun shi kira tareda ajiye kayan dake hannun shi akan kujerar dake lafiyayyan falon nashi da ya mugun kaya tuwa da kayan Alatu,


Da gudu ya fito yana " yes sir "Emanuel who came? " oga na da madam way day give me money come,


Wani irin mugun kallo ya watsa mai tareda cewa "you are very stupid didn't I warn you ?


" sory sir ya fada yana kamewa kafin yace wani Abu yaji tace "hy M.A ta fada cikeda yanga da kara'i raya gaba daya surar jikinta a bayyane yake don kusan rabin kirjinta da sukayi ruku'u a bayyane suke,


Matsowa tayi tareda rungume shitsam wanda yayi sanadiyyar watsawa Emanuel mugun kallon da ya kwasa a guje yayi kitchen din gidan,



Saurin janyeta yayi tareda daure fuskar shida Sam dama ba Alamar fara'a atare da ita,


" why the you come? Marai raicewa tayi tareda cewa "come on baby I miss you so much that's is why I came,



Kafin ya bude baki yayi magana wata budurwa ta fito daga cikin dakin baccin shi sanye da T-shirt dinshi na Como flag rigar ko cinyar ta bata rufe ba domin idan tayi kyakkyawan motsi za a iya ganin pant dinta,


Wani irin kallo ya bita dashi tareda kwalawa Emanuel kira cike da bakin ciki,


Da gudu ya fito rike da cooking spoon yana sarawa " yes sir, wani irin disgusting look yake aika mai kafin ya ce,


"Are you stupid,? " no sir Am sory "na she tell me say..... " come on keep quite, ya fada yana mai ture su duka cike da fada "now All of you out of my house, you All no my rules no one comes to my house without my permission,


" and you I will del with you letter, ya nuna Emanuel da hannu kafin ya wuce ciki, binshi sukayi da kallo domin sun saba da halin shi na wulakanci don haka kowacce ta kama gabanta kafin ya jona su da mugayen kuratan yaran shi,


Wanka yayi kawai ya haye gado domin ya sauke farali a office kuma bayajin yunwa he just need to rest before going out,

______________________
A zaune suke a barandar kofar apartment dinsu suna shan iska shida iyalin shi kana ganin y'anda yake tarai rayar ta kasan Akwai soyayya mai karfi a tare dasu,



Gefe daya d'an karamin yaron sune ke wasa akan d'an keken shi na yara,
Kara shigewa tayi jikin shi tsam,


"Ya Akayi ne farin cikin Ahmed? Murmushi tayi tareda fara yimai shagwaba,

" wallahi na matsu Yasmin batazo ba inaso inga babana Baban Auwal, "k'arki damu maman Auwal dina komai yazo karshe insha Allah,


Tsayuwar mashin din da ya dakko ta yasa tayi saurin mikewa tareda rugawa da gudu ta rungume ta,


Itama cike da zumudi ko akwatin ta bata d'auka ba ta rugo suka rungume juna cike da so irin na yan uwan da suka mugun shakuwa da kuma son junan su,



Daka gansu kaga jini daya saidai Yasmin tafi Maryam kyau nesa ba kusa ba duk da ita din kyakkyawa ce sosai Amma Yasmin tafita don ita farinta har wani daukar ido yakeyi,


Yarinyar kamar Aljana ga jikinta dai dai da ita, saida suka gama murnar su sannan ta kalle ta " ina babana?


"Wallahi baba ya tafi zaria Anki rashi wurin aiki shiyasa nazo ni kadai Amma yace shi zaizo daukata,



Wani iri tayi domin taso ganin mahaifin nata sosai tasa rai, tsaye yayi tareda nan nade hannu yana zabga murmushi domin ganin Abinda sukeyi,


Shi ya matso tareda Sallamar mai mashin din ya kallesu to mushiga daga ciki idan kun gama murnar ni ko gani na kanwata batayiba wannan karon nayi fushi,


" lah yayana wallahi tsabar murnar ganin rabin jiki ko boy dina Bangani ba sai yanzu ta ruga tareda rungume shi tsab "I miss you my boy,



Ta fada with so much excitement yayi dariya shima yaron kamar ya ganeta


A kan kujerun da suka tashi ra zauna tareda zubawa kofar katon gate din ido,


" Aunty ina bunsurun can gidan? Saurin rufe mata baki tayi "kiyi shiru kar Baban Auwal ya jiki wallahi kina zagar mai oga,


" ai Aunty ban taba ganin namiji mai d'an banzan son mata ba irin shi wallahi ana fadan sojoji na kwashe kwashe nashi karshe ne,


Shiyasa bana ko kaunar ganin shi A Rayuwata I hate him to the extend,


"Ikon Allah wai maikarfi na bara ina ruwanki da bawan Allah da baruwan shi da harkar mutane kuma bai ko San Allah ya tsiroki ba Amma kinsa mai ido,



" ai Bazai ma San daniba har abada d'an iskan mtsww ta mike tareda nufar cikin gidan domin maganar shi kawai tasa ranta ya baci,



Dariya kawai Maryam tayi domin tasan halin y'ar kanwar tata, ta shiga ciki itama,



Tare sukaci Abinci suna hira atsaka nin su kafin ta fito mata da tsarabar da takawo ma yaron ta na kayan wasa da kuma kayan sawa masu kyau,


Sai su kubewa da Daddawa da sauran kayan gargajiya irin na bahaushe daga mama domin tasan basa samu a bariki,



Saida tayi wanka ta shirya cikin kana nan kaya San nan ta dora after dress akai domin tana son tafita tasha iska a wajen gidan dama ta saba duk tazo nan ne wurin zaman ta tana karewa bariki kallo,



Yaron ta ta d'auka ta fito tana tafiya a hankali kamar bataso hannun ta rike da wayar ta hot 8 ta zauna tana karewa gidajen kallo kafin ta sauke akan katon cikin su wato na oga kwata kwata,



Emanuel ne ya fito daga gate din hangota da yayi yasa ya zo da sauri bakin shi har kunne,


"My friend don come, ya fada with so much excitement da jin dad'in ganin ta domin sun saba sosai kuma shine ummul khaba isin da yasa ta kara tsanar M.A domin shike bata labarin komai,



Washe mai fararen hakoran ta tayi cike da jin dadi tace " yes woo friend how are you?


"Fine mam hope you are not going back and leav me here again? " yeah I will but I will spend one month here with my friend, ta fada tana dariya,



Da yake ba wani kan gado gareshi ba ya ce "come escort me na oga send me' itama kan narawa tace ok Am coming


Ciki ta koma tareda janyo hijabi ta dora akan kayan jikinta ta saba yaron ta akafada tace Aunty zamuje yawo da EMA,


Kallon ta tayi kafin tace " keda EMA ko sai gyaran Allah kun hadu kun dace wallahi,


"He is very funny and friendly wallahi inajin dad'in hira dashi Akwai shafta " kodai gulma ? Keda yayanki ba ruwana



Fita tayi tana dariya sunyi tafiya mai nisa yana gabza mata labari da kuma Abinda ya faru dazu shida ogan shi yaja ya tsaya tareda dora hannu aka,


"Ewo I don die I forget wetin oga tell me wo ' come mo we go back and ask him, kallon shi takeyi cike da mamakin wautar shi ko waye ya dauke shi a aiki oho,



Da sauri sauri suka juyo domin yasan yayi laifi karya kara wani,

Shikuwa M.A da ya dauki lokaci yana jiran Emanuel ya kawomai sako yaji shiru kuma yanaso ya fita dole ya fito ya tsaya sanye cikin tree quarter da t-shirt na Como flag yayi masifar yin kyau ga wani Annuri da haske dake bayyane a fuskar shi,



Isowar Ahmed wurin shi yasa ya fara mai magana cike da takaici, " you have to find better cook for me I don't like this guy at All can you imaging him letting Kate and that stupid girl chioma in my house?


Dariya Ahmed yayi kafin yace "oga sun cika naci ne wallahi bebs din nan naga ka gama yayin su Amma sunki hakura,



" ni bansan me yasa duk Yarinyar da na sake mata fuska sau daya ba sai ta nace min, "farin jini ne oga, Ahmed ya fada cikin dariya,


" kodai rashin class I hate that kind of girls, "am idan mun fito daga gidan Hajiya zamu biya unguwar shanu inason inyi renewing wasu'



Yafada tareda yin wani tsadadden murmushin shi mai kyau, dariya Ahmed yayi " oga Karfa mu samo wasu karfen kafar kuma kuma kasan zuby ta kusa zuwa karka hada rigima,



Dariya yayi sosai tunawa da zubyn tashi da yayi domin tsohuwar budurwar shice kuma itace y'ar gidan ministern kudi Yarinyar naji da kyau da gata sun dade tare da juna suna Kwasar muguwar soyayya atsaka nin su,


Bata kaunar ganin shi da ko wacce mace duk da itama tana nata Rung's din a kasar wajen da take karatu,



Karaso wa sukayi itada Emanuel suna Kwasar dariya, tunda suka matso yake kallon ta yana mamakin wace mahaukaciyar ce take hira haka da Emanuel gata daga gani kamar tanada hankali,



Tana hango mijin yayar tata da wani a wurin tayi saurin tsayawa daga nesa domin tasan da shine ogan nasu da ake fada kuma wannan ne karon farko da ta fara ganin shi fuska da fuska,


"Amma anyi kyan dan maciji ta furta a...


Read / Download BARIKI AUREN SOJA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album