Join Our WhatsApp Group

DAME AKE ADO Complete Hausa Novel Document by DAME AKE ADO


DAME AKE ADO

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 56087



DAME AKE ADO

Reading Time: 4 Hours

Added On: 28, Jul 2023

Author: Jamila Umar Tanko ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 337.59 kb

File Type: txt

Views: 3012+

Download: 1492+

Last download: 13 hours ago

Description/Story:  DAME AKE ADO part (1)
1⃣Mahaukaciya yarmacukule mahaukaciya tasaci zare dandazon yaran da suka zagaye mahaukaciyar ke ihu suna fada yaukam adurkushe take tana kuka tarike cikinta sabanin canbaya da idan suna wannan wakar take rawa eyehuuh eyehuuh kuka takeyi yau babu rawa suka kakama fada suna ihu malam sulaiman dayake dosowa tundaga nesa yacika yacika dataikaicin yanda yaran unguwar suka takurawa matar dababu wanda yasan daga indatake kawai an wayi garine anganta a unguwar yadauko tsumagiya yayi kansu yafara dukansu sai suka watse sunaci gaba da ihu dawakarsu filin yazama sai ita kadai harlokacin tana durkushe tana kuka
2⃣ya isa gurinta yana fadin baiwar Allah tashi kitafi abinki kinjiko wayyo Allah cikina mutuwa zanyi maganar datafito daga bakin mahaukaciyar kenan wacce tasanyashi kara kallonta da mamaki dan tsawon wata tara dayasan matar baitabajin tayi maganaba saiyau kuma abin dayabashi mamaki baiwuce jin maganar tata yau irin tamutumin dayasan ciwonkasa baceba kafin yakai gacewa wani abu yakuma jin tace wayyo Allah zanmutu saiyaga jini yanazubowa ta karkashinta dasauri yace subhanallahi haihuwa ce zakiyi dandama tanada ciki wanda akezargin wanine yayimata akan bolar datake kwana tabayan gidan malam sulaiman din baiyi wata wataba yakamota dasaurinsa danjin kamar tana nishi ga yaran basu bar gurinba sai ihu suke tayi yaciccibeta yakaita soron gidansa dake jikin bolar ya tura kyaure
3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu

3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu

5⃣Allah zaitaimakeshi mlm din yafada cike da matsananciyar damuwa ko ajikinta wai antsikari kakkausa sai ma cewa tayi gaskiya saidai kayi hkr amman bazan iyatabataba abinda akace wurinda akahaifi shege ka taka kaida arziki har abada nidazakuji ta tawa ma aidakunfita daga soron gidanmu kada tashafamana talauci karabuda ita malam kaje kasamo mota akai matar nan asibiti zubar jini tayi yawa tafi don Allah kada ta mutu malam din yayi duru duru sannan yafice dasauri yajanyo kofar lami tayi tsaki takoma cikin gidanta tana cigaba da fadin Allah daiyakawo mlm wlh waje za.ayi da ita bazata goga mana talauci ba daman kulum anata fama sai anfita asamu dakyar ita dai Deeje kamo mahaukaciyar tayi dake tafadin wayyo cikina mutuwa zanyi
6⃣deeje tace kinga daina cewa wayyo kama salati ringa kiran sunan Allah Aikuwa cikin ikon Allah mahaukaciyar takama kiran sunan Allah dakarfi deeje tana rike da ita tadinga wani irin wani irin nishi saiga katon da deeje tace insha Allah sauraki mahaifa daure kiyi nishi kozata fado takama yin nishi da karfinta deeje tafara fadin subhanallahi ahankali zakiyi Amman ina yitakeyi da iyakar karfinta sai deeje takula ba ita takeyin numfashinba daga Allah ne kawai saigigice ta rude ganin mahaifar tafado jinin kuma yana bulbula kamar fanfo dakyar ta iya janyo yaron tayanke masa cibiya jin yana ihu daidai lokacin mlm sulaiman yaturo kofar yana fadin deeje gamai motar nan kota haihu ne cikin kuka take fadin shigo mlm shigo kaga halinda take ciki yaturo kofar yashigo kallo daya yayimata

7⃣hankalinsa ya dugunzuma yakama cewa da deejan kamota muje Asibiti deejan nakokarin kamata sai dai mahaukaciyar tariko hannunta tana fadin mutuwa zanyi kada kukaini asibiti kuwahala sunana Asma.u haki yakamata deeje takuma rudewa tana fadin innalillahi kifadi gidanku wacece ke maimakon ta iya cewa wani abu sai kalmar farko da deeje ta ambata ta innalillahi wainna ilaihi rajuun raiyayi halinsa talangabe anan hankalinsa deeje da mlm yayi matukar tashi deeje tafashe dakuka tanafadin mlm munshiga ukku hankalin mlm sulaiman yatashi jikinsa yaduki rawa duk yarudema yarasa abinyi deeje ce tace mlm kasanar da jama.ar unguwa sukawo mana
8⃣ dauki Allah yasani niyyar taimako mukayi mlm yanafadin dole saimun sanar da hukuma kulada yaron da gawar bari na je nadawo kafin takara cewa wani abu yabazama yafice tatsugunna tana kallon yaron daketa wutsil wutsil cikin zani kyakkyawa gwanin bansha.awa son yaron yafara shigarta Lami taleko tana fadin yaya tahaihu ne tayi turus cike da tsoro tana kallon mahaukaciyar saita dafe kirji tanaci gaba da fadin badai tamutuba deeje wane bala.i kuke shirin kawomuna wlh babu ruwanmu takoma dabaya deeje tadaga kai tana harararta ranta abace amman tagaza cewa komai don takaici
9⃣tana nan zaune tsawon minti arba.in tajiyo karar jiniya tamike jikinta yana bari jin datake bata taba shiga police station ba amma yau ga motar police harkofar gidansu tana nansaiga mlm sunshigo dayan sanda ukku kowanne dauke da bindiga daya dagacikin su yakalli mlm sulaiman yana fadi mlm katabbata abinda kafada shine gaskiyar magana wlh babu kari ko ragi Allah yana kallona mlm yafadi dasauri har lokacin hankalinsa tashe dansanda yagirgiza kai yana fadin duk dahaka zamu tafi dakai da matarka danzamuyimaku wasu tambayoyi deeje tawaro ido tana fadin nashiga ukku don Allah yallabai kayimini rai wlh bantaba shiga irin wannan
1⃣0⃣motarba yakatseta kada kidamu hjy bawani abu zamuyikiba tambayoyi kawai zaku amsa jiyo karar zuwan motar yankwana kwana suka kuma rudewa haka nan akasanya mahaukaciya deeje rungume dayaron suka fice daga gidan cikin rakiyar yansanda Lami tana labe tana lekensu ta kofa tana dariya tana ganin sun fice tafara fadin Allah yakara maganinku masu neman suna kenan banda haka daga ganin mahaukaciya tana nakuda har wani kinkimota kukawo kamar kukukafi ubankowa imani koda yake ai neman sunane kuma kunsamu tamurguda hannu ta tafa acinya tana juya idanuwa sanda suka fice jama.ar unguwar sun fito cirko cirko ana kallonsu kowa da abinda yake fada mlm jibrin yashigo gida fakan fakan cike da tashin hankali yana kwalama matarshi kira Lami Lami
1⃣1⃣DAME AKE ADO ......Tafito daga daki dasaurinta tanafadin mlm lfy wannan irin kiran kamar zaka tsagan dodon kunne yakalleta cike datashin hankali yace jinayi ance yansanda sunzo gidanmu sunyasheku gabadaya Anyi police station daku wai antsinci gawa agidan tarike kugu tana kada kafa A.a bakarya bane gaskiyane saidai ba.abaka lbr dai dai ba andaitafi dayaya da deeja dansu suka debo ruwan dafakansu kamar yaya kinanufin yanzu shi yayan da deeje suna can wurin yansanda? Dagaske kenan Ansami gawar kaibakacin ribar zance wlh katsaya nagayamaka yanda Abin yafaru mana
1⃣2⃣DAME AKE ADO Baikoma tankawaba hartasanar dashi duk Abinda yafaru tadora dacewar danhaka nibaganin laifin yansanda wlh sunyi daidai kokai yayakagani? Yadansaki rai yana fadin nasha gayawa yaya wannan halin nasa watarana saiyaja masa masifa gashinan kuwa mutum yace kofada yaga anayi saiya raba can yaje yakarata idan naga abin yayi tsananani naje nasarwa da Abokinsa mlm Habu bani ruwa nasha nakoma kasuwa yakarasa magana yana haki
1⃣3⃣DAME AKE ADO Malam sulaimai da deeje suna zaune agaban tebur din DPO kusan awannisu shidda kenan apolice station din DPO yadaga kai yakallesu shikenan malam tamutu kada kadaina taimako domin ladanka yana gun Allah yanzu zaku wuce dayaron gobe zamu turo wasu jami.an namu zasu amsheshi amikashi gidan marayu Allah yasaka da Alkhairi Ran mlm yayi fari yamike daidai lokacin damatar tasa ta mike itama tana fadin babu damuwa ranka yadade dahaka sukabar ofis din deeje tana rungume da yaron suna isa gida deeje tadora amurhu tawanke yaron tas wanda yayi kuka haryagaji malam yasamo zam zam da 1⃣4⃣ DAME AKE ADO ...Dadabino akabashi yasha sannan ya kuma yasiyo madara irin tagari akajika masa da ruwan zafi yasha saigashi yakama bacci Auwalu da sani diyoyin deeje sai murna suke wai ansiyo musu yaro akasuwa sun sami kani mahaifiyar tasu dariya kawai take musu tana rungume dayaron dayake kuma shiga ranta duk bugun dakika mlm yadawo daga masallaci yataddata rungume dashi yayi dariya yana fadin Deeje uwa kenan ki ajiye dannan koyafijin dadin yin bacci tayi dariya tana kwantarda shi agado tace wlh mlm jinyaron nake kamar nice nahaifeshi yayi dariya yana zama sallamar malam jibrila daga bakin kofa takatse musu hirar tasu mlm sulaman yatashi dasauri ya leka yana fadin jibrilu yaya akayi ne? Free Mode See Photos
Facebook logo
Go To Home
Jamila Umar Tanko Books
DAME AKE ADO part2.
Jibrila yagyara tsayuwar sannan yace wani lbr nakeji yanzu gurin Lami danadawo wai ankaiku police station amman yaya ka kasa aikawa agayamani ai da na biku naji abinda yafaru yayi dan yake yana fadi gani nayi ba wata babbar bace ba shiyasanya ban Aiki maka ba amman yanzu komai yawuce da izinin Allah to Aishikenan Allah yakiyaye gaba amman dai yaya karage halin nan naka watarana zai iya janyo maka adaureka mlm sulaiman yayi murmushi yana fadin kayya duk Abinda da Allah yakaddarowa bawa babu makawa saiya sameshi Amman kuma dai yaya ance gidan da aka haifi shege masifu suna sauka acikinsa yanzu baka gudun abinda zaije yazo madaukakin mamaki yaziyarci mlm sulaiman yadinga kallonsa baki bude da ................. Dakyar yadaure yace A wanne hadisin ko ayar kaci karo da wannan batu Ya kama sosa keya na rashin madafa yasan halin yaya nasa sarai zai iya yimasa wankin babban bargo dan haka ya wuce dasauri yana fadin aishikenan Allah dai yasa ruwan sama yawanke mana daudar yabishi dakallo har yakule sannan yaja tsaki cike da taikici yakoma ...Dasafe tun Asuba Deeje tadora ruwan wanka ta wanke yaron tas tasanya masa kayan jarirai mlm yashigo tana rungume dashi tana bashi madara a filinboti ya kama kuwa yata zuka yakalleta tana dariya yace tomasu amsar yaron sun iso kishirya muwuce akaishi tadaga kai takalleshi nandanan hankalinta yatashi yakula dahakan danhaka yayi sauri yadauke kansa yafice GIDAN RAINON YARA Ankammala duk rubuce rubuce da dakaura hotuna harda na gawar Asma.u mahaukaciya mlm da deeje zaune gaban shugabar gidan tana tana musu godiya takirawo wata cikin ma.aikata data amshi yaron wanda harlokaci deeje take kankame dashi dan angama bincike ta goyeshi abaya ma.aikaciyar jinyar tayi tsaye kikam tana jiran deeje takwanto yaron amman taki mlm sulaiman yadan zungureta yana fadin kwantoshi mana deeje sai tamanne kafada suka zubamata ido da mamaki sai kawai tafashe muru dakuka mamaki yacika kowa agurin shugabar gidan takasa magana tana kallon ikon Allah koda yake takula dayanayin deeje tunda suka shigo bakuma yaune tafara ganin irin hakaba saidai amatsayinsu na.ama aikata bazusuturawa mutum da baisanya kansa ba dangudun azabtarda yaron nidai dan Allah Abarmini yaron nan tunda kunada su dayawa mlm sulaiman yadibeta damamaki Allah yasani abinda keransa kenan amman kuma baisaniba ko anayin hakan ba shugabar Hjy Amina tayi dan murmurshi gami da komawa takwanta jikin kujerarta tana fadin daina kuka malama deeje zamu iya barmiki yaron nan saidai akwai wasu sharudda da zamu gidayamiki 1⃣9⃣ wlh nayadda da duk sharadin da zaku gindayamani takatse shugabar cikin hanzari Atake anan shugabar tagindaya musu sharadin amsar yaron suka amince harda sanya hannu a rubuce sunrabu da shugabar akan duk wata guda zasu dinga kawo yaron anaganinshi da haka sukayi sallama cike da jin dadi suna tafe ahanya deeje takara kankame yaron tna dariya kai mlm da.ankwace yaron nan dasainayi jinya yaron dashi rai yake wlh yayi dariya yana fadin ke kam da baki taba haihuwa ba da anshiga ukku kin kankame yaro kamar zaki maidashi ciki to barka da mlm wane suna zakasanya masa kuwa Ta tambaya Aubakiji sunandana fadi gurin cike takaddunba koda yake lokacin kin rude aitinjiya da daddare nayi masa huduba da AHMAD 2⃣0⃣ idan Allah yakaimu ranar sunansa ta zagayo sai ayanka hakika ayi radin sunan A masallaci gurin shayawar ne dai nake tunani yanda za.ayi tunda kina dauke da cikin wata ukku bamu sani ba ko zaiyiwu kishayar da shi amman dai matambayi malaman Asibiti tayi ajiyar zuciya kuma kaga na shekara ukku rabona da haihuwa sai dai mu shayarda shi madara siyo madarar shanu yakama ka kenan kullum tana dariya to yaya na iya tunda Allah yabani da haka suka isa gida cike da nishadi lami tana jiyo sallamarsu takwasa da gudu tana lekowa sam basu kula da itaba tarike haba cike da mamaki ganin sun dawo dayaron abayan Deeje dan haka takuma tabbatarwa har cikin gidan taleka taga sunata shigowa dakayan arziki wanda hjy Amina tahado su da shi tayi musu Alkawarin zata dinga zuwa tana dubashi 2⃣1⃣ don Ta amshi Adireshinsu duk da sunce zasu dinga kaishi din sanda jibril yadawo yatadda Lami a cunkushe ya tambayeta abinda ya faru saita fitittike tana fadin sai dai azabi daya azaman gidan nan ko ni ko shegen yaron can sunfa dawo dashi dayaya zamu yadda murayu da shegen a gida yagyara tsayuwa yana kankance ido don Allah kada ki gaya mini zancen banza inace da safe suka tafi da shi kina nufin sun kuma dawowa dashi tagalla masa harara to zanmaka karyane ka shiga gidan nasu kagani mana kuma da alama da shirin zama ya dawo don nagansu da siyayyar kayan jarirai kala kala ya shuri takalmi cikin bacin rai yayi gidan yayan nasa ko sallama babu suna tsakar gida azaune deeje tanayiwa Ahmad gashin cibiya
2⃣2⃣ Malam sulaiman yadaga kai ya kalleshi da mamaki yana fadin lfy dai jibrilu kashigo babu ko sallama yasamu guri yazauna yana muzurai ramsa abace yace kayi hkr yaya rainane abace nashafa.a jinayi ance wai kadawo dashegen yaron nan me kuma yadawo yi? Ransa yabaci amman yadanne yace ba shege yakeba sunanshi Ahmad kuma yawuce wai tunda hargashi nan kana gani ana masa gashin cibiya haba yaya wanne irin tonon siline saikace baka taba haihuwaba idan karin ya'ya kakeso basaikaje kadauki nawaba ko kuma kaje kauye kadauko wasu ba Amman saika bige da dauko shege nagayamaka kada kakuma kiransa da shege kajiko kuma naki daukar naka dan ko kuma nakauye shidin dainakeso idan kuma kaine sama dani sainaji marar kunyar banza ..........2⃣3⃣ irin naka duk wani abu dazaka aikata na Alkhairi saiyazamana kaidashi kake gaba wannan yaron kasan iyakacin baiwar da Allah yayimasa to tsaya nagayamaka daga yau yashiga cikin 'ya'yana zan kuma rubuta wasiyya ko bayan na mutu araba dukiyata kashi shidda Abashi kaso daya don Allah baihalasta Wani yagaji wani bane ba danace yagajeni jibrilu yayi shiru cike da takaici don yasan halin yayan nasa akwai fada idan kataboshi danhaka yamike sumi sumi yang fadin Aishike nan nidaman inaguje maka illar da akace zama da shege yana kawowa ne inji ubanwa aihar yau kakasa kawo mini hadisi ko ayar datace hakan nakuma gayamaka kadaina Ambaton dana Ahmad dashege kajiko yakarasa ficewa yana gunguni babu yanda zaiyi
2⃣4⃣ malam sulaiman yacigaba dafada sokon yaro sai mace ta...


Read / Download DAME AKE ADO

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album