Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

📚 OGA HABIB 📚
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*


https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

TSARAWA DA
RUBUTAWA
FADILA SANI BAKORI(Faddy baby).

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CrrZExGxsLSGblRVfxdnj7

My Facebook group :Fadila Sani
https://m.facebook.com/groups/565235401564189/

ALHAMDULILAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH,
ALLAH INA GODIYA GAREKA DA KABAN IKON GAMA SO NE SILA LAFIYA.

OGA HABIB
YADDA NA FARA LAFIYA ALLAH KASA IN GAMA LAFIYA.

ABINLURA.
BANYI OGA HABIB BA DA NIYYAR CIN ZARAFIN KOWA BA.

GARGAD'I!
BANYADA BA BAN KUMA LAMINTA BA, WANI KO WATA YA CANZA MIN LABARI BA BATA RE DA IZININA BA, KO A JUYAMIN LABARI BA, YIN HAKAN KUSKURE NE BABBA, AKIYAYE!!.

SADAUKAR WA.
OGA HABIB DAGA FARKON SHI HAR K'ARSHEN SHI SADAUKAR WA CE GAREKI 'YAR'UWTA D'AYA TAR KAM DA DUBU, OGA HABIB KYAUTA CE GAREKI KIYI YADDA KIKE SO DA SHI, HASSANA SANI MPAPE ABUJA BARRISTER.


SAK'ON GAISUWA GAREKU ABIN ALFAHARINA.
YAYA SAIFULLAHI SANI MPAPE ABUJA.
BARRISTER HASSANA SANI MPAPE ABUJA.
AUNTY ZEE MPAPE ABUJA.
AMARYA MAMAN AMATULLAH MPAPE ABUJA.
AUNTY MARIYA FUNTUA.
AUNTY ZAINAB YAHAYA BAKORI.
SISTER HAFSAT YAHAYA
BAKORI.


GODIYA.
INA GODIYA GA MASOYANA A DUK INDA KUKE, BA KU DA TA HANYAR DA ZA KU NUNA MIN K'AUNA SAI TA HANYAR COMMENT D'IN KU.


DUNIYA KAMAR INUWARKA CE;DUK INDA KA TAFI ZA TA BI KA, AMMA IDAN KA TAFI NEMAN TA ZA TA RIK'A GUDU, KUMA BA ZA KA TAB'A CIM MA TA BA. WASU MUTNE KAMAR SUKARI SUKE A CIKIN RAYUWARKA. KO KA DAINA GANIN SU AMMA D'AND'ANONSU YANA NAN.
ALLAH YAYI MI KI RAHAMA MAHAIFIYATA.




Shafi na 1&5.


Bismillahir rahamanir rahim.


GARIN ABUJA.
Wani tabkeken Company ne, asamansa ansa,: SANAT YOGHURT.
Daga k'asan sunan kuma ayi rubutu da k'anan bak'i, kamar haka, :sanat yoghurt company , zone e apo Abuja.
tsaye nake ina kallan tsaruwar SANAT YOGHURT company, ina nan tsaye, sai naji wani yana cewa, "Barka da fitowa Oga Habib ". koda na juya dan ganin wannan wanda aka kira da Oga Habib.
Na makara sai dai motar da yashiga nabi da kallo, koda na duba motar da kyau sai naga, corolla S ce.
Motar nabi da kallo, motar black ce, mai pure white glass.
Gudu sosai motar ke yi.
Sunyi tafiya mai nisa sosai, dan har sun shiga garin kaduna.
Tafiya suke sosai, su biyu ne a motar Oga Habib, sai driver shi.
Habib cikin siririyar muryar shi, mai cike da izza, ya ce, "Bilya tsaya!.
D'an tsawa ce ya yi maganar, wanannan nature ne na Habib haka yake abisa lurar da nai me.
Bilya, cikin girmama Ogan shi, ya ce, "Oga Habib Lafiya zamu tsaya anan? kabari mushiga gari mana, kasan yanzu ba ko'ina ake parking ba".
Habib cikin tsawa, ya ce, "Bilya na ce kayi drup d'ina anan kana kawo min wasu Questions".
Bilya tsayawa ya yi, Habib ya d'auki faron da yasha ya rage ya fita da shi.
Bilya driver da mamaki, ya bi Habib da kallo, ya ce, "Oh wai dama gayannan fitsari zai yi ya ke min wani muzurai.
Habib da sauri ad'an tsorace ya dawo ya na haki alamun kamar yaga wani abun tsoro.
Bilya driver da sauri ya bud'e ma Habib burfin motar ya shiga.
Bilya cikin girmama ya ce, "Oga Habib lafiya kuwa? ".
Habib kamar ba zai magana ba, sai kuma ya ce, "Bilya gawar mutum nagani anjefar".
Bilya cikin tsoro ya ta da motar zasu ta fi.
Habib ya da ka mai tsawa yace, "meye haka?, baka ji abinda na ce bane!? ".Bilya driver cikin bin umarnin Ogan shi Habib, ya tsaya da motar, ya kalli Habib, ya ce, "Oga Habib zamu d'augawa ne a mota?, kasan fa yanzu rayuwa ba kamar daba, gaskiya ricks ne Oga mu d'auki gawar da...... ".
Tsawar da Habib ya yi ma Bilya ne, ya sa ya yi shiru.
Habib cikin d'aga murya, ya ce, "ka fita ka duba min ka gani".
Bilya fita yayi kawai dan bashi da yadda zai yi, amma a ainihin gaskiya a tsorace ya fita.
Bilya cikin tsoro ya fita ya dudduba amma bai ga wata gawa ba.
Bilya dawo wa ya yi, ya kalli Habib cikin girma, ya ce, "Oga Habib banga gawar kowa ba fa".
Habib tsaki ya ja, ya fito daga motar.
Habib na ta fiya, Bilya na binsa aba-abaya.
Habib kallan Bilya ya yi, yana nuna mai abinda ya gani, ya ce, "Can me ye? ". Da d'an k'arfi ya yi maganar. Yana nuna gawar mutum da yagani kwance agun.
Bilya cikin tsoro ya ce, "Oga Habib zamu fa jefa rayuwarmu cikin had'ar...... ".
Tsawar da Habib ya yi ma Bilya ce tasa ya yi shiru, ya kama bakinsa bai k'arasa fad'in abinda ya ke fad'aba.
Habib cikin b'acin rai dan ya tsani arik'a jayayya da shi, cikin fushi ya ce, "Your very stopped, ina maga kana quarrel da ni, Bilya baka da wani amfani Wallahi".
Idan da sabo Bilya yasaba da fad'an Habib. Hakan yasa Bilya cikin bin Umar nin Ogan shi yak'arasa inda gawar ta ke.
Bilya cikin al'ajabi ya ke, kallan gawar matashiyar budurwar, Bilya matsawa ya yi kusa da ita sai yaji kamar tana numfashi kad'an-kad'an.Hakan yasa Bilya dawo wa inda Habib ya ke tsaye.
Cikin girmamawa Bilya ya ce, "Oga Habib ba gawa bace,dan da alamun tana numfashi".
Habib batare da ya kalli Bliya ba, ya ce,"ka d'akkota ka shigo mu tafi".
Bilya da mamaki ya kalli Habib, amma gudun kar ya yi laifi yasa baice ko mai ba ya bi Umarnin Ogan nashi, ya je ya d'akko ta.
Habib tashi ya yi ya koma site d'in driver ya zauna.
Ita kuma Bilya ya shimfid'ar da ita a mazaunin baya.
Tafiya kad'an ta idasa da su Oga Habib kano.
Suna shiga kano sun yi tafi bawani sosai ba. Habib ya ce, "Bilya samu gu kai parking"
Bilya tsayawa ya yi, kamar yadda Ogansa ya Umar ce shi, ya ce, "Oga Habib mun tsaya".
Wata private hospital Habib ya nuna ma Bilya ya ce, "Bilya ka shiga hospital d'in nan ka kaita".
Bilya kamar zai yi kuka, dan shi a ganinsa idan ma tai mako Habib d'in ya ke son yi tom shi yi yi mana da kanshi ba sai ya bashi wahala ba.
Baliya badan ya soba ya d'akko wannan baiwar Allah da ke kwance kamar matatta ya shigar da ita hospital d'in.
Bilya na shiga aka amsheta.
Bilya kallan likitar ya yi, ya ce, "Likita dan Allah tare da Ogana muke, ki bata duk wata kulawa da ya ka mata zan dawo yanzu".
Likitar cikin mamaki ta kalli Bilya ta ce, "Haba bawan Allah ya za ai bamu sanka ba, ka kawo mana yarinyar da bamu san taka mai-man abinda ke damunta ba, kuma ka ce mana wai za kaje ka dawo. Gaskiya ammana irin haka da yawa anan kano kuma basu dawowa. gaskiya haka ba zai yuwuba ".
Bilya cikin rok'on likitar ya ce, "Karki damu Insha Allah ni zan dawo nai miki alk'awari". Likitar kallan Bilya ta yi ta ce, "sure". Bilya cikin tabbatar wa ya ce, "Yess am very sure insha Allah ".
Bilya number shi ya ba likitar ya ce zai dawo ba da dad'ewa ba.
Bilya fitowa ya yi inda ya yi parking d'in motar Oga Habib, ya shiga.
Habib bai tambayi Bilya ya sukai ba, shin tana da rai ko bata da rai make damunta, bai tambayi komai ba.
Shima kuma Bilya ganin bai tambaye shi ba yasa shima yaja bakinsa ya yi shiru.
Direct inda Oga Habib keda Meeting Bilya ya kai shi.
bliya na yi parking Habib ya sauka, hotel d'in da za su yi meeting d'in.
Lokacin da Habib ya shiga har sun gaggaji da jiran shi, dan harma sun fara fidda ran zai zo, in da shi Ka d'ai su ke jira dama.
Habib be fi hour d'aya da shiga taron ba ya fito ranshi a b'ace.
Habib cikin jin haushi ya bud'e murfin motar ya shiga ranshi da alamun b'ace ya ke.
Habib na shiga ya kalli Bilya cikin jin haushi, ya ce, "Jamu bar gurin nan aikin banza ai kin wofi".
Bilya da sauri ya sa ma motar key suka bar gurin.
Bilya cikin jin tsoro ya kalli Habib ganin ranshi kamar ab'ace ya ke, ya ce, "Oga Habib ina zamu".
Habib shiru ya yi ya yi banza da Bilya.
Bilya cigaba da tafiya ya yi batare da yasan ina zasu ba, so yake ya k'ara tambayar Habib amma kuma yana jin tsoro.
Wayar Habib ce ta yi ringing, Habib da sauri ya yi picking call d'in, dan ringing tone d'in mommy shi ce.
Habib cikin sakin fuska da murmushi, dan indai kaga Habib na waya yana murmushi tom mutum d'aya ce, wato Mahaifiyarshi.
Habib cikin sweet voice d'in sa, ya ce, "Mommyna kina lafiya".
Banji mai akaje ba daga can b'angaran sai dai naji Habib ya ce, "Mommy ina hanya fa, na kusa dan Allah kijirani mana".
Banji mai Mommyn Habib ta kuma cewa ba, sai ji nai ya ce, "Mommy ki barsu kawai, ni dama nasan bawai maganar kirki bace dan dai ma kin matsamin ne shiyasa nazo, Mommy wai fasaha suke so mu saida masu, suma su rik'a irin yoghurt d'in mu ak'asarsu, Wallahi Mommy tsabar haushi ko magana ban musuba nabar gun, dan dana san wannan maganar ce Allah Mommy da banje ba".
Can b'angaran bajin me ake cewa nake yi ba, sai dai naji Habib nai mata fatan Allah ya dawo da ita lafiya, kuma dan Allah karta dad'e kamar yadda ta yi wannan karan.
Bilya ko jin wayar Oga Habib ce ta sa ya fahimci, Habib yagama abinda ya kawo shi kano, yanzu Abuja zasu nufa.
Hakan yasa Bilya ya kama hanyar Abuja.
tafiyar 4 hour's ta kai su garin Abuja.
Bilya direct gida ya yi da Habib dan ya san ba zai koma Company ba, in dai ya yi tafiya ba ya komawa sai washe gari.
Bilya na aje Habib , Ya koma Company, dan Bilya aiki biyu ya ke ma Habib, yana aiki a SANAT YOGHURT.
Sanan kuma shike driving d'in Habib duk in da Habib zashi.
Albashi mai tsoka Habib ke biyan duk mai aikacin da ke aiki ak'ark'ashin sh. Wannan shine da lilin da yasa kusan duk suka jure cin mutuncin da Habib ke masu.
Bilya bayan ya koma SANAT YOGHURT COMPANY har an tashi ya koma gida, da ya ke gidan Oga Habib ya ke zaune.
Bilya bayan ya koma gida ne wayar shi tai ringing yad'aga, daga can b'angaran, fad'a sosai ta ke, ta ce, "Haba ya za ai kabarni da yarinya mara lafiya gashi ta farkaba tun d'azu amma kuma baka dawo ba".
Bilya zaune ya tashi daga kwancan da ya ke, dan ya manta sham da maganar, wata Yarinya.
Bilya cikin damuwa alamun shima bai ji dad'in haka ba, ya ce, "Ayyah dan Allah ki yi hak'uri Wallahi na manta sham. kuma Wallahi yanzu haka ina Abuja, amma ki yi hak'uri da safe zan ma Ogana magana".
"Gaskiya ni ba inda zan kaita, sai dai in tasan in da zata. Cewar likitar.
Bilya kashe wayar ya yi, ya ce mata dan Allah yana zuwa ta bashi minti d'aya.
Bilya cikin fargaba dan yasan Oga Habib ya hana shi kiran shi in dare ya yi.
Habib na kwance kan makeken gadonsa na alfarma sai game ya ke awayar shi dan shi Mayan game ne. Habib na cikin game kira ya shigo wayar shi.
Habib k'in picking call d'in ya yi, har sai da Bilya ya yi mai kira Uku.
Habib d'aga kiran ya yi ya, ya kanga akun nan shi, yana sauraran abinda Bilya zai ce masa.
Bilya ko cikin tsoran halin Ogan nashi da ba wuya ka b'ata mai rai, ya ce, "Oga Habib dama Yarinyar da muka tsinta ce d'azu, wadda muka kai hospital , tom shine likitar da naba Yarinyar ta kirani, yanzu , akan in zo ta far.......... ".
Habib cikin tsawa ya katse, Bilya ya ce, " Bilya kana ko da full sense, awannan lokacin zaka kirani kana min wannan maganar!?, Yarinya kuma da ka ke magana,duk yadda kaga dama kayi da ita bai shafan ba, karka kuskura ka sake min magana akanta!. ".
Wata zufa mai zafi ce ta fara karyoma Bilya. Ko tunanin mafita Bilya bai fara yi ba, kira ya kuma shigowa wayar shi.
Bilya koda ya duba yaga Number likitar nan ce, Bilya cikin rashin sanin abinda zai ce mata ya yi picking d'in call d'in.
Tun kafin ta yi magana, Bilya ya rigata da cewa, " Ki yi hak'uri kinga yanzu dare ya yi ba damar in zo Kano, amma zuwa gobe zaki ganni".
Likitar jin abinda Bilya ce yasa ta kashe wayarta.
Bilya sosai abinda Habib ya yi mai ya b'ata mai rai, taya zai ta kuramai ya d'auki ya rinyar, yanzu kuma yazo yana nai man lik'amai bala'i.
Bilya shiru ya yi, ya na nazari, ya ce, Tom ni yanzu ko ma kano nace zan je in d'akko ta ina zan kaita.
Bilya da sauri ya ba kanshi amsa da cewa, Wallahi sai dai in barma likitar ita, idan ma ta sake kirana bazan d'agaba.
Bilya blocking number likitar ta ya yi.
Cikin jin dad'in shawarar da yankema kanshi bacci ya kwasheshi.
Washe gari misalin k'arfe goma na safe, kamar yadda Habib ya saba sai ya je office sannan ake kai mai abin break fast , haka aka yi.
Bilya ko dama so ya ke ya yi magana da Oga Habib , amma bai samu dama ba, dan tunda ya d'akko shi da safe ya ke waya har suka isa company bai dai na ba. Wanan shine ya hana Bilya yi ma Oga Habib maganar Yarinyar.
Ga shi kuma tunda safe likitar ta da mai da kira, dan tana ganin ya yi blocking Number ta ta kira shi da wata Number. Hakan yasa Bilya ya ke son ganin Ogan nashi sosai.
Gashi in dai Habib ya shiga office d'in shi ganin shi na da wuya sosai, sai dai in Allah yasa ya fito.
Bilya na nan tsaye yana nai man hanyar da zai bi yaga Oga Habib , Sai ga masu kawo mai break fast sun iso, tattawan mata ne guda biyu, amma ba wai sun tsufa bane sosai.
Bilya na ganinsu cikin da bara, ya yi gurin su, ya ce, "Baba lami sannunku da k'ok'arin kula da Ogan mu ".
Tsofaffin cikin girmamawa su ka amsa ma Bilya.
Bilya kallan Baba Lami ya yi, ya ce, "Baba abin k'arin Ogan mu ne ko? ". "Eh Bilya shi ne".
Suka bashi amsa.
"Baba ku kawo dan Allah in kai mai dama ina son magana da Oga Habib Wallahi amma narasa yadda zan yi".
Wadda ya kira da Baba lami, wayayyar tsohuwa, murmushi ta yi, ta ce, "Tom Bilya ka dai son ko mai,ka san babu wanda Hajiya turai ta yadda ya ba Oga Habib abinci hannu da hannu sai mu, tom kuma dai kasan Oga Habib yadda ya ke abu kad'an za kai mai babu ruwansa da bashi ya d'auki mu aiki ba, yanzu sai ya da katar da Mutum aiki ba ruwansa, dan haka kayi hak'uri, amma idan nashiga zan gwada mai magana kana son ganinsa k'ila idan akaci sa'a yabari ka shiga".
Godiya Bilya ya yi ma Baba lami. Sannan suka shiga.
Su Baba lami sun dad'e atsaye suna jiran Comment. Amma shiru.
Habib sai da ya gama abinda ya ke sannan ya basu izin shigowa.
Bayan sun Baba lami sun kaima Habib abin break fast ne. Har za su fita, Baba lami ta yi k'arfin halin bada sautin Bilya.
Baba Lami cikin girmamawa kamar yadda ta saba ba Habib d'in, ta ce, ", Oga Habib, dama yaran nan ne, driver ka, Bilya ya ke Son magana da kai wai".
Habib batare da ya kalli Baba Lami ba, ya ce, "Ba yanzu ba".
Baba Lami fita ta yi, tana alawadai da dukiyar da zata sa Mutum ya d'auki kan shi haka, kamar yadda Habib ya d'auki kan shi.
wata zuciyar ta ce mata tom kodai kyan shine yasa ya ke yin haka ne.Nan dai su Baba Lami suka fito suna mai Allah wa dai da ji da kai da tak'ama irinta Habib.
Bayan su Baba Lami sun fito ne.
Bilya ya k'arasa in da suke da saurinsa ya ce, "Yauwa Baba ya ce in shiga ko? ". Baba Lami cikin nuna rashin jin dad'in ta, ta ce, "ka yi hak'uri Bilya kasan yaron nan dama ba wai mutunci gare shiba, bai ganin kowa da Mutun ci, Wallahi ya hana. Sai dai ka yi hak'uri idan ya fito, ko in za ka kaishi wani gun".
Bilya cikin d'an bacin rai ya ce, "Wallahi Baba Oga Habib na mulkamu yadda ya ke so, amma babu da muwa, ko mai nada lokaci, akwai lokaci".
Baba Lami ta fiya su kayi bayan sun ba Bilya Hak'uri.
Bilya ko yana nan tsaye yana ganin fitowar Habib amma shiru, har akai Sallar azahar.
Bilya na nan tsaye kira yak'a shigowa wayar shi tai ringing, Bilya na dubawa yaga Number likitar ce, sosai gabansa ya fad'i dan k'aryarsa ta k'are.
Biya na d'auka ya ce, "Ki yi hak'uri dan Allah nima banso haka ta faruba, ko ba komai na k'arya alk'awarin da nai miki, amma Wallahi duk abinda kika ga ya faru ba laifina ba ne laifin Ogana ne, amma bari yanzu in turomiki Number sa, dan Allah ko kinkira bai d'aga ba karki gaji ki ta kira zai d'aga".
Bilya na kashe kiran ya tura mata Number Habib.
aiko tana ganin Number ta danna mata kira, dan bata son yau ta sake kwana mata agida.
Habib ko na zaune a Office d'in shi yana aiki a laptop, kira ya shigowar shi.
Habib ko duba Number bai tsayiba ya ci gaba da aikinsa. Ita ko da yake taji abinda Bilya ya ce mata, hakan yasa taita kira.
Habib cikin jan tsaki ya d'aga kiran ya sa akunne, yana sauraran mai magana.
Ita ko likitar tana jin and'aga kiran ta ce, "Ranka shi dad'e dan Allah, kuzo ku amshi amanar da kuka ban dan Allah ". Habib cikin rashin fahimtar maganar, ya ce,"Wrong Number ". Yana fad'in haka ya katse kiran.
Likitar ko bata gaji ba k'ara kira ta yi, cikin b'acin rai ta ce, "Oh wai kunyi satar Yarinyar ne kuke tsoran asirinku ya tuni, koko ku 'yan kidnappin...... ".
Habib cikin daka tsawa ya tsayar da ita, yana kunfar baka. Magana ya ke son yi ya kasa, kawai sai ya kashe wayar shi baki d'aya, dan shi harga Allah ya manta wata yarinya da suka kai hospital.
Bilya ko tunanin ko anda ce ne, yasa yakira, likitar dan ya ji yadda su kai da Habib.
Likitar cikin b'acin rai ta ce,ma Bilya "Karka rainamin hankali malam, yarinya kuma ku kuka sani, amma daga yau na gama kwana da ita".
Bilya hak'uri ya ba likitar sosai sannan ya ce, mata,"Wallahi ba maganar wasa gobe zai yi samma kon zuwa kano d'in ". Ai ko haka akayi Bilya tun da daddare ya nemi permission gurin Ogan shi, akan tafiya kano.
Washe gari da wuri Bilya ya tafi kano, hakan yasa 12:00pm a kano tai mai.
Bilya bacin ya biya likitar hak'uri Sosai ya ba ta.Sannan ya zauna yana jiran fitowar 'yar tsuntuwar tasu, shiga Ogan shi, wanda shi ya ma manta da batunta.
Bilya na nan zaune 'Yar tsuntuwar su ta fito sanye ta ke da wata doguwar riga ta atamfa wadda likitar ce ta bata dan ganin bata da kaya, yasa likitar ta bata a tamfar.
Bilya kallanta ya yi, sannan ya ce, " 'Yan mata ke 'Yar wana gari ce, yanzu in kaiki gidan ku, dan mu ahanyar mu ta zuwa kano muka tsince ki".
Matashiyar budurwar da bazata haurama shekara goma sha bakwai ba.
Cikin siririyar muryarta ta ce, "Ni marainiya ce, bani da kowa, dan Allah ka tai ma ke ni".
Bilya da tausayi ya ke kallanta, dan shi aganinshi tabbas marainiyarce. Bilya shiru ya yi, dan yasan bai da in da zai kaita.
Ito ko Yarinyar ganin Bilya ya yi shiru alamar ba zai tai maka mata ba, ya sa, ta ce, "Dan Allah katai makan Allah banda kowa".
Bilya cikin tausaya mata ya ce, "zan tai make ki ki, amma tai makon ba mai tsawo bane, zan tai make ki ne kafin Hajiya turai ta dawo,kuma ni ba nan nake ba Abuja nake kin yarda zaki bini?, Sannan kuma duk sanda Hajiya turai ta dawo zaki kama gabanki , kin yarda? ".
Da sauri ta ce, "Eh na yarda na godee.
Bilya tashi ya yi Yarinyar na binshi aba suka je in da ya yi parking d'in motarsa da Ogan sa Habib ya yi masa kyautarta, suka tafi. Suka kama hanyar Abuja .
Kasan cewar Bilya yana gudu sosai da mota, hakan ya sa, ana Sallar magriba suka shiga gida.
Allah ko ya tai maki Bilya sosai dan lokacinda suka shiga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment