Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD



Tofa ananne Naseer din yake fada masa cewar.

“Ajiyan ankai Malam din Zanna Hospital, amma kuma an sallamosu Yanzu dai Malam din yana gida, kuma babu laifi jikin da d’an sauki. “

Kai Rayyern din ya jinjina, tare da cewa Naseer din ya turo masa adireshin gidan Malam din zaizo anjima.

“To.” Naseer din ya fada cikin minti kadan kuwa ya turowa Dr Rayyern din, da text message na address din gidan Malam Mai-nasara.

12: am dai-dai Rayyern ya kammala duk wani abu abunda yakeyi acikin hospital din.

Haka ya fito daga cikin office dinnasa yana taku cikin nitsuwa da kuma zarransa dake kara bayyana kwarjininsa da haiba na cikakken da na miji.

Kaitsaye compound din asibitin ya nufa, yana zuwa kuwa ya shige cikin motarsa batare da bata lokaci ba, driver yaja motar suka fice daga cikin asibitin gaba daya.

Bayan sun hau titi ne kuma drivern ya juyo yadan kallasa, kana aladabce yace.

“Ranka ya dad’e Ina muka nufa?.”

“Hausawa sabon titi.” Ya fada atakaice.
Tare da sanya hannu ya zare glass din dake manne a idanunsa.

A dai-dai wannan lokacin kuwa Ramadan Riyyam da kuma Naseer ne, acikin motar Ramadan din kirar Range rover velar 2019, inda suma kaitsaye suka nufi Unguwar ta Hausawa sabon Titi, wanda suna tafiyar ne kuma bisa jagoran Naseer.


After some 20mn suka iso gaban wani gate din makeken gida mai tsananin kyau da girma.

Wanda kuma yake nanne gidan Malam Mai-nasara.

Horn Ramadan dake driving ya danna.

Jin karan horn dinnasa ne kuma yasa maigadi, Dan lekowa ganin dalleliyar motar da yayi ne da kuma Naseer a gaba ne yasashi karasawa da hanzari ya wangale babban farin gate din.

Wanda hakan ya bawa Ramadan daman tura kan motar tasa ciki.

Wanda shigansu cikin gidan kuwa. yayi dai dai da wani irin masifeffen bugawar zuciyoyin Riyyam-nsra da Ramadan.

Kokarin maida gate din maigadin yasomayi saidai kuma ganin wata dakekkiyar motar again BMW ta faso kaine, yasashi wangale gate din.

Inda matukin motar ya tura hancin motar ciki.

Wanda saukan tayoyin motar acikin gidan, yayi dai-dai wani irin azabebben harbawa da zuciyar Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara yayi.

Cikin wani irin matsanancin faduwar gaban da yakeji, da kuma dukan da zuciyarsa keyi ya bud’e idanunsa inda ya saukesu A...!




Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻‍🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻‍🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻

By
*GARKUWAR FULANI*







📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 10
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


*FREE PAGE ne*

*Na kuɗine littafin Special Group 1k ƙaramin group 500 ne kacal, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, ko kuma ki sai katin MTN ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp*


Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻‍🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻‍🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻


Akan motar su Ramadan, wanda tuni Naseer ya fito daga cikinta, Yayinda Ramadan da Riyyam ke kokarin fitowa suma.

Tsumammun eyes d’insa masu dauke da wasu sinadarai na musamman ya lumshe, tare da sanya hannu ya dafe dai-dai saitin zuciyarsa.

“Yah Allah kabani nutsuwa, k’arfi da kuma k’warin guiwa ako da yaushe!”.
Yafad’i hakan acan k’asar zuciyarsa dake harbawa da sauri-sauri.
Kwata-kwata baisan meyasa agaba d’aya y’an kwanakin nan, zuciyarsa ke yawan harbawa da k’arfi ba.
Saidai kuma koma meye yana fatan ya zame masa alkhairi.

Bud’e murfin motar yayi ahankali tare da zuro kyakyawan k’afafunsa waje.

Dai-dai lokacin da ya gama fitowa acikin motar kuwa, su Ramadan da Riyyam suka k’araso.

Riyyam-nsra kuwa da murmushi ya kasa buya akan fuskarsa ne yace.

“Laa Hamma Rayyern kaima ka iso?”

Kai Rayyern din ya jinjina masa alaman.
“Eh.”
Naseer kuwa dake tsaye agefe, wayarsa ya zaro tare da dannawa lambar Uncle Mustapha (Kawunsa, yayan mamansa) kira.
Bugu daya kacal kuwa Uncle Mustapha ya d’aga wayar.

Jin an d’aga wayanne kuma yasa Naseer cewa.

“Uncle Mustapha gamu nan cikin compound tare da Dr. Rayyern din dana gaya maka cewa zaizo ya duba jikin Malam.”

Uncle Mustapha dake zaune acikin falo, kuwa saurin mikewa tsaye yayi, batare kuma daya katse wayan ba yace.

“Masha Allah to Naseer ka shigo dashi mana, ku shigo ku shigo.”

Yanayin yanda yayi maganar yana me nufar hanyan fita daga cikin falonne kuma, yasa sauran yan uwansa dake zaune acikin falon suka dan kalleshi.

Daga waje kuwa Naseer ne ya kalli Rayyern din, hade da cewa.

“Hamma Rayyern mu shiga..”

Bai gama rufe bakinsa ma baiyi ba, saiga Uncle Mustapha d’in ya fito, fuskarsa dauke da yalwatacciyar murmushi ya soma takowa inda su Rayyern din suke.

Idanu Rayyern da kuma Ramadan suka ɗan zuba mishi.

Kamar kuwa yanda suka zuba mishi idanu, haka shima ya zuba musu nashi idon, musamman akan Rayyern da kuma Riyyam, wani irin kallo yake musu mai dauke da mamaki, da kuma yanayi mai bayyana alhini., ciki kuwa harda fuskar Ramadan da yakewa kallon ya taɓa sanin mai irin fuskar farin sani.

Isowar Kawu Mustapha’n kusa da sune kuma yasa, duk tunanin da suke suka tsaya cak.
Hannu Rayyern ya mik’awa kawu Mustaphan, wanda shima ya mik’o masa nasa hannun fuska asake, sukayi musabaha.
Bayan sun gaisa da Rayyern dinne kuma, Kawu Mustapha’n ya bawa su Ramadan da Riyyam-nsra hannu suka gaggaisa.

Cikin kuma yanayin dake bayyana zallar farinciki da mutum tawa, Uncle Mustapha’n ya dubi Rayyern, kana atausashe yace.

“Masha Allah Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara barkanka da isowa.
Cikin ikon Allah Jiya iwarhaka munata fama da neman damar yanda za’ayi muganka, sai gashi kuma yau kaida kanka ka tako k’afarka izuwa inda muke, kai Masha Allah sannunku ku iso mu shiga daga ciki.”

Murmushi Rayyern yayi kana anutse yabi bayan, mutumin da ayanzu kawai ya shaida da karamcinsa.

Su Ramadan ma rufa musu baya sukayi, Yayinda Riyyam ke tafiya yana k’arewa katafaren gidan kakan abokin nasa kallo, wanda aka matuk’ar k’awatasa, kasancewar kuma gidan nada part-part da yawa ne, shiyasa ya zama kamar wani mention, Yayinda Kota ina dake cikin gidan, aka cikasa da shuke shuken korayen trees.

Isowarsu bakin kofar da zai sadaka da babban falon dake cikin gidanne, yasa Rayyern d’an lumshe idanunsa, saboda hakan yaji harbawar da zuciyarsa keyi na sauk’a, Yayinda zuciyar tasa kuma keyi sanyi.

Haka kuma yakejin wani irin abu na ratsa cikin tafukan hannaye da k’afafunsa.

Kasancewar kuma shike bayan Uncle Mustapha dinne, yasa shiyayi na biyun shiga cikin falon, da girmansa yayi a had’a manya manyan faluka guda biyu awaje daya.

Taka k’afarsa ta dama da yayi acikin falon kuwa, shiya sanya shi jin wani irin sanyi na game duk jikinsa.
Ajiyar zuciya ya sauke ahankali, wanda yayi dai-dai da sauk’e ajiyar zuciyar Ramadan da kuma Riyyam-nsra suma duk alokaci daya.
Kamar kuma yanda Rayyern din yaji azuciyarsa, haka suma sukaji.

Shigowarsu cikin falonne kuma, yasa gaba d’aya ahalin Mai-nasara da y’ay’a da kuma jikokinsa dake kewaye dashi, duk suka d’ago kai suna kallonsu.

Atake kuwa tsananin mamaki da tu’ajjudi ya bayyana akan fuskar wasu manya daga cikin mazauna falon.
Inda suka kafe su Rayyern din da ido, basa ko k’yaftawa, hakan yafaru ne kuma saboda wani tsananin kama da suka hango.

Kawu Mustapha ne yadanyi murmushi saboda Kallon da yaga y’an uwannasa nayiwa su Rayyern, wanda kuma shima yasan dalilin da yasa y’an uwannasa ke kallonsu haka.

D’an juyowa yayi ya fuskanci y’an uwannasa cikin kuma bayyana farin cikinsa yace.

“Manyan bak’i mukayi, domin babban Doctor din da ya shahara, ya kuma yi kaurin sunane da kansa yazo dan duba Malam, Wannan shine Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.”

Yakai karshen maganan yana meyi musu nuni da Rayyern dake tsaye.

Ajiyar zuciya suka sauke gabaki d’ayansu tare kuma da had’a baki wajen yiwa su Rayyern din iso.

Karasa shigowa cikin falon su Rayyern din sukayi, kana kuma cikin girma da mutumtawa Rayyern ya shiga bawa, manyan mazan dake zaune acikin falon hannu suka soma gaiggaisawa.
Kowannensu fuskarsa dauke da murmushi.
Bayan kuma sun gama gaisawa da Rayyern dinne, su Ramadan suma suka matso suka gaggaisa dasu.

Yayinda Rayyern kuwa ahankali ya sauk’e idanunsa akan fari kuma kyakkyawan Dattijon dake kwance, wanda ayanzu ya soma d’an yunkurin tashi, musamman saboda jin shigowar su Rayyern din.
Dattijo ne mai matuk’ar kamala, mutumci da kuma haiba, haka kuma duk da yana da yawan shekaru da y’ay’a, amma hakan baisa tsufansa ya yawaita ba sabida hasken Addini da riƙo da ibada.

Idanu Rayyern yadan lumshe tare kuma da budesu alokaci guda, yana me ambaton sunan Allah da ya sauk’ar masa da wata iriyar nutsuwa, acikin y’an mintunonin da basu wuce 5 ba.

Su Uncle Mustapha kuwa ganin Malam Mai-nasara dake kishingid’e akan lallausa kuma tattausan sofa, na kokarin tashi zaune ne, yasa cikin tsananin kulawa da kuma kauna suka taimaka masa ya tashi zaune.

Idanu Malam Mai-nasara din ya zubawa kyakkyawan matashin saurayin dake dan nesa dashi wato Rayyern.
Wanda kuma shima Rayyern din kallonsa yakeyi.
Yayinda acikin zuciyarsa yakejin wani irin sanyi, da kuma rauni mai tsananin gaske.
Ga kuma wani abu da yakeji na game dukkan mashigan ramin iska dake jikinsa.
Yanaji ajikinsa tamkar wata duniya ce sabuwa ya shigo.
Yayinda Ramadan da Riyyam dake bayansa suma sukejin thesame irin abunda Hamma Rayyern dinnasu yake ji.

Wanda kuma bawai iya sukad’aine sukejin hakan ba, harda shi kansa Malam Mai-nasara, domin kuwa har izuwa yanzu ya kasa dauke idanunsa daga kan Rayyern.
Sannu ahankali kuma ya d’aga hannunsa tare dayin alama akan Rayyern d’in yazo kusa dashi.

Aikuwa Rayyern din kamar jira yake, cikin nutsuwar da ya zame masa jiki, ya matso kusa da Malam din sosai, hakanne kuwa ya bawa Malam din daman kamo hannun Rayyern d’in ya rik’e acikin nasa.

Nannauyar ajiyar zuciya mai sauti suka sauƙe atare shida Rayyern d’in, saboda had’ewar hannayensu waje d’aya shiya haifar da daidaiton bugun zuciyoyinsu.

Kai Dr. Rayyern ya d’an rank’wafar cikin kuma muryarsa mai tsananin taushi, dake bayyana nitsuwa da mutumtawarsa ga Dattijon mai tsananin karama a idanunsa yace.

“Malam barka da rana, ya ƙarfin jikin naka?”

Idanu Malam Mai-nasara ya lumshe tare dajin wani irin sanyi acikin zuciyarsa, wanda lokaci guda ta d’auki soyayyar Rayyern din ta ajiye awani waje na musamman.
Tabbas fuskar Rayyern din ta ratsa shi, Yayinda ta kuma so tono masa wasu abubuwa da suka faru a shekarun baya masu yawa.

Sake rik’e hannun Rayyern din da kyau yayi, tare da cewa.

“Alhamdulillahi jikina da sauki, kaine Dr. Rayyern Basheer Muhammad Mai-nasara ko?”

Kai Rayyern ya jinjina masa, tare kuma da cewa.
“Eh Malam ni ne Dr. Rayyern Basheer Muhammad Mai-nasara.”

Ya kare maganar yana me fadada murmushin dake kwance akan fuskarsa, tayaya ma zai iya boye farincikin da yake ciki ayau din? Bayan gashi ga mutumin da yake matuk’ar so da kauna, fiye da duk sauran Malama’n da yake sauraran wa’azinsu, Dattijon da yake son gani akullum, kana Dattijon dako kallonsa yake acikin tv ko laptop yakanji sanyi acikin zuciyarsa.

“Alhamdulillahi! Masha Allah!! Lallai godiya ta tabbata ga Ubangijin talikai!!!”

Malam din ya fad’a adai-dai lokacin daya sauke idanunsa akan Ramadan da kuma Riyyam, wanda suke gaidashi.

Fuskarsa cike da tsananin mamaki ya amsa musu, tare kuma da dawo da kallonsa ga Rayyern dake zaune agabansa, har yanzu kuma suna rik’e da hannun juna.

Rayyern kuwa ganin irin Kallon da Malam din keyi masa ne, yasashi yin ƙasa da kanshi.

Malam Mai-nasara kuwa, fuskarsa dauke da mamaki yace.

“K’annanka ne?”

Kai Rayyern din ya jinjina, cikin halinsa na girmamawa kuma yace.

“Eh k’annena ne, wannan Ramadan, k’aramin kuma shine Riyyam.”

Idanu Malam Mai-nasara yadan lumshe hade kuma da jinjina kansa, Cikin yanayin gamsuwa kuma yace.

“Masha Allah. Allah Ubangiji ya d’ayyabaku ya kuma ci gaba da rayaku cikin aminci dajin dad’i amman Riyyam kuma sunane cikekke!?.”

Da “Ameen.” Gaba d’aya falon suka amsa.
Kana Ramadan da Rayyern kuma suka ɗan kalli, Riyyam-nsra.
Murmushi ya ɗanyi kana yace.
"Cikekken sunan *Zakariyyah* ne".
Murmushi Malam dasu Uncle Mustapha sukayi, wato sunan gayu ko?.
Malam yace cikin barkwanci.
Murmushi ya kumayi tare da gyaɗa mishi kai.

Gyara zama Rayyern yayi, tare da fuskantar Dattijon, kana atausashe yace.

“Malam yanzu inada inane yake maka ciwo? sannan yakakejin yanayin ciwon naka idan ya tashi?”

Idanu Malam Mai-nasara yad’an lumshe, tare kuma da tankwashe kafafunsa waje daya.

Ahankali kuma yace.

“Sau dayawan lokuta nakanji ciwon kaine kawai maitsanani, sai kuma jiri amma ba wani mai yawa ba, baya ga haka kuma sai k’afafuna da idanuna wanda nakejin watarana sunayi min nauyi, da kuma zazzab’i, amma dai yanzu kam Alhamdulillah jikin nawa isashshen k’arfi ne kawai babu.”

Ajiyar zuciya Rayyern ya sauk’e, tare da kuma gyara zamansa, kana anutse yace.

“Eh kamar dai yadda su Dr Sulaiman suka shaida min cewa.
Hawan jini da kuma ciwon sugar ne ke damunka Malam a binciken da sukayi maka, kuma hakanne.
Domin shi yawan ciwon kai da kuma jiri hadi da zazzab’in da kakeji duk alamane na hawan jini, sannan kuma shi yanayin ciwon kan yakan iya sauyawa, domin watarana zakaji ciwon agefen kanka ta b’ari d’aya ne, watarana kuwa zakaji ciwon kan asaman goshinka ne, wanda idan yayi karfi har yakan iya sauk’owa ya rik’e jijiyoyin idanun mutum, wannan duk cases ne da hawan jini kan haifarwa, shi kuwa nauyin da kakejin k’afafu da kuma idanunka nayi da yawan haɗa zufa, suma alamace ta ciwon sugar, wanda kuma suma bako da yaushe ne suke tashi ba, domin zaka iyajin hakan da safe, kafun zuwa rana kuma sai kaji abun ya lafa, baya ga haka kuma zaka iyajin hakan da yamma idan maraice ya rufa, sannan kuma akwai yawan fitsari da zakaji kanayi akai akai, koda kuwa ace baka sha wani ruwa mai yawa ba da jin kamar wani abu na bin jikinka...”

D’an numfasawa yayi kana ahankali ya sake rike hannun Malam Mai-nasara daya zuba masa idanu yana mai gyaɗa mishi kai alamun duk abinda ya faɗa hakane.

Atausashe yace.
“Insha Allah zaka samu sauki Malam, sannan kuma ciwon naka bai wani zama abun tashin hankali ba, saboda mafi akasarin mutane suna samun hakan idan girma ya cimmusu, kamar dai kai ayanzu daka tara manyan y’ay’a da jikoki, akwai kuma magunguna da zan rubuta maka, wanda zasu taimaka k’warai wajen kawo maka Sauk’in ciwon, sannan kuma akwai kalolin abincin da ya kamata ace su zakana ci, saboda zasu bada nasu taimakon sosai wajen Inganta lafiyar jikinka.”

Gaba d’aya falon kai suka jinjina cike da gamsuwa akan abunda Dr. Rayyern din ya fad’a.

Shikuwa Dr.Rayyern abun rubutu ya ciro daga cikin aljihunsa, tare da wata yar farar takarda.
Rubutu yayi asaman takardar bayan kuma ya kammala rubutun ne yayi sign acan k’asan takardar.

Alhaji Ibrahim wato babban dan Malam Mai-nasara din dake gefe kad’an ya mik’awa takardar, tare da cewa.

“Way’annan sune magungunan da ya kamata yana shansu a koda yaushe, Insha Allah zai samu lafiya nan bada jimawa ba.

Karb’an takardan Alhaji Ibrahim din yayi, tare da yiwa Rayyern d’in godiya maitarin yawa.

Saidai kuma baikai ga ida godiyar tasa ba, muryarsa ta mak’ale a kasan makoshinsa, sakamakon daura idanunsa da yayi akan sign din da Dr. Rayyern din yayi acan kasan paper’n.

Idanu ya k’urawa sign din cike da ɗan mamaki hadi da al’ajabi, ya d’ago ya kalli Baban nasu, wato Malam Mai-nasara da kuma sauran y’an uwansa.

Cikin tu’ajjudin da yake ciki dinne kuma direct ya mikowa Malam Mai-nasara din takardan.

Aikuwa Malam Mai-nasara na karb’an takardar idanunsa suka sauk’a akan signing din dama salon rubutun kanshi.

Cike da mamaki wanda har saida ya kasa b’oye hakan ya d’ago ya kalli Rayyern.

Rayyern kuwa da Sam bai fahimci komai adangane da irin Kallon da yaga sunayiwa takardar ba, kwata kwata sam baidamu ba.

Saima juyowa da yayi ya kalli Ramadan.
Cikin kuma bada umarni yace.

“Yauwa Ramadan yanzu amshi takardar sunayen magungunan Malam ɗin kaje ka d’auko masa a pharmacy.”

Kai Ramadan ya jinjina tare da cewa.

“To.”

Cikin abunda bai wuce 2 minute ba kuwa Uncle Mustapha ya miƙawa Ramadan takardar sunayen magungunan.

Hakan yasa batare da wani b’ata lokaci ba, Ramadan din ya juya ya tafi, dan d’aukowa Malam din magungunan da zai nasha.

Bayan fitar Ramadan dinne kuma, Naseer ya kama Hannun Riyyam-nsra suma suka fice daga cikin falon.

Haka kuwa mutanen dake cikin falon suka dinga fita daya bayan daya.

Hardai saida falon ya rage daga Malam Mai-nasara sai Rayyern da kuma Uncle Mustapha, Alhaji Ibrahim, da kuma dayan kaninsu mai bimusu Alhaji Abdallah.

Alhaji Abdallah’n dinne kuma ya kalli Dr.Rayyern kana cikin sakin fuska yace.

“Masha Allah Dr. Rayyern munji dadin zuwanka k’warai, mun kuma gamsu da duk wasu bayanan da kayi mana, amma kafun zuwan ka da har mun gama yanke shawarar cewa zamu fitar da Malam din waje, can k’asar Egypt, Saboda ya samu kyakkyawar kulawa, amma dai yanzu Alhamdulillah tunda ga kanan, domin dama da way’anda zamu gani acan din da kuma kai d’in duk abu daya ne.”

Murmushi Rayyern yayi, kana anutse yace.

“A’a basai an fitar dashi ba, sauk’i na Allah Ne kuma Insha Allahu zai samu lafiya.”

“Allah Yasa.” Duk suka amsa cike da gamsuwa.

Yayinda Uncle Mustapha yad’an muskuta had’i da cewar.

“To Dr. Rayyern ka fad’amana kud’in maganin sainayi maka transfer ko.”

Kai Rayyern d’in ya girgiza, tare da hade kafafunsa waje daya ya tankwashe su.

Hannunsa na dama ya d’aura akan na Malam d’in, Cikin yanayin mutumtawa yace.

“A a ku barshi banzo nan dan abiyani ko sisin kobo ba, haka kuma duk wani magani dana sa Ramadan ya kawowa Malam banyi hakan dan abiyani ba, Malam mahaifi ne agareku ni kuma Kaka ne agareni, saboda haka komai da nayiwa Malam nayisa ne saboda matsayi da kuma darajarsa, fata na dai shine Allah Yabashi lafiya.”

“Ameen Summa Ameen.” Gaba ki d’ayansu suka had’a baki wajen fad’an hakan, Yayinda suka sake shaida mutumci, karamci da kuma kyakkyawar tarbiyar da Rayyern din ya samu, Lallai acikin zuk’atansu sun gamsu da cewar Rayyern d’in mutumin k’warai ne, wanda kuma ya taso a hannun iyayen k’warai.

Shikuwa Malam Mai-nasara murmushi ne ya fadada akan fuskarsa, domin kuwa alokacin da yaji Rayyern din ya kirasa da sunan Kaka, bakaramin sanyi yaji acikin zuciya da gangar jikinsa ba, Lallai Tabbas shima ya d’aukesa amatsayin jikansa.

Hannunsa na dama ya d’aura akan Rayyern d’in, Cikin kuma yanayin nuna godiyarsa agaresa yace.

“Masha Allah Allah Ubangiji yayi maka al'barka Rayyern, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma dauwamar da farinciki acikin zuciyarka da na ahalinka.”

Da “Ameen.” Duk suka amsa.

Inda Malam din ya sake d’ago Kai ya kalli Yayan nasa, cikin aminci yace.

“Tabbas Dr. Rayyern ya gwada mana karamcinsa, saboda haka kamar yanda ya daukeni amatsayin Kaka nima na daukesa amatsayin jikana, zan kumayi masa kyauta da karamci kamar yadda yayi mini, Ibrahim shiga cikin dakina, ka bude wajen da nake ajiye kayana na musamman ka d’auko masa sabbin alkyabba da hirami.”

Murmushin farinciki dukansu sukayi inda Alhaji Ibrahim kuwa ya mik’e cikin girmama maganan mahaifinnasu kaitsaye ya nufi dakin Malam Mai-nasara din dake cikin falon.

Har yakai bakin kofarne kuma ya juyo tare da Kallon mahaifin nasu, kana aladabce yace.

“Malam alkyabba da hiramin guda nawa za’a d’auko masa?”

“D’auko masa kala bakwai, saboda zasu fi isansa domin zai saka guda daya acikin kowacce rana, Kaga kenan kala bakwai zasu isar masa har sati guda yana sawa yana tunani.”

Kai Alhaji Ibrahim ya jinjina, tare da bud’e kofar dakin mahaifinnasu ya shige.

Cikin abunda bai wuce mintuna goma ba, kuwa sai gashi ya dawo hannayensa dauke da manya manyan alkyabba, da hirami irin wanda limaman makka suke sakawa ajikinsu, alkyabbu ne masu kyau da kuma tsadar gaske.

Mikawa Malam din Alhaji Ibrahim yayi, Yayinda shikuwa Malam din ya mikawa Rayyern dake zaune, wanda fara’a da kuma farincikinsa ya kasa b’uya.

“Wannan kyautace agareka Rayyern domin kuwa nasan zasuyi maka kyau sosai, shigace irin ta kamala.”

Kai Rayyern ya jinjina cike da tsananin jin dad’i kuma yace.

“Godiya nake maitarin yawa Malam, Allah ya kara arziki da lafiya.”

“Ameen.” Malam Mai-nasara din ya amsa cikin jin dadi.”

Dai-dai lokacin kuwa Ramadan Riyyam da kuma Naseer suka shigo cikin falon.

Karasowa Ramadan yayi ya mik’awa Hamman nasu babban ledan magungunan dake hannunsa.

Karb’an magungunan Rayyern yayi, hade kuma da mik’awa Ramadan alkyabba bakwai din daya same su amatsayin kyauta daga Malam.

“Kyauta na samu daga wajen Malam.”

Yafad’a adai-dai lokacin daya gama mikawa Ramadan din kayan.

Idanu Ramadan din yadan zaro fuskarsa cike da tsananin farinciki yace.

“Masha Allah Malam godiya muke.”

Hararan wasa Rayyern ya watsa masa, kana cikin sigar tsokana yace.

“Godiya muke kaman yaya, nawa nefa ba namu ba.”

Dariya kusan gaba dayansu suka sa, ciki kuwa harda Malam.

Riyyam kuwa jin hakanne yasashi, d’an shagwab’e fuska, tare da matsowa kusa da Malam din yace.

“Ayyah Kaka Malam toni Ina nawa alkyabban.”

Murmushi Malam Mainasara yayi, tare dasa hannu ya shafa kan Riyyama din.

“Kaima taka tananan tana jiranka amma sai ka ƙara girma, yanzu idan na baka yawa zasuyi maka.”
Malam din ya fada da matuk’ar kulawa.

Aikuwa Riyyam kamar dama abunda yake jira kenan, cikin yanayinsa na sakewa daya zame masa sabo, ya kalli Ramadan tare da cewa.

“Yeh za’abani ba za a bawa wani ba.” Ya kare maganan yana meyiwa Ramadan din gwalo.

Abunda ya matuk’ar bawa su Alhaji Ibrahim dariya kenan.

Shikuwa Ramadan durk’usawa agaban Malam din yayi, cikin sigarsa ta shagwab’a shima yace.

“Shikenan na fahimta yanzu wariyar launin fata za’a nunamin, da farko an bawa Hamma Rayyern alkyabba, yanzu kuma an shafa kan Riyyam amma ni ba a shafa nawa ba.”

Ayanzu kam Dariya Malam Mai-nasara yayi, har saida hakwaransa suka bayyana, cikin matsanancin kauna da kuma soyayyar yaran da yakeji acikin ransa, ya sa hannu ya dan jawo Ramadan din jikinsa.
Kansu ya shafa dukansu tare dayi musu addu’a, domin hakanan yakejinsu acikin zuciyarsa tamkar jikokinsa na gaske.

Rayyern kuwa duk abunda kannen nasa sukayi kallonsu kawai yakeyi, bayan kuma ya gama bare magungunan da ya kamata ace Malam din yasha ne, yasa Naseer ya miko masa bottle water marar sanyi.
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment