Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

cikin kulawa.
Juyo mata fuskar wayar yayi.
Da sauri ta zsro idonta waje cike da mamaki tace.
"Dama H...!


📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

ASSALAMU ALAIKUM, Masoyana ma karantan littattafaina, ina mai farin cikin sanar daku, yau d’in nan MON, 18 OCT 2021 za'a fara biyan kud’in samun damar karanta littafin TUBALI akan farashi mai sauk’i Biya 500 k’aramin farashin na k’aramin group, kana sai *Special people Group* akan farashi mai sauk’i 1k kacal babban group a yawan posting babancinsu yake, zaku biya ta asusuna.

ACCOUNT NO 0661110170.

BANK NAME: AISHA ALIYU GARKUWA

BANK GTBank

sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan numben tawa da nakeyin whatsApp da ita 09097853276.

*PLS TAKE NOTE BAND VTU*
kada kiyi min VTU ko transfer'n katin ta wannan numben etisalat d’in idan kuwa kikayi wlh babu ruwana dan na fad’i miki. Please and please in dai da hali kada ki turo min katin, kiyi min transfer'n ruwan kud’i ta bank account na, in kuma babu dama to sayi katin MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta whatsApp.

Gareku mutanen jamhuriyar Niger ku tuntub’i Mommy akan layinta +22790899076, ta wurinta zaku biya, hoton katin zaku d’auka ku tura mata ta wannan numben a whatsApp, Special people group 1k ne (1000) k’aramin group kuma (500) kacal,
Please dan Allah babbar macece mai yara da tarin jikoki da y’ay’an jikoki mu kyautata lafazi da mu'amala gareta dan Allah don in ka girmama iyayen wasu wasu zasu girmama naki🙏🏻...

Littafin TUBALI littafine na musamman mai salo na musamman mai cike da abubuwa masu tarin yawa.
*Tausayi, Sark’ak’iya, jan hankali, Fadakarwa, Nishad’antarwa, ilimantarwa, al'ajabi, Sa'ar rayuwa, riƙon amana, cin amana, ribar kyautatawa, kana da sassayar soya mai salon narke jiki da zuciya*

Ga number wayata da nakeyin whatsApp da ita, 09097853276 idan kina son biyan kudin samun damar karanta littafin TUBALI sai ki biya ta wannan ac no din dai 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, dan Allah ki biya kafin kiyi min mgn kina turo shaidar biyanki ina gani zan saki a group, in Kuma baki da ac no ko yanayin zaman wani k’asa ko wani luggun ki sayi katin MTN na 1k in special group kikeso ki turo min. In Kuma k’aramin Group kike so ki sayi katin *MTN ki copy number's din ki turo min ta whatsApp number'n na 09097853276 kada kiyi min VTU ko transfer'n katin 9mobile dan layin nada matsala*

Za'ayi tsawon mako ɗaya ana biya ina kafin in fara update domin samun sassaucin aiyukan sauraron mutane, za'a fara biya yau *MON 18 OCT 2021. Kana zan fara posting ranar MON 25 OCT 2021 rana ita yau kenan in mai kowa mai komi ya kaimu bisa rai da lfy*

🙏🏻Na rokeki da girman zatin ubangiji in dai kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina dan Allah ki bar kud’inki kiji tausayin marainiya, kada ku cutar da marainiyar Allah,😭🙏🏻🙏🏻🙏🏻.


Nasan daga yau har zuwa na gama littafin Chart zaimin yawa zai hausawa aiyuka zasu yawaita gareni, amman babu kamar makonni ukun forko zuwa biyar, Please ina neman al'farmar uzuri in kinga kinyi min mgn ban amsa mikiba, na tuba kiyi haƙuri ba raini bane ko wulak’anci face yawan mutane wata k'il ban isa kan Chart naki bane, Amman muddin na isa na kuma bud’e na gani tabbas zan baki amsa in katine zansashi yana shiga zan saki a group in bai shiga kuma in gaya miki, in Kuma ta account kika turamin ina ganin shaidar biyanki zan saki a group, 🙏🏻Dan Allah in kinsan ba littafi ko maganin gyara namu na mata kikeso ba to kiyi haƙuri da min mgn sai na d’an samu salama🤝🏻😘🙏🏻😂.


*Sayan na gari maida kuɗi gida sai kinzo*










By
*GARKUWAR FULANI*




📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*
PAGE 2

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


"Hausa ya keyi fa ko?". Cike da kaɗuwa Sulaiman yace.
"Eh abinda ya ban mamaki kenan.”
Sai kuma ya kalleta jin tana cewa.
"Koda yake ba mamaki wani ne ya rubuta mishi, tunda kaga ai yace.
Ethiopia Addis Ababa to Nigeria kano State. Kanawa zan zo muku.
Wata ƙil wani ne ya rubuta mishi".
Komawa yayi da baya ya jingina bayanshi da jikin kujera.
Numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
"Kai Sumayyah gsky da mamaki fa.
Kalli Comments ɗin mutane fa da amsar da yake basu."
Ya ƙare maganar yana shiga comments section ɗin ƙasan video'n da ya saka a shafin nasa.
Inda wani Abis Fulani yake cewa.
"Eyyeh Riyyam-nsra a Nigeria, kanawa nama fatan isa lfy".
Cike da mamaki Sumayyah ta kalli amsar da ya baiwa Abis Fulani.
"Ngd aboki na". da alamun musabaha.
Sai kuma tayi ƙasa ganin inda wani.
Ahmad MG ya fara mgn da zaro ido alamun mamaki tare da cewa.
"Riyyam-nsra da yin Hausa, ko mafarki nakeyi".
Dariya yayi tare da bashi amsa.
"Noh Ahmad zahiri ne".
Tofa wannan abun yasa comments ɗin mutane zubowa kamar ruwan sama domin shi dai ɗan ƙasar Ethiopia ne, kalarsa, harshensa, cimarsa, rayuwarsa, komai na canne, bai taɓa koda maganar Nigeria a shafinsa ba, sai gashi yau kuma yayi video cewa zaizo Nigeria, kuma yana rubutu da hausa yana kuma karantawa.
Cikin kaɗuwa Sumayyah taci gaba da bin comments ɗin mutane na farko-farko da ya iya basu amsa sabida yawan mutanen.
Cikin mamaki tace.
"Lah kalli tambayar da wani ya mishi."
Amsar wayar Sulaiman yayi.
Ya fara duba saƙon da Imran yayi mishi.
"Riyyam-nsra kasan Nigeria ne? Ko Ka taɓa zuwane? Ko wannan ne zuwan da zakayi na forko?".
Alaman murmushi yasa tare da cewa.
"Nasan abu da yawa kan Nigeria".

"Da sauri yace gaya min kaɗan daga ci."

"Ok kamar me kake son in gaya maka".
Da sauri yace.
"Ka iya taken ƙasa. Ko rantsuwar al'ƙawarin ƙasa."

Cikin lumshe ido, Riyyam-nsra dake kwance a ɗakinsa.
Ya rubuta mishi amsa, da bari in baka amsar a video."
Take kuwa ya tashi zaune yayi taken ƙasarmu Nigeria ƙasarmu ta gado kana da rantsuwar al'ƙawarin ƙasa.
Wannan video da ya saki
Yayi matuƙar jan hankali al'ummar Hausawa duniya baki ɗayansu more Especially ƴan Nigeria bama ya kanawa.
Da sauri Sulaiman ya fara rubutu.
A karo na forko a rayuwarsa da zaiyiwa wani comment a TIKTOK.
Rubutu yayi cikin harshen nasara.
"Hey Riyyam-nsra you knew much about Nigeria you are a patriot".
Yayi mgnar da gayya ne dan ya gano ko dai ɗan Nigeria ne basaja ne da karya yasa yake ciwa ɗan Ethiopia ne, wata ƙil karatune ya kaishi can.
Murmushi yayi tare da rubuta mishi amsa.
"Baƙon Nigeria dai mai kishin Nigeria amman ni ɗan Ethiopia ne.
Sai dai Nigeria ƙasar babban abokina ne da mukayi karatu tare a US."
So daga ganin wannan video, akai ta cewa.
"Haba shi yasa mana.
Nasir Ahmad ne wanda shine abokin nashi ya fito, yanata mishi tsiya a nashi shafin. Nanfa aka gane sanadin zuwansa da kuma inda ya koyi Hausa ras.

Ɗan gajeren tsaki Sulaiman yayi tare da cewa.
"Wadannan yaran gaba ɗaya TIKTOK ta haukata mana matasa wanda sune TUBALIn al'umma sai gashi kuma muɗin ma suna shirin haukatamu".
Dariya Sumayyah tayi tare da cewa.
"Dama haka ai Rayyern ɗin ke ce maka, in baka dena biyewa social media ba, zaka rasa lokacin kanka".
Kwaffa yayi tare da rufe datarsa kana yace.
"Nima fa Ibrahim ne ya sani fara wannan abun sabida, kamannin Rayyern da wannan yaron."
Daga nan sukaci gaba da hira kan kamanninsu.

Washe gari da safe ranar talata.

Gidan Alhaji Idi Sale Dakata.
Su kusan shida ne cikin falonshi.
Wanda huɗu daga cikin manyan yan kasuwane masu faɗa a ji masu juya sule ta koma million ɗaya ko tako wanne irin halin ƙaƙama ko talaka zaiji daɗi haka ko bazai jiba.
Biyu daga ciki kuma ƙusoshin gwamnati ne masu ƙarfin iko daga ta jiha zuwa ta ƙasa.

Alhaji Yawale ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Yaron nan fa yanayi mana illa ba tare da mun ankare ba.
Gaba ɗaya ya rarake tubalin da mukayi tsawon shekaru muna ginawa muna samun wuri na jawo mana wuri."
Cikin tsananin takaici Alhaji Abdu Tababa ne yace.
"Tun-tuni nake gaya muku haka.
Mu kauda yaron nan a doron ƙasa shine kawai mafi sauƙin mu.
Kunaga yadda kasuwan cinsa ke haɓaka, kamfanonin sa suna bunƙasa daga Arewacin Nigeria har ya koma kudanci ya kafu.
Uwa uba yanzu duk ƙasashen Afrika yanada rassai.
Ya maida kayan abinci da araha tamkar ruwan sama cikin damuna.
Duk inda ka shiga a kasuwannin Mai-nasara race, ke cike.
A farashi mai sauƙi ta yaya za'ayi a saurari kayan kamfanonin mu".

Ɗaya daga cikinsu ne ya miƙe tsaye tare da cewa.
"Ni tambaya ta a kullum ma shine
menene Tubalin kasuwancin yaron nan?
Yaushema aka haifeshi? Sa'an yaran cikin mune fa!
Ta ina ya samu Wannan tarin dukiyar da har ya samu damar razana mana kasuwanci ya raunata mana Company's.
Yaushe yayi ginin duk a lokacin ɗaya menene Tubalin dukiyarsa da matakan ikonsa!?."
Ya ƙare maganar yana kallon Bala Tambari wanda shine shugaban tsare-tsaren ginin masana'antu a gwamnatance, dole sai yasa hannu za'ayi gini ya za'ayi ka bashi izini da damar yin gini a duk inda yake so a ƙasar nan".
Cikin takaici Bala Tambari ya fesar da numfashi tare da cewa.
"Tsohon yarjejeniya ne, yana da dukkan abin buƙata, yanada sa hannun da suka gabaceni kuma kan tsari suke.
Naso in ƙalu balanceshi.
Tun shekaru biyar baya lokacin da ya fara gina babban campany dake Nan birnin Kano wanda yanzu yake gab da kammalashi so naga komai da hujja yakeyi.
Yaron shegen taurin kai ne dashi, gashi da ɗan banzan tsaurin ido.
Kana mgna zai tsira maka waɗannan siraran idanun nashi masu kama da soyayyan gujjiya, tsakar idon ka ya baka amsa da hujjar da baka isa kayi mgna ba".

Dr.Lukman ne ya fesar da iska a baki tare da cewa.
"Ni ta ko ina ya tosheni
A fannin likitancin gaba ɗaya yana bi yana rarake privet Hospitals.
Ɗan banzan komai na asibitinsa mai sauƙi kuma ga kula ya za'ayi aje irin namu asibitocin."

Alhaji idi Sale Dakatane ya miƙe a fusacen shina kana yace.
"Nifa gaba ɗaya ya ta'azzara min campany na na shinkafa.
Sannan kafin kace ka motsa sai ka samu ya toshe ko ina.
Hegen yaro mai jajayen kunnuwa.
Yana nan tamkar Wahainiya, samun ganinshi ma ya zamewa mutun aiki."

Dr Lukman ne ya ɗan sauƙe numfashi tare da cewa.
"Cikin satin nan zai dawo Nigeria yanzu haka yana Ethiopia yaje, shugaban kasar can da kanshi da manyan likitocin sune, suka karrama shi.
Sabida taimakon da yayiwa wasu daga cikin mutanen ƙasar Ethiopia cikin Airport kan hanyarsa ta zuwa US, dan karramashi a matsayin ɗan kasuwan da yafi ko wanne sauƙin farashin kayan masarufi.
Kaga yana tafi kuma yazo wai kuma Ethiopia zasuyi mishi wata karramawar.
Yaro kamar ɗan ruwa, komai yasa kai sai Nasara".
Bala Tambari ne, ya kalleshi tare da cewa.
Toh yanzu dole kai zaka nema mana zama dashi.
Yana dawowa muna buƙatar shi mu gwada sayan farashinsa.
Muyi mishi tayin harƙallarmu yasan irin ribar da muke shigarwa, wata ƙil zai amince mu haɗa hannu in kuma yaƙi tabbas zamu gina mishi gadar zare.".
Da sauri Alhaji Idi Sale Dakata yace.
"Uhumm ai In Kuma yaƙi amincewa mu haɗa hannu.
Toh lokacin wasan zai fara, dan in taurin kaine da gsky da samun ƙarfin iko bai kai.
Mai-gaskiya da wasu ba, da muka gama dasu shekaru ashirin da biyu baya ba, danni cinnaka ne ban bar na gida Bama, bare shi baare."
Haka dai suka tashi a taron nasu.
A nufin sai ya dawo su zauna dashi.

A cikin gidan kuwa. Jannart ce ke
Tsaye a kitchen, inda take sanye da wani half gown mai masifar kyau wanda ya d’an bayyana fararen legs d’inta, rigar irin mai kauri da kama fatar jiki dinnan ne, wanda hakanne kuma yasa had’add’iyar Surar jikinta dan bayyana, kasancewarta y’ar gayu, Tabbas Jannart macece mai matuk’ar son fashion, shiyasa hatta suturun da take sawa ya banbanta da sauran na y’an Nigeria, saboda sometimes tafi yin shiga irin na wasu daga cikin larabawa, ko kuma shigar mutanen turkey🇹🇷.
Tsaye take a kitchine din cikin kuma nutsuwa take aikinta.
Yayinda Mom ke tsaye a gefenta.
Cikin kula Mom ta kalleta tare da cewa.
"Jannart kamar Yayanki ne ke kiranki".
Cikin bugawar zuciya tace.
"Yah Junaid!?."
Da sauri tace.
"Eh shi dai".
Bugawa zuciyarta ya kumayi, tare dajin wani iri acikin jikinta, saidai kuma babu yanda ta iya, haka ta juya cikin sanyi ta nufi falon.

Can tsakar falon ta hangoshi tsaye, saurayi ne, mai murd’addiyar Surar jiki da kuma tarin gashi akansa irin busu-sun nan, duk da cewar kyawun nasa bawani na zarce hankali bane amma baza’a tab’a k’iransa da mummuna ba, wata riga
marar hannuce ajikinsa, sai kuma wondon dake jikinsa wanda ya tsaya masa iya guywa.
Bisa alamu kuma yanzu ya tashi daga bacci.
saboda yanda idanunsa sukayi jazir.

Kallonta yayi, tare kuma da d’an cije labb’ansa, still Cikin binta da wani irin mayataccen kallo yace.
"Kije ki share min ɗakina".

Fuskarta ta d’an b’ata cikin kuma tsanar shiga ɗakin nashi tace.
"Yah Junaid breakfast nake haɗa mana".
A fusace ya juyo kanta cikin takaicin abubuwan dake haɗe mishi a kanta ya yarfa mata wani irin gigitaccen mari a kan kunneta na dama, saida ya bada wani irin sauti ƙauuuuu! Da ɗan karen ƙarfi.
A gigice tasa tafin hannunta ta tallabe ƙuncin ta.
Yayinda wasu taurari suka fara gilma mata a gani.
In da sabo yaci ace fuskarta ta saba da marukan Yah Junaid Wanda tun tana yarinya take shansu gashi sanadin su, kunnuwanta sun samu matsala jinta ya raunata.
Wasu irin hawaye ne masu masifar zafine suka silalo mata.
Ba tare da tace komaiba ta juya ta nufi ɗakin shi.
Ta yaya zuciyarta zata samu sauƙin ɗan uwanta da take bata da wani sama dashi tunda shine suke uwa ɗaya uba ɗaya amman yafi kowa tsanarta a duniya.
Ba shaƙuwa ko tausayawa a tsakaninsu.
Sannan mahaifinsu babu ruwanshi ko a gabanshi Junaid zai daketa babu ruwanshi sai yayi kamar baya wurin ma.
In Mom tayi mgna ya gwatsaleta yace babu ruwanta sunfi kusa.

Wannan ne ya ƙara tsananta zubda hawayen ta.
A haka ta fara tattara mishi falon da gaba ɗaya ya birkitashi.

Shigowa yayi ya zauna yana mai Binta da ido, duk inda tayi.
Wani irin abu yakeji a kanta.
A hankali ya miƙe yabi bayanta lokacin da ta shiga Bedroom.
Da sauri ta juyo jin shigowarsa.
Gefenta ya matso fuska a murtuke hakan ne yasa bugun zuciyarta ya ƙara tsananta.
Har kana iya ganin yadda numfashin ta ke fita da yanayin tsoro.
Fuska ya kuma murtukewa.
Kana yace.
"Munafuka, sai kace da gaske haka kike tsoron maza, ji yadda kike tafiya ba bra kina wani karkakaɗa ƙirji irin ke gaki ƴar iska mai son maza ko?."

Idanunta ta rumtse da k’arfi cikin kuma ƙunan ran ƙazafin da Yah Junaid ke jifarta dashi murya na rawa tace.
"A'a".
Cikin haɗe fuska ya daka mata tsawa tare da cewa.
"Toh meya hanaki sa bra?".
Murya na rawa tace.
"Dr. Lukman ne yace in daina sa bra, sabida matsalar numfashin da Athsman ɗina ke jamin. In nasa ya matse min ƙirji sai numfashina yayi ta shaƙewa".

Wani irin dogon tsaki yaja tare da cewa.
"Ubanki zanci in baki dena raina min hankali ba, matse ƙirjin da ƙatti keyi bai shaƙe numfashin ba sai saka bra ne zai cushe miki numfashin."
Fice min da gani!!". Ya k’are maganar a tsawace.

Jin hakanne kuma yasa da sauri ta juya ta fita, hawaye na zubo mata sabida raɗaɗin marin daya yarfa mata da zafin kalaman zargi da yake binta dasu.

A falo ta samu Mom da sauri ta faɗa jikinta.
Cikin sakin sassayan kuka tace.
"Mom ki gaya musu wlh ni ba yar iska bace, Meyasa Mom Meyasa Ya Junaid ke jifana da mugayen maganganu, shifa yaya nane..”

Jawo hannunta Mom tayi suka zauna bisa kujera, a hankali tasa tafin hannunta tana share mata hawaye cikin yin ƙasa da murya tace.
"Na sani Jannart kuma Allah ya sani, ke ba ƴar iska bace. Yaushe ma kika samu sakewar rayuwar duniya kullum kina cikin takunkumi.
Ko ina zakije da masu gadinki.
Na rasa wannan masifar tsaron na menene kina girma ana ƙara killaceki kamar abun rashin gsky."
Cikin shessheƙan kuka tace.

“Mom shi Yah Junaid gani yake, su masu tsaron nawa dasu nake iskanci.
Daddy Kuma gani yake in ya cire masu tsaron da wasu zanyi iskanci.
Wlh na sani Mom bawai dan tsaron lfyata bane yasa Daddy ware min masu tsaro.
Shima zargina yakeyi ko Mom?".
Jin yadda numfashin ta ke fitane yasa mom gyara zamanta kana ta fuskanceta da kyau.
Allah ya sani tana son Jannart tamkar ƴar cikinta.
Amman duk yadda zatayi bata burge Alhaji Idi da Junaid, gani suke kamar so take Jannart ta lalace ne don ba ita ta haifeta ba.
Cikin kula da tausasawa uƙubar da suke shayar da ita tace.
"A'a Jannart Daddynku baya zarginki, shi ya bada masu tsaronkine sabida larurar ciwonki, kina buƙatar makusanci a koda yaushe, tunda abu kaɗan ke tada miki athsman ɗin wanda kinga tun da yana nimoniya, kina girma yana canzawa ya riƙa har ya zama asman shiyasa yake tsananta kulawa a kanki.
Sabida abu kaɗan ke tada miki shi.
Kuma Yah Junaid ɗinki yana sonki.
Ɗan uwa, uwa ɗaya uba ɗaya ya wuce wasa.
Sun haɗa da son da Mamanki zatayi mikine da tana raye".
Cikin zubda hawaye tace.
"Mom kin bani son da ya kamata uwa ta bawa ƴarta, ni banyi maraicin kyakkyawan tarbiyar uwa ta gari ba.
Kawai dai basa so nane".
Cikin kafeta da ido Mom tace.
"Jannart ki yarda dani, tashi muje kici abinci".
Cikin nitsuwa tasa hannunta ta share hawayenta kana ta miƙe.
Dinning area suka nufa.
Suna zama Daddy ya fito da hakama Junaid da Abdul.
Nan suka zauna sukayi breakfast.

A hankali ta sauke numfashi ganin Junaid ya miƙe ya bar wurin.

Sai kuma ta ɗan kalli Alhaji Idi Saleh Dakata.
Cikin takatsantsan da girmamawa tace.
"Daddy Ina son zanje gidan Aunty Rabi'ah akwai wani aikin da zamuyi a can".
Ido ya ɗan zuba mata.
Ita kuwa da sauri tayi ƙasa da kanta.
Tana tasbihi cikin ranta, da addu'ar Allah ya ɗaurata a kanshi.
Juyawa yayi ya fara sauƙa kan steps ɗin tare da cewa.
"Kada ki daɗe.
Kuma ƙafarki ƙafarsu Sunday."
Cikin sabo da hakan tace.
"Toh".
Kana ta miƙe ta nufi ɗakinta. Mom kuma ta fara tattara kan table ɗin.

Wanka tayi cikin nitsuwa da kuma sauri-sauri.
Tana fitowa, ta zauna ta tsane jikinta kana ta busar da tattausan suman kanta.
Ta shafa mishi mayuka, sannan ta tubkeshi.
Mai ta ɗan shafa kana ta Murja farar hoda, tare dasa man baki.
Sosai tayi kyau duk da bata cika kwalliya a fuskarta ba.
Wasu tattausan riga da wondo pallazo farare ƙal ta zaro,
Sai wata doguwar riga budaddiya mai igiya a tsakiya.
pantie tasa, kana ta zira dogon wondon daya kasance yayi tightin fatar jikinta.
Dole sa bra baya cikin jadawalin rayuwarta sabida larurar ciwonta.
Sai dai takan sa rigunan su ɗan matseta.
Rigar ta zura irin mai wuyanan nane wato, high neck, naɗe wuyan tayi ta gyarashi.
Cib-cib rigar tayi mata a jikinta gwanin burgewa ƙirjinta yayi cas a tsaye babu alamun ronƙofowa bare zubewa.
Lafaffen cikinta ya taimaka kwarai wurin bayyana tsayeyyun breast ɗinta.

Doguwar rigar kimono blue color mai ɗigon fari-fari'n ta ɗaura saman riga da wondon, cib kuwa kimonon yayi mata ajikinta, inda kuma har ƙasa yazo mata.
Igiyoyin dake sarƙafe tsakiyan rigar ta kama ta ɗaure.
Hakan ya bawa tsakiyar rigar haɗewa, sama can kan ƙirirjin ta kuma gefe da gefen ya rufu har ya samu damar rufe nimples ɗin ta.
Sai kuma tsakiyan bai ida rufuwa ba.
Sai kuma can ƙasa ta nan zaka gane riga da wondone a ƙasan doguwar rigar farin mayafi rigar ta dauko tayi Rolling kanta fuskarta ta fito a ciki kamar sifili (0) a ciki.
Sosai shigar tayi masifar mata kyau.
Wanda kuma sune suturunta na yau da kullum wanda tafi so da jin daɗin sawa, kasan cewar rigunan cikin masu taushine suna buɗuwa dai-dai jikinta.

Turare mai sauƙin ƙamshi ta fesa, sanin sa mai tsananin ƙamshin yana da illa ga baliga in zata fita da kuma lfyarta.
Wasu fararen takalma sau ciki masu taushi tasa.
Kana ta zari babbar wayarta kiran iphone11promax ta fito.

A bakin ƙofar shigowa falon tayi kiciɓis da Mom cikin.
Yanayin sakin fuska Mom tace.
"Kai masha Allah ɗiyata kinyi kyau".
Cikin yanayin jin daɗi tace.
"Ngd Mom bari inje da wuri in samu in dawo da wuri".
"Toh hamzarta ɗiyata, sai kin dawo".
Toh tace kana ta fita ta tafi.

Tana fitowa harabar gidan
Wadannan garadan marasa kan gado suka miƙe baki ɗayansu.

A hankali ta matso kusa da Driver'n'.
Cikin kula yace.
"Jannart yau kuma ina zamu je, naga yau ba ranar aiki bane?".
Cikin jin daɗin yadda dattijon ke mata mgn ta mutuntaka tace.
"Baba Ado, gidan Hajia Rabi'ah zamuje".
Marfin motar ya kama da nufin buɗe mata, da sauri tace.
"Baba Ado ka bari zan buɗe".
Murmushi yayi kana ya bude mata, ta shiga.
Suma sauran suka shiga sauran motocin suka tafi.

Suna isa gidan Hajia Rabi'ah.
Bayan sunyi parking ta nufi cikin gida su kuma suka zauna a waje.

Da sallama a bakinta ta tura ƙofar.
Da sauri taja da baya ganin Asiya dake fitowa.
Sai kuma ta shigo ganin taja gefe tana hararanta.
Da sauri tayi ciki jin Hajia Rabi'ah na cewa.
"A a Jannart kin iso ko.
Maza shigo daga ciki".

Cikin jin daɗi ta shigo.
Ta zauna inda Hajia Rabi'ah ke nuna mata.
Cikin girmamawa tace.
"My Aunty Ina kwana".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah ya ƴan tsaron ki".
Cikin yin gajeren murmushi tace.
"Gasu can a tsaye a bakin gate tamkar dogaran sarki".
Dariya ta ɗanyi kana ta kalli wani ɗan matashi dake zaune can bisa kujarar Dinning area tace.
"Toh Mahmoud ga Jannart ɗin ta iso.
Tunda kaƙi bawa Asiya amsa ko ɗaya".
Da sauri ta juyo ta kalli inda aka kira Mahmoud.
Shi kuwa tasowa yayi ya nufo cikin falon yana mai cewa.
"Aunty naga kamar hasadace ke cinta, kuma ma bada ita nai wayaba.
Ita kuma wanna sai saiɓi.
Kin san tun safe ina nan kin ajiyeni kamar mara aikin yi".
Cikin nitsuwarta tace.
"I'm so sorry. Ina kwana".
Gefe ya zauna kana yace.
"Wuni dai tunda 12 tayi".

Nan suka gaisa kana Jannart ta fuskanceshu da kyau.
Cikin sani makamar aiki tace.
"Yaushe jirgin Ethiopia zai diro Nigeria a wanne gari ɗaya Abuja ko Lagos ne?".
Murmushi Mahmoud yayi tare da cewa.
"Wato zaki nuna min ke yar jaridace, tuni kin fara tambaya da wayo.
Jirgi zaki tambaya ko shi?".
Kwaɓe fuska tayi tare da kallon Hajia Rabi'ah kana a hankali tace.
"My Aunty menene ma sunan nashi?".
Cikin zuba mata ido Hajia Rabi'ah tace.
"Iyeh wato ma har kin mance sunan nashi. Kin manta cewa sunan nashi ne kawai makaminki."
Cewar Hajia Rabi'ah.

Ita kuma Jannart takwara kanta tayi bisa kafaɗa kana tace.
"Please my Aunty gaya min zan riƙe".

"Rayyern". Ta bata amsa a takaice.
Ita kuwa ido ta lumshe tare da fesar da numfashi can cikin zuciyarta tace.
*"RAYYERN! RAYYERN!! RAYYERN!!!* Ta maimaita sunan sau uku kana ta juyo ta kalli Mahmoud cikin nitsuwa tace.
"Mahmoud ranar yaushe zai dawo? Da wanne lokacin jirginsu zai iso daga Abuja ko Lagos zuwa Kano?".
Gyara zamanshi yayi kana yace.
"J....!


free PAGE .


📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

ASSALAMU ALAIKUM, Masoyana ma karantan littattafaina, ina mai farin cikin sanar daku, yau d’in nan MON, 18 OCT 2021 za'a fara biyan kud’in samun damar karanta littafin TUBALI akan farashi mai sauk’i Biya 500 k’aramin farashin na k’aramin group, kana sai *Special people Group* akan farashi mai sauk’i 1k kacal babban group a yawan posting babancinsu yake, zaku biya ta asusuna.

ACCOUNT NO 0661110170.

BANK NAME: AISHA ALIYU GARKUWA

BANK GTBank

sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan numben tawa da nakeyin whatsApp da ita 09097853276.

*PLS TAKE NOTE BAND VTU*
kada kiyi min VTU ko transfer'n katin ta wannan numben etisalat d’in idan kuwa kikayi wlh babu ruwana dan na fad’i miki. Please and please in dai da hali kada ki turo min katin, kiyi min transfer'n ruwan kud’i ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment