Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA



By
*GARKUWAR FULANI*





📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*


PAGE 18
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


*WANNAN PAGE D’IN SHINE K’ARSHEN FREE PAGE, DAGASHI BABU WANI FREE PAGE IN KIN GANSHI A WOJEMA TO SATA PAGE NE daga wannan PAGE 18 na gama free PAGE, dan sonku da Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina 1k ko 500 da kika bada bawai yana nufin kin biya kin mallakeshi bane kuɗin karantawa ne, dan Allah nace ba don niba, in Zaki saya ga ac no 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in baki da damar tura ta account ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo minshi ta WhatsApp 09097853276.*

_Masu karanta Audio books kuyiwa girman Allah ku kiyaye min littafina domin zama lafiya yafi zama ɗan sarki, ga number birjik a pages idan ki/kana so ki/kayi min mgn mu dai-dai ta masu posting a wasu shafukan kuyi girman Allah ku barmin books na, 09097853276_


Shiru Jannart tayi tare da zuba mishi idanu, tana mai nanata kalmar daya suffanta Daddy'nta dashi.
“Hankaka!!!?”. Ta faɗa can ƙasan zuciyarta tana mai son nazartar ma'ana da tushen kalmar a hausan ce.

Gyara zama Abba yayi tare da fuskantar ta da kyau cikin tsananin kulawa, tausayi ƙauna, jinƙai.
Murya a sanyaye yaci gaba da cewa.
“Bazaki fahimta ba Jannart kada ki tsauwalawa kanki tafiya nazari ko tunanin sarƙaƙiyar dake cikin rayuwarki.
Bazaki ganeba sai an ganar dake, ina cikin matuƙar damuwa mai tarin yawa.
Na yadda zan samu in zama GARKUWAR ki, ina tunanin kamar yarda da kikayi min tana da rauni bazan samu amincin da nake buƙata daga garekiba. Na amsar umarni na sawa ko hanawa!!!”.
Hawayen dake kwaranya bisa fuskarta tasa hannun ta ta share kana a take wasu suka kwaranyo.
Hakan kuma baya rasa nasaba ne da yadda taga idanun ƙanin mahaifin nata yana kwaranyo da hawaye.
Tana hango tsananin tausayinta cikin kwayar idanunshi.
Numfashi ta fesar a hankali tare da danne shessheƙan kukan dake son kumbce mata cikin aminci da dukkan yarda da yaƙini murya na rawa tace.
“Abba kana da ƙarfin iko a kaina.
Ni ɗiyace a gareka, kuma zan zamo mai biyayya akan dukkan umarninka, zan kuma nitsu in fahimci abun da kakeso in fahimta bani da wani katanga jigo majingini sai kai, Abba inada kekkyawan yaƙini kaine TUBALIN farin cikina”.
Wani zazzafan numfashi Barrister Kabir ya fesar kana ya ƙara jawo kujerar ta matso kusa da ita, cikin sanyi ya kama tafin hannunta murya can ƙasa yace.
"Yadda na riƙe hannunki haka.
Ana haifoki mahaifiyarki ta damƙa min amanarki.
Tana mai jaddada min cewa in zama Garkuwanki inyi miki zaɓi mijin na gari wanda naga ya dace dake, in gaya miki ke marainiyace tace in faɗawa duk wanda zan bawa aureki cewa ke marainiyace dan ya duba maraicinki.”
Ina shessheƙan kuka wanda yake tafe da zazzafan tsohon dafi mai ciwo a zuciyarsa ya danne mgnar.
Itama kukan ta farayi.
Wanda Har Aunty Dijat dake woje ta fara jiyo sautinsu.
Cikin tsananin rauni ya kalleta murya na rawa yace.
“Jannart in nayi miki zaɓi da miji kamar yadda mahaifiyarki ta roƙa, zaki amince dashi, zaki yarda da duk tsarin da zan zo miki dashi dan mu cika fatan mahaifiyarki!!! In Kuma samar miki ƴanci!?”.
Cikin kukan ta gyaɗa mishi kai.
Hannunshi yasa ya sharce hawayen sa kana ya tsareta da ido tare da cewa.
“Zaki iya amincewa in ɓoyeki, in bada ajiyarki a killataccen wurin da zaki tsira da ranki da lfyarki tun kafin wa'adin da suka tsara a kanki ya cika”.
Zuwa yanzu kanta ya ƙara ɗaurewa, duk da ta saba jin waɗannan zantukan a bakin ƙanin mahaifin nata, amman har yau ta gaza samar musu muhallin ajiyewa.
Cikin rashin fahimta tace.
“Abba na amince”.
Kai ya gyaɗa kana yayi ƙasa da murya yace.
“Har Daddynki fa zaki bari bazaki kuma sanar mishi komaiba, bazai san inda kikeba”.
Hannu tasa ta dafe ƙirjinta tare da zaro ido kana tace.
“Abba in na dawo Yah Junaid zai kasheni, kuma Daddy na zai shiga tashin hankali!”.
Numfashi ya fesar kana a hankali yace.
“Lokacin da zaki dawo, zaki dawo da encinki mai ƙarfi, Junaid ko farcenki bazai taɓa ba, Daddy kuwa kunya zata makantar da idanunshi sabida ya gaza zama uba kuma Garkuwa a kanki.
Sai dai hakan bazai faruba sai da amincewarki da sahalewarki.
Kuma sai haka ta faru zaki gane kurman baƙin dake cikin rayuwarki.
Shin kin amince!!!?”.
Cikin zulimi tace.
“Abba har na tsawon wani lokacin zaka ɓoyeni? Kuma ina zaka ɓoyenin?”.
Da sauri yace.
“Bana tantance lokacin ba, amman zan ƙiyasta wata takwas zuwa shekara ɗaya.
Sannan inda zan ɓoye ki kuma shine ban gama tantancewa ba, amman ki aminta dani GARKUWA zan nema miki”.
Ajiyan zuciya mai nauyi ta sauƙe kana a hankali tace.
“Abba na aminta da kai nasan baza cutar dani ba”.
Da sauri yace.
“Toh ki adana wannan mgnar amanace tsakaninmu kada ki gayawa kowa, duk faɗin duniyar nan.
Nan kusa kuma zan samu wurin adanaki mai inƙanci”.
Cikin sauƙe numfashi tace.
“Toh Abba”.
Shigowar Aunty Dijat ce yasa suka katse zancen.

*Wannan shine PAGE na karshe a FREE PAGE in ki. Kuma ganin ci gabama to na satane baiwar Allah in kinaso ki saya, in bazaki iyaba babu dole ga littatafai da dama na kyauta, special Group 1 karamin group 500 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU*

A nan gidan nasu kuwa.
Mom na komawa ta shiga Kitchen aikin ta farayi yayinda Abdul ke gefenta yana tayata kana yana mgna, da Yah Azeez ɗinshi wanda.
Kwanan ya koma Macsow kasan cewar acan yake aiki.
“A jikin da sauƙin Yah Azeez yanzuma Mom ta dawo anjima in munje zan haɗaku a waya”.
Abdul ya bawa Azeez amsa.
Cikin tausayawa Azeez yace.
"Toh shi kuma wawan ina yake”.
Mom ce ta ɗan ja tsaki tare da cewa.
“Yoh waya sani tun jiya da abin ya faru daya fita bai dawo ba”.
Kwaffa yayi tare da cewa.
“Allah zai saka mata”.
Daga nan dai sukaci gaba da mgnar suna aikinsu.
Saida suka gama aikin ta shiga Bathroom Dan yin wonka.

_Dan Allah daga wannan PAGE din kada a fidda wani_

A can Gidansu Dr Rayyern Mai-nasara kuwa kasan cewar yau jumma'a.
Basu dawo masallaci da wuriba,
Sai kusan ƙarfe takwas suka shigo
A jere da ma'aikatan gidan baki ɗayansu.

Yayinda suka gaggaisawa suna tambayar jikin Rayyern.
A hankali ya kalli Baba Mauɗo tare da cewa.
"Alhamdulillah Baba Mauɗo na saumu sauƙi banjin komai sai baccin da nake ji bai isheni ba”.
Cikin jin daɗi Baba Mauɗo yace.
"Alhamdulillah Allah ya ƙara mana lfy”.
Amin Amin sukace baki ɗayansu.

Abba ne ya ɗan kalli Ramadan dake cewa.
“Eh kasan mgnin ne zai ɗan saka jin bacci”.
Kai suka gyaɗa alamun gamsuwa.

Dai-dai lokacin da suka shiga falon ne Riyyam-nsra ya lumshe idonshi sabuda sabida ƙamshin masar da Mamy ke toyawa wanda duk ranar jumma'a take yinshi bisa umarnin Rayyern za'a cika manya-manyan kuloli kana ta dama kunun gyaɗa suna kaiwa tsangayar al'majirai”.

Da sauri ya nufi Kitchen din yana cewa.
“Mamy Barka da safiya”.
Murmushi tayi tare da sauƙe kaskon tuyan dan tun ƙarfe huɗu take farawa in lokacin salla yayi sai taje tayi kana tazo taci gaba.
So yanzu ta gama.
“Barka dai Riyyam-nsra kun dawo ko”.
Kai ya gyaɗa mata yana kallon tukunyar ferfesun data sauƙe.
Shaƙan zazzafan ƙamshi yayi tare da cewa.
"Wow special Mamy girkinki da daɗi”.
Juyowa tayi ta da sauri jin ƙamshin turaren Rayyern.
Ƙarasowa yayi cikin Kitchen din.
Gefenta ya ɗan tsaya, tare da buɗe manyan kulolin.
Ita kuwa foodflask ɗin da ta zuba musu breakfast ɗinsu a ciki ta nunawa Riyyam-nsra tare da cewa.
“Kai manasu Dinning”.
Da sauri yace to kana ya ɗauka ya fita.

Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa.
“Rayyern ya jikin naka?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Na worke”.
Cikin jin daɗi tace.
“Alhamdulillah, Allah ya ƙara mana lfy”.
Amin Amin suka amsa shida Riyyam-nsra.

Ramadan kuwa da Abba suna can falo, da alamu mgnar aure Ramadan keyiwa Abba duk ya marairaice.
Cikin haɗe fuska Abba yace.
"Kai da Allah tafi daga nan, Yayanka ma baiyi aureba sai kai ai dole dai ka jira sai yayi ko”.
Fuska ya kwaɓe tare da longobar da kai kana cikin girmamawa yace.
“Toh Abba”.
Yana faɗin hakan kuma ya miƙe ya nufi Kitchen ɗin.
Da ido ya bishi yana mai jin zafin tsawar daya daka mishin a ransa Allah ya sani baya son yin abinda zai b’atawa yaranshi rai more especially Rayyern.

```Special people group 1k ne karamin group kuma 500 BABBANCINSU a yawan posting ne```

Rayyern kuwa dake gefen Mamy cikin nitsuwa yace.
“Mamy kada Ramadan ya kai masar tsangayar malam Babayo.
Ya bari yau tsanƙayar Malam Mai-nasara zan kaishi, in Abba ya amince”.
Juyowa tayi ta ɗan kalleshi tare da cewa.
“Toh Allah yasa ya amincen”.
Amin yace yana mai bin bayanta suka fito.
A Dinning area Suka haɗu da Ramadan da yayi fuskar tausayi,
Ɗan zuba mishi ido yayi kana ya kauda kanshi ya nufi tsakiyar falon.

Mamy kuwa gefen Ramadan da Riyyam-nsra da suka zauna bisa Dinning table tayi kana ta kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Baka kaiwa su Baba Mauɗo nasuba”.
Da sauri Riyyam-nsra ya miƙe tare da cewa.
“Toh”.

Kana ya ɗauko kulolin da plate cups and spoons. Ya wuce.

Shi kuwa Rayyern a nitse ya zauna gefen Abban nasa, cikin sanyi yace.
“Abba”.
Numfashi ya ɗan fesar kana yace.
“Na'am Rayyern, ya akayi”.
Yayi mgnar cikin tsananin kulawa.
Cikin yanayin neman al'farma yace.
“Abba sadakan nane nace, dan Allah yau ka amince mu kaishi tsangayar Mai-nasara”.
Ga mmkinsa sai yaji Abba yace.
“Toh Allah ya bada ladan”.
Cike da mmki yake kallonsa yana kuma muƙewa,
Numfashi ya fesar fahimtar Abba yana cikin zurfin tunanine shiyasa ya amsa a sauƙaƙe.
Hakan yasa da sauri ya dawo Dinning area.
Cikin bada umarni ya kalli Ramadan da Riyyam-nsra da ya shigo yanzu yace.
“Yauwa taso maza ku ɗauki womas ɗinan ku kai min cikin mota”.
To sukace kana suka fara ɗauƙa.

Shi kuwa da sauri ya haura sama ya ɗauko car key ɗin nasa.

Koda ya sauƙo a hankali yace.
“Toh Abba na tafi”.
“Sai ka dawo”.
Ya bashi amsa da alamun har yanzu yana cikin nazari ne.

Yana fita su Ramadan na fita da kulolin ƙarshe.


Riyyam-nsra ne ya buɗe mishi gate ya fita.

Kana ya rufe sannan suka dawo cikin gida.

Bayan duk sun zauna kan table.
Mamy ta kalli Ramadan tare da cewa.
"Kira Abbanku”.
To yace kana ya miƙe ya sauƙo steps ukun tare da cewa.
“Abba breakfast is ready”.
Wani dogon numfashi mai nauyi yaja ya sauƙe a hankali kana yace.
“Toh”.
Sannan yazo saida ya zauna ya kallesu cikin kulawa yace.
“Rayyern fa!?”.
Cikin nitsuwa Riyyam-nsra yace.
“Abba ba yanzu ya fita kai abincin al'majirai ba”.
Kai ya jinjinawa Riyyam-nsra.
Ita kuwa Mamy cikin fahimtar halin da yake ciki ta zuzzuba musu breakfast ɗin kana suka fara ci.


Mai-nasara Hospital.

Suna cikin hirar Jannart ta ɗan gyara konciyarta tare da lumshe idonta lokaci ɗaya bacci yayi awon gaba da ita.
Hakanne yasa Abba koma gida.
Aka bar Aunty Dijat.
Abba na tafiya ba dadewa Mom da Abdul suka iso.

Kasan cewar tana baccine yasa suka koma gefe suka zauna suna ɗan taɓa hira sama-sama gudun kada su tasheta.

Yayinda Abdul yake riƙe da wayarta.
Yana mgna da Salman.

Nan ya gaya mishi suna asibiti.

Koda Dr Sulaiman yazo ya dubata.
Ganin tana bacci ya shaida musu jikin da sauƙi sosai.


Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara.
A hankali yayi parking a gaban tsangayar malam Mai-nasara.
Kana ya fito,
Cike da Mamiki Uncle Mustapha da shima yanzu ya iso da abincin al'majirai da yake kawowa daga gidansan.
Dan al'majiran malam Mai-nasara basa yin Bara shi da yaransa suke ciyar dasu.

Da sauri ya nufi Dr Rayyern cike da mamaki yake cewa.
“Ikon Allah wa nake gani kamar Dr Rayyern Mai-nasara?”.
Da sauri ya juyo suka fuskanci juna, musabiha sukayi cikin jin daɗi yace.
“Ya Malam da jiki?”.
Cikin jin daɗi yace.
“Masha Allah mu isa ciki, malam na nan jiki yayi lfy sosai fa!.”
Ya ƙare mgnar yana miƙawa wani Gardi key ɗin motarsa tare da cewa.
“Yauwa Yayana gashi fito muku da abincinku”.
Da sauri Dr Rayyern Mai-nasara shima ya miƙa masa key ɗin motarsa tare da cewa.
“Ga wannan ma ka duba baya ka fito muku da abincin”.
Cikin jin daɗi Wanda Uncle Mustapha ya kira da yaya ya amshi key ɗin. Tare dayi musu godiya.

Shi kuwa Uncle Mustapha jagora yayiwa Dr Rayyern Mai-nasara,
har cikin gidan Malam Mai-nasara.
Kana suka nufi wannan falon.
Yana mai cewa.
"Duk ranar jumma'a Malam bai fiye amsar baƙiba, amman nasan kai na musamman ne, mu shiga”.
Ɗan guntun Murmushin yayi kana suka kutsa kai tare da sallama a baki.

Can Dr Rayyern Mai-nasara ya hango Malam Mai-nasara, zaune tsakiyar falon.
Yayinda wata kekkyawar tsohuwa ke gefenshi, da alamun abin karin kumallo take zuba mishi.
Ganin Dr Rayyern Mai-nasara ne yasa Malam yunƙurawa ya tashi zaune.
Cikin yalwataccen murmushi ya miƙo mishi hannu tare da cewa.
“Masha Allah. Wa nake gani kamar Dactana mai Nasara”.
Hannunshi ya miƙa mishi ya jawoshi ya zaunar dashi kusa dashi.
Yayinda ya kalli Uncle Mustapha dake cewa.
“Ai kuwa shine dai Malam”.
Hannunshi ya ɗaura tsakiyar kan Dr Rayyern Mai-nasara tare da cewa.
“Lallai.kuwa yau ka amsa sunanka Mai-nasara dunda kayi nasarar ganina da safiyar jumma'a.”
Cikin son dattijon yace.
"Alhamdulillah Nasara ta haɗu da nasara kenan”.
Murmushi sukayi baki ɗayansu.
Yayinda tsohuwar nan kuma ta zuba mishi ido tana mai mishi wani irin kallo.
Kai ya juyo ya kalleta tare da cewa.
“Barka da safiya”.
Gyara zamanta tayi tare da sauƙe numfashi kana cikin kulawa tace.
“Barka dai Mai-sa'a. Yau dai da Malam zakayi karin kumallo”.

“Sosai ma kuwa”.
Malam Mai-nasara yace yana mai gyara zamanshi.
Ita kuwa tsohuwar kekkyawan akoshin dake tururin danderun naman ragon ne, ta turo tsakiyarsu.
Kana ta jawo ɗayan kuma tuƙeƙen tuwon alkmana ne mai kyau.
Da miya a kanshi miyar ɗanyar kuɓewa mai kyau tana ƙamshin man shanu, da ƙamshin ɗumamen.
Sai kuma bread mai kyau na masu ciwon sugar sai flask. Da cups biyu.
Misa alamu dai da basu zoba da tare zasuci abinci da tsohuwar.
Kai Rayyern ya ɗan jinjina tare da cewa.
“Alhamdulillah fa malam kaci kawai”.
Cikin kula Malam yace.
“Ina muci dai, ai dole kaci, tunda ba giya bace, ko kyamar tsoho kakeyi ne?”.
Da sauri ya jujjuya kanshi alamun a a.
Ita kuwa tsohuwar nan ɗan ƙaramin kwaryar dake gabanta da ruwa a ciki ta tura masa tare da cewa.
“Toh wonke hannunka kuci”.
Abu kamar wasafa dole suka matsa mishi.
Allah ya sani yana son tsohon haka yasa ya ɗan gyara zamanshi,
cikin nitsuwa yace.
"To a bani tea”.
Da sauri ta haɗa mishi tea.
tare da amsar akoshin danderun da Malam ke miƙo mishi.
Dole yasa hannunshi cikin kwaryar ya wonke.
Kana ya gyara zamanshi tare da kallon Malam yace.
“Malam ya jikin naka kuma?”.
Loman tuwon daya sa a baki ya haɗiye kana yace.
“Alhamdulillah Rayyanu naji sauƙin jikina sosai sai yawan ci”.
Juyowa yayi ya kalli Uncle Mustapha dake cewa.
“Dan Allah Dacta kaci girkin Innayinmu, zaka jishi da banne dana sauran matan duniya”.
Ya ƙare mgnar yana miƙewa tsaye.
Yayinda ita kuwa Innayi tayi murmushi tare da cewa.
“Kwarai kuwa har matarsa ma”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Toh ki bari a yaba miki mana”.
Dariya sukayi duka.
Kana su suka fita.

Ya rage dagashi sai Malam Mai-nasara.

Wanda ya maida hankali kan cin abinci.
Shi kuwa tea ɗin ya ɗan zuƙa a hankali.
Idanunsa ya lumshe tare da buɗe su.
Tabbas Mamynshi ƙarshece a girki amman daga shayin tsohuwar nan yaji da ban.
A hankali ya ɗago kanshi ya kalli Malam dake cewa.
“Dan Allah Rayyanu kaci naman nan zakaji dadinshi”.
Kai ya jinjina kana yasa hannunshi cikin akoshin.
A nitse ya ɗan yagi tattausan tsokar kana ya kai bakinshi.

Wani irin tsinkewa yaji yawunsa yayi tare da amsar saƙon ɗanɗanon naman nan mai cike da ƙamshi.
“Ya Salam”. shine abinda ya faɗa a zuciyarshi.
Tea ya kurɓa kana ya ɗan kalli Malam cikin hikima yace.
“Ni ko Malam sunan kakanka ne Mai-nasaran ko?”.
Kai malam ya jujjuya mishi alamun a'a.
Cikin jin daɗi ya gyara zamanshi tare da ɗan ture akoshin gefe.
Sosai naman ya mishi daɗi to amman matsalar bazai iya cin abincin nama da sassafe hakaba.
In yasha tea ɗin kawai ya gamsu sai irin 11-12 haka zai iya cin wani abu kuma.
“Kaci mana”.
Malam yace.
Kai ya gyaɗa kana ya kafe kofin a baki ya zuƙe team ɗin kana ya ajiyeshu gefe, tare da cewa.
“Toh Alhamdulillah na ƙoshi”.
Murmushi kawai malam yayi tare da wonke hannunshi.
Shi kuwa a hankali yace.
“Toh Malam menene Tubalin sunan naka”.
Toro mishi kwaryar malam yayi tare da yin dariya sosai.
Hannunshi yasa yana wonkewa yana kuma kallon tsohon yana murmushi ganin yadda yake dari.

Cikin tsagaita dariyar Malam yace.
“Lallai kam ka nemi jin tsohon lbri”.
Sai kuma ya ɗan kishingiɗa.
Da sauri Dr Rayyern Mai-nasara yace.
“A'a Malam tashi zaune, ba'ason mutun ya kwanta bayan cin abinci a take, anfi son ka ɗan zauna koma motsa jiki, ko ga masu lfy kwanciya da zaran an gama cin abinci yana haifar da cutar sugar.”
Da sauri Malam yace to kana ya zauna tare da cewa.
“Tubalin sunana ya samo asaline tun ina yaro ɗan shekaru tara a duniya, da aka kaini al'majiranci.
Anan na samu sunan Mai-nasara nawane na kaina bana Babana bane ko kakana”.
Sai kuma ya ɗanyi shiru ganin hakane yasa Dr Rayyern cewa.
“Tah yaya aka sama sunan?”.
Numfashi ya ɗan fidda kana yace.
“Asalina ɗan jihar Adamawa state ne, yankin Jada al'majiranci iyayena suka kawoni jihar Kano.
Nazo kano bani da kowa sai Allah sai malamina, wanda a ƙalla yakeda ɗalibai sun kai ɗari biyu,200 baya shayar damu bare ci damu.
Mafi akasari ranaku ɗalibai kaso 100 cikin 200 da yunwa suke kwana da wuni.

Wasu kan shiga gidaje 7 ba'a kirasu ba, cikin ikon Allah ni kuma duk gidan dana shiga sai an kirani kuma sai an bani abinci.

Haka yasa abincin da nake samu yafi ƙarfin cikina, sai nake rabawa yara kamata.
Yayinda wasu manyan ma ke zuwa suna roƙata inje musu Bara, duk wanda ya bani akoshinsa sai na cika mai nake dawowa.
Toh fa daga nan ɗalibai suka samin Mai-nasara. Cikin ikon Allah kuma nasarar ta bini. Nayi karatu na tsawon shekaru goma sha biyu na haddaci al'ƙur'ani mai girma da tarin littattafai.
Daga nan kano ta zamemin uwa goya marayu, malam ya bani yarsa itace wannan data tafi yanzu na aura.
Kana na fara kasuwanci Allah cikin ikonsa ya samin al'barka a harkar kasuwanci na.
Na ƙara mata biyu ƙannena suka dawo gareni da iyayena.
Allah ya azutani da yara sama da 37.
Kaga ai nasara ta yiwu, duk da bayan nasarar na fuskanci ƙalubale akan d’a mafi soyuwa a gareni”.
Cikin gamsuwa Dr Rayyern Mai-nasara yace.
“Allah sarki”.
Da sauri ya katse shi da cewa.
“Kai kuma menene TUBALIn sunan naka”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“Nima ɗalibai ƴan uwanane suka samin shi.
Sabida duk jarranawar da zanyi bana faɗunwa.
Kuma duk abinda nasa gaba sai na cimmasa”.
Shigowar Uncle Mustapha ne yasa suka tsagaita da hirar, kana akaci gaba da hirar dashi.
Har sai tara dai-dai suka sallami Malam suka tafi

A bakin gate suka samu wannan gardin ya basu keys ɗin su suka tafi.

Daga nan kai tsaye gida ya koma.

~0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 special Group 1k karami kuma 500~

A can MAI-NASARA Hospital kuwa.
Ma'aikatan Arewa 24 TV ne, kusan su shida ke cikin ɗakin da Jannart ke konce.
A hankali ta kalli Aisha Lawal dake ta gyara mata gashin kanta dake kan kafaɗunta.
Salman ta ɗan kalla cikin nitsuwa tace.
“Yah kiraka kuwa?”.
Cikin yanayin tausayawa yace.
“Keda baki da lfy me ruwanki da kiran wani”.
Hajia Rabi'ah ce ta ɗan yi murmushi tare da cewa.
“Yoh keda ma gaki a asibitinsa”.
Aunty Fauziyya D Sulaiman kuwa cikin kula da nagarta ta ɗan shafa goshinta tare da cewa.
“Ai dukkan uzuri bayan lfy yake, kada ki damu kinjiko Jannart MD da kansa yace a gaidaki da jiki”.
Cikin jin daɗi ta kalli Fauziyya D Sulaiman tare da cewa.
“Ngd matuƙa My Aunty”.
Mom kam dake gefe sai godiya takeyi musu.
Sun jima anan kana suka ajiye ledodin Fruits da suka kawo mata,
Kana suka fita.
Har sunje bakin ƙofar fita Salman ya juyo jin tana cewa.
“Salman kada ka manta fa saura kwana biyar kacal”.
Murmushi yayi tare da cewa.
“In dai ina raye to kisa a ranki kinada GARKUWA”.
Yana faɗin haka suka fita.


Kasan cewar yau jumma'a haji babbar ranace yasa, dukkan Al'ummar musulmai suke cikin yanayi na musamman duk kan maza nata shirin zuwa sallan jumma'a tako ina.

Sha biyu da rabi dai-dai haka take a gidansu Dr Rayyern Mai-nasara ma.

Yayinda hakama Barrister Kabir kasan cewar duk a Nassarawa G.R.A suke yasa gaba ɗaya masallacin Al'furƙan suke da niyar zuwa.


A hankali ya kalli Mamy dake ce mishi.
“Toh Rayyern me kake so in dafa maka ne? Ni bana son zamanka da yunwar nan fa”?.
Yana mai haurawa saman yace.
“Mamy yanzu lokacin jumma'a ya ƙara to, bari inje inyi shirin salla in na dawo zanci abincin”.
Da ido kawai ta bishi ganin tuni ma ya haura sama.

A hankali ya ɗan juyo ya kalli ƙofar Bedroom din Ramadan jiyo muryarsa shida Riyyam-nsra alamun suma shirin tafiya jumma'a sukeyi.
Dan yana jiyo muryar Riyyam-nsra na cewa.
"Nima fa mai gare zaka bani in saka Hamma Ramadan”.
Kai kawai ya jinjina ya wuce Bedroom ɗinsa.
Kai tsaye Bathroom ya wuce.

Bayan 15mn ya fito ɗaure da towel.
Gaban dreesing mirror'nsa ya nufa cikin yanayin sauri-sauri ya busar da sumar kanshi tare da shafa mai kana ya miƙe ya nufi gaban ƴar ƙaramar Driver'n'shi na glass dake gefen babban durowar.

A hankali ya buɗe, ido ya ɗan zubawa ƙananan kayanshi dake kimtse a ciki.
Wata tattausan boxer and single ya zaro masu ɗan karen taushi.
A hankali ya meda marfin ya rufe, sauri-sauri yasasu kana ya zare towel din ya cilla gefe ganin ɗaya ta kusa cika.

Babbar durowar ya buɗe,
Wasu kayan ya zaro Getzner fara ƙal mai masifar kyau da sheƙin maiƙo.
Riga da wondo.
Sauri-sauri ya saka su.
Kana ya koma gaban Driver'n'shi na glass din hula damanga ya zaro Royal blue kalan zaren surfanin da akayi wa Getzner aikin rigar.
Sunkuyowa ya ɗanyi toms masu masifar kyau samfarin Italy ya zaro suma Royal blue.
Kana ya dawo gaban dreesing mirror'nsa.
Kafa hular yayi irin kafin nan da matasa ke cewa.
Babu ruwanka da duniya.
Wato ya ɗan ture hular ta koma baya kaɗan hakan yasa tattausar sumarshi ta fito tana zuba sheƙi sajenshi ya kwanta lib sai sheƙi yake siraran lips dinsa suma suna sheƙin taushi.
Sai kuma ya sunkuyo yasa fararen sawunsa cikin takalman.

Agogon Daimond dake kan mirror'n ya saka.
Turarensa Oud Zauji mai masifar daɗin shaƙa ya fesa.
Kana ya zari car key ɗinsa Dan lokacin ya ɗan so ƙure mishi.

Da sassarfa ya sauƙo kan steps din har yana takawa bibbiyu.

Ba kowa a falon yasa da sauri yasa kai ya fita, ko su Baba Mauɗo duk sun tafi sai Ari.


Haka yasa ya buɗe mishi gate kana Suka tafi tare haka nan yake ta jin tsinkewan zuciya da faduwan gaba.

Numfashi ya ɗan fesar lokacin daya shiga cikin masalacin sabida har yanzu huduba akeyi.

Inda ake hudubar akan illar cin riba.

Sosai aka nitsu, bayan an ida hudubar ne kuma aka kabbarta sallan...

Bayan sunyi raka'a biyun, an zauna zaman tahita.
Sun ida zasuyi sallama sunyi gefen dama sun juyo hagu.
Kenan Barrister Kabir ne dake gefen daman Rayyern ɗin ne ya ɗan leƙo fuskar Dr Rayyern bayan ya sallame.

Wata iriyar sassayar ajiyar zuciya mai nauyi ya sauƙe tare da ɗaga hannunshi sama ya fara yiwa ubangiji kirari cikin zuciyarsa yana ƙara neman zaɓin Allah kan manufarsa da addu'a in al'khairi ne Allah ya nufeshi da ida nufinsa a wannan lokacin.
Yayinda shima Rayyern da mafi akasarin mutane hakan sukeyi.
Bayan an idar da salla ne, Dr Rayyern na fita yaji an riƙo hannunsa tare da ce masa.
“Assalamu alaikum”.
Da sauri ya juyo tare da cewa.
“Wa alaikassalam”. Fuskarshi ya ɗan yamutsa alamun tunani kana a hankali yace.
“Lfy”.
“Lfy lau Alhamdulillah Dakta”.
Barrister Kabir ya faɗa yana mai jawo hannun Dr Rayyern ya nufi can kan titi wurin motarsa.

Ba tare da ya ƙara mgna ba yabi bayansh.
Suna zuwa ya buɗe suka shiga....!

Anan asibitin kuwa, da Yamma Dr Sulaiman ya bawa Barrister Kabir takardar sallama, sabida sosai jikin Jannart yayi sauƙin.

Ya ƙara da cewa.
“Idan an barku kun ƙara kwana tofa sai ranar Monday za'a sallameku. Toh kuma tunda jikin da sauƙi gwara
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment