Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD



Da kasan ya bawa Malam magungunan yasha.
Tare dayiwa su Alhaji Ibrahim bayanin yanda akullum Malam din zaina shan maganinsa.

Godiya sukayi mishi sosai, ganin da yayi kuma lokaci yadan ja sosai ne, yasa shi kallon su Ramadan tare da cewa su tashi su tafi.

Cikin aminci sukayi wa Malam din sallama, inda Rayyern ya shaida masa cewar zaidawo ya sake dubashi.

Koda suka tashi tafiya kuwa har wajen motocinsu Uncle Mustapha da kuma Alhaji Abdallah suka rakasu.
Basu koma cikin gidan ba kuma harsaida suka ga tafiyansu Rayyern din.

Daga b’angaren su Raayyern kuwa kaitsaye gida suka nufo.

Direct Rayyern dakinsa ya wuce, saboda yana son yin wanka, sannan akwai kuma wani aiki da zaiyi a laptop d’insa.

Yayinda su Ramadan da Riyyam kuwa, anan falo suka zauna inda Mom ta kawo musu abinci suka ci.

Bayan sun gama cin abincinne kuma suka wuce masallaci danyin sallan azahar, ciki kuwa harda Rayyern wanda ya sanja shigarsa zuwan wata farar jallabiya.


Jannart.

Kwance take akan makeken gadonta, wanda akoda yaushe yake shumfud’e da lallausan bedsheet na alfarma.

Irin kwanciyarnan ta rubda ciki tayi, Yayinda ajikinta take sanye da wata baby gown marar nauyi.

Lumsassun Idanunta ta ware ahankali tare kuma da sauke wani ajiyar zuciya mai
Cike da tarin damuwa.

Lallai Tabbas tana da buk’atar y’anci acikin rayuwarta, rayuwar da har yau ta kasa tantance wacce kalar rayuwa ce, rayuwar da kwata kwata babu haske acikinta sai tarin damuwa, kunci da kuma kadaici.
Mirgina wa tayi a hankali kana taci gaba da tunani.

Yayinda akowanni kwanan duniya da irin kalubalen da take fuskanta, acikin kowanni sa’a kuwa zuciyarta na bugawa da tarin tsananin tsoron abunda zaije ya dawo.

Lallai Tabbas tana da buk’atar haske acikin rayuwarta, haka kuma tana da buk’atar abokin rayuwar da akoda yaushe zai debe mata kewa, Sam arayuwarta batasan wani abu Waishi ingantaccen farinciki ba, akullum damuwa kawai da tsoro ta sani.
Haka kuma akowani bayan minti guda tsoronta yakan rub‘anya, tare da mummunan bugun zuciya akan abunda Yayanta Junaid ke neman aikata mata.

Saudayawan lokuta takan tambayi kanta, cewar shin Ya Junaid wani irin d’an uwane? Meyasa akoda yaushe bashi da fata ko buri saina keta haddinta?
Tabbas tunaninta yakan neman watsewa aduk lokacin da ta tuna cewar Ya Junaid din yayanta ne Uwa daya Uba daya.

Shin Meyasa Rayuwa take garari da ita?

Karar wayarta dake aje bisa bedsite ne ya katse mata duk wani tunanin da takeyi.

Ahankali tasa hannu ta share dan guntun hawayen dake kwance agefen Idanunta, wayartata dake ta faman tsuwa ta dauka, ganin kuma sunan Salman ne ke yawo akan screen din wayar yasata picking da dan hanzari.

“Y’ar Hutu wato kinanan kina hutawa agida ni kuma kinbarni da wahalan aikin ki ko.”

Cewar Salman.

Itakuwa Idanunta ta lumshe tare da d’an gyara kwanciyarta.

Cikin muryarta da tayi sanyi sosai tace.

“Sorry Salman gaba d’aya yau banajin karfi sosai ajikina ne, Impact ma nina fara sarewa da wannan aikin wallahi, I’m tired because mutumin nan kamar bazamu samu daman ganinshi ba.”

Murmushi Salman yayi tare da d’an gyara zamansa kana cikin son bata karfin guiwa yace.

“No Jannart don’t stress your self, Insha Allah yau zamu had’u dashi, kinsan na samo mana information akansa, so Yanzu dai anjima kishirya muje hospital d’insa, Insha Allah zamu samu ganinsa.”

Idanunta dake alumshe ta bud’e tare da sauke ajiyar zuciya.

“Thank you so much Salman Insha Allah zan shirya by 3 pm sai muje, zanzo office saimu tafi aboye batare da kowa ya sani ba.”
(Hattara garemu iyayen yara, yawan tsaro baya hana yaranmu yin abinda suke so. Tsananta addu'a da jawo yara a jiki yafi tsananta tsaro da zafi),
“To saikinzo.”
Salman din ya fada tare da kashe wayar.

Itakuwa Jannart bayan ta ajiye wayartata agogon dake sakale ajikin Bangon dakin ta kalla.
Wanda ya nuna mata 2:30 pm.

Zuro kafafunta kasa tayi daga kan bed din, batare da ta tsaya sanya ba kuwa ta shige bathroom danyin wanka.

Sanin da tayi cewar basu da enough time ne kuma yasa bata wani bata lokaci awajen yin wankan nata ba.

Koda ta fito mai kawai ta shafa ajikinta, sai kuma powder and oil lipstick.
Yayinda tabi zara zaran eye lashes dinta da mascara.

Bayan kuma ta feshe jikinta da sassanyan body spray ne.

Ta karasa gaban Sif din kayanta, inda ta zaro wani dogon wandon pallazo white and white colour roba t shirt wanda yake da ɗan fadi kaɗan ta kasa kuma yazo kusa da guiwarta.

Cikin nutsuwa ta sanya kayan ajikinta, tare da daukan wani hill shoe mai kalan blue ta saka ak’afanta, kana kuma ta yane kanta da wani dan vail shima mai kalan blue.
Akan tsintsiyar hannunta kuwa wani anklet ta saka mai kyau.

Wanda ya sake kawata kyaun kwalliyar tata.

Murmushi ne ya dan bayyana akan fuskarta, saboda Kallon irin kyaun da tayi acikin madubi, Yayinda kayan jikin nata kuwa sukayi matukar amsarta tana matuƙar son ƙananan kaya, ta gaza gano illar sasu a ko ina.
Tabbas ayau din ko makiyinta bazaiyi mata kallo daya ya dauke kansa ba sosai kam tayi kyau.

Wata yar madaidaiciyar handbag blue colour ta rike ahannunta bayan ta rike wayarta ahannunta na dama ne kuma ta juya ta fice daga cikin dakin.

Anan Cikin falo ta samu Momy da kuma Abdull zaune.

Ganin ta cikin shiri da sukayi ne kuma yasa Momy cewa

“A’a Jannart fita zakiyi ne.”

“Eh Momy zanje office amma bazan jimaba Zan dawo Insha Allah.”

“To adawo lafiya”

Da Ameen ta amsa, Yayinda Abdull kuwa yace idan tazo dawowa ta kawo masa abundadi.
Da to kai ta amsa masa kana tasa kai ta fice daga cikin falon.

Tana fita compound din gidan kuwa, kattin samudawan guard dinta suka tattaso.

Har acikin ranta Allah Yasani kwata kwata batason wayanann mutanen da suke tsaronta, saidai kuma babu yanda ta iya.
Haka ta shiga mota suka fice daga cikin gidan.

Direct Nasarawa G.R.A ta nufa inda anan wajen aikin nasu yake.

Suna isa kuwa ta fito daga cikin motar, kaitsaye ta wuce cikin Arewa 24 din ɗan madaidacin ma'akatane, wanda yake kamar irin manyan gidajen nan ne na al'farmar.
Sam wurin gidan TV'n bai cika girmaba, dan bazaifi wani gidanba, ma, sai dai zubi da tsarin wurin shine mai tafi da hankalin mai kallo, kota ina ka wulga shuke-shuke ne masu kyau da ɗaukar hankali kamar a kasashen turawa, Gate ɗinsu daya ne ta inda ka shiga ta nan zaka fita, can ciki kuma Office-office. Masu kyau ma dai-dai-ta na al'farmar da hall ɗinsu sai ɗakunan haska shirye-shiryen su.

Duk inda ta gilma kuwa sai abokan aikinta sun bita da ido, Yayinda kowa ke yaba irin baiwar kyau da Allah ya bata manya daga ciki irinsu Aunty Fa'iziyya D Sulaiman kuwa ƙuruciyarta suke gani a fili da illar shigarta da ta meda jikinta.

Direct office dinsu ta wuce kaitsaye.

Inda ta samu Salman da kuma Aysha Lawan suna zaune.

Nanfa ta tsaya gaisawa da Aysha kawartata.
Acan gidansu Rayyern kuwa.

3:00 am dai-dai ya fito daga wanka, inda ya shirya kansa cikin wani black tracksuit, masu kyaun gaske, da suka matuk’ar amsar jikinsa.

Yayinda ak’afansa kuwa ya saka wasu had’add’un sneakers shoe masu kyau da taushi.

Bayan ya gama kimtsa kansa ne kuma, ya shafa wani irin fitinannen turare mai tsananin kamshi.
Bud’e drawer’nsa yayi.
Shiru ya ɗan
Tsaya yana mai kallon Alkyabbun dake jere a saman kayanshi.
Haka nan yaji yana son gwada sa alkyabbar a jikinsa yaga ya shigar zatayi mishi.
Numfashi ya ɗan fesar a hankali inda anutse ya zaro daya daga cikin alkyabbun da Malam Mai-nasara ya bashi.

Warware alkyabban yayi tare da soma kare mata kallo baƙace mai kyau irin mai sheƙin nan gefe da gefenta an ƙawayashi da zare golding, kai ya jinjina saboda shi kansa ya yaba da kyau da kuma haduwarta, musamman daya fahimci cewar ba karamin kudi aka saka wajen sayan duk alkyabbun ba fuska ya dan yamutsa dan sun cika nauyi.

Addu’an sanya sabon kaya ya karanta, "Alhamdulillahil laxee kasani haxal saubah warazaƙani min gairi hauli minni walaƙuwah".
dai-dai lokacin daya ke daura alkyabban akan kayan dake jikinsa.

Tare kuma da daukan harami ya daura akansa.

Ya Allah!
Bakaramin kyau Dr.Rayyern Mai-nasara yayi ba, alokacin daya gama kimtsa kansa Cikin alkyabbar.

Kyau yayi sosai da sosai, wanda shi kansa saida ya sake yiwa Allah Godiya daya halittosa amatsayin bil’adama musulmi mai shiga ta kamala.

Koda ya kalli kansa amadubi numfashi ya ɗan fesar a hankali saboda yanda yaga ya fito tamkar Limami.

Wayarsa da kuma wata yar jaka dake gefen gadonsa, wanda ya kusan cika cikinta da chocolates ya d’auka, tare da rik’e jakan ahannunsa, kaitsaye ya fice daga cikin dakin.


Ahankali yake saukowa daga kan steps d’in...!


Uhum muje-muje dai sunan wata mota, lbrin yanzu anka fara.



By
*GARKUWAR FULANI*






📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*


PAGE 11
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE ne*

_Littafin TUBALI na kuɗine hamzarta ki biya ki karanta cikin salama special Group 1k ne karamin group 500 kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, ko kuma ki sayi katin MTN ki copy number's ɗin katin ki turo min_

*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

*NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki Hajia yan mata. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da ni'imantaccen kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*


Sautin takun takalminsa dasu Ramadan sukaji ne kuma yasa su maida hankali zuwa gareshi.

Idanunsu gaba daya suka zuba mishi, tare da had’a baki gaba dayansu suka ce.

“Masha Allah! Tsarki ya tabbata ga sarkin daya halicce mu ya kuma halicci Hamman Rayyern dinmu.”

“Innalillahi kai Hamma Rayyern kayi kyau sosai, wallahi kamar daga Saudiya kazo.”

Cewar Riyyam-nsra daya hangame baki da hanci yana Kallon Rayyern d’in.

Shikuwa Rayyern karasa saukowa cikin falon, yayi ganin Abba da Mamy zaune ne kuma yasashi, d’an rusunawa ahankali yace.

“Mammy a bani Bootle water mai sanyi.”

Mamy da ita kanta ta yaba da tsananin kyawun da al'kyabban jikin nasa tayi masa ne ta saki murmushi, tare da fadin.

“Masha Allah Rayyern kayi kyau, wannan suturar tayi maka kyau, Lallai kuwa ashe Rayyern din nawa ya kerewa sa’a.”

Ɗan guntun Murmushin yayi, Cikin kuma alaman jin kunyar yabonsa da Mamyn nasa tayi yace.

“Nagode sosae Mamyna.”

Abba daya kafe Rayyern din da ido kuwa baya ko k’yaftawa, fuskarsa cike da mamaki yace.

“Rayyern wannan shigar fa yaushe ka fara ta? sannan a ina ka samo alkyabba mai tsananin kyau haka?”

D’an sunkuyar da kansa k’asa yayi, tare da kama y’an yatsun hannunsa ya soma murzawa.
Sam arayuwarsa shi bai iya k’arya ba, impact ma arayuwarsa babu abunda yafi tsana kamar k’arya, bayayin k’arya bakuma yaso ayi masa.

Duk da kuwa yasan Abban nasu bazai so abunba so gskyar da zai fada ba, amma ya zama dole ya gaya masa gaskiya, saboda karya ba d’abi’arsa bace.

“Kayi hakuri Abba Malam Mai-nasara ne ya bani kyautan Alkyabbu guda bakwai.”

Idanu Abba ya kankance cikin kuma nuna rashin jin dadin hakan ya kawar da kansa gefe.

Ganin hakanne kuma yasa Rayyern d’in, ya d’an rank’wafar da kansa.

Kana cikin sigar ban baki yace.

“Kayi hakuri Abba, idan bakason shigartawa sainaje na cire.”

Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kana ahankali yace.

“A’a ni Bance Banason shigarka ba, kayi kyau Tabbas kuma shigar alkyabba shigace da take da matuk’ar mutumci, gashi kuma ta bayyana tsananin haiba da kwarjininka, saidai amma ka kiyaye nan gaba bafa na son wata alaƙa a tsakaninku.”

Kai Rayyern din ya jinjina kana cikin girmama zancen Abban nasu yace.

“Nagode Abba kuma Insha Allah zan kiyaye.”

“Shikenan.” Abban ya fad’a atakaice.

Riyyam-nsra kuwa cikin kasa kosawa da Kallon yanda Hamadan nasu yayi kyau yace.

“Please Hamma Rayyern Ina zakaje.”

“Polo.”
Ya bawa Riyyam din amsa a taƙaice kuma dai-dai lokacin da yake kokarin fita daga falon.

Da sauri Riyyam din ya tashi yabi bayansa, yana me fad’in.

“To Hamma Rayyern tsaya muyi video dan Allah.”

Ramadan dake zaune ma mik’ewa tsaye yayi yabi bayansu.

A compound din gidan suka tsaya, inda Riyyam sarkin tiktok ya saita wayarsa ya soma yi musu video dukansu uku.
Harda sa musu wata y’ar wak’a, shidai Rayyern Kallon Yaron kawai yakeyi, domin a wuni biyu kawai da sukayi da yaron, ya fahimci wani abu, da kuma irin d’abi’a da yaron yayi shura akai.

Saidai kuma baisan Meyasa ba yakejin yaron acikin zuciyarsa hakan yasa yake kasa yakiceshi.

Gama k’arasowarsu compound din gidan kuwa, yayi dai-dai da fitowan Baba Maud’o daga cikin d’an madaidacin Part ɗinsa dake gefen gate.

Yana fitowa dinne kuma ya sauk’e idanunsa akan Rayyern, dake sanye cikin al-kyabba.

Wani irin tsayuwa Baba Maud’on yaji zuciyarsa tayi, take kuma wasu irin abubuwa suka shiga dawowa cikin tunaninsa.
Saidai kuma Ina ayanzu kwakwalwarsa bata da wani buk’atar amsar kowani irin sak’o, wannan dalilin yasa zuciyarsa ke cigaba da bugawa da harbawa a hankali.

D’an matsowa kusa dasu Baba Maud’on yayi, tare kuma da sauk’e idanunsa akan Riyyam wanda keta faman bin wak’ar Justin Bieber me suna (Peaches) dake tashi awayarsa.

Idanu Baba Maud’o ya tsurawa yaron baya ko k’iftawa, Yayinda zuciyarsa ke cike da zallan mamakin, kamannin Rayyern dake kwance akan fuskar yaron.

“Baba Maud’o barka da yammaci.”

Cewar Rayyern.

Wanda maganan nasa ne kuma yasa Baba Maud’o dawowa cikin tunaninsa.

Murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa, duk da kuwa cewar rabin fuskartasa arufe take, amma hakan bai hana Rayyern din gane cewar Baba Maud’on murmushi yayi ba.

“Yauwa Barka dai Rayyern, yau kuma inazaka je haka naga kayi shigar da ta bayyana kyau da cikar haibarka.”

Murmushi Rayyern din yayi, tare da dan matsowa kusa da Baba Maud’on kana yace.

“Wurin wasan polo zanje Baba Maud’o".

Kai ya jinjina alamun gamsuwa.
"Shin ko akwai wasu abubuwan buk’ata naka da suka k’are, idan nazo dawowa saina sayo maka.”
Rayyern ya tambayeshi cikin mutunta ma'aikatan gidan nasu.
Again Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin kuma Jin dadin kulawan da su Rayyern din sukeyi dashi yace.

“A’a Alhamdulillah ayanzu kam bana buk’atar komai, saidai nace kayi kyau sosai cikin wannan shigar, amma baka daura hiramin naka dai-dai ba, Bari na gyarama irin yanda samarin makka suke saka nasu.”

Murmushi Rayyern din yayi, kana ya matso Baba Maud’o d’in ya gyara masa sakun hiramin.

Riyyam-nsra kuwa da d’an mamaki ya kalli Hamma Rayyern dinnasu, tare da cewa.

“Hamma Rayyern waye wannan mutumin, naga jiya da nazo banganshi ba.”

“Sunansa Baba Maud’o.”

Ramadam ya bashi amsa.

Saurin jinjina Kai Riyyam yayi, kana ahankali ya matso kusa da Baba Maud’o din.

Fuskarsa dauke da murmushi yace.

“Rawanin da kasa akanka zuwa fuskarka yayi kyau sosai Baba Maud’o, Dan Allah Hamma Rayyern kuzo mu d’auki hoton selfie tare dashi, saboda Idan na koma Ethiopia zan nunawa Mammyna, na kuma bata labarin yanda wasu daga cikin yan Nigeria sukeyin shigarsu.”

Ya fad’i hakan saboda baisan cewa Baba Maud’o’n shigar buzayen Niger 🇳🇪 yayi ba.

Kamar yanda ya buk’ata kuwa matsowa Rayyern da Ramadan sukayi, inda suka saka Baba Maud’o da Riyyam din atsakiya.

Hakanne kuwa yasa Baba Maud’o da Riyyam din ke iya jiyo sautin bugun zuciyar kowannensu, saboda yanayin yanda sukayi kusan ci sosai da juna, domin Riyyam dan sarkin son jiki, har rungume Baba Maud’on yayi ajikinsa.


Yayinda Ramadan ya karb’i wayar Riyyam d’in, yayi musu hoton selfie har kala biyu.

Bayan ya mikawa Riyyam din wayarsa ne kuma,
Rayyern ya juya ya shiga motarsa, driver’nsa yaja suka fice daga cikin gidan.

Ramadan da Riyyam kuwa zama sukayi dab’as Akan wani dan dogon Bencin da Baba Maud’o ke zama, haka kuwa suka sa Baba Maud’on agaba sunata hira, musamman Riyyam daya bud’e baki ya dinga shararawa Baba Maud’on labarai kala-kala, wanda duk rabinsu na abun dariya ne.


*Arewa 24 TV*

Jannart ne da Salman ke tafe acikin babban corridor din, da zai sadasu da compound din gidan tv'n nasu.

Anutse Jannart take takunta, Yayinda time to time take Kallon fuskar wayarta dake rike ahannunta.

Salman dake biye da ita kuwa, idan hankalinsa yakai dubu to duk akanta yake.

Baisan meyasaba hardai idan Jannart tana waje, baya tab’a iya dauke kansa daga gareta, koda kuwa yaya baya iya gajiya da Kallon tafiyarta mai kama data hawainiya.

Yayi Imani azuciyarsa cewa Jannart macece ta gasken gaske, ko acikin mata irinta basu da yawa.

Isowarsu jikin motarsa ne kuma yasa Jannart fakon idanun guard dinta ta shige cikin motar, kana cikin sauri tace.

“Please Salman kayi sauri mubar nan, Domin idan wayannan kattin suka ganni dakai ina mai tabbatar maka cewar akwai matsala.”

“Nikuwa nasan da cewar akwai matsala ai Jannart, abu mai sauki ne ma su samin bindiga akaina su harbeni, tsoron da ake baki agidanku ko Gwamna iyakaci.”

Salman din ya fada adaidai lokacin da yake ta da motar suka bar wajen.

Suna hawa titi kuwa Jannart ta sauk’e ajiyar zuciya tare da fad’in.

“Allah Yasa dai mudace mu samu ganinsa yau, amma mutum dan ya zama richest man shikenan kuma ganinsa saiya zama wahala.”

Shidai Salman murmushi kawai yayi kaman zaice wani abu kuma saiya fasa.

Kaitsaye suka nufi Mai-nasara Hospital.

Tafiyar mintuna kad’anne ya kawosu bakin kofar katafaren asibitin.

Kasancewar kuma ba ashiga can Cikin hospital din da mota, matuk’ar ba emergency bane, yasa Salman parking motar anan babban parking lot na asibitin, wanda shi kansa ya kusan kwatan wata karamar unguwa.

Bud’e murfin motar Jannart tayi ta fito, tana me k’arewa kyau da had’uwar asibitin kallo.
Lallai privet Hospital ne daya amsa sunansa, saboda daga ginin asibitin ma kasan ba kananan billions aka kashe masa ba.

“Mai-nasara Hospital! Lallai asibitin ya had’u.”

Jannart din ta fad’a tana me Kallon Salman.

Shima Salman din kallonta yayi, tare da cewa.

“To Kema da bakinki kin fad’a, yanzu kiyi imagine tayaya za ace kinsamu ganin mamallakin wannan wajen acikin sauki? karki manta kuma bawai iya Hospital dinnan ya mallaka ba, yana da companies, bama a iya Nigeria ba, wallahi Jannart wannan mutumin *Richest Man* ne na k’arshe.”

Kai Jannart d’in ta jinjina, domin ita kanta ayanzu ta yarda da hakan.

Kaitsaye kuma suka kutsa cikin asibitin.

Acan b’angaren Rayyern kuwa kaitsaye Wajen buga wasan polo suka nufa.

Koda suka isa wajen da haduwarsa da kuma kyawunsa ya darawa kwatance.

A parking lot driver’nsa yayi parking.

Bayan ya fito daga motar nasa ne kuma kaitsaye ya nufi cikin wajen.
Da kwata-kwata babu mutane acikinsa.
Duk da tsananin girman wajen kuwa, amma bakajin motsin komai saina tarin dawakai da kuma tsirarun masu kula dasu.

Wanda kuma hakan ya faru ne saboda zuwan Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, kasancewar idan har zaizo wajen To yakan biya mak’udan kud’ad’e ne, ta yanda ranar baza'a amshi kuɗin wasuba, harsai yayi wasansa ya gama ak’alla na tsawon awa 2, bayan ya tafi ne kuma sauran jama’a zasu dawo su cigaba da harkokinsu bawai kuma yana haka dan isa bane, sai dan sosai hayani kan iya sa mishi ciwon kai, yana kuma jin daɗi wasan polo a jikinsa.

Shigarsa cikin babban wajen wasan buga Polo dinne kuma yasashi, zare alkyabban dake jikinsa ya ajiye, tare da wayoyinsa harma da y’ar bag din da yasaka bottle water mai sanyi aciki.

K’arasawa yayi wajen tarin dokunan da akeyin wasan dasu, tare da zab’o wani farin doki, wanda mafi yawanci idan yazo shi yake hawa.

Batare da wani bata lokaci ba kuma ya dale saman dokin tare da rik’e Sandar buga k’wallon nasa ya soma sukuwa, tare da gabatar da wasan.


Mai-nasara hospital.

Salman da kuma Jannart dake tsaye abakin k’ofar office d’inne suka tsaya suna Kallon juna.

Salman ne ya gyara tsayuwarsa tare da cewa.

“Please Jananrt mushiga mana, kinfi kowa sanin irin wahalan da muka sha, kafun mu samu aka nuna mana wannan office din, wannan ita kadaice daman mu ta karshe, kada muyi wasa da ita.”

Kai Jannart ta jinjina kana asanyaye tace.

“To.”

Knocking kofar Salman yayi, inda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment