Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

wasu su sauk’a akanta.
Domin fataucin rayuwarta sukeyi, tamkar wanda yaje farauta yagaji bai samu komai ba, haka suke ayanzu, da zaran lokaci ya cika akanta zasu dire, suna son su kasheta, suna tsananin son ganin bayanta,
Alhamdulillah yau inajin na sauke wani nauyi akaina...”

Kasa karasa maganan nasa yayi, saboda kukan da yakeji na tasar masa.

Yayinda Jannart kuwa tuni kuka yaci karfinta, ba abunda ke tashi kuwa face sautin kukan ta.

Wanda hakan yasa gaba daya su Abba, Mamy, da Baba Maud’o duk jikinsu yayi sanyi.

Shikuwa Rayyern zuwa yanzu ya tankwashe kafafunsa, tare kuma dayin shiru, ya sunkuyar da kansa k’asa.
Haka kuma yakejin kansa na.
Dan sarawa, Yayinda yakejin jijiyon dake cikin kannsa nayi masa ciwo.
Badon komai ba kuma saidan saboda yanda yakejin kukan yarinyar na hawa kanshi.

Barrister Kabir kuwa Hannun Rayyern din ya kamo.
Da sauri Rayyern ya ɗago kansa ya kalleshi.
Sai kuma yayi ƙasa da ida nunshi ganin yadda mutumin mai girma yana kuka.
Shi kuwa Barrister Kabir.
cikin sanyin da jikinsa yayi yace.
“Rayyern ga amanar diyata matarka”.
Ya ƙare mgnar yana mai ɗago hannun Jannart ya saka acikin tattausan tafin hannun Rayyern din tare dasa nashi hannun ya rumtse tafin hannun Rayyern dake riƙe dana Jannart ya rumtse ya haɗe su...!


*Littafin TUBALI na kuɗine special Group 1k ne ƙaramin group 500 yawan posting ne banbanci su, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in baki da halin turawa ta banki to ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp na*




By
*GARKUWAR FULANI*





Wani irin raunataccen kuka ne ya kwabcewa Jannart cike da rauni shessheƙan kukan yake fitowa, yana ratsa kunnuwansu.
Banda kukan Jannart dake tashi, shiru gaba d’aya falon ya d’auka.

Yayinda Rayyern kuwa ya sunkuyar da kansa k’asa, tare kuma da rumtse idanunsa gam dan jin fatan saman idonsa nata karkarwa.
Domin kuwa adai-dai lokacin da hannun Jannart din ya sauk’a acikin nasa hannun, wani irin harbawa zuciyarshi tayi tare da buɗewa da azaban ƙarfi.

Duk da cewar kuwa ba wannan bane first time nasa daya fara tab’a jikin mace, musamman Idan akayi duba da irin yanayin aikinsa, saidai kuma a iya tsawon rayuwarsa, bai tab’a rik’e jikin mace, da sunan wai dan yaji wani abu ajikinsa ba, yana rikewa ne kawai idan takama dole, enfact ma shi baicika son duba mata ba, sai idan abun yayi worst ya kuma zama lallai dole shidin ake da buk’atar ya duba su.
Sam bai tab’ajin wani abu makamancin haka ba.

Tamkar kuma yanda zuciyar tasa ke bugawa haka ma Jannart, da itama takejin wani irin bugun zuciya, badon komai ba kuwa saidan samun hannunta da tayi acikin nasa, haka kuma Wannan shine karo na farko a rayuwar ta, da wani d’a Namiji wanda bata sani ba kuma ba Muharraminta ba ya tab’a jikinta, domin kuwa Bayan Yah Junaid, Daddy, Abba Kabir, Abdull, sai kuma Dr Lukman wanda ya kasance Dr dinta ne, babu wani wanda ya tab’a kama Koda farcenta ne, sai wannan ayanzu da hannunta yake cikin nasa.

Wanda kuma hakanne yasa taji zuciyarta tayi mata nauyi, Yayinda duk wani rauni dake narke acikin zuciyarta ya sake hauhuwa, lokaci daya taji tamkar wani mafakan kuka ta samu.
Dan tsabar kukan dake cinta har wani seizing numfashinta keyi.

Cikin muryarta da ta dashe sosai, ta saki Sabon kukan da sauti da amonsa ya zarce na baya mai cike da rauni.
Domin ayanzun kuka take da duka zuciya da gangar jikinta, kukan dake bayyana tsananin tarin damuwa da maraicin rayuwarta, kukan dake bayyana rauninta, haka kuma kukan da yasawa kowannensu matsanancin tausayinta.

Musamman Mamy da gaba daya k’walla ya cika mata idanu.

Rayyern kuwa har yanzu idanunsa a rumtse suke, saboda yanda sautin kukan nata ke ratsa cikin kunnuwansa, yasa gaba d’aya yaji kansa na juyawa, Sam bayason wani hayaniya ko kuma yawan koke-koke, kwakwalwarsa bata iya jure hakan.

Abba Kabir kuwa wasu irin hawaye masu zafi ne, suka gangaro daga kan fuskarsa, sake matse hannunsu awaje daya yayi, cikin kuma muryarsa da tayi rauni sosai yace.

“Rayyern ga amanar y’ata Jannart na kawo maka, ayanzu kaine Mijinta majiɓamcin lamuran rayuwata, kaine kuma wanda nakesa ran zaka zame mata Garkuwa, Rayyern Jannart marainiyace, wacce tataso acikin kad’aici da tarin damuwa, Jannart batasan wani farinciki ba Rayyern.
Domin ako da yaushe damuwa da kuma fargaba suke cika zuciyarta, Karikemin amanar Jannart Rayyern, Domin ayanzu duk wani motsinta yana karkashin kulawanka ne da ikonka, Jannart ta rayu akan wata turba ta daban, sannan an tarbiyantar da ita akan biyyya da kuma karb’an umarni akan duk wani abu da aka sata, ko kad’an bani da haufi akan Jannart, Domin kuwa Ina da tabbaci akanta, nasani Jannart bazata tab’a sab’amaka ba Rayyern idan kuma ta saɓa maka to ajizancin ne da yake halittar ɗan Adam.
Dan Allah ka kula da ita, Koda ace bazaka dauketa awani matsa yi na musamman ba, To Ina fatan ka karb’eta amatsayin k’anwarka, Jannart tana buk’atar kulawa Rayyern, tana kuma buk’atar farinciki, saboda ita din Marainiya ce...”

Ya Kai k’arshen maganan cikin muryarsa dake rawa, hadi da alhinin sark’ak’iyar dake cikin rayuwar Jannart din.

Ahankali kuma ya dawo da kallonsa ga Jannart din, cikin matukar sanyin murya da kuma son kwantar mata da hankali yace.

“Jannart ga Mijinki nan, kiyi masa biyayya kamar yanda kika saba, ki kuma gujewa duk wani abu dazai b’ata ransa, Dan Allah Jannart ki kiyaye kinji, Insha Allah watarana zaki samu ingantaccen farinciki, watarana duhu zaiyaye inda haske zai cika cikinsa, ako wani bayan kunci akwai farinciki,sannan ako wani bayan k’addara akwai sauki, komai da muke yi yanzu da kuma wanda zamuyi anan gaba, rubutacce kuma tsararrene, wanda Allah ya tsara mana, babu wata damuwa da zata Tabbata Jannart nasan kinyi imani da hakan.”

D’an tsagaitawa Abba Kabir din yayi, cikin kuma hawaye dake zuba a idanunsa, ya zare hannunsa dake saman nasu, tare da tallafo fuskarta, ya sumbaceta akan goshinta.

“Zan tafi Jannart, ki kula da kanki, kada ki sab’awa kowa dake cikin gidannan, Domin ayanzu sune y’an uwa kuma Garkuwarki.”

Abba Kabir din ya fad’a yana me kokarin mik’ewa tsaye.

Jannart da kuka ya riga daya ci karfinta, saurin rik’o k’afafunsa tayi, tare da sake fashewa da kuka.
Domin hakanan takejin kamar Idan ya tafi bazai dawo ba, tayaya zata iya jure zama amatsayin matar aure?
Hakan wani rayuwane da bata sanshi ba, batasan wacce irin kalubale ne zata fuskanta ba, Tabbas ta sani acikin rayuwarta gaba d’aya duhu ne, ita da batasan menene cikakken fari ciki ba, tayaya zata iya bawa wani?

Rayyern kuwa cikin takaicin kukan nata dake shirin fasa masa kwakwalwa ya zare hannunsa, tare da kawar da kansa gefe, yana mejin tamkar yasa hannayensa ya toshe kunnuwansa ko bakinta.

Abba Kabir kuwa kukan da Jannart din keyi ne ya matuk’ar karyar masa da zuciya.

Ahankali ya d’an sunkuyo, tare da kama kafad’un Jannart din cikin tausasawa hadi da rarrashi yace.

“Jannart din Abba ki daina kuka, tafiyar da zanyi ayanzu bawai yana nufin bazan dawo bane, Lallai Zan dawo Jannart, ki saki ranki ki dauka nan tamkar gidanku ne, kuma suma iyayenki ne, kamar yanda muke kulawa dake haka suma zasu kula dake, ako da yaushe Ina miki fatan al'khairi da nasara Jannart, Allah ya sanya al'barka acikin rayuwar aurenki.”

Cikin matsanancin kukan dake addabarta, ta Dan soma jujjuya Kai.

Ganin hakanne kuma yasa Mamy da ta kasa tsaida ruwan hawayen daya zubo daga cikin idanunta tace.

“Zo Jannart kema y’atace kamar yanda su Rayyern suke yayana, ki daina kuka kinji, Insha Allah zan zame miki mahaifiyar dake share kukan yayanta, ki sa aranki kuma cewar kina tare da mahaifiyarki ce, ki kalleni amatsayin wacce ta haifeki, bawai matsayin suruka ba, ni kuma har abada zan rikeki amatsayin y’a, Domin dama Allah baibani y’a Mace ba,.
To yanzu gashi ya turo min ke amatsayin kyauta biyu, y’ata kuma suruka ta, Insha Allah bazamu bari kiyi kuka ba.”

Mamyn ta fad’a tana me jawo Jannart din jikinta, tare da kwantar da kan Jannart din akan cinyarta.

Hakanne kuma yasa Jannart din, lafewa ajikin Mamyn tana sakin sheshshek’an kuka akai akai.

Abba kuwa da Baba Maud’o duk mik’ewa tsaye sukayi, saboda Ganin Barrister Kabir din da sukayi ya mik’e.

Koda ya soma tafiya, Mara masa baya sukayi, Dan yi masa rakiya.


Suna fita daga cikin falon, kuwa Rayyern da yake jinsa tamkar akan k’aya ya mik’e tsaye, ko kallon inda Jannart din take kuwa baiyi ba, kaitsaye ya haura sama, yana Jin tamkar shi dinma ya fashe da kuka suyi tayi a tare tsabar takaici, haka kawai an takura yarinya.
Tazo da wani shegen kukanta tazo ta saukar masa da ciwon Kai.

Mamy kuwa, hannu tasa ta soma sharewa Jannart din hawayen dake kan fuskarta, wanda kuma saboda tsabar kukan da tayi, har saida idanunta suka zama jajur.

“Kiyi hakuri Jannart, ki daina wannan kukan kinji, haka rayuwar kowacce ya mace yake, Aranar da aka rabata da gidan iyayen ta, saboda haka hakuri zakiyi, da sannu kuma zaki saba da zama damu,
ba amatsayin surukata kawai kike ba, ke y’ata ce.”

Mamyn ta fad’a tana me shafa bayan Jannart din alaman rarrashi.

Saidai kuma duk da haka Jannart din ta kasa tsaida hawayen dake kwaranya daga cikin idanunta, kukan ya riga dayaci karfinta, duk yanda taso tsaida kukan nata ita kanta ta gaza, amma saidai jin kanta da tayi ajikin Mamyn, ya d’ansa zuciyarta tayi sanyi ko yanzu tasan ta samu madadin Mom.

Yayinda Acan waje kuwa har bakin mota Abba da kuma Baba Maud’o suka rako Barrister Kabir.
Ganin yanda shi kansa damuwa ke bayyane akan fuskarsa ne kuma yasa Abba da kansa yace.

“Ka kwantar da hankalinka Barrister, Domin kamar yanda ka aminta damu, ka d’auko Jannart ka kawo mana ita cikin gidannan Insha Allah, bazamu bari hawayenta su zuba ak’asa ba, zamu zame mata iyaye na gari, idan tayi rayuwar maraici abaya Ina mai tabbatar maka da ayanzu Jannart bazata sakeyin rayuwar maraici ba, Zamu zame mata Garkuwa da yardar Allah, ka bamu amana kuma zamu rik’e, Jannart ba zata sakeyin kukan kadaici da maraici ba, zamu bata duk wani farinciki.”

Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da kamo hannun Abban yace.

“Nagode kwarai Alhaji Bashir, Lallai Tabbas yanzu na sake gamsuwa da cewar, na kawo Jannart inda ya dace, na kawota inda za’a bata kulawa, inda bakuma za’a bari tayi kunci ba, Alhamdulillah Allah ya tayaku rik’o”.

“Ameen.”
Abba da Baba Maud’o suka amsa.

Hannu Barrister Kabir din ya mik’awa, Abba da Baba Maud’o suka sakeyin musabaha.

Bayan yayi musu sallama ne kuma ya bud’e motarsa ya shiga, Ari ne kuma ya bud’e masa gate din gidan ya fice.

Har acikin ransa yana mejin gamsuwa na abunda ya aikata, Domin yasani acikin abunda ya aikatan Kwata-kwata babu kuskure, Allah yaga zuciyarsa da kuma kyakkyawan nufinsa.

Burinsa shine fito da gaskiyar da azzalumai suka b’oye, wanda kuma yake da tabbacin Allah zai bashi sa’a, akan dukkan komai, Domin Allah ba azzalumin kowa ba ne, saidai wanda ya zalunci kansa.

Su Abba kuwa ganin tafiyarsa ne, yasa Baba Maud’o wucewa makwancinsa kaitsaye, inda shi kuwa Abba juyawa yayi ya koma cikin gidan.

Barrister Kabir kuwa kaitsaye gidansa ya nufa.

Koda ya isa cikin gidannsa karfe 12:40 na dare.
Kaitsaye dakinsa ya wuce, bayan yayi wanka ne kuma Aunty Dijat ta kawo masa Coffee.

Sai-dai ganin yanda gaba daya jikin mijin nata ke sanyaye ne yasa, ta gyara zama tare da kamo hannunsa, cike dason basa kwarin guiwa tace.

“Ka kwantar da hankalinka Abban Hafeez, Domin nasan duk wani abunda ke damunka, ayanzu bai wuce akan Jannart, meyasa zaka damu Abban Hafeez, bayan kasan cewar wannan auren shine abunda zai kawo sauyi da farinciki acikin rayuwar Jannart, wannan auren shi zaisa Jannart tasan wacece ita, shi ne kuma zai warware mata duk wani k’ulli dake cikin rayuwarta, Tabbas wannan auren al'khairi ne, kuma Insha Allah akwai lokacin da Jannart zatayi al'fahari da wannan Auren, musamman alokacin da ta gano cewar ka zab’a mata miji, mai nagarta irin wanda bashida saukin samu, sannan ka ceci rayuwarta daga sharrin mak’iyan dake kewaye da ita, way’anda take kwana acikinsu, take tashi batare da ta sani ba.”

Kai Barrister Kabir din ya jinjina, Cikin samun karfin guiwa kuma yace.

“Insha Allah Jannart zatayi farinciki, komai kuma zai yaye, ayanzu duniyarta zatayi sanyi, Domin tafita daga cikin magauta, hakika ko ayau na mutu, nasan na mik’a Jannart ga inda za’a tsaya mata, inda babu wani maitsaurin ido daya isa zuwa yaci mutumcin ta, saboda Rayyern ba kanwar lasa bane ba kuma mutum bane kamar kowaba, shi na musamman ne domin naga tsoronshi cikin idanun Magautan nasa da Jannart.
Tun ran forko kuma dana ganshi ya tunomin wani ma irin zarrarsa a tsakiyar su Yaya idi wanda sukayi nasarar kaudashi a duniya.
Sai naketa kamar Allah ya turo Rayyern garesune dan ya tono jiyansu ya tsaida yau ɗinsu ya birkita gobensu yadda yake musu mgna kamar ɗan fansa ne, Insha Allah kuma watarana Jannart sai ta zamo wani sashi na jikinsa.”

Murmushi Aunty Dijat tayi, saboda ta fahimci kalaman da mijinnata ke nufi.

Acan gidan su Rayyern kuwa, Koda Abba ya dawo cikin falon, anan ya sameta zaune ita da Jannart din, da har yanzu ta kasa daina zubda hawaye.

Zama Abban yayi
Tare da tausasa muryarsa cikin aminci yace.

“Jannart”.
Wani irin sanyi taji muryar Abba ya sakar mata.
Shi kuwa a mutunce yace.
“Jannart d’ago kanki ki kalleni.”

Jannart dake sakin shesshekan kuka, sake Jin Muryar Babban mutum acikin kunnuwanta ne yasa ta d’ago kanta Ahankali, da kuma Idanunta wanda sukayi luhu-luhu ta kalleshi.

Kai Abban ya girgiza, kana cikin lallashi da ban baki yace.

“Kada kiyi mini wani kallo na daban Jannart, inaso ki kalleni amatsayin mahaifinki, ni Babanki ne, kada ki ajiyeni amatsayin suruki kawai, saboda na daukeki ne amatsayin y’a, wanda har abada kuma bazan tab’a bari kunci yayi tasiri acikin zuciyarki ba, wannan gidan kada ki daukeshi amatsayin gidan aurenki kawai, ki daukeshi amatsayin gidanku, kafun yanzu bamu sanki ba, amma ayanzu kedin tamuce, kin zama daya daga cikin iyalinmu, munzama iyayenki ke kuma kinzama y’armu, Ramadan ya zama shak’ik’in d’an uwa agareki, dama kuma duk wani wanda yake tare damu, duk wani damuwa da ya dameki kuwa ki sanar mana.
Insha Allah zamu magance miki ita, saboda haka ki daina kuka kinji, kisa aranki cewa muna tare dake, kuma Allah Ma yana tare dake.”

Kanta ta d’an jinjina, saboda yanda kalaman Abban sukayi tasiri a zuciyarta, duk da cewar ta kasa tsaida hawayen dake zuba acikin Idanunta.

Cikin sanyi hadi da muryarta wacce bata fita sosai tace.

“Nagode Abba, nagode da karamcin da kukayi min Allah ya kara girma.”

Murmushi Abban yayi, kana cikin jin dadin biyayyar yarinyar yace.

“Ba komai Jannart, Insha Allah zamu zame miki iyaye na gari, Mamyn Rayyern Ina Rayyern din kuma ya tafi.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Mamy.

“Rayyern ya haura sama.” Mamy ta fad’a tana murmushi.

Kai Abban ya jinjina, kana cikin kulawa yace.

“To dare na tayi, ki Kai Jannart masaukinta ta kwanta.”
Ya ƙare mgnar yana nuna mata side din da zata kai Jannart ɗin.
To Mamyn tace, tare kuma da kama Hannun Jannart din suka nufi, wata had’add’Iyar k’ofa dake nan cikin falon, kusa da side din kitchine da kuma dining area.

Ahankali Mamy ta tura k’ofar d’akin.

“Ki shigo da bismillah.”
Mamyn ta fad’awa Jannart Cikin kulawa, hakan kuwa akayi da bismillah Jannart ta jefa k’afarta ta dama acikin falon.

Falo ne mai kyaun gaske wanda aka k’awata cikinsa, da wasu had’add’un royal cushions masu kyau, sai kuma labulayen da aka k’awata jikin window dana bedroom door dashi, atsakiyar falon kuwa, wani lallausan carpet ne maikyau da girma, sai kuma babban tv’ plasma’n da aka daurasa akan wani babban tv stand.

Sosai falon yayi kyau, duk da cewar babu wasu tarkace masu yawa acikinsa, amma komai da komai mai tsada ne.

Sanyin AC da kuma daddad’an kamshin room freshener dake tashi acikin falonne yasa Jannart lumshe Idanunta.

Inda Mamy kuwa kaitsaye ta wuce jin wata kofa dake cikin falon, still kuma tana rik’e da hannun Jannart ta bud’e kofar suka kutsa ciki.

Bedroom ne madaidaici wanda aka zuba masa furnitures na alfarma, bed, drawer, and dressing mirror with bedside drawer then shoe rug.

Komai dake cikin d’akin kalan pink and white ne, shiyasa haduwarsa yake dajan hankali, kamar dai falon, Domin shima cushions da labulayen cikinsa duk pink and white ne.

K’arasa shigowa cikin dakin sukayi, Yayinda Mamyn ta zaunar da ita bakin gadon daya sha bedsheet na alfarma.

Kallonta Mamyn tayi, kana cikin tausasawa tace.

“Jannart Nan shine masaukinki, zaki zauna ne kuma kafun agama gyara miki asalin inda zaki zauna.
Dan Allah Jannart ki saki jikinki, babu wani wanda zai takura miki, akwai komai na amfani da zaki buk’ata, duk abunda kikeso kuma kiyi min magana, banason kiyi kuka kinji ko Jannart”.
Cikin sharce hawayen ta gyaɗa kai alamun.
Eh taji.
Cikin jin daɗi Mamy tace.
“Kinga ke amanace agaremu, zubar hawayenki kuma zai zamo damuwa azuciyoyin mu, duk wani abunda ya dameki ki sanar dani, kada kiji shakka ko kuma nauyi na.
Domin bana daukanki amatsayin suruka, sannan kada ki bari damuwa tayi nasarar tank’wasar da zuciyarki, kowani bawa yana d’auke da irin salon k’addararsa, saboda haka ki kwantar da hankalinki, ke taki k’addarar ahaka tazo, Insha Allah kuma watarana komai zai wuce, babu wani damuwa dake tabbata, kiyi farinciki aduk wani yanayin da kika samu kanki kinji Jannart.”

Kai Jannart din ta jinjina, tare kuma da kama y’an yatsun hannunta cikin sanyi tace.
“Insha Allahu Mamy zanyi duk abinda kikace.”

Murmushi Mamyn tayi, cikin tsananin jin dadi da farinciki tace.

“Yauwa Jannart, Allah Yayi miki albarka, naji dadin biyayyarki.
Domin duk wani wanda yake daukar maganan na sama dashi, har abada bazai tab’ayin dana sani ba.”

Ta ƙare mgnar tana nufar Bathroom.

Ruwan wanka mai dumi Mamyn ta had’awa Jannart acikin bath, tare kuma dasa mata turaren wanka mai dadin k’amshi.

Koda ta fito daga toilet din, hannun Jannart din ta kamo ta miƙar da ita, tare da cewa.

“Yauwa Jannart kije kiyi wanka ko nasan..”

Sauran maganan Mamyn ne ya mak’ale, saboda yanda taji duk jikin Jannart din ya dau zafi.

“Subahanallah Jannart gashi duk jikinki zafi, nasan kuma hakan bai rasa na saba, da kukan da kikayi, kije kiyi wanka, akwai sabin towels acikin toilet din saikiyi amfani dasu, akwai kuma ruwan dumi dana had’a miki a bathtub.”

“Nagode Mamy.”
Jannart din ta fad’a, Ahankali tare kuma da zare dogon hijab din dake jikinta.

Mamy kuwa murmushi tayi, kana ta juya ta fice daga cikin d’akin.

Koda ta fito nan cikin falon nasu, kaitsaye kitchine ta wuce.

Yar ƙaramar tukunya tasa akan gas, cikin abunda baiwuce.
15mn ba kuwa ta kammala had’a indomie’n da ta dafawa Jannart din, wanda yaji kayan hadi da kifi, bayan ta juye indomie’n a plate ne kuma, ta had’a tea mai kauri acikin mug.

Bayan ta gama kimtsa komai ne kuma, kaitsaye ta haura sama zuwa dakin Rayyern.

Zaune yake akan gadonsa, inda ya sanja shigar jikinsa, zuwa kayan bacci masu taushi.

Yanayin yanda yayi zaman duka k’afafunsa na k’asa, sannan kuma ya dafe kansa da hannayensa duka biyu.

Idanunsa arumtse suke, kana kuma time to time yake fesar da wani irin numfashi mai kama da ajiyan zuciya.

Mamy kuwa isowarta jikin kofar ne yasa ta d’an soma knocking.
Sai-dai har tsawon mintuna 2 tana knocking amma bataji a bud’e k’ofar ko kuma bata izinin shigowa ba.

Hakan kuwa shi yasa ta murd’a handle din kofar a zayonta ko yana bacci ne, ga mamakinta kuwa sai taga kofar ta bud’u.

Ahankali ta tura kanta cikin dakin tare dayin sallama.

Anan zaune ta hangosa, ya dafe Kai, da dukkan alama kuma yayi nisa acikin duniyar tunanin da yakeyi.

Idanu Mamyn ta Dan tsura masa cike da mamaki, saboda wannan ne karo na farko da taga Rayyern din acikin yanayin zallar damuwa.

Rayyen kuwa da yayi nisa acikin duniyar tunaninsa, Sam baisan cewa Mamyn ta shigo ba.

Gaba daya hankalinsa ya tafi, izuwa sabuwar k’addarar daya samu kansa aciki.
Yayinda har yanzu ya kasa tantance wani irin aure ne aka daura masa, Sam ya kasa tantance marabar auren dana dole, shi ya sani bayason lamarin mace acikin rayuwarsa, but why za’a takura masa? Yasan meye aure yasan manufarsa yasan hakkokin mata a kan mijinta.
Yasan bashi da lokacin saukesu da reno da tattalin mace yadda ya kamata shiyasa bai kawo mace a rayuwarsa meyasa zasu liƙa mishi ita a dole su lika mata shi a dole.

“Rayyern! Rayyern!!”



https://chat.whatsapp.com/IM6PrgYNy9s6lP0aXmBkaN


Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!

By
*GARKUWAR FULANI*




https://chat.whatsapp.com/IM6PrgYNy9s6lP0aXmBkaN


Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!




Mamy ta kira sunansa da d’an k’arfi, wanda hakan yasa shi dawowa daga duniyar tunanin daya fad’a.

D’ago da kansa yayi Ahankali ya kalli Mamy’n, da ta tsare shi da ido.

“Mamy yaushe kika shigo?”
Ya tambaya da dan mamaki akan fuskarsa.

“Tayaya zaka san lokacin dana shigo, bayan kanason takurawa rayuwarka, dason sawa kanka damuwa akan abunda kasan ya zama wajibi akanka.”

Mamyn ta fad’a.

Longoɓar da kansa yayi, kamar zaice wani abu kuma saiyayi shiru.

Mamy kuwa Ajiyar zuciya ta sauk’e, had’e da cewa.

“Idan akwai magananin zazzab’i awajenka, ko paracetamol ne ka bani, Jannart ce jikinta duk ya d’au zafi.”

Jin abunda Mamyn ta fad’a ne kuma yasashi d’ago kansa ahankali ya kalleta, fuska ya kwab’e kana cikin muryarsa mai kama da shagwab’a yace.

“Ni kam Mamy bani da wani magannin zazzab’i.”

Harara Mamyn ta watsa mishi tare da gyara tsayuwarta tace.
“Taya zaka cemin babu bayan bakaje ka duba ba.”

Sake langwabar da kansa yayi, still yace.

“Mamy nasan fa babunne, kuma yanzu ni bana ajiye magani, saidai ko ki tambayi Ramadan.”

“Katashi Kai kaje ka karb’omin maganin awajen Ramadan.”
Mamyn ta fad’a adake.

Jin hakanne kuma yasa shi mik’ewa jiki asanyaye, ya nufi dakin su Ramadan.

Yana zuwa kuwa ya samu Ramadan da Riyyam-nsra kowannensu na rike da waya ahannu.

Ko Kallon kirki baiyi musu ba, ya tsaya tare da d’age kansa sama, kana yace.

“Ramadan bani paracetamol.”

Da mamaki Ramadan yake kallonsa, kamar zaiyi magana kuma saiya fasa, kaitsaye ya bud’e wani Dan box maganin zazzab’i ya ciro ya mik’awa Rayyern din.

Yana karb’a kuwa ya fice, inda ya samu Mamy abakin k’ofa ya mik’a mata.

Amsan maganin Mamy tayi, batare da tace masa komai ba kuma ta juya ta sauk’a k’asa.

Shikuwa d’akinsa ya koma, zuciyarsa cike da takaici.

DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment