Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

idon zata sake kallonshi? kuma shi dinma ayanzu wani irin kallo zainayi mata karo na forko a rayuwarta da taji haushin irin shigar da takeyi.

“Wata macen da batasan ciwon kanta ba, bata iya ankilta kantaba.”

Zuciyarta ta bata amsa atake.

Idanunta ta rumtse cike da takaici.

Dai-dai lokacin kuwa Salman Ya ware idanunshi a kansu tare da dawo da kallonsa gareta.

Fuskarsa dauke da d’an mamaki yace.

“Ha’a Jannart lafiya kuwa kizo mutafi mana..”

Sauran maganar tasance ta mak’ale, alokaci da yaga jikin Jannart din lullub’e da Al'kyabban, da dazu ya ganta agefen mutumin da har yanzu baisan sunanshi ba.

Jannart kuwa fuska tad’an marairaice, kana cikin sanyin jiki ta soma takowa zuwa inda Salman din ke tsaye.


“Jannart wannan Al'kyabban fa? Kin sanshi ne?”.

Salman din ya tambaya, saboda yayi mamakin ganin ya sawa Jannart din da al'kyabban k’warai.

“Shi ne ya bani.”

Jannart din ta fad’a kaitsaye, bisa kuma sanin rashin dacewar Salman din yasan gaskiya abinda yasa yasa mata, shi yasa ta fad’a masa hakan, batare kuma da ta bada wata kofar da Salman din, zaiyi mata wata tambayar ba ta soma tafiya.

Salman kuwa idanunsa ya zuba mata, yana mai Kallon yanda al'kyabban tayi mata matuk’ar kyau duk da tayi mata yawa, saidai kuma Jin tace wancan mutumin ne ya bata, yasa shi jin babu dadi acikin zuciyarsa.

Saidai kuma bashi da ikon bayyana hakan.

Ab’angaren Dr. Rayyern kuwa Koda ya fito daga wajen wasan, kaitsaye Inda motarsa ke fake ya nufa.

idanun y’an tsirarun mutanen dake wajen ke kansa, duk da cewar kuwa basusan shi din asalin waye bane, amma kallo daya zakayi mishi kafahimci cewa mutum ne mai zarra.

Baya ga haka kuma ga tarin baiwar kyau da Allah Yayi mishi.

Tun kafun ya karasa isowa Parking lot din wajen kuwa, Hadi driver’nsa ya fito tare da bud’e masa k’ofar motar.

Yana shiga kuwa driver’n ya rufe k’ofar, tare da zagayawa cikin sauri ya tada motar.

Suna ficewa daga Parking lot din kuwa, su Jannart na isowa.

Nanfa kallo kuma ya dawo kan Jannart, domin al'kyabban dake jikin nata ya k’ara bayyana asalin kyau da kuma kawata shigar dake jikinta da jawo hankalin mutanen dake wurin kanta.

Murfin motar Salman din ta bud’e, tare da zagayawa gidan baya ta zauna, wanda tayi hakanne kuma, saboda idan sunzo shiga cikin gidan tv’n nasu, kada masu tsaronta su ganta, ko kuma wani wanda yasanta .

Salman ma shiga cikin motar yayi, tare da yiwa motar keyi suka fice daga cikin wajen wasan gaba d’aya.

Jin sun hau titi ne kuma yasa ta lumshe Idanunta, tare da sauke wata irin ajiyar zuciya mai karfi.

Lallai ayau din tana cikin tarin damuwa tsananin kunya da kuma takaicin kanta da kanta.

Yayinda acikin zuciyarta kuwa take fatan Allah Yasa.
Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din yazo, kamar yanda wancan yayi musu alkawari, kan.

Numfashin ta fesar a hankali tare dayin mgnar zuci.
"Allah yasa kada in sake haɗuwa dashi har abadan, wannan kayan kunyar ina zan kaishi."
Tayi mgnar cike da kunya.

“Idan shi Dr Rayyern Mai-nasara kuma baizo bafa, shikenan na rasa aikina?”

Tayiwa kanta tambayar, dayasa duk taji zuciyarta ta Karye.

Salman dake driving, wanda kuma tun dazu yake satan kallonta ta cikin madubi ne yace.

“Munsamu full confidence din samun daman yin hira da Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, amma kuma sai naga kamar bakya cikin farinciki, kamar akwai wani abu dake damunki, please ki fad’amin wacce irin damuwa ce haka ke damunki?”.

Idanunta dake alumshe ta bud’e, tare kuma da k’ak’alo murmushi ta daura akan fuskar ta.

“Ina farinciki mana Salman, Ina cikin farinciki Tabbas, saidai bansan me yasa ba zuciyata keson sanyamin wasu/wasi, Ina fargaban kada ace wancan mutumin raina mana hankali kawai yayi.”

Ta fad’i hakan tana me gyara zaman al'kyabban jikinta.

Salman kuwa jin hakanne yasashi yin Murmushi, cikin son karfafa mata guiwa yace.

“Karki damu Jannart Insha Allah zakiyi hira da Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, domin na tabbata wancan mutumin da muka hadu dashi awajen wasan polo bazaiyi mana karya ba, Lallai nagamsu akan cewar yasan shi, ki duba da kyau shima ai daga ganinsa ba karamin mutum bane, duk da kasancewarsa matashi amma yayi ruwan mutane masu kamala da dattaku”

Maida idanunta tayi ta lumshe, batare kuma da ta sake cewa Salman din komai ba, ta shiga fesar da numfashi ahankali.
Domin zuwa yanzu zuciyarta tatafi wani waje na daban.

Lumshe idanun nata da tayi kuwa, yayi dai-dai da lumshe idanun Dr Rayyern Mai-nasara, dake zaune acikin motarsa.

Gaba d’aya ya yamutsa fuskarsa, saboda yanda yakejin zuciyarsa na d’an tashi kad’an kad’an.

Tabbas jinin da yagani ajikin yarinyar ya b’ata masa rai, Yayinda kuma yasa shi jin wani irin takaici had’i da tashin zuciya.

Kwata-kwata arayuwarsa bayason ganin wani abu daya shafi jinin sirrin mace shiyasa ya wadata asibitin sa da likitoci mata da zasu iya lura da ɓangaren haihuwa Allah ya sani bai son ganin jini.

Ayanzu kuwa idan akwai abunda ke bashi matuk’ar takaici, To bai wuce yanda yarinyar ta jawo ya shiga harkarta.

D’abi’arsa ce baya shiga harkar kowa, more especially ma mata, sometimes bayan Uwa mahaifiya yakanji babu wata alaka da zai iya kullawa da wata Mace awaje ta daban, sai gashi bisa dole wata can ta shigo harkarsa.

Wanda kuma yayi imani cewa badon sanin rashin dacewar barinta ta tafi a haka da jini ajikinta ba, To da bazai tab’a bata al'kyabbarsa mai matuk’ar daraja da kyau ta sanyawa jikinta dake abude ba, domin ai bashine yace tana yawo haka babu hijab ba.

Shidai kam Sauda yawan lokuta yana mamakin, yanda wasu matan ke yawo haka sakaka, babu wata kulawar kirki da suke bawa kansu ina iyayensu?.

Yar gajeriyar tsuka yaja, tare da bud’e idanunsa.

Dai-dai lokacin kuwa suka iso cikin farfajiyar katafaren asibitin nasa.

Anan cikin babban parking lot, Hadi driver yayi parking motar.

Yana gama dai-dai-ta parking din motar, kuwa Dr Rayyern ya bud’e murfin motar ya fito, fuskarnan tasa kuwa babu alaman murmushi akanta.

Dan Kallon Hadi driver din yayi, kana cikin yanayin dake bayyana, rashin iya tsawaita maganarsa yace.

“Kaje gida ka huta idan na tashi zanyi driving din da kaina .”


Kai Hadi ya jinjina, kana cikin girmamawa yace.

“To Ranka ya dad’e nagode.”

Karb’an makullin motar yayi, batare kuma daya sake cewa Hadin komai ba, ya kutsa kansa cikin asibitin.

Saboda mood din daya samu kansa aciki ne kuma yasa, ko iya amsawa tarin ma’aikatan dake gaishesa baiyi ba, kaitsaye ya wuce office d’insa.

Yana shiga cikin office dinnasa kuwa, ya murzawa kofar key.

Saboda ayanda yakejin kansa kwata kwata bayason damuwa.

Karasawa gaban dan madaidaicin fridgen dake cikin office din yayi, tare da zaro bottle water mai sanyi ya kafa abakinsa.

Bai dauke goran daga kan bakinsa ba kuwa har saida yasha fiye da Rabin ruwan dake cikin goran.

Take kuwa ya soma sauk’e ajiyar zuciya, Yayinda yakejin sanyin ruwan na mamaye kirjinsa.

Wanda hakan yasa acikin kaso 10 na b’acin ransa, kaso 6 yayi kaura.

K’arasawa yayi ya zauna akan wata had’add’iyar leather sit dake cikin office din.

Cikin kuma son rage tarin ayyukan dake gabansa, ya jawo laptop d’insa dake kan desktop.
Atsanake ya soma shigar da wasu bayanai akan Campany'shi da aketa aikinshi yanzu, wanda yafi duk sauran na jahohin girma.

Still kuma time to time yake sauke ajiyar zuciya.

Acan b’angaren su Jannart kuwa, daga wajen buga wasan Polo’n, basu wani dau lokaci mai tsawo suna tafiya ba, cikin mintuna kalilan suka iso gidan television din nasu, na Arewa24.

Kamar yanda suka fita asace kuwa haka yanzun ma suka dawo asace.

Inda Salman yayi parking motar tasa acan baya, inda babu wanda zai gansu.

Hakanne kuwa yasa cikin sauri Jannart ta fito daga motar, tare da sanya hannayenta duka biyu ta gyara zaman al'kyabban dake jikinta.

Ahankali ta soma tafiya sai-dai kuma taku daya zuwa biyar kawai tayi ta tsaya cak, tare da juyowa ta kalli Salman wanda ya zuba mata idanu baya ko kyaftawa.

Murmushin daya kara bayyana kyawun fuskarta tayi, batare kuma da ta fahimci ma’anan irin Kallon da Salman din keyi mata ba tace.

“Nagode sosai Salman, nagode da taimakonka, tabbas ka taimakeni awannan tafiyar, saboda nasan cewar badon kaiba dana rasa wannan babbar daman dana samu ayau.”

Idanu Salman din ya lumshe, cikin kuma nuna mata girman matsayinta awajenshi yace.

“Akoda yaushe bana buk’atar godiyarki Jannart, domin Ina tabbatar miki da cewar kin wuce haka awajena, kamar kuma yanda kikeson aikinki, haka muma mukeson aiki dake, bamason rasaki Jannart, saboda haka duk wani abu daya shafeki ya shafeni.”

Ya fadi hakan yana mai bayyana iya gaskiyar abunda ke kwance acikin zuciyarsa.


“Bazan iya daina gode maka ba Salman, saboda akoda yaushe kana iya kokarinka wajen bani kwarin guiwa, thanks alot ni zan wuce gida sai munyi waya.”

Ta kai karshen maganan nata tana me juyawa, kaitsaye ta nufi wajen da guard dinta suke.

Shikuwa Salman da idanu ya rakata, har saida ta b’acewa ganinsa, kafun ya juya ya nufi cikin office d’insu.


Yayinda itakuwa tana isa bakin motarta, gaba daya guard dinnata suka mimmik’e, Shashashai duk acikinsu kuwa babu wanda yasan cewar ta fita.

Bud’e murfin motar tayi, bayan ta shiga ta zauna ne kuma driver’nta yaja sukayi gaba, Yayinda sauran guard dinnata suka rufa mata baya.

Kwata kwata kuwa Tafiyar 40 minute ne ta kawosu katafaren gidansu Jannart din.

Inda suna shigowa compound din gidan motar Junaid ma na shigowa.

Ganin motar yah Junaid dinne kuma yasa zuciyar Jannart bugawa da wani irin karfi, lokaci daya kuma taji duk fargaba da tsoro ya lullub’eta.

Tabbas ita kanta tasan cewar tana matuk’ar tsoron Yah Junaid, wanda kuma hakan ya samo asali ne saboda yawan takurawan da yakeyi mata.

Al'kyabban da yake jikinta ta kalla, sanin da tayi kuma cewar idan Yah Junaid din ya gani, zai iya fassarata da wata manufa tasa ta daban, yasa cikin sauri ta zare al'kyabban daga jikinta, tare da sauko da ita ta daura akan waist dinta.

Cikin yanayin tsoro da kuma fargaban dake kwance acikin ranta, ta bud’e murfin motar ta fito.

Hannunta rike da jakanta ta soma tafiya ahankali.

Dai-dai lokacin kuwa Junaid ya fito daga Cikin motarsa, hannunsa rike da karan sigari yana zuk’a tare da tankadi alamun a bige yake yayi tatil da barasa, dishi-dishi yake ganin komai hakan ke sashi tangadin


Idanunsa ya dan kurawa Jannart din, Yayinda yakejin kamar ya rufeta da duka, dan tsananin takaicin rashin samun Galaba akanta da bayayi.

“Daga Uwar Ina kike?”

Ya tambaya cikin kakkausar murya tare da son gano meke daure a kugunta kuma ya kasa.

Jannart kuwa da sautin fitar muryar tasa, yasa hanjin cikinta kad’awa Idanunta ta rumtse, kana cikin muryarta dake bayyana zallan tsoronsa tace.

“Daga wajen aiki nake.”

“Wajen aiki? Munafuka makaryaciya sai yanzune ake tashi daga wajen aikin karfe shida saura?
Makaryaciyar yarinya wato kinje kin gama rabawa kattin banza jikinki kin more sun more, shine sai yanzu zaki dawo ko, tafi daga nan wajen kona tattakaki nayi kasa-kasa dake.”

Ya fad’i maganar amatukar tsawace da maye.
Hakanne kuwa yasa Jannart d’in, Cikin yanayin sassarfa ta nufi cikin gidan kaitsaye, domin tasan ba karamin aikinsa bane yayi kasa kasa da itadin kamar yanda ya fad’a.
Sam tasan baya mutumta duk wani abu nata.
Yayinda akullum take sake ganin wutar mugunta acikin idanunsa.

Duk da kasancewarsa dan Uwanta amma yana muzantata, kwata-kwata babu ruwanshi da cewar ita k’anwarsa ce.
Komai yazo bakinsa furta mata yake.

Harsai yaushe ne zata tsallake rashin mutumcinsa? Harsai yaushe ne Yah Junaid din zai mutum tata amatsayinta na kanwarsa?
Yaushe zai daina gwada mata kiyayya da kuma tozarci?

Wasu siraran hawaye masu zafi ne suka silalo daga cikin idanunta, adai-dai lokacin da ta karasa bakin kofar da zai shigar da ita babban falonsu.

Hannu tasa ta share hawayen nata, kana ahankali ta murda handle din kofar ta shiga.

Rashin ganin kowa acikin falonne kuma yasa ta sauk’e ajiyar zuciya, batare kuma da ta.
Nemi Mamy ko Abdull ba, kaitsaye ta wuce bedroom dinta.

Tana shiga bedroom din kuwa ta soma rage kayan jikinta, tare da shigewa cikin toilet ta kimtsa kanta.

Koda ta fito kwanciya tayi lub akan gado, tana me tunanin yanda halin rayuwa keyi da ita.
Sam babu wani farinciki da take samu acikin gidan nasu.

Kullum Cikin fargaba da tsoro take, awaje daya kawai takejin dadi, shine wajen aikinta, ananne take yin farinciki batare da wani ya tsangwameta ko ya harareta ba.

Idanunta dake dauke da danshin hawaye ta lumshe.

Kana cikin sanyin murya tace.

“Allah Kazama gatana akoda yaushe.”

*Dr Rayyern Mai-nasara.*

Ajiyar zuciya ya sauke tare kuma da mikewa tsaye, ahankali ya soma tattare tarin takardun dake gabansa.

Bayan ya kammala had’a takardun ne kuma ya d’auki waya da makullin motarsa dake aje akan desktop.

Kaitsaye ya fice daga Cikin Office din.


Koda ya fito compound din asibitin, bai wani tarar da yalwan mutane ba, kasancewar lokacin magriba ta fara yi.

Direct wajen da motarsa ke fake ya nufa.
Bayan ya shiga ya zauna ne kuma yayiwa motar key, tare da cillata kan shumfud’add’iyar Titin dake cikin asibitin har zuwa waje.

Tuk’i yakeyi cike da nutsuwa, Yayinda ahankali kuma yake bin karatun Alminshawy dake tashi acikin motar.

Da fitansa acikin Hospital din kuwa, yanzu ak’alla yakai 18minute, inda kai tsaye ya nufi masallacin Al'furƙan dake Cikin unguwarsu ta Nassarawa G.R.A.

Dab da zai shiga cikin layin masallacin kuwa, ahankali ya d’ago kansa ya kalli madubin dake Cikin motar, kasancewar kuma aikin madubin shine bayyana maka wanda ke bayanka, hakan yasa idanunsa suka gane masa wata bakar mota mai tint dake biye dashi.

Kawar da kansa gefe yayi tare da ci gaba da tukinsa, isowarsa Cikin layin dinne kuma yasa shi shiga wata kwana.

Aikuwa d’aga kan da zaiyi sai yaga wannan motar dake bayansa itama ta shigo kwanan.

Idanu ya d’an tsurawa motar, fuskarsa dauke da mamaki, saboda zuwa yanzu ya tabbatar da cewa motar shi take bi.

“Bibiyata akeyi.”

Ya fad’a fuskarsa d’auke da dan murmushi, ba tare kuma da tsoro ko fargaba ba ya cigaba da tafiyarsa, inda tuni ya d’auki numbern motar dake bayansa din ya rike akansa.


Isowarsa gaban babban masallacin Al'furƙan dinne kuma ya sashi parking motar, tare da bud’e murfin motar ya fito, domin zuwa lokacin an soma kiraye kirayen sallan magriba.

Fitowarsa daga cikin motar ne kuma yasa, motar dake biye dashi din, yin reverse cikin sauri matukin motar da ba a iya ganin fuskarsa, ya Karkata akalan motar zuwa wani waje daban.

Dr Rayyern kuwa ganin wanda yake bibiyannashi ya juya ne, yasa shi sakin Murmushin dake dauke da ma’anoni daban daban.

Wayarsa ya maida cikin motar, bayan kuma yayi alwala da bottle water’n da ya d’auko acikin motar ne, kaitsaye ya wuce cikin masallacin.

Koda aka idar da salla’n bai fito daga cikin masallacin ba saida ya kammala addu’o’insa kana akayi sallan isha'i sannan ya fito.

Daga masallacin Al'furƙan din kuwa kaitsaye gidansu ya nufa.

Yayinda acan gidannasu kuwa Abba da Baba Maud’o ne zaune acikin compound din gidan, inda suke hira cike da girmama juna da Kekkyawar mu'amala.

Dai-dai lokacinnne kuma Rayyern din ya iso bakin tankamemen gate din gidan.

Horn din motar tasa ya danna.

Wanda hakan yasa Baba Maudo tashi da dan sassarfa.
saurin dakatar da Baba Maudon Abba yayi kana cikin girmamawa sanin tabbas Baba Mauɗo ya girmeshi yace.

“A'a Baba Maud’o zauna ka huta, yau bari in taya ni zan bud’e gate din.”

Cike da mamaki Baba Maud’o ya koma ya zauna, ganin da yayi kuma har Abban ya karasa jikin gate dinne yasa shi komawa ya Zauna tare da zuba mishi idanu.
Kana a hankali ya lumshe su tare da sauke nannauyan numfashin.

Abba kuwa bud’e katon gate din yayi, Inda Rayyern ya tura hancin motar tasa cikin gidan, saidai kuma ganin da yayi cewa Abban nasa da kansa ya bud’e gate din gidanne yasa, batare daya kutsa can ciki ba yayi parking motar.
Tare da bud’e murfin motar ya fito.

Cikin dan girmamawa hade dayin kasa dakai yace.

“Abba Baba Maud’o barkanku da dare, amma Abba da ka bari ai na fito da kaina ma zan iya bud’e gate din.”

Kai Abban ya girgiza tare da cewa.

“A’a ai hakanma baiwuce motsa jini bane, Baba Maud’o ma da kansa yace zai bud’e amma nace masa ya bari, sannunka da dawowa ya hospital din?”
Abba Yayi masa tambayar cikin kulawa.

“Alhamdulillah Abba,".
Kana ya kalli Baba Mauɗo cikin kulawa yace.
"Baba Mauɗo gsky ni na gaya maka bana son kana aikin nan naka, zamu Ari ya rinƙayi aikin gadin, wlh bana jin daɗi inga kana buɗe mana gate.”
Murmushi Baba Mauɗo yayi tare da cewa.
"Rayyanu kenan to me a ciki ai motsa jiki ne kawai”.
Kanshi ya jujjuya kana ya kalli Abba tare da cewa.
“Ramadan yana ciki ko.”

Kai Abban ya jinjina masa, tare da cewa.
“Eh shima Ramadan din yanzu ya dawo ya maida wancan bakon yaron masaukinsa.”

Dan jinjina kai yayi kana kaitsaye ya wuce cikin gidan.

Ahankali ya tura kofar falon ya shiga bakinsa dauke da sallama.

Ramadan da kuma Mamy dake zaune acikin falonne suka amsa masa.

Cike kuma da farincikin ganinsa Mamy tace.

“Masha Allah Rayyern ka dawo.”

Kansa ya jinjina tare da cewa

“Eh.”

“Barka, ya hospital din.”

“Alhamdulillah.”ya fada yana me karasowa cikin falon.

“Hamma Rayyern sannu da dawowa, tun dazu Riyyam ke jiran dawowanka, amma ganin baka dawo da wuri ba, yasa na maidashi masaukinsa dan yaƙi ya tsaya yaci abinci ma, sai zuba mishi Mamy tayi ya tafi dashi.”

Cewar Ramadan Wanda yake Kallon Hamman nasa.

Gajiyayyun Idanunsa ya d’an lumshe, tare kuma da gyad’a kanshi ahankali, cikin yanayin kasalan daya saukar masa ya nufi stairs din dazai haurar dashi sama zuwa d’akinsa.

Da kallo Mamy da Ramadan suka bishi har saida ya b’acewa ganinsu, kana Mamy taja dogon numfashi tare da sauk’e ajiyar zuciya...!


*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA




By
*GARKUWAR FULANI*





📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 13
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

*FREE PAGE ne*

*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya kafin ki karanta cikin salama da aminci special Group 1k ƙaramin group 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 in Kuma baki da halin turawa ta account sai ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp 09097853276*

Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻‍🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻‍🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻


Yayinda acikin ranta take fata da kuma burin ganin auren d’an nata, Tabbas tana matuk’ar son ace mata Rayyern dinnata yayi aure, domin kuwa ko babu komai zai samu macen da zata kula dashi, Wanda zata jib’anci duk wani al’amuransa, kama daga ci da sha zuwa farin cikinsa kula mishi da tsabtan muhalinsa ko Ramadan ma ya huta.

Sai-dai kuma amma ya zata yi, tunda duk sun fahimci cewar ba son auren yake ba, baya shiga harkar mata, balle harsu saka ran cewar watarana zai samu wacce zata yi mishi.
Ido ta zuwa Ramadan wanda kiran wayarsa da akayi yasa ya miƙe ya nufi Dinning area, bisa kujera ya zauna.
Bisa alamu duk.
Raihana ce ta kirashi budurwarshi.

Rayyern kuwa yana isa cikin bedroom din, kayan jikinsa ya rage tare da shigewa cikin bathroom ya sakarwa kansa ruwa.

Idanunsa ya lumshe adai-dai lokacin da yaji Sauk’an Sassayan ruwan showern akan fatar jikinsa.

Haka yakejin wani irin nutsuwa na musamman na sauk’ar masa.

Ahankali kuma yakejin duk tarin gajiyar da yayi yana sauka.

Atsanake ya kammala wankan nasa, inda ya fito daga shi sai towel dake daure a kugunsa, ad’ayan hannun nasa kuwa mini towel ne Wanda yake tsane jikinsa dashi.

Bayan ya kammala ne kuma ya Shafawa jikinsa wani had’add’en mai, tare da men spray mai dadin kamshi.

Sabin riga da wandon da ya ciro daga cikin drawer d’insa ya sa.

A hankali ya fito dan sauƙa ƙasa, coffee yake so ya ɗan sha.

Yana fita falo kuwa ya samu Abba da Ramadan a tsakiyar falon da alamun mgnar Aure Ramadan yakeyiwa Abba.
Shi kuwa Abba idanu kawai ya zubawa Ramadan yana kallonsa, ya sani a zatonsu bai damu da mgnar auren Rayyern bane.
Shi kuwa yasan sunada babban buri da manufa da shi yakeso yaga Rayyern ya cimmawa, so ganin bai damu da harkar mata bane yasa ya zuba mishi ido, tunda shi nuna musu yake baima san me akeyi da maceba shi kanshi yasan aiyukan daya ɗaurawa Rayyern sun mishi yawa sunfi ƙarfin shekarunsa kawai ƙarfin hali ne da ƙwazo da jarunta yasa yake iya leading komai yadda ya kamata, amman ya rasa lokacin kansa, yana son ya sashi ya saki aikin asibitin ya fuskanci kasuwanci su, to kuma yasan likitancin shine burinsa badon hakaba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment