Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Allah Riyyam kaiko daga wacce k’asa kake?”

Riyyam dake cin abinci gyara zamansa yayi, tare da fuskantar Mamy’n, kana aladabce cikin bagwariyar sausarsa yace.

“Ni d’an k’asar Ethiopia ne, acan mahaina da kuma y’ar uwata suke, acan aka haifeni kuma acan na taso nayi rayuwa, nazo nan Nigeria ne kuma saboda, abokina Naseer.”

Ya k’are maganar tasa yana me nuna Naseer dake shan Chapman din da Mamyn ta had’a.

Mamy kuwa still murmushi tayi tare da soma cin abincinta.

A Dai-dai lokacin ne kuwa Rayyern ya soma sauk’owa daga kan steps din falon, wanda ya sake shirya kansa cikin wasu had’add’un riga da wando, na normal jeans.
Sai-dai ganin da yayiwa su Abba da kuma Riyyam-nsra akan dining table ne, ya sashi tsayawa tare da zuba musu ido.

Abba kuwa da har yanzu baidainajin bugawar zuciya ba, d’ago kansa yayi ya kalli Naseer tare da cewa.

“Kai kuma a ina kake, su waye kuma iyayenka?”

Jin tambayar da Abban yayi ne yasa Naseer gyara zama, cikin dan girmamawa yace.

“Sunan Babana Alhaji Ahmad Dasuki, mu asalin yan Nigeria ne, kuma muna zaune anan cikin garin kano unguwar Rijiyar zaki.”

D’an Jim Abba yayi alamun dogon nazari, kana anutse yace.

“Sunan mahaifinka Alhaji Ahmad Dasuki, amma gaskiya bangane shiba.”

Murmushi Naseer yayi, tare da cewa.

“Eh gaskiya bai shahara sosai ba, saboda ba a b’angaren kasuwanci yake ba, saidai Mamana yar gidan Malam MAI-NASARA ce, ni jikansa ne.”

Lokaci guda walwalan dake kwance akan fuskar Abba ta kau, take duk wani annuri da murmushinsa suka gushe, badon komai ba kuwa saidan jin an ambata masa sunan Malam MAI-NASARA.

Ganin hakanne kuma yasa Ramadan, d’auke kansa daga Kallon Abban nasu da yake, inda ya sauk’e idanunsa akan Rayyern dake tsaye akan steps, wanda shi d’inma kuma Abban nasu yake kallo.
Sam gaba d’ayansu basu San dalilin daya sa, Abban nasu baison gani ko jin wani abunda ya shafi Malam MAI-NASARA’n, basusan wannan sirrinba, haka kuma basusan dalilin ba.

Kai Ramadan ya d’an sunkuyar ahankali cikin kuma rauni, dayin k’asa da murya yace.

“Abba yanzu ma abunda ya dawo dani gida kenan, dazu aka Kai mana Malam Mai-nasara hospital dinmu bashi da lafiya, hypertension and diabetes na damunsa, so akwai buk’atar Lallai lallai Hamma Rayyern ya duba sa, so Ya Sulaiman ya kikkira wayan Hamma Rayyern d’in amma kwata-kwata baya shiga, shiyasa na dawo gida saboda inasaka ran cewa zan iya samunshi, Dan gaskiya jikin Malam din ya tashi sosai!”

Fuska Abba ya sake had’ewa tamau, cikin kuma nuna halin ko inkula yace.

“Babu inda Rayyern zaije, ai bashi kad’ai bane Babban Dr. acikin garin Kano, akwai Doctors da dama, akaishi wani asibitin mana.”

Shiru gaba d’aya falon ya dauka, Yayinda Ramadan ya sunkuyar da kansa k’asa.
Shikuwa Rayyern dake tsaye idanunsa ya d’an rumtse, acikin zuciyarsa yana mai tambayar kansa, dalili da kuma hujjar da tasa Abban nasu bayason alak’arsu da Malam Mai-nasara, Tabbas da ace baisan waye mahaifin nashi ba, zuciyarsa zata iya sak’a masa abubuwa da yawa, saidai kuma amma yasan cewa mahaifinnasa mutumin kirki ne, babu yanda za’ayi wani mummunan tunani yayi tasiri acikin zuk’atansu sun san wayeshi mutun ne managarci daya ginasu kan kekkwan tubali nagarta.

Idanunsa da suke alumshe yadan bude, tare kuma da karasa saukowa akan steps din, kaitsaye ya nufo dining table din, duk da kuwa cewar har zuwa yanzu yanajin kansa nadanyi masa ciwo.

Isowarsa dining table dinne kuma yasa duk suka dago kansu suka kalleshi, Yayinda Abban cikin matsanancin kulawa yace.

“Masha Allah Rayyern ka dawo, ya meeting din naku?”

Kujerar dake gefen ta Abban nasu yaja ya zauna, kana aladabce yace.

“Eh Abba na dawo, meeting kuma Alhamdulillah komai ya tafi yanda ya kamata.”

Kai Abban ya jinjina cike da gamsuwa tare da fadin.
“Alhamdulillah haka akeso ai akoda yaushe.”

Gyara zamansa yayi, kana ahankali cikin kuma yin kasa da murya, hadi da sigar roko yace.

“Abba dan Allah kayimini al'farmar samun daman duba Malam Mai-nasara, tunda Ramadan yace yana da buk’atar taimakona sosai, please Abba dan Allah me zai hana bazaka bari naje na dubashi ba!!”
Ya k’are maganar tasa cikin k’ank’an da kai.

Yayinda Abba kuwa ya dauke nasa kan, tare da sake hade fuskarsa.

Ganin hakanne kuwa yasa Naseer zaro wayarsa, ya dannawa lamban Umminsa kira, cikin sa’a kuwa bugu biyu ta d’auki wayar.

Saidai kuma irin yanda Naseer din yaji sauti da Amon muryarta ne, yasa hankalinsa tashi.
Cikin fargaba yace.

“Ummi ya naji muryarki haka? meyake faruwa kodai jikin Malam ne ya tashi?”

Daga can b’angaren kuwa cikin sheshshek’an kuka Ummin tace.

“Eh Naseer jikin Malam ya tashi sosai, yanzu haka ankaishi Mai-nasara hospital, amma Dr da ya kamata ya dubashi bayanan, gashi kuma yanajin jiki sosai, domin sauran Doctors din da suka dubashi, sun tabbatar mana da cewar jininsa ne ya sauk’a, ga kuma diabetes.”

Idanun Naseer ne sukayi raurau lokaci daya kuma suka ciko da hawaye, ahankali yadan share k’wallan da suka zubo masa, kana yace.

“Kiyi hakuri Ummi Insha Allah Malam Mai-nasara zai samu lafiya, ki daina kuka muma zamu zo nan asibitin nida abokina Riyyam nsra.”

Daga haka kuwa bai sake cewa komai ba ya kashe wayar tasa, ya maida ita cikin aljihu.
Sai kuma ya dago kansa ya kalli Abba wanda har yanzu kansa ke gefe.

Dan jan kujerar da yake kai baya yayi, tare da mikewa tsaye ya iso har gaban Abban ya durk’usa, cikin muryarsa irin ta masu neman al'farma yace.

“Dan Allah Abba kayi hakuri kabar Hamma Rayyern yaje ya duba Malam, yanzu haka Mamana kuka takeyi, kuma tace jikin Malam din ya tsananta sosai, dan Allah Abba kayi mana al'farma, Malam shine duk wani hasken cikin familyn mu, rasashi dai-dai yake da yankewar farincikin mu.”

Still Kai Abba ya sake kawarwa gefe batare daya ce komai ba.

Ganin hakannen kuma yasa gabaki d’ayansu sukaji zuciyoyinsu sun raunata, babu ma kaman Rayyern da hakanan yakejin duk wani al’amuran daya shafi tsohon acikin jinin jikinsa.

Riyyam-nsra kuwa ganin yanda Abban ya kawar da kansa gefe ne, yasashi saukowa daga kan tasa kujerar shima ya durkusa agaban Abba’n.
Cikin sanyin da muryarsa tayi yace.
“Dan Allah Abba kayi hakuri, kabari Hamma Rayyern din yaje ya dubasa.”

Idanu Abba da ransa ke ab’ace ya rumtse, kamar kuma zaice wani abu saiya fasa hade da mikewa tsaye, kana yasa kai ya wuce bedroom d’insa kai tsaye...!




Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg's domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg's sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg's herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba🤗

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg's domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali
Ina masu pimples
Tabo(spot)
Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance
Sister's masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai🧖🏻‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg's insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu

Sannan munada beauty kit wnd yk mayarda fata tadawo tamkar madubi wnd yajaraba shine zai tabbatar
Set din yakunshi Abu 6
Soap,body cream,face cream,scrub, cleanser, glow oil

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself
100%tested nd trusted
Beauty kit:11k
Soap price:3k
Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549
Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg's herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai🙏

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta🙏adade anayi sai gsky🤭🤝

Mg's skincare

By
*GARKUWAR FULANI*







📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 9
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*


*FREE PAGE ne*

*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya ki karanta cikin salama, special Group 1k ne kana akwai karamin group 500 kacal ne 0661110179 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, ko kuma ki sayi katin MTN ki turo ta whatsApp ɗin*



Hakanne kuwa yasa suka bishi da kallo dukansu harsaida ya b’acewa ganinsu.

Ahankali Rayyern da Ramadan suka dawo da kallonsu ga Mamy wacce itama tayi zugum, da dukkan alama kuma bata da abuncewa.

Naseer kuwa mik’ewa tsaye yayi, kana jikinsa amatuk’ar sanyaye ya kalli Mamy, cikin bayyana godiyarsa agaresu yace.

“Zan tafi Mamy, mungode sosai da karramawarku agaremu nida abokina Riyyam.”

Jin abunda Naseer din ya fad’ane kuma yasa Riyyam ma saurin mik’ewa, tare da cewa.

“Naseer jirani mu tafi asibitin tare.”

Kai Naseer din ya girgiza tare da kama kafadun Riyyam, cikin sanyi yace.
“A’a Riyyam ka zauna, kada kace zaka bini, saboda asibitin Mai-nasara bak’aramin asibiti bane, ko ni da zanje yanzu sainasha tambaya kafun zan iya gano ward d’in da suke, kayi hakuri kaji duk yanda ake ciki zan kiraka awaya Insha Allah ina dai zaka gane hotel ɗin da ka sauka?.”

Kai Riyyam yadan jinjina batare kuma daya soba, haka yabar Naseer ya tafi shi kad’ai.

Ganin fitan Naseer dinne kuma yasa, Rayyern mikewa ahankali, cikin kuma takin dake bayyana nutsuwarsa, ya nufi dakin Abban nasu kai tsaye.

Ajikin k’ofar ya tsaya tare da daura hannunsa akai ya d’anyi knocking.

Daga ciki Abba dake zaune akan wata kujera ya jingina kanshi ya rumtse idanunshi ya bada izinin shigowa.

Ahankali Rayyern ya tura kofar dakin ya shiga, bakinsa dauke da sallama.

Amsa masa sallamar nasa Abban yayi, tare kuma da kafesa da ido.

Shikuwa Rayyern anutse ya karaso ya zauna agaban Abban nasa.
Rank’wafar da kansa k’asa yayi, sannan aladabce yace.

“Kayi hakuri Abba, duk da bansan manufarka ta aikata hakan ba, amma Ina mai rokonka daka bani daman zuwa duba lafiyar Malam Mai-nasara, yau akaron farko yazo hospital dinmu, yana kuma cikin halin buk’atar wanda zai kula da lafiyarsa, dan Allah Abbana kayimin wannan alfarmar, domin kuwa hakkina ne na kula da duk wani marar lafiyar da yazo asibitin mu, aiki na ne hakan, nabawa duk wani marar lafiya kulawa, Dan Allah Abba karkace a’a, domin yin akasin hakan tamkar wulakanta marar lafiya ne.”

Idanu Abba ya lumshe, tare da sakin ajiyar zuciya, domin kuwa Tabbas yasan cewar shi ya d’aura Rayyern din, akan turban da duk yanda abu yake, idan aka rokeka da Allah da Manzon sa to zaka aiwatar.
Yasani kwarai ya gina ƴaƴan nasa, akan tubalin tausayawa duk wani mai neman taimakonsu.

Ajiyar zuciya ya kuma saukewa akaro na biyu, kana cikin tausasa murya yace.

“Shikenan tunda ka had’ani da Allah Rayyern, kaje ka dubashi, amma iya taimakon daya kamata kawai zakayi mishi, da zaran yaji sauki kuma, ayau nakeso ka sallameshi banason ya kwana acikin asibitin.”

Dagowa Rayyern yayi fuskarsa dauke da murmushin jin dadi, yace “Insha Allah Abba, idan yaji sauki ayau yau zan sallameshi, nagode sosai da wannan alfarmar!”

Kai Abban ya jinjina, kana shikuma batare da wani b’ata lokaci ba ya tashi ya fice daga cikin dakin.

Direct bedroom d’insa ya nufa, Yayinda ya d’auko wayoyinsa da kuma yan k’ananun abubuwan da yasan dole zai bukata.

Koda ya sauko kasa, haka ya samu Mamy Ramadan Riyyam sunyi zugum.

Kallon Ramadan din yayi, cikin yanayin saurin da yakeyi kuma yace.

“Ramadan zo mu tafi hospital din.”

Ai kuwa jin haka yasa Ramadan mikewa cikin sauri, ya marawa Rayyern din baya, kasancewar tuni harya fara tafiya.

Koda suka fito cikin mota d’aya suka shiga, ak’agauce kuma Hadi drivern yaja motar suka fice daga cikin gidan.

Ak’alla saida sukayi tafiyar 17mn, kafun suka iso babban katafaren Mai-nasara Hospital d’in, wanda aka k’awata gininsa kamar ak’asar turai.

Koda driver yayi parking Rayyern baijirayi komai ba, cikin hanzari ya bude murfin motar ya fita.
Yayinda Ramadan ya take masa baya.

Sulaiman da yanzu fitowarsa daga cikin office dinsa, hango Rayyern din da yayine yasashi k’arasowa da sauri.

Rayyern kuwa ak’agauce, batare ma daya bari sun gaisa da Sulaiman din ba yace.

“Awani ward aka kwantar da Malam Mai-nasara?”

“Emergency ne, amma kuma abisa tunanin ba zai samu ganinka yau ba, yasa Manyan ya'yansa suka daukeshi zuwa wani hospital din na daban.”

Idanu Rayyern din ya kankance tare da dafa kansa, dake sarawa da d’an k’arfi yace.

“Shitt! Why Sulaiman? Meyasa bazaka ce musu sujirani ba?”

Kai Sulaiman yad’an girgiza tare da cewa.

“Nakira duka wayoyinka is not available, gashi jikin nasa yana ta tsananta, kuma kaine wanda ya dace ka dubasa, domin mu munyi iya yinmu, yan uwannasa kuma sun kasa hakurin jiran zuwanka, shiyasa suka daukeshi zuwa wani asibitin daban.”

Idanunsa da suka d’anyi ja ya rumtse, saboda Sam ba haka yaso ba, hakika yaso ace shida kansa ya duba mutumin.

Juyawa yayi ya nufi office d’insa, yana maijin ransa duk a jagule, ga kuma ciwon kansa da a yanzun yake sake karuwa.

Koda ya zauna acikin office din, ji yayi gaba daya zaman asibitin ya ishesa, hakan yasa shi tashi ya fito.

Anan yasamu Ramadan ma na shirin komawa gida, saboda yasan sunbar Riyyam shikad’ai acan.

Kamar yanda suka zo kuwa atare suka koma.

Inda Koda suka shigo cikin falon gidan, azaune suka iske Riyyam-nsra kan lallausan carpet din dake malale a tsakiyar falon, agefensa kuwa Mamy ce, Yayinda shi kuwa yake rik’e da wayarsa yana sana’arsa ta chatting.

Saidai kuma duk da chatting din yake, amma bakinsa baiyi shiru ba, labarai kawai yake ta bawa Mamy kala kala, wanda kuma duk rabin labaran nasa akan Mammynsa da kuma Zaytoon abokiyar tagwaicin sa ne.

Mamy dai itakam zamanta da yaron ya sata nishadi sosai, saboda labarai ne na abun dariya yake bata.

Kallon Riyyam-nsra da Mamyn Rayyern yayi, batare kuma da yace wani abuba kaitsaye ya haura sama, saboda so yake yasha magani ya kwanta, ko zai samu relief na headache din dake damunsa.

Ramadan kuwa zama yayi suka sha hiransu, kafun daga bisani ya kama hannun Riyyam din, suka haura dakinsa dake sama.


Acan b’angaren Jannart kuwa, sunyi waya da Salman.
Inda yake shaida mata cewar.

Ya samu information akan sunan hospital din su Rayyern din, da kuma yanda za ayi su samu ganinsa idan sunje hospital din.

Ajiyar zuciya Jannart ta sauk’e adai-dai lokacin da ta zare wayar daga kunnenta.

Cikin kuma halin Kosawa tace.

“Yah Allah Kataimakeni, ka had’ani da wannan mutumin, da nemansa yafi na kud’i wahala, mutum shiba Diamond ba amma ace wai ganinsa ya zama aiki, yau shine can Gobe shine nan, wai dole saikabi wasu matakai kafun ka iya ganinsa, babban ma abun takaicin shine Kwata-kwata, ko a social media babu wani information akansa, baya Facebook baya Instagram only Twitter kawai, still kuma a Twitter dinma, babu wani information akansa, ko hotonsa babu.”

Yar siririyar tsuka taja, tare kuma da turo dan karamin bakinta gaba, kana ashagwab’e tace.

“Idan ma ba munafurci ba da rashin gaskiya. Meyasa yake boye kansa, da har za’ace kwata-kwata babu wanda ya tab’a ganin fuskarsa? A jaridu ko a TV Maybe ma shidin irin ɗima-ɗiman alhazawan nanne masu tafiya da kyar da kuma katon ciki ne, shi yasa yake boye kansa.”

Momy dake tsaye abayanta ne tace.

“Lafiyarki kuwa Jannart keda wa kike ta tashin k’ananan maganganu?”


Juyowa tayi tare da Kallon Momyn kana ta kwab’e fuskarta.

“Momy aiki aka bani a office, gashi kuma aikin sai wahalar dani yakeyi.”

Ta kare maganar tana me zare earpiece din dake kunnenta.

Dan Murmushi Momy tayi hade da cewa.

“To Allah Ya baki sa’a, amma dai yanzu kam ki ajiye aikin kitchine dinnan haka kije ki huta, zan karasa dafa pepper meat din da kika fara.”

“To Momy.”
Tafad’a a sanyaye tare da ajiye baban spoon din dake hannunta.

Momy kuwa da kallo ta bita harta gama ficewa daga cikin kitchine din, Allah yasani duk da cewar ba itace ta ta haifi yarinyar ba, amma tana matuk’ar so da tausayinta.
Saboda yanda rayuwar yarinyar yake cike da sarkakiya mai daurewar hankali da tunani.
Wanda kuma ita kanta haryau ta kasa gano gaskiyar hakikanin abunda ke boye.


Jannart kuwa Koda ta fito daga cikin kitchine din, anutse take tafiyar ta batare kuma da ta lura da Yah Junaid dake zaune acikin falon yana shan shisha ba, direct ta wuce bedroom dinta.
Dan dauro alwalan sallan Magriba.

Junaid dake zaune kuwa da idanunsa yabi manya manyan hips dinta harsai da ta b’acewa ganinsa,
(Yana ɗaya daga cikin illolin da sa suturun banza suke jawa ɗiya mace, koda kuwa a cikin gidanku ne).
Kafun ya iya rumtse idanunsa, tare da shakawa cikinsa hayakin shisha.

Allah Yasani yana matuk’ar so da buk’atar kanwartasa fiye da komai aduniya.
Domin akanta yakanji kamar ana ingiza sa kowacce rana.

Haka kuma idan dai zai ganta sau dubu da irin shigar data zame mata ɗabi'arta to Tabbas zaiji sha’awarta sau dubu yanayin shigarta ke ingiza lafiyar samartakarsa.

Mikewa tsaye yayi kamar zai bi bayanta kuma sai ya fasa, tare da komawa ya zauna ya cigaba da bankawa cikinsa hayakin shisha, duk da kuwa yanajin ana kiran sallan magriba, amma haka yayi biris tamkar ba yaji.
To dama sallan bawani damunsa tayi ba.


Acan gidansu Rayyern kuwa har akayi sallan Isha suna tare da Riyyam.
Wanda kusan atare ma sukaje masallaci sukayi sallan magriba dana isha.

Yanzu ma kammala dinner dinsu kenan, Riyyam din ya mike tsaye, tare da duban Abba da Mamy.
Cikin girmamawa yace.

“Abba Mamy zan koma masaukina, na kuma nagode da karramawarku sosai.”

Ramadan dake zaune ne ya rik’o hannunsa tare da fadin.

“Haba Riyyam-nsra a daren nanne zaka koma hotel, please ka kwana anan mana, ai duk munzama daya....”

Sauran maganan dake bakin nasane ta makale amakoshinsa, sakamakon mummunan kallon da yaga Abba ya watsa masa.

Shikuwa Riyyam-nsra da bai lura da Kallon da Abban yayiwa Ramadan dinba, murmushi yayi.
Kana cikin nuna godiyarsa yace.

“Kayi hakuri Hamma Ramadan watarana ai Zan dawo.”

Kai Ramadan din ya jinina, Cikin waskewa kuma yace.

“Shikenan ba matsala To muje na saukeka.”

Saida safe Riyyam din yayiwa Mamy da Abba, inda suka amsa masa amutumce.

Kallon Rayyern dake zaune Riyyam din yayi, kana ya dan rankwafo ya rungumesa, cike da k’aunar Rayyan din da yakeji acikin zuciyarsa yace.

“Saida safe Hamma Rayyan.”

Kai Rayyern din yadan jinjina masa.

Yayinda Ramadan kuwa ya kama hannun Riyyam-nsra din suka fice.

Saida suka hau titi ne kuma Riyyam-nsra din yake fadawa Ramadan hotel din da zai kaisa.

Yayinda acan gidannasu kuwa , bayan tafiyar su Ramadan din Rayyern tashi yayi ya wuce bedroom d’insa.

Wanka yayi bayan ya fito ne kuma ya d’auki system d’insa, ya soma latsawa, Yayinda akai akai yake saka nutella chocolate abakinsa.


Agaban babban Hotel din na Taheer Guest Palace Ramadan ya sauke Riyyam, tare dayin exchanging phone number atsakaninsu.

Bayan kuma Ramadan din yace da Riyyam Gobe yazo suyi breakfast tare ne, suka sakeyin sabuwar sallama, Yayinda Riyyam kaitsaye ya wuce cikin hotel din.
Shikuwa Ramadan juya akalar motarsa yayi zuwa gida.

12:30 am dai-dai Rayyern ya kashe laptop dinnasa, tare da mirginawa ya kwanta akan gadonsa.
Wanda daga zaman nasa awajen zuwa yanzu yashanye fiye da rabin Kwalban Nutella chocolate.

Idanunsa yadan lumshe saboda yanda yakejin bacci na game cikinsu.

Sannu Ahankali kuma ya soma ambaton sunan Allah ahaka har baccin ya daukesa.

Acan sashin Riyyam-nsra kuwa, koda ya shiga dakinsa na hotel din, haka ya tarar da komai nead.

Wanka yayi tare da zuwa ya fada kan gado, hade da jawo wayarsa ya runguma, bayan ya kunna data ne kuma ya shiga whatsapp sama sama yayi chatting acikin whatsapp din, kana daga bisani kuma ya dawo ta inda yafi karfi Wato Tiktok.

Atakaice dai saida yakai kusan 2am yana sheke ayarsa kafun bacci barawo ya daukesa, haka kuwa yayi baccin yabar data d’insa akunne.


Washegari.

Kamar koda yaushe yauma 7:30 am ya gama shirya kansa tsab, cikin royal high quality black suit, tare da white long sleeve wacce tayi masa kyau sosai.

Kasancewarsa mai kyau ne kuma shiyasa komai ya saka saiyayi masa kyau.

Ahankali yake saukowa daga kan steps din falon, Yayinda briefcase d’insa ke rike ahannunsa na dama.

Mamy dake tsaye tana shirya dining table ne ta dago ta kalleshi.

Ɗan guntun Murmushin gefen baki yayi, wanda ya ɗan bayyana fararen haƙoransa, kana cikin nitsuwa yace.

“Good morning Mamyna.”

Murmushi itama Mamyn tayi, cike kuma da soyayyarsa tace.

“Morning My beautiful son, kafito a dai-dai maza zokayi breakfast dinka.”

Karyar da wuyansa gefe yayi, tare kuma da duban agogon hannunsa.
Muryarsa adan sanyaye yace.

“I’m sorry Mamyna yau sauri nakeyi, amma idan Ramadan yazo fita ki hada masa breakfast dinnawa a basket ya kaimin office.”

Murmushi Mamy tayi tare da cewa.
“To ba matsala adawo lafiya Allah ya tsare ya kuma bada sa’a.”

Da “Ameen.” Ya amsa kana cikin jin dadi ya Sakai ya fice daga cikin falon.

Dai-dai fitowarsa compound din gidanne kuma, Riyyam da Ramadan suka shigo atare.

Cikin sauri Riyyam ya karaso, tare Da dan rungume Rayyern din, fuskarsa dauke da Murmushi yace.

“Good Morning Hamma Rayyern!”

Idanu Rayyern din yadan lumshe tare dasa hannu ya shafa kan Riyyam din, cikin kuma yanayinsa na rashin sabo dayin magana yace.

“Morning Riyyam, Ina fata kunyi waya da Naseer yau, ya jikin Malam din?”

Kai Riyyam din ya jinjina tare da fadin.

“Eh munyi waya dashi, ya kuma tabbatarmin cewa jikin Malam din da sauki.”

Kai Rayyern din ya jinjina tare da cewa.

“Okay bani numbern Naseer din.”

Yafada yana me mikawa Riyyam wayarsa dan yasa masa numbern Naseer.

Ramadan kuwa kai ya jinjina cike da gamsuwar lallai Hamman nasa ya dauki lamarin malam da matuƙar mahimmanci.

Hakan kuwa akayi domin cikin abunda bai wuce 1mn ba Riyyam ya sakawa Rayyern din numbern.

Ramadan kuwa dake tsaye fuskarsa dauke da dan mamaki yace.

“Hamma Rayyern me zakayi da numbern Naseer kuma?.”

“Zanje na duba Malam Mai-nasara ne, tunda har Abba ya a mince dana dubasa din, tofa Tabbas saina duba sa, zan kira Naseer din idan basa hospital har gidansa zanje na dubasa.”

Rayyern din ya fada in full confidence.

Ramadan kuwa Kai ya jinjina cike da gamsuwa, sai kuma suka hada baki atare shida Riyyam wajen cewa suma zasuje gidan Malam Mai-nasara din.

Kansa kawai ya kad’a, adai-dai kuma lokacin da yake shiga cikin motarsa yace.

“Okay nidai yanzu hospital zan wuce, sai Idan na tashi ne zan biya can gidan nasa, amma idan kuna da chance zaku iya zuwa maybe mu hadu acan .”

Yana gama fadan hakan yaja murfin motar ya rufe, batare kuma daya saurari mai zasu sake cewa ba, yasa Hadi driver yaja motar suka bar wajen.

Su kuwa Ramadan da Riyyam kaitsaye cikin gidan suka wuce.

Koda suka karasa cikin falon Riyyam aladabce ya gaishe da Mamy da kuma Abba wanda yake yanzu fitowarsa daga daki.

Cikin farincikin ganinsa Mamy ta amsa, Yayinda Abba ma ya amsa masa fuska asake.

Anan kan dining table sukayi breakfast.
Bayan kuma sun kammala ne Riyyam da kansa ya gyara wajen, tare da kai plates din da suka bata kitchine ya wanke.

Mamy kam cike da mamaki take kallonsa, domin kuwa duk da ta hanashi saida yayi, inda yake bata labarin cewa ai yanayiwa Mammynsa ma, saidai watarana dagangan sai yakiyi dole Zaytoon ce zatayi.

Mamy dai itakam dariya kawai takeyi, saboda daga jiya zuwa yau din kawai, zama da yaron ya zame mata sabo.
Abba kuwa ido ya zuba musu da inda yake zaune can tsakiyar falon yana nazartar ƙarfin halin Riyyam-nsra da shisshiginsa garesu anya kuwa!?.
Ya ɗiga ayar tambaya a kan yaron.

Acan hospital kuwa Rayyern bayan yadan duba wasu daga cikin patients dinsa ne, ya d’auki waya ya kira Naseer.

Bayan sungaisa ne kuma yake tambayar Naseer din, jikin Malam Mai-nasara.
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment