Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

daya taji wani irin karyewar zuciya, wanda hakan yasa dole ta d’an janye jikinta gefe, tare da matsawa gefen had’add’un shuke shuken flowers din dake wajen.

Duk abunda takeyi kuwa Salman na lure da ita.

Yayinda Asiya kuwa taketa murmushi jin daɗi tunda itama ta rasa dama suna Allah yasa su rasa.
Wato irin a mutu har liman din nan

Suna tsaitsaye awajenne kuma.

Suka hango shigowar wata masifeffiyar mota had’add’iyar BMW bak’a mai matukar kyaun gaske da tsada.

Wani irin bugawa Jannart taji zuciyarta tayi, lokaci daya kuma duk suka kakkafe motor da ido hardai aka gama dai-dai-ta parking.

Bayan motor ta tsayane kuma, wani mai bakaken kaya ya fito cikin hanzari, inda ya zagaya ya bud’e murfin motar Usman P.A Kenan wanda shine yaja motar ma.

Ahankali ya zuro da k’afafunsa wanda sukasha tsadaddun bakaken takalma waje, lokaci daya kuma shima ya fito waje.

Yayinda ajikinsa yake sanye da royal blue suit masu masifar kyau.


Idanu Jannart ta zazzaro waje, Yayinda takejin tsanantawan da bugun zuciyarta yayi.

Amatuk’ar rud’e take binshi da kallo, lokaci daya kuma ta kwab’e fuska kaman zatayi kuka.

Cikin hanzari kuma ta nufi inda yake tsaye.

Matsowa tayi gab dashi, batare kuma dako lura da hakan da tayi ba, tace.

“Kai kuma, ya haka?
Toh ina yake Ina Dr. din? Bakace zaka zo dashi ba, Meyasa To zaka zo Kai daya kuma me zakayi mana? Kai me zanyi da kai”

Idanunsa yadan zuba mata.

Dai-dai lokacin ne kuma MD yakaraso wajen da matukar sauri.
Yace.

“Masha Allah sannu da zuwa.
Sir Sannu da zuwa, Mara ba da zuwa gidan tv’n mu, Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara!!”

Dammmmmm haka zuciyar Jannart ta buga, alokacin da taji abunda MD din nasu ya fad’a.

Idanunta ta zazzaro waje tana me Kallon mutumin da taji ankira da Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.

Shikuwa Rayyern hannu ya mikawa MD n suka gaisa cike da mutuntaka.

Ganin hakanne kuma yasa duk sauran ma’aikatan dake wajen suka karaso, fuskarsu dauke da matsanancin farinciki sukeyi mishi sannu da zuwa cikin iya aikinsu da karrama manyan baƙinsu na musamman ne.
8Kusan irin karramar da za'ayiwa Dr Rayyern Mai-nasara.
In AYSHA ALIYU GARKUWA taje ba irinshi za'ayimata ba. Kunsan ace tuwon girma miyansa nama)
Da matukar girmamawa kuwa MD'n Yayi masa iso zuwa, cikin wani babban dakin tarban baki dake sashin.


Salman da Jannart kuwa kasa Koda motsawa sukayi, saboda tsananin mamakin da suke ciki.

Kallon Salman Jannart din tayi, cike da tsananin mamaki tace.

“Wai gizo idanuna keyi ne Salman ko kuwa gaskiya ne?”

Salman da shima ya shiga shock sosai, Kai ya Dan girgiza tare da cewa.

“Ko d’aya Jannart ba gizo idanunki keyi miki ba, shidinne dai, amma muje saboda mu sake tabbatarwa.”

Saurin jinjina masa Kai Jannart din tayi, tare da bin bayan Salman din suka shiga ciki.

Yayinda acan cikin kuwa, gaba daya MD ya rude da tsananin farincikin ganin Dr. Rayyern din mutumin da duk kafafen sada lbaran kasar Nigeria'n ke nema ganawa dashi basu samu. Sai su a yau ai yana cikin farin ciki.

Hakan yasa da kansa ya shiga debo masa drinks yana Jerawa akan babban table din dake tsakiyar dakin cike da mutuntaka.

Still kuma har yanzu bakinsa baiyi shiru ba, sannu da zuwa kawai yaketa Jerowa su Rayyern d’in.

Yayinda shikuwa Rayyern ke dan sakin murmushi, saboda yawan magana ba al’adarsa bace.

MD kuwa saida ya cika gaban su Rayyern din da kayan ciye ciyen fruit kala kala.

Cikin kuma sakin fuskan, dake bayyan tsananin jin dadinsa yace.

“Bismillah Dr ka sha ruwa, Domin yanzu saura mintuna 5 a fara shirin, kasamu kadan taba wani abu.”

Kai Rayyern din yadan girgiza, Cikin kuma muryarsa dake bayyana ajinsa akoda yaushe aji irin na mutunta kai ba girman kai.
A mutunce yace.

“Alhamdulillah Nagode, saidai kuma bani da ishashshen time, Ko zamu iya wucewa inda za’a haska shirin kaitsaye?”

Kai MD ya jinjina da sauri, cikin jin dadi da murna yace.

“Mezai hana ai muje kawai, mu zuwanka ayanzu ya fiye mana komai.”

Mikewa sukayi inda MD din ya shige gaba da sassarfa dan nunawa Rayyern din dakin da za’a haska shirin.

Inda tuntuni Jannart ta shiga cikin babban hall din ta zauna, gaba daya hall din cike yake da cameras, da kuma abubuwan daukan sauti da sauran na'urorin daukar hoto da sauti kai tsaye.

Yayinda aka shirya camera's sukayi layi, Yayinda duk suka zaku da son Ganin bakonna su.
Ba kuma ga iyasuba harda sauran ma’aikatan dake gidan TV, da kuma mutanen cikin ƙasar mu Nigeria kasancewar Tashar Arewa 24 TV tashece mai inkantattun kayan aiki da haziƙan mahaikata.
Kasancewar shirin live ne kaitsaye za’a haska shi wa duniya alokacin da ake tsaka da daukanshi.

Jannart kuwa da take zaune akan kujerar dake tsakiyan wajen.
Yayinda can gefe kuwa kujerune a jere.
Inda wasu daga cikin ma'aikatan ke zazzaune

Jannart kuwa.
Shiru tayi tana me mamakin yanda al’amarin ke shirin kasancewa.
Yayinda Salman dake can gefe shidinma zallar mamakin faruwar hakan yake.

Shigowar Dr. Rayyern da kuma MD wajen yayi dai-dai da cikar lokacin da za’a fara shirin.

Wannan yasa tun kafun Dr. Rayyern din ya karaso kan babban stage din da mazauninsa yake suka fara dauka.

Yayinda Rayyern kuwa ganin wace zatayi masa tambayoyin, yasa ya d’an hade rai.
Acikin zuciyarsa kuwa cewa yayi.

“Kenan karya sukamin itace zata gudanar da shirin, bawai wancan namijin ba.”

Azahiri kuwa karasowa kan stage din yayi, tare da zama akan kujerar dake fuskantar na Jannart din.

Yayinda Jannart kuwa ta danne duk wani tunani dake ranta, juyawa tayi ta kalli camera hade da cewa.
“B....!


*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.


Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*




By
*GARKUWAR FULANI*





D’an gyara zamanta tayi, tare da sake fuskantar cameras din dake shooting fuskarta.

Ajiyar zuciya ta d’an sauke tare da nemo jarumtarta dake suɓuce mata,
cikin Taushi da kuma amon muryanta zakin tace.

“Assalamu Alaikum Masu kallonmu, sannunmu da arzikin sake saduwa, acikin shirinmu mai farinjini wanda mukeyi Domin farincikin ku, wato Bak’onmu na Mako, To ayau dai shirin namu ya gam da katar yayi babban kamun gayyato muku wani babban bak’o, wanda nasan idanuwanku suna cike da dokin ganinsa. Wannan bako kuwa ba kowa bane face. Dr...!”.
Sai ta kuma datse sunan tare da sakin murmushi.
Wanda hakan yasa kab masu kallo suka ɗokanta da son jinnwayene baƙon makon.
Mayafin kanta ta ɗan gyara tana mai jin harshen ta bazai iya furta sunansa ba, cikin nitsuwa ta tare da lumshe taci gaba da cewa.
“Sanannen mutumin da sunansa yayi shuhura acikin kasarmu Nigeria dama wajenta baki daya, nasan da yawan masu kallo basu tab’a Ganin wannan bak’on namu ba.
Dan yauce rana ta farko daya amsa gayyatar wata kafar sadarwa ta jarida, da TV. Alhamdulillah sai namu a yau.
Kasancewarsa Babban Doctor kuma babban d’ankasuwa da duniya ke damawa dashi, saboda haka yau dai gamu gashi, zakuma mu haska mukushi, inda zai fayyace mana koshi din waye.”

D’an tsagaitawa da maganan nata, tayi tare da juyowa Ahankali ta fuska ce sa.
Cikin muryarta mai taushi tace.

“Doctor barkanka da zuwa, barkanka kuma da shigowa cikin wannan tasha tamu mai Al'barka, da fari dai munaso ka gabatar da kanka ga masu kallonmu.”

Numfashi ya d’an sauk’e, batare kuma da wani sakin fuska ba, ya dago da kansa ya d’an kalli cameran a fakaice, cikin muryarsa da ako yaushe yake kara bayyana asalin wanene shi yace.

“Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.”

Ya k’are maganan atak’aice, Cikin kuma halin nitsuwa.

Kai Jannart din ta jinjina, tare da hade yatsunta awaje daya, cikin tsananin kwarewa da sanin makamar aikinta tace.

“Masha Allah to Dacta, yanzu dai ka gabatar da kanka awajen al’umma, saura kuma mu shiga cikin shirin namu ka'in da na'in,.
Dai-dai lokacin kuma aka ɗan ɗauke fuskokinsu aka sa ɗan sautin tambarin tashar Arewa 24 din.
Kana aka dawo dasu.
Cikin nitsuwa ta ɗan kalleshi a fakaice kana a hankali tace.
“Shin amatsayinka na cikakken Likita, wanda kasa keji dashi, wacce irin shawara zaka bawa al’umma dan kula da lafiyarsu da matakan kariyar riga-kafi?.
Sannan kuma ya kake Ganin irin yanda al’amarin k’asarnan yake, ma’ana irin halin da al’ummar k’asar take ciki, da kuma irin k’alubalen da muke fuskanta more Especially wurin kiwon lafiyar kananan yara da mutanen karkara da tsofaffinmu, Sannan wani irin hanya da kuma mataki zamu bi, Domin mu samu nasara akan yaƙar cututtukan dake addabar al'ummar ƙasar mu?
Then menene matsalarmu aharkar malaman kiwon lafiya?”.

Kanshi ya ɗan kauda gefe tare da yamutsa fuska, ɗan gajeren tsaki yaja.
Ji yadda yarinyar nan take zuba babu ƙaƙƙautawa kamar carbi ya tsinke ko numfashin bata ja.
Ta wani jero min tambaya kusan goma, a dungule.
Ni Radio ne ko ni parrot ne da zan iya haka.
Duk yayi tunanin cikin second 5.
Numfashi ya ɗan fesar kana cikin haiba da dakewar murya yace.
“Privet Hospital!!!
Sune matsalan kiwon lafiyar kasarmu.
Domin sune suke dak’ushe asibitocin gwamnati, har suke zama ba masu inganci ba.”

Ya fad’i maganan kai tsaye, batare kuma da wani dar ko shakka ba.

Jannart kuwa Kai ta d’an jinjina, tare da sake rik’on wani farin card dake hannunta, saboda acikine duk wani tsare tsaren tambayoyin da zatayi masa suke.

Kanta ta d’ago daga Kallon takardar da takeyi, still kuma Cikin muryarta da akoda yaushe take fitar da daddad’an sauti tace.

“To Dakta. munji abunda kace. Kuma al'umma zata iya gamsuwa da hakan.
Toh amma kamar wani mataki za’abi, Domin asamar da ingancin asibitocin Gwamnati da kiyaye lfy?.”

Numfashi ya ɗan fesar a hankali kana yace.
“Dole gwamnati ta tsaya ta gyara asibitotin ta, ta ingantasu hade da kawo nagartattun kayan aiki, da kuma kwararrun ma’aikata, baya ga haka kuma ta rika biyan likitotin isassun kudaden da zasu iya biya musu bukatunsu, saboda mafi akasari acikin kasar bawai Nagartattun Doctor’s dinne bamu da suba, kawai dai basa samun yanda suke sone, hakanne kuma yasa suke fita wasu k’asashwn suje su fara aiki Acan, ko kuma kowannensu saiya zaga gefe yaje ya bud’e asibitin kanshi, saboda baisamu yanda yake so a gwamnati ba, wannan dalilin yasa ayanzu asibitocin gwamnati suka lalace suka zama kara zube,, Domin anriga da ancire Tubalin abunda aka gina asibitin akai haka yasa duk mai ƙarfi da yar wadata bazaibi ta kan asibitin gwamnatin ba, wanda kuma da al'ummar ƙasa aka ginasu.
Sannan yana da matukar muhimmanci ga iyayen yara suke kula da tsabtar jikin raya da muhalli da abinda zasuci domin shine babban rigakafi.”
Ya k’are maganan yana me gyara zaman necktie din dake wuyansa.
Sosai yayi masifar kyau yadda yake dan jujjuya fararen yatsunshi

Inda Jannart kuwa ta ci gaba da cewa.

“To Doctor yaya za’ayi agyara matsalar Government Hospitals din domin in ƙantasu ta yadda al'ummar ƙasa zasuje garesu da kekkyawan yaƙini!?.”

Dan muskutawa yayi still kuma cikin rashin tsoro ko fargaba cikin yaƙinin da Kekkyawar manufa yace.

“To Da farko dai asibitotin gwamnati abunda zai gyarasu abu maisauki ne!?”.
Da sauri ta ɗan fuskanceshi tare da cewa.
“Duk da lalacewar da sukayi gyaran mai sauƙin ne? Ta yaya ko kuma ta ina gyaran zai fito da sauki!?”.
Cameras din ya ɗan kalla kana ya gyara zamanshi tare ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya cikin masakaicin amo yace.
“Idan har gyara akeso ta yadda zasu in ƙanta tofa dole daga kan, Shugaban k’asa, Governors, Ministers, senator's har zuwa kan ciyamomin kana kama daga Sarki, Waziri, Galadima, Wambai, Chiroma, Durbi, Garkuwa, Ɗan buram, Majidadi, Ma'aji, dama duk wasu masu fad’a aji, na siyasa da masarautun gargajiya. suyi kokarin daina zuwa asibitotin kudi, ko fita kasashen waje Dan duba lafiyarsu, su tsaya su ingata asibitotin Gwamnati, ta hanyar dasu kansu asibitotin zasuna basu Kekkyawar kulawa,
Ya zama asibitin da Sarki zaije.
To shi fadawan sarki zasuje.
Kana asibitin da shugaban kasa zaije ya zama shine na talakawa, ta hakane zai sa shugabanni su san halin da asibitocinsu suke ciki, da inƙancin likitocin da kayan aikin.
Haka zai sa a kula da in ƙancin asibitocin.
Domin duk wani asibitin gwamnati matukar akwai ingantattun Doctor’s da kayan aiki da watar tsabtacewa.
Toh dai-dai yake da duk wani asibitin kudi, hakanne kuma zaisa asibitotin kudin su dakushe, su durkushe.
saboda yawnacinsu bawai anginasu Dan taimakon al’umma bane, anginasu ne kawai saboda neman kudi irin na yaki haram yaki halal, tayanda talaka bazai tab’a amfana dasu ba sai dai su cika aljihunsu.”
Da sauri Jannart ta juyo ta kalleshi.
Ido cikin ido sukayi da juna,
Bakinshi ya taɓe tare da yimata wani irin munafukin harara, hakane yasa tayi saurin yin ƙasa da kanta
Kai ta jinjina, cike kuma da gamsuwa da kalaman nasa tace.

“Tabbas maganarka tatafi Kan hanya mai kyau, sai-dai kuma amma baka ganin yin hakan zai dakushe mutane da dama, musamman ga masu privet hospital kamar yanda ka fad’a!!!.”

Kansa ya d’an girgiza, sannan kuma akaro na farko da tun zamansa awajen ya dago kansa da nufin ya kalleta da kyau dan tambayar da tayi masa.
Saidai ko secan daya bai dauka yana kallontan ba yakau da kansa gefe.

In don’t care manner yace.

“Hakan ba wata matsala bace ai, Domin bani da yakinin cewa yin hakan zai tauye musu hakkinsu”.
Da sauri ta kuma cewa.
“Toh kuma kake bada shawara a rushe asibitocin?”.
Wani irin kallo ya ɗan watsa mata.
Sabida ta mishi tambayar cikin gajin haƙuri irin nasu na ƴan jaridu.
Dan bata tsaya taji ya dasa Ayaba.
Koda yake haka suke.
Yan jaridun suna jin daɗin jefowa mutun tambaya kamar sauƙawar aradu ko kuma titsiye.

Cikin tsare fuska yace. “Dama meyake sawa su bude nasu asibitotin?”.
Ya mata tayarma tare da tsareta da ido.
Yar-yar haka taji tsikar jikinta na tashi.
Haka yasa da sauri ta kauda kanta gefe.
Shi kuwa kai ya jin jina tare da cewa.
“Baki sani bako?
To bari in gaya miki...”
Ya kare mgnar yana mata hararan ƙasan ido kana yaci gaba da cewa.
“Dama rashin samun isasshen abunda zasu rufawa kawunansu asirine, saboda sometimes acikin asibitotin Gwamnatin, gwamnati bata biyansu al'bashi akan kari, baya ga haka kuma bata basu isassun al'bashin da zasu dauki nauyin iyalansu sabida gwamnatin tayiwa malaman jinya dana makarantu riƙon sakainar kashi Alhamdulillah gwarama wannan gwamnati da muke ciki.
Duk da haka ana buƙatar ƙari.
Domin duk lokacin da Gwamnati ta fara biyansu isassun al'bashi, To ba wani abu da zaisa suje su bude privet Hospital toh ko sunje sun buɗewama wa zai je musu in dai asibitocin gwamnatin nada inkanci , Domin ak’asarnan ba yawan asibiti muke da bukata ba, ingancinsu kawai shine abun buk’atar mu, tayanda talaka da maikudi da fulanin daji zasu samu gamsashshiyar kulawa, batare da nuna wani banbanci ba!!!.”

Ajiyar zuciya Jannart ta sauk’e, kana kuma cikin yanayin nutsuwa tace.

“Mungode sosai Dr. inafatan kuma Gwamnati zataji shawarar daka bada kuma tayi aiki dashi, yanzu kuma zamu shiga babi na biyu. wanda ya shafi b’angaren kasuwanci kafin mu dawo nan a likitance.

Yah Salam shine abinda ya faɗa a ransa.
Sabida ya lura yau bakinshi sai yayi tsami sabida magantuwa da wannan fitinenneyar yarinyar take sashi.
Kamar a tsakiyar kanshi yaji ta kuma cillo mushi tambaya.
“Shin Dakta wacce irin shawara zaka bayar, agame da yanda sha’anin saye da sayarwa ya zama acikin k’asarnan, misali ta yanda ayanzu kayan abinci yayi tsada sosai, akullum wasu daga cikin yan kasuwa k’ara farashin kayansu suke, rayuwa tayiwa talaka tsada, manyan y’an kasuwa da kamfanoni sun had’e kai da baki waje daya, Koda yaushe farashin kaya hauhawa yake, tayaya ne za’a samawa al’umma sauk’i, musamman manoma, wanda sune ma suke noma abincin amma kuma Idan ya shigo kasuwa sai yazo yafi karfinsu, shin wacce shawara zaka iya bawa manoma?.”

Numfashi ya dan fesar ta bakinsa, saboda yanda yaji labbansa sun soma gajiya da yawan motsasu da yake.

Hakanne kuma yasa batare daya dago ya kalli ko cameran ba, saidai atausashe yace.

“Shawarar da zan iya bawa Manoma itace, duk wani manomi Idan har ya noma abunda zaici, To kada yayi gangancin saidawa, har sai ya tabbatar daya ware ishashshen abincin da zai isheshi, har na tsawon wata shekarar da zai sake noma wani abincin, kafun nan sai yazo ya saida wanda zai sayar, saboda gudun kada ayi gaban mai haƙar rijiya. kai ka noma ka gama shan wahala, sannan kuma ka tattara ka sai dashi lokacin da yake araha, bayan y’an wasu watanni sai yayi tsada, ga kuma wanda kake dashi ya riga ya k’are ga damuna ta sako sama ruwa ƙasa ruwa, fita nemowar ma wata rana sai ya gagara, kaga kenan nakan daka saida shi zaka sake zuwa ka saya, akan farashi mai masifar tsada, kenan Kai Manomi kaine ka wahala a banza.
Sannan kuma ya kamata manyan kamfanoni su dinga tausayawa talakawa, su daina yi musu irin wannan hawan k’awaran, zuwa su sai abincin manoma tun yana gona basu shigo dashi gari ba su kuma manoma ku farga da wannan sagegeduwar da akeyi muku.
Sannan kuma su manoman kansu, su daina sayarwa masu manyan kamfanoni abincinsu tun yana gona, saboda wasu tun abunda suka noma yana yabanya suke saida shi, atunaninsu ko da ace abun da suka noma din baiyi kyau ba ko sanadin fari ko tsuntsaye ko kwari ko tsutsa, su dai sun samu kudi, da yawan mutane basu san al'barkar dake cikin kayan gonansu ba, saboda haka yana da kyau, ka dinga girbe abunka kana gyarawa da kanka, ka kididdige abinda ka samu ka ware na buƙatunka kafun ka mik’ashi ga wasu, sannan kuma duk wani manomi yayi kokarin saida abincin daya noma, akan farashi mai kyau, saboda ko yaya guminsa ya keci.
Domin shi kadai yasan wahalar daya sha wajen noma ta, sannan yanzu Idan akayi dubi, gaba daya manoma da talakawa su suke shan wahala, musamman Idan aka shiga cikin damuna, haka komin ruwa da iska zasu tsaya neman abunda zasu rufawa kansu asiri suyi noma dan ciyar da al'umma duk kudinka fa, in manomi baiyi noma koda kuɗin ka bazaka samu abincin ba, shin zakaci kuɗin naka ne!!!?. Sannan ku kuma y’an kasuwa da kamfanoni masu karawa kayan abincinsu kudi, ba komai kuke ciba face *RIBA* haramtacciya, wanda kuma kowa yasan hakan ba abubane mai kyau bane, ga wanda suke sayan abinci su b’oye sai yayi tsada su fito dashi, suma duk Allah naganinku, kuma Allah da kansa baya tausayawa wanda baya tausayin na kasa dashi.”

Kai gaba daya mutanen dake boye abayan cameras din suka jinjina, hatta MD da kansa shima ya samu cikakkiyar gamsuwa da bayanan da suka fito daga bakin Dr. Rayyern din.

Ba kuma a iya cikin tv station din ba, har acikin gaba daya k’asar tamu, mutane da yawa dake Kallon Live Program din sun samu cikakkiyar gamsuwa, Yayinda kalaman Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya ratsa zuk’atansu, ciki kuwa harda mafiya yawan manoma da suke kallon shirin, sabida Tashar Arewa 24 TV tayi zarran birni da ƙaune suna kallonta maza da mata manya da yara.

Adai-dai lokacin kuma Abba Kabir zaune yake agaban tv yana Kallon shirin, shi kansa ya gamsu da kalaman Dr. Rayyern din, saidai kuma sosai zuciyarsa ta cika da tsananin mamakin, ganin da wanda Jannart din ke hira yau.

Acan babban falon gidansu Jannart din kuwa, Alhaji Idi Sale Dakata, Dr. Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa ne, zaune sun zubawa babban TV plasma din dake cikin falon idanu.

Wanda kuma yanzun akayi musu kira na musamman, akan su kunna tashar Arewa24 Dan Ganin hirar da akeyi da Dr.Rayyern din.
Hakance kuma ta kasan a wurare da dama yadda wasu ke kiran wasu manyan ƙasar suna shaida musu su kunna tv tashar Arewa 24 TV suga program ɗin da akeyi da Dr Rayyern Mai-nasara.

Jin abubuwan da Rayyern din ya fad’ane kuma, yasa Alhaji Abdu Tababa yin k’wafa, kana cikin takaici yace.

“Amma dai wannan yaron anyi d’an iska, mai tsaurin ido, kujifa abunda yake fad’a, wai gwamnati ta rushe asibotin kudi ta inganta nata, Lallai yaron nan bashi da tsoro.”

“To shi nashi asibitin na uban meyene, shegen yaro mai jajayen kunnuwa.”

Cewar Dr. Lukman da yakejin kansa kamar ya kurma ihu yayi fiffige yaje ya shaƙo wannan yaron.

Yayinda Alhaji Idi Sale Dakata kuwa ya rumste idanunsa, saboda shi ayanzu ko son Ganin yaron bayayi, hasalima gaba daya tunaninsa ya tafi ne akan yanda zai ga bayan Rayyern din, saboda al'ƙawari ne da yayiwa kansa cewar saiya b’atar da yaron daga Doron k’asa.

Acan cikin tashar ta Arewa24 kuwa, Jannart ce ta sake gyara zamanta, batare kuma da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On TUBALI
avatar
khadija-dauda

7 months ago

Reply

Pls inason littafin tubali

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to khadija-dauda

ki karanta anan

avatar
fatima-muhammad-8-7

4 months ago

Reply

Pls ina Sauran chapters din tubali naga wanna chapter 30 ya tsaya kuma bai kai kar she ba

Please Login or Register in order to submit comment